100% found this document useful (1 vote)
368 views602 pages

Gudun Kaddara 2

Uploaded by

hauwam070
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as DOC, PDF, TXT or read online on Scribd
100% found this document useful (1 vote)
368 views602 pages

Gudun Kaddara 2

Uploaded by

hauwam070
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as DOC, PDF, TXT or read online on Scribd
You are on page 1/ 602

An dauko wannan littafi daga shafin https://novels.com.ng ku ziyarci shafin na https://novels.com.

ng
domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don
masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin
littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap
da wannan nambar +2348062902098

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi
kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku
littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da
PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku

This hausa novel was uploaded and downloaded from https://novels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel


Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book
summary,commentary and others via this number +2348062902098 its free we do not charge for our
services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person
that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels
through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and
download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those
with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC

those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 05

_______________________________

*_Shin kin isa mace?,don magana akeyi ta ISASSUN MATA_*

*_SUTURA ABAR TUNQAHO_*

*_Ado da kwalliya shine cikar 'YA MACE_*


_Magana akeyi ta_

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*

_GIDAN QAWA ADO NA KECE RAINI_

*_INA AL'UMMAR KADUNA ABUJA SULEJA DAMA NIGER......HAR MA FADIN NIJERIA GABA DAYA_*

*_KIN SHIRYA FITA KUNYA?_*

*_MAZA HANZARTA KI LALUBI KALOLIN SUTURAR DA TA DACE DAKE,KAYAN ADO MASU_*

*KYAU*

*QUALITY DA DAUKAN HANKALI*

*LACES NE,SHADDA CE,ATAMFOFI NA 'YAN QWALISA*

*GA KUMA DESIGNERS TAKALMA DA JAKANKUNA NA ALFARMA DA FITA KUNYA*

*_ZAKU IYA SAMUN MAMALLAKIYAR KAMFANIN KAI TSAYE TA WANNAN NUMBER WAYAR_*

08135142610
*INSTAGRAM* UMMU_MAHNOOR_LUXURIES

*FACEBOOK* MUSA GARBA SHIFA

*_Ga wadanda ke cikin garin abuja kuma zasu sameta kai tsaye a_*

*_system property Nefelix estate,near amasco,galadimawa roundabout_*

*_KARKI BARI A BAKI LABARI,KARKI KUSKURA KI ZAMA 'YAR KALLO_*

*TASTED AND TRUSTED*👌👌👌

__________________________________

".............ya fada soyayya?,yana nufin kenan aure yake da buqatar yi?,bama fadawa soyayyar
ba,wadda ya fada soyayyar da ita, yarinyar dake da gatan da ya kerewa nasa,suke da dukiya da tarin
gatan da ya yiwa hankali nisan tazara,kai koda ma ace ya kammala karatunsa ya kama aiki ina yaga kudin
auren hamdiyya abdu me kano?,ko yana da kudin aurenta dinmma sakayyar da zai yiwa bibi da
mohmoud dake tsaye a kansa ba dare ba rana?,ya tattara 'yan kudinsa yayi aure ba tare da sun mori
komai daga gareshi na wahalar da suka sha dashi ba?. Kansa ya girgiza yana bawa kansa amsa da
A'AH,ya zama dole ya sake nisanta kansa da zuciyarsa daga soyayyar hamdiyya,hatta da mohmoud sai
yanzun yaga an fara tada zancan aurenshi,idan bai manta ba wancan satin yaga ya fara shigo da akwati
guda uku bibi na mata wajen ajiya,ta yaya shi da yaie sanya ran zai zamesu musu sanyin idaniya ya buge
da wannan zancan?. Dama bai bari ko kadan zancan hamdiyya ya fasu cikin gidansu ba saboda gudun
tashin hankalin bibi da kullum tsaronta akansu ne,sai kawai ya yanke shawarar fara janye jiki daga gareta
da kuma dukkan al'amuranta.

Hakan bai haifar da komai ba saima sake dagula al'amarin da yayi,ta zube dukkan wautar dan
fari da shagwabarta,kwatsam sai kawai gashi ta dauko mahaifinta tun daga Nigeria yayo tattaki ya
iskeshi har cikin makaranta wai yazo sasantashi da hamdiyya,tace batasan laifin data yiwa yayanta
hamidou ba yake gudunta. A ranar hankalinsa yayi matuqar tashi,ganin babban mutum me girman
daraja wai yazo gareshi ban haquri?.

Kame kame ya dinga yiwa abban don baisan ma me zaice masa ba. Daga qarshe kawao abban ya
saki murmushi yana dubansu

"Inaga gwara kawai na yanke muku wannan wahalar da kukeyi akan juna,kai yayan hamdiyya,indai ka
aminta kanason hamdiyya ka shaidamin zan baka aurenta,ku sasanta kanku bari na baku waje" abinda
abba ya fada kenan ya fita daga wajen cin abincin daya kama musu table daya.

Kamar zata hadiye zuciyarta haka ama taji sanda taji furucin bakin mahaifinta,tabbas inda ace
ita daya ce a wajen ihu zatayi tayi tsalle tayi shewa,amma.yanzun duk yadda albishiri din yakai ga faranta
mata dole ta kame kanta ta kuma zuba masa idanu tana jiran jin ta bakinsa. Kau dakai tayi sanda yayi
nufin kallonta,a yanzun yana jin bazai iya boye mata komai ba

"Ina tsananin qaunarki hamdiyya bazan iya boye miki ba,amma kuma bani da halin aurenki saboda a
yanxu nidin ba kowa bane,kuma bani da komai ban kuma bawa kowa ajiya ba,idan nace zan aureki
hamdiyya na cutar dake,bani da arziqin riqeki,ki bari kiyi aurenki na gata,ki auri dan gata irinki da zai iya
baki irin rayuwar data dace dake..."

"Ba wanda yayimin cikin maza babu kuma wanda nakeso saikai, hamidou xan aura ba alatun duniya
ba,dukka maganganunka a yanxun ba hujja bane,saidai idan kanaso ka fake ne,ni hamdiyya ban maka
ba" ta fadi tasirin sonsa na yawo cikin idanunta da wani irin kaifi.

Duk da ba'a mode da zaiyi dariya suke ba amma sai daya murmusa,bayajin tana masa rabin son
da Allah ya jarabceshi dashi nata

"Baya ga bibi da 'yan uwana ban taba jin soyayyar wata halitta a zuciyata ba haka....."

"Indai hakane ka sanya a ranka ni hamdiyya matarka ce,ban kuma fi qarfinka ba" ta tari numfashinsa kai
tsaye.
A nan gurin ta lalata masa dukkan wani tunani nasa da zazzafar soyayyarta ta hanyar kalaman
bakinta,suka rabu suna kewar juna ainun saboda a yau din dukka wani qulli ya kwance soyayya kuma
tayi ambaliya ta bayyana kanta.

Wajen tara na dare yana rungume da littafi yanason yayi karatu amma ya kasa saboda
tunaninta,wayar hannu sai me wadata,su dinma ada akwaita cikin gidan,amma yanzun da rayuwar ke
neman fin qarfinsu dole suka sakata a kasuwa suka saida.

Yana kwance daga daki yana jiyo hirar bibi da mohmoud,ya dawo daga aiki futu futu da tarin
gajiya bibi ta zaunar dashi tace sai ya fara cin abinci kafin yayi wanka. A hankali yaji suna sako batun
aurensa da bintou,da yadda za'a yi asiri ya rufu ayi komai a gama,don ma itama bintou din ba yar gidan
wani bace,asalima bafulatanar katsina ce,yanayin aiki ya kawosu nan din,saidai kuma suna da tarin rufin
asiri daidai gwargwadon yadda dan adam zai iya rayuwa cikin walwala. Yadda yaji suna maganar ya sake
sanyayar masa da jiki,sai yaji batun hamdiyya tamkar ya ajeshi a gefe don baiga ta inda zai yiwu ba.

Washegari jinkirin isowarta makaranta kadai akan lokaci ya hautsinashi,ya gaza shiga aji ya zauna
har sai da driver dinta ya ajeta. Ta fito tana masa hararar wasa da fararen idanunta

"Kada kacemin komai,ina shakka akan son da kace kana yimin,tunda har na qara awa daya kusan da rabi
amma ka gaza zuwa ka taho dani har sai da driver ya taho dani" murmushi kawai yayi yana jin sassauci
cikin qirjinsa tunda ta iso lafiya.

A ranar kafin su rabu ta damqa masa waya me kyau a hannunsa

"Mu dinga communicating,dare yanamin tsaho kafin wayewar gari nazo na ganka" amsa din kawai yayi
yana juyata a hannunsa,bayason zaqewa ko zura jiki da yawa,bayason kuma su sake nisa shi da ita abun
yazo baiyiwu ba ya zame musu ciwo shi da ita. Baice bazai karba ba bai kuma ce ya karba din ba,yabar
wayar a hannunsa dai ya kuma shiga gidansu da ita.

Sam ya manta tana jikinsa har suka gama hira da bibi yaci abincinsa,yana shirin shiga daki ya
watsa ruwa kira ya shigo,shi da bibi din duk sukayi sak sai ya ciro wayar yana dubawa. Alarm ne,
kasheshi yayi ya matsa gaba ya ajjiye wayar gaban bibi yau yana yankewa a ransa ya shaidawa bibi
komai,tunda cikin maganganun da sukayi a yau da hamdiyya ta shaida masa abbanta ya bawa aba din
damar fitowa neman aurenta saboda duniya ta shaida shima ya huta da zirya da neman irinta da ake
faman zuwan masa.

Yana fara gayama bibi komai sai ga mohmoud shima ya shigo,duk da lokacin shigowarsa baiyi
ba,hannunsa biyu dauke da.ledoji niqi niqi yana fadin

"Bibi yau nayi babban samu,nace bazan iya jira lokacin tashi yayi ba banzo na shaida miki addu'arki ta
daren jiya ta karbu ba,bibi yau kaji kawai zamuci a gidannan" yanayin da ya gansu ya sassauta
karsashinsa,sai bibi ta nuna masa gefanta

"Zauna nan" ba musu ya aje ledojin ya kuma zauna din,aba kuma ya dora da bayaninsa.

Bai boye musu komai ba,komai ya bayyana musu,falon yayi shuru kowa yana juya abun cikin
ransa. Tsahon wasu mintuna sannan bibi tace

"Kai yanzun kana ganin hamdiyya kininka ce?" Ta jefa masa tambayar kai tsaye wadda ya kasa amsa
mata

"Banason na sake jin wannan zancan,hamdiyya ba tsararka bace,koda ka dage kan zaka aureta ba lallai
ka samu abinda kakeso daga matarka ba,cikin abinda akeson miji yafi matarsa akwai dukiya wadda
kusan ita ke riqe da auren,kai kuma baka da ita,uwa uba ma yanzun haka dan uwanka ake maganar ya
samu ya fara auren,kada na sake jin wannan batun"

"In sha Allah" ya amsa mata cikin matuqar girmamawa,har ransa kuma yakejin ya gamsu da hakan zai
kuma yi qoqarin bi iyakacin qarfinsa.
*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261
*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 06

Shi da hamdiyya dukka sun dauki abun da wasa,bayan ya shaida mata zai haqura din saboda
rashin goyon bayan mahaifiyarsa da bai samu ba,ita dinma zuciyarta tadan tabu,kuka ta amince zata
dafa masa baya akan hakan,amma sai su duka zukatansu suja gaza jurewar. Qarewa suka dinga yi suna
rama shi da ita harda qananun lalure lalure,at last dai abban hamdiyya ya sake shiha maganar,yayi
tattaki da kansa ya iske bibi har gida,ya kuma bata tabbacin amincewarsa shi da hamdiyya din,sannan
kuma ya qara mata da albishir din cewa baya buqatar komai daga hannun hamidou illa sadaki. Abban
hamdiyya ya barsu da tarin kyautatawa da alkhairinsa wanda baya boyuwa daga cikin kyawawan halayen
da yake dasu.
Yabar bibi cikin tarin tunanin yadda wannan al'amarin zaiyiwu,sam ba batun auren hamidou bane
a gabansu,batun auren mohmoud sukeyi,ta yaya za'a dauko mata abinda ba zata iya ba?.

Cikin dare MAHMOUD ya tayar da hamidou dake kukan zuci yana dubansa, murmushi ya saki

"Haba,ba'asan namiji da karaya bafa.....kada ka damu,muddin ina raye kuma hamdiyya kakeso zaka
aureta"

"Ta yaya hamma?,bayan bibi har yanzun bayan wucewar abban hamdiyya batayi na'am ba?"

"Zan dosheta kuma zata fahimta" ya fadi yana duban idanun hamidou cikin bashi tabbaci.

Washegari bayan mohmoud ya gama shirin fita wajen aiki ya zauna da bibi akan maganar,
hamidou yana labe ya kasa zaune ya kasa tsaye yana jiran yaji me bibi ta yanke?. Mohmoud yasha fama
da ita ba kadan ba kafin tayi amanna,tsananin murna ta sanya hamidou fitowa daga inda yake laben ba
tare daya shirya ba. Da kallo galala bibi ta bishi

"Ja'iri dan nema,dama kana a wajen kenan" kunya ta kamashi,ya samu waje ya zauna yana sinne kai.

"In sha Allah bibi na miki alqawarin ba zakuyi nadamar shigowar hamdiyya cikinmu ba,hamdiyya bata da
wani aibu ko makusa ta fannin tarbiyya,ni kaina inda nasan da matsala bibi wallahi bazan saki jiki da
lamarin ba"

"Allah yayi zabin abinda yafi alkhairi"

"Yanzun abinda na yanke hamma ya samamin wani aikin da zan dinga yi,duk sanda bamu da lecture sai
na fito nayi na koma makaranta" kai mohmoud ya girgiza yana murmushi,a duniya bashi da burin da ya
wuce yaga farincikin 'yan uwansa
"Aiba wani lokaci za'a diba ba mallam,zaka tsaya tarin kudin aure kenan?,wannan yammatan yadda kuka
mato akan juna banajin zata iya jiranka" kunya tadan kama hamidou amma kuma yana mamakin yadda
za'a hada komai a qaramin lokaci,duk da abban yace baya buqatar komai daga wajensu face
sadaki,amma ko bazai yadda ya auri hamdiyya baiyi komai cikin hidimar aurenta ba,ko yaya ne zaiyi
daidai iya abinda Allah ya hore masa,a qalla dai da babu gwara ba dadi.

"Zakayi lefe kaman yadda kowanne namiji yakeyi in sha Allah,za kuma ka biya sadaki" abinda mohmoud
ya fada kenan yana miqewa zai wuce wajen aiki.

Tunda yaji mohmoud ya fadi hakan yasan zai matsawa kansa ne,kuma sai yayi dukka abinda ya
fada din,wannan ya sanya a sace shima ya soma 'yan buga bugarsa,abun kamar wani yayewar lullubi sai
yayita samun ayyuka,abun ya dinga bashi mamaki,saidai yayi shuru bai gayawa bibi ko hamma
mohmoud ba,saboda yasan yanzun zai hanashi yace karatu kawai zaiyi,shi dinne zaiyi komai. Cikin wata
guda kacal ya samu 'yan kudadensa a hannu masu dan kauri,yanata mamakin yadda daga fara buga
bugarsa qofofi suka dinga bude masa,aka dinga kiransa ayyuka daban daban da kuma kudi masu gwabi.
Da yake su din damuwar danuwansu shine tasu,akwai asusu da yake yiwa oumar na jarabawar da
zasuyi,wanda ya kallafawa kansa shine zai biya wannan karon hamma mohmoud ya huta shima,asusun
ya bude,ga mamakinsa ya tara kudi ashe ba laifi ba kamar yadda yake tunanin bai wani tara abun arziqi
ba,ya ware kudin jarrabawar oumar y dauki sauran ya hada da kudin hannunsa ya aje yana jiran
dawowar hamma oumar.

A falo suke hira yana cin abinci,a kaikaicw hamidou ke kallon hamma mohmoud din saboda
yadda gaba daya shekarunsa suka ninka akan nasa saboda da wahala da neman na abinci,har ya
kammala mohmoud din ya kalleshi

"Ya kaketa kallo na ne kaman kaga hamdiyya?" Dariya dukka sukayi sai ya soma sude miyar hannunsa
yana cewa

"Ka kwantar da hankalinka,lefenka ya gama haduwa,amma saidai su karba da haquri,akwati biyu ne"
baki hamidou ya bude yana kallonsa,yayi imani ba wani lefe,lefensa ne da ya kusa shekara yana hadawa
zai sadaukar masa,sai ya girgiza kai

"Aah hamma,ni bazan karba lefenka ba saboda na tabbatar shine,ni ina da kudadena da na tara"
"Kajimin yaro,yo kudadenka daka tara ai bance ba za'a karba ba,a ciki za'a fidda sadaki ka samu na
dinkunan biki da dan abinda zaka bawa amarya ko bibi?" Ya fada yana maida dubansa ga bibi wadda ta
kasa magana,wani irin abu me nauyi dake sauka zuciyar uwa akan danta ya tsaya mata iya wuyanta,zata
iya cewa bata taba ganin mutum me tausayi da rahama ba irin mohmoud dinta,wanda ke maida
matsalar wani tasa

"Haka ne,amma mohmoud kaine kafi cancanta da kakai lefen nan,ko ba komai kaine babba" murmushi
yayi kawai yana nade hannun rigarshi

"Karki damu bibi,muddin kina mini addu'a tabbas zan hada wasu a kurkusa in sha Allah" daga bibi har
hamidou ba wanda baiyi qwalla ba

"Yanzu gidan da zaka zauna nake qoqarin sama maka a biya haya kota shekara daya ce" mohmoud ya
sake fada

"Wa?,ni?,ba inda zanje, gidanmu akwai wadatar sassa da babu kowa a ciki,a ciki zata zauna hamma ba
inda zani na barku" hamidou ya fada da sauri.

Abinda suka kai sam hamdiyya ko mahaifanta basu raina ba,hakazalika ita da kanta ta qarfafi ta
zauna dasu bibi din. Sashe daya cikin biyun dake cikin gidan aka bude aka yiwa dan kwaskwarima. Da
yake gini ne dama asalam na masu kudin,rayuwace dai kawai data samesu sai wajen yayi kyau ya kuma
dace da zaman rayuwarsu da tsarin kayan alatun da ake burin zubawa hamdiyya.

Sanda labarin aurensu ya fantsama dukka makaranta sai ta dauki dumi,saboda ba kowa keda
masaniyar soyayyar dake tsakaninsu,don daga hamidou har hamdiyya kamammu ne,sun kame kansu
sosai,basa wani abun da zai nuna ma akwai soyyaya tsakanin. Mazan da hamidou ya kasa suna da tarin
yawa, cikin makaranta cikin nijer dama nigeria,sun kuma cizi yatsa ainun da ganin wanda hamdiyyan ta
zaba ya kuma kasasu.

Biki akayi na hanakali, ba'a barnatar da dukiya ba,saidai duk abinda mohmoud ya tara saboda
nashi auren ya narkar dashi gurin auren qaninsa hamidou,ya sadaukar da komai nasa ga hamidou din,ba
abinda ya ragewa kansa,ya kuma tsaya ya zame masa makwafin uba mahaifi,duk abinda uba zaiyi shi
yayi masa,hasalima shine alwalinsa,shi ya karba masa auren hamdiyya. Anyi biki lafiya an watse lafiya
amarya kuma ta tare a dakinta.

To zamansun zama ne me dadi matuqa,duk yadda bibi da farko ta dinga dari dari da tsoron halin
yaran masu wadata hamdiyya ta goge mata wannan,babu raini ko ganin ta fisu,ta sake sosai tamkar
itama bibi dince mahaifiyarta. Biyayya takewa.bibi kaman yadda takewa hamidou, bashar oumar da auta
dukkansu ta maidasu kaman jininta ne,ta zama dai 'yar gida sosai,ba zaka taba cewa surukar bibi bace.

Karatunta taci gaba dayi hankali kwance,don tare suke fita da hamidou a motarta da tuni ta
mallaka masa ita,saidai yaqi sakin jiki ya karba din,har zuwa sanda ya gama nasa karatun ya zama ita ta
rage amma shike kaita ya kuma koma ya dauko matarsa.

Duk wasu shares da dukiya ta hamdiyya mahaifinta ya tattaro ya damqa amanarwa hamidou
saboda yadda da yayi da tarbiyyarsa. Bai boye komai ba yace ga amana nan. Qememe hamidou yaqi
amsa,yace zaidai aje mata takardu da kayayyakinta. Wannan qin amsar shine karon farko da suka fara
samun sabani shida hamdiyya,ta dinga fushi tana cewa ya qullaci wani abune akwai a ransa game da ita
ko kuma bai aminta da ita da kuma soyyayar da take masa ba dari bisa dari, Sharia har gaban hamma
mohmoud da bibi,suka rasa me zasu yanke saboda su kansu ba zasuso ya cusa kansa cikin dukiyar ta
ba,ko a yanzun jigila da kuma hidima take masa da kudinta da jikinta,itace cefane itace siye siyen kayan
more rayuwa cikin gidan,hakanan komai ta gani ya burgeta saita siya masa. Ba shiri ya dakatar da abun

"Munyi alqawarin zaki aureni ki zauna dani daidai qarfina,bamuyi dake zakina mun hidima ba" nan ma
dai haushi taji,tilas amma ta rage wasu abubuwan saboda cika umarninsa. Wannan dalili ne ya sanyashi
fara neman aiki ka'in da na'in. Allah kuma cikin hikimarsa sai gashi ya jefo masa da aiki da matsakaicin
albashin da yasan zai iya riqeshi da yardar Allah.

Wani lokaci abba ya kawo musu ziyara,ya kuma samu hamidou ya soma aikin nasa. Sam aikin
shi bai masa ba,saboda salary din da suke basun baifi albashin qaramin ma'aikaci a kamfanin hamdiyya
ba. Wannan karon da kansa ya sake neman arziqin hamidou ya dawo aiki kamfanin hamdiyya kaman
hakan zaifi dacewa,ya jima yana juya abin,ya kuma gayawa bibi tace ya nema zabin Allah,sannan uwa
uba mutumin surukin arziqi ne,bai kamaci ace yanata neman alfarma kala kala daga garesu suna
sullubewa ba,wannan shine silar da ya fara jagorantar dukiyar hamdiyya,saidai komai yana yine cikin
takatsantsan da kiyayewa,albashinsa kuma ya yankewa kansa kamar na kowa,daga gefe guda kuma ya
fara saving duk wani halalinsa da yake samu silar aikin da tunanin fara shima gina kansa,saboda
bazaiyiwu ace zai dawwama yana qarqashin dukiyar matarsa ba. Duk da cewa wannan abun ba abinda
ya qara face soyayya me qarfi da qarin girmamawa daga wajen hamdiyyan,iya tarbiyya ta sameta,sam
batasan wulaqanta dan adam ba.

Rayuwa ta fara daidaita gidan marigayi mayak'i silar wanzuwar hamdiyya a cikinsu. Abu daya
ne a yanzun ya fara musu cikas shine rashin samun haihuwa shekara ta biyu da aurensu. Tun bata damu
ba duk da maitar son yara da Allah ya zuba mata,to amma saboda lokacin tana cikin kai kawon
karatunta har hankalinta ya fara dawowa jikinta saboda a sannan karatu ya kammala sai business dinta
da takeson kamawa.

Sannu a hankali ta fara tadawa hamidou hankali,har takai anje an gwadasu,an kuma tabbatar
musu mahaifar hamdiyya ce take da dan rauni. Hankalinta yayi mugun tashi duk da yadda hamidou ya
nuna shi hakan ba matsala bacea wajensa,ya dinga qoqarin kwatanta mata da kwantar mata da hankali
amma ta birkice masa,sun dauki watanni a haka kafin ta dan sanyawa zuciyarta salama,sai kuma zancan
auren mohmoud ya taso Gadan gadan.

Haka kawai shaidan ya sanyata ta dinga jin babu dadi cikin ranta,saita dinga tsarguwa kaman za'a
qaro wata surukuwar ne cikin gidan don itadin bata haihu ba. Wannan dalilin ya sanya har akayi bikin
aka qare aka kawo amaryar hamma mohmoud daya sashen a tsarge take,wannan ya sanya tayi bala'in
kamewa daga shiga shirgin matar hamma mohmoud.

Bintou baiwar Allah,gwanar haquri da kawaici,kyakkyawar bafulatanar katsina,wadda tasha


gwagwarmayar mayar rayuwa da wahalar riqo hannun kishiyar uwar da aka fita aka bar mata. Girmama
hamdiyya takeyi duk da itace matar yaya,amma tana kallon cewa ta rigata shigowa gidan,bata da
hayaniya bata da magana,shuru shuru da ita kullum. Yanayin rayuwar da bibi tasan tayi ya sanyata take
yawan jan bintou jikinta don ta samu ta ware ta kuma dinga jinta mutum kamar kowa. Akwai banbancin
rayuwa sosai tsakaninta da hamdiyya data taso cikin gata da soyayyar dangi gaba daya. Wannan abun sai
ya dinga yiwa hamdiyya ciwo kadan kadan,duk da bata taba nunawa ba amma tana jin babu dadi a
ranta,tanajin kamar Bibi nason wareta ne da nuna mata banbanci don bata haihu ba,wannan yayi mata
tasirin data soma janye jiki daga al'amura da yawa na gidan,ta zama 'yar ba ruwana,dabi'ar
miskilancintanan ya motsa,sai ayi abu cikin gidan ma bata sani ba,inda zakaji motsinta kawai ayi baqi
yara ko ayi baqi da yara a cikinsu yanzunnan zakaga yadda zata sake jiki tayita hidimawa
yaran,musamman idan akwai baby girls a ciki. Tanason 'yar yarinya mace sosai,takancewa hamidou
tafison ta haifi mace akan namiji.
Tun bibi na qoqarin fahimtarta da son fahimtar meye ya sanyata sauyawa ta nuna babu
komai,har bibi ta haqura ta barta da sabon halinta,tundai ba fada takeyi da kowa ba cikin gidan,tana
kuma ci gana da girmama kowa kamar yadda takeyi a baya.

Ba jimawa kwatsam ciki ya bayyana jikin bintou,yadda gidan ya rude da murna kuma kowa
hankalinsa ya koma kan cikin sai ya soki zuciyar hamdiyya sosai(kusan duk macen dake neman haihuwa
bata samu ba tana da shigen wannan ciwon a ranta,ko hirar haihuwa akeyi saita tsargu taga kaman da
ita ake bare ace wance ai ciki ne da ita,ba wanda zai fahimci hakan sai wanda ya taba tsintar kansa a irin
situation din),wannan ya sanya ta sake kame kanta da zama a sassanta ita kadai. Sai taji bata sha'awar
ta rabi kowa ko wani ya rabeta,to Allah baisa cikin yana da dogon zango bama bintou tayi barinsa. Sai
kuma a sannan hamdiyya ta dinga jin ba dadi,ta kuma dinga tausayin bintou, hankalinta kuma yayi
mummunan tashi sanda bintou ta dinga ciwe ciwe, daga bisani gwaji ya bada cikakken bayanin bintou
sicklier ce.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200
_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 07

Ta tsorata ainun hamdiyya a sannan,don mutum uku cikin familyn ummanta da taga yadda
sukaci wuya da ciwon sicklier daga bisani kuma dukkansu suka rasu,wannan yayi sanadiyyar da tayi
matuqar tsanar ciwon sicklier. Hatta da hamidou duk son da take masan sai da sukayi gwaji kafin aure.

Cikin hikima ta ubangiji a sannan din ashe tana maqale da cikin ALIYYU MAINA,wanda kwata
kwata sam ko da alama bata sani ba bare kuma hamidou(aba). Bata tashi sanin da ciki a jikinta ba sai da
yayi watanni hudu ya fara harbawa a mararta,ta tsorata dajin hakan ba shiri suka wuce asibiti. Bibi bata
hanasu ba illa dariya da take musu qasan ranta, tasan yadda sukaje haka zasu dawo da borin kunyarsu.

Ilai kuwa sai gasu din,sun dawo mata shabe shabe da kukan murna da kuma kunya. Fadin yadda
hamdiyya ke lele da qaunar cikin aliyyu ma kai tsaye za'a iya cewa bata baki ne, ba'a taba jarabtarta da
wani abu da takeso sama da cikin ba baya ga mahaifin yaron. Motsi kadan kuma bini bini suna hanyar
asibitin wai check-up a duba lafiyar yaronta,tun bibi na zuba musu idanu har ta gaji da gani ta tsawatar
musu,sai suka koma fakar idanunta suna zuwa,sai kawai ta tarkatasu ta watsar.

Shirin haihuwa sukayi na garari,da ba'a qasar taso haihuwa bama amma ganin yadda bibi da
bintou ke da kwadayin ganin yaron ya sanya ta haqura. Cikin aminci ta haifi aliyyu maina,sambalelen
yaro da ya gaji kyau ta fannin uwa da uba da 'yan uwan uba dinma duka. Tun asali da farinjininsa maina
yazo,uwa naso uba naso qannen uba naso,hamma mohmoud kuwa ba'a ma maganarsa,don yadda
yakejin haidar din har cikin jininsa,yadda yake qaunarsa da qulafucinsa har yaso ma yafi mahaifinsa.
Sannu sannu tun haidar na jaririnsa sai zamansa yaso yafi qarfin hannun hamdiyya,duk da mahaukacin
son da take masa. Yadda sukeson janye haidar din sai yadan fara tabata,ganin kamar ganin yaron yanaso
yafi qarfinta,shayarwa ce kawai ke dawo dashi wajenta.

Cikin ikon Allah watan haidar shida uku kacal Allah ya albarkaci bintou da wani cikin,tayi murna
qwarai ita da hamma mohmoud sosai. Haidar maina nada shekara guda kacal bintou ta sambalo tata
yarinyar da taci sunan NAFESSA.
Da nafessa da haidar kusan duka rainon bintou suka koma,saboda tun haidar nada watanni
hudun yasan idan yana kuka aka ajjiye baby nafessa a gabansa watsal watsal dinta ya dauke masa
hankali ya tsaida kukan da yakeyi. Sanda ya cika shekara ta biyu kuwa yasan ya kama hanya tiryan tiryan
zuwa sassansu nafessa,duk kuwa da dan banzan qyuya da yake da ita. Ya kama sunan hamma mohmoud
da suke kira da pappa da kuma sunan NAFESSA daram a bakinsa fiye da sunan kowa.

Wasa wasa wata irin mahaukaciyar shaquwa ce ta shiga tsakaninsu ta yadda bacci ne kadai ke
rabasu,saidai idan sunyi baccin a dauke nafessa shima a daukeshi a maida sassansu.

Alaqar dake tsakaninsa da nafessa din ta nesanta shi da ama din,tun bai isa yaye ba,tun kuma
bata saba ba har ta saba. Kusan duk yininsa yana wajen bintou ne,idan kima nafessa na sashen bibi
shima yana can acan zasu wuni sur saidai ya leqota. Kishin hakanne ya fara kamata ganin sannu sannu
yana barin sassanta da kuma raguwar shaquwar dake tsakaninsu duk da irin qulafucinta da yakeyi. Gashi
daga itan har bintou daga kan yaran ba wadda ta sake samun wani cikin,gwara bintou dama an
shawarcesu da daukan dogon hutu kafin ta sake samun wani cikin saboda yanayin lalurarta, hakanan ta
sha wuya sosai wajen haihuwar nafessa,nisan kwana kadai ya kawota yau. Duk yadda zata ja maina a jiki
abun ya faskara,ta kuma lura ita bibi hakan yana mata dadi qwarai,tana yawaita fadin Allah ya qara hada
mata kansu shi da nafessa din.

Nafessa na da shekara hudu maina nada shekara biyar alamun ciwukan sicklier suka fara
bayyana a jikinta,yau ciwo gobe lafiya,qwarai bintou taso aje ayi mata gwaji amma tsoron kada ya
tabbata nafessa nada sicklier hamma mohmoud ya qiya,amma dole da gumu tayi gumu ya bari akaje aka
gwadata din. Ta tabbata sicklier dince kuwa, sicklier dinma irin chronic sicklier dinnan,don kuwa kwata
kwata rayuwar nafessa kusan rabinta a ciwo take.

Allah ya mata halitta me sanyi,nafessa din yarinya ce me tsananin sanyin hali,shuru


shuru,matuqar girmama duk wanda ya girme mata,ga tsananin son karatu kamar me?,saidai kuma
karatun nata kusan rabi ne,rabin tana yinsa ne ga gadon asibiti. Duk da ana cewa sickle suna girma
ciwonsu yana qara ja baya,ga nafessa abun ba haka yake ba,tana girma ciwon yana sake nuqurqusarta.
Duk sanda ciwon nafessa ya tashi ba zaka iya banbance waye me ciwon ba tsakanin ita da maina. Ita
kuka maina kuka,idan kaga walwalarsa to nafessa ta samu kanta. Koda bacci yakeyi muddin yaji murya
ko nishin nafessa bacci ya qare masa. Abun ya sake dagawa ama hankali,tana ganin shaquwar kamar ta
wuce hankali. Buqatun nafessa da hidimarta itace gaba data kowa cikin gidan,walwalarta itace tashi.
A haka shekaru suka dinga tafiya,shine komai na nafessa,shine gatan nafessa shine kuma mai
tsaya mata,muddin yana wajen ba wanda ya isa ya tabata. Ya wuceta da aji daya,amma yasa aka
maidashi baya ya koma ajinsu nafessa din,daga boko har islamiyya haka yayi ba tare da ama ta sani ba.
Ranar data samu labari kuwa tashin hankali tayi sosai,har ta dinga ji a ranta anya wannan abun nashi na
lafiya ne?. Tun nafessa nada shekara goma daga mohmoud har bintou raayinsu yazo daya na aurar da ita
da wuri,saboda yanayin lalurarta suna ganin taci gaba da karatu ma kamar sun wahalar da lafiyar gangar
jikinta ne.

FURUCIN da bibi tayi a wani lokaci kusan shi ya sake sanyata tsaiwa da qafafunta akan aliyyun
nata. Ranar suna tasowa daga makaranta,sai ta rigashi tahowa,ashe wani ya biyota ya kuma
tsaidata,maina din ya shigo gida yana cika yana batsewa, bibi tayi dariya tace

"To ko 'yar gida za'a yi?, irin wannan kishi haka maina?" A kunnuwan ama tayi zancan,saidai bata daga
kai ta kallesu ba,saidai maganar ta sauka sosai cikin zuciyar ama din,ta kuma tsaye mata a rai,daga
lokacin ta fara takatsantsan da fara janye maina din daga nafessa dama harkokin gidan gaba
daya,makaranta ta sake samar masa wadda zai zamana sai kusan bayan isha'i zai samu sakewa cikin
gidan. A lokaci shi da nafessa din duka suna ss.2, shekara daya kawai ya rage musu su zana jarrabawar
kammala secondry school.

Rashin ganin maina din kwanakin da suka biyo baya ya sanya nafessa din zuwa har sassan wajen
ama nemansa,abinda ba kasafai ta fiya yinsa ba idan ba mamanta ko bibi ta aiketa ba,duk da cewa ba
wani abu ama ke nuna mata ba,hasalima tana mata komai na kyautatawa kaman kayan qyale qyalen
rayuwa da sauransu saboda ita daya ce mace a gidan,don ko da su oncle bashar da ocle oumar sukayi
aure yara mazan suma matansu dukka suka haifa,sannan ita dinma data sake samun ciki namijin dai ta
sake haufa,duk da addu'ar data dinga yi da kuma qulafucin samu diya mace data dinga yi. Haka kawai dai
ba sakewa tsakaninsu,ita ama zurfin alaqar dake tsakaninsu dinne bataso,da yadda dukka haidar ya
tattare tsakaninsu da kuma bibi,ita din ta zama kamar ta haifa musu shine kawai.

"Yana makaranta" kawai ama tace da ita,sai ta miqe a sanyaye ta fice. A wannan tsakanin hamani ya
dawo gidan sanadiyyar karatu da ya maidoshi nan garin,hamani d'a ne ga qanin mahaifinsu aba,hamani
din kamar cousin yake a wajensu. Yana da matuqar kirki da son jama'a,uwa uba matashine me addini
kamewa da sanin ya kamata.
Cikin lokaci qanqani ya fara sabawa da kowa na gidan,dukka yaran idan sukaji shuru na wasu
awanni basujishi ba sun shiga cigiyarsa ina oncle hamani,harda nafessa kuwa,don kusan shike mata
lesson din da yanzu maina baida cikakken lokacin yi mata shi yadda suka saba a baya.

A lokacin manema suka fara zuwanma nafessa din,duk wanda zayazo gurinta ko yace yana sonta
sai maina ya sani,tare suke shawarar komai.

Kusan a kowacce qasa,kuma kowacce al'umma da yawanmu suna da qyamatar auren masu
lalurar sicklier,to irin wannan qalubalen ne nafessa ta fara fuskanta. Tana da kyau ainun dake jan
hankalin kowanne namiji,tana da nutsuwa da kamun kai dake bawa maza sha'awa,to amma kuma da
zarar sunji irin lalurarta sai ka nema mutum ka rasa. Da yake auren bai kanta da farko bata wani damu ba
har sai da tafiya ta fara nisa ta fahimci qalubalen dake a gabanta,ta kuma ga zallar damuwa tattare da
mommanta. A hankali ta soma fahimtar komai,ya kuma soma damunta,maina dinne dai abokin shawara
da fadawa damuwarta,sai kuma oncle hamani. Duk sanda wani yazo ya tafi da maina take tattauna
damuwarta

"To sai meye?,yayita tafiya,Allah zai kawo miki wanda ya fishi" duk sanda ya fadi hakan hankalinta yana
kwanciya sosai.

Ranar da zuciyarta ta karye sosai ranar da wani hafizzou ya shaida mata soyayyarsu ba zata iya ci
gaba ba. Shigowar maina gidan kenan daga makarantar manya ta dare,yaga fitar hafizzou ya kuma ga
shigewar nafessa ciki da sassarfa sassan bibi,sai kawai ya take mata baya yana addu'ar Allah yasa bame
afkuwa bace ta auku.

Yana shiga ya sameta saman cinyar bibi din tana sharba kuka. Aba na falon haka haka ama,suna
list na abubuwan da bibin keso ama zata taho mata dasu daga Nigeria,don saura kwana uku ta wuce can
din,kasancewar bata rabo da zuwa don suna da tamfatsetsen gida a can da idan sunso suna iya share
wata uku ciki kafin su dawo niger,ita da aba ko ita daya dinma.

"To sai meye?,a kansu kike zubda hawayenki nafessa?,suyita tafiya din,ni zan aureki,na yarda ni aliyyu
zan aureki" ya fada cikin tsanani fushi da zafin zuciya. Ba ama kadai maganar ta yiwa luguden duka
ba,har bibi da ita kanta nafessa din. Dif falon yayi abinda maina bai tsaya wani la'akari dashi ba yaci gaba
da zazzaga masifa.
Sakale ama kawai tayi tana kallon ikon Allah kuma zatonta yana sake qarfafa lallai aliyyun wasu
ta haifawa. Zuciyarta ta gaza daurewa ta daka masa tsawa me qarfi

"Yima mutane shuru dalla,shashasha!,fita ka bawa mutane guri" ta fadi a harzuqe. Har ya fitan suka
gama abinda sukeyi ta fice itama babu wanda yace komai akan maganar.

Cikin kwanakin ukun tanata shirin tafiya Nigeria amma ranta a matse yake,gaba daya ta rasa
walwalarta,hatta aba da maina sunga canzawarta,tanata juya furucin maina a ranta,tana kuma hankalce
da yadda suketa dan shige da fice a sassan bibin lokaci zuwa lokaci. Bataji koda d'ar ba,saboda ta riga ta
sama ranta ko sama da qasa zasu hade ba zata yarda maina ya auri nafessa ba,abumma sam bai kama
hankali ba,ko ita da mahaifinsa da sukayi aure duniya nada ragowar kwanciya ai dukkansu sai da suka
mallaki hankalin kansu sannan sukayi,uwa uba ma kuma bataga dalilin da zai sanya ta bari maina din
data dora buri a kansa ya auri sicklier ba,duk da nafessa bata da matsala ko makusa tako ta ina,amma
abun ita sam bai kama zuciyarta bama bare hankalinta.

Haka ta tattara harda maina din suka wuce Nigeria,abinda yasa ta gane da wani abun a qasa,tun
sanda zasu taho basuyi sallama da aba ba yadda suka saba,sannan a qa'ida tare suka tsara zasu tafin
amma shi ya janye tashi tafiyar,bataji dadi ba amma ko a jikinta suka wuce din.

Sanda ta kammala kwanakin data diba zatayin sai taji kwata kwata bata sha'awar komawa
nijer,tayi zamanta a nan din duk da lura da tayi maina ya takura su koma din. Suna hutu ne a
sannan,kuma hutunsu yakan dauki dogon zango wani lokaci wata uku har hudu ma,ba guntun hutu irin
namu ba,wannan ya sanya ta sake miqe qafa,tayi biris kamar bata karanci damuwarsa ba.

Sati guda ta qara akan ainihin kwanakinta aba yayi mata dirar mikiya. Hakanan kadaran
kadaham babu wannan karsashin kamar yadda suka saba. Kwana daya kwana biyu shuru,a kwana na
ukun suna breakfast da safe ya dubeta yana gaya mata labarin da ta jishi kamar saukar aradu

"Mun yanke shawarar daura auren maina da nafessa" a wani hargitse ta dago tana dubansa
"Wanne maina din?,kana nufin aliyyu haidar?,wanda ko qaramar secondry bai gama ba?dududu
shekarar haidar din nawa?,,baya ga haka ka manta nafessa sa'arsa ce?,watanni sha biyu kacal ya
bata?,ka manta matakin lafiyarta?"

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 08

"Dukka wadannan lissafinki ne,ba ruwana dasu" ya furta cikin halin ko in kula.

Wannan magana ita tayi silar kawo rikicewar familyn MAYAK'I a karon farko,ta nesanta zazzafar
soyayyar dake tsakanin aba da ama me matuqar danqo,soyayyar da bibi bata taba sasanci ba a
tsakaninsu,saboda ba qarya hamdiyya ta iya riqon miji qwarai da gaske.

Batayi qasa a gwiwa ba ta yanki tikitin komawa nijer saboda ta tabbatar ba shi daya yayi wannan
shawarar ba. Ta dire gaban bibi takuma lissafa mata dukka hujjojinta na rashin amincewa da batun
auren maina da nafessa. Bibi din jinjina kai kawai tayi, bata fidda matsayarta ba,don a duniya ba wanda
zai kaita son ganin maina da nafessa qarqashin inuwa guda.

Ganin yadda abubuwa keta rikicewa cikin gidan ya sanya oncle mohmoud wanda tunda aka fara
lamarin har sanda su bibi suka yanke hada auren bai taba magana ba sai yanzu ya gurfana gaban bibi
yace yana roqon alfarmar abar wannan batun,ko don hamidou ya samu zaman lafiya da iyalansa,maina
kuma ya samu albarkar mahaifiyarsa. Kai da fata aba yace shifa baisan zance ba,ya riga ya bawa maina
nafessa,babu kuma fashi, saidai hamdiyya tabar aurensa.

Sosai maganar ta taba bibi,salin alin ta kwabeshi itama,tace kuma an janye maganar. Kamar jira
hamani yakeyi yace shi zaya auri nafessa. Ba wanda ya qyamaci abun a cikinsu,saboda hamani din
managarcin mutum ne,kuma dama can shi bame kule kule bane,hasalima babu wata yarinya da yake
nema. Dai dai sanda ya kammala Phd dinsa daidai sanda nafessa ta kammala secondry school,babu
jinkiri aka gabatar da komai,aba ya daure qarqashi akayi gagarumin biki, Wanda kamar ama tasan za'a yi
hakan ta saka maina a gaba suka wuce Nigeria.

Tunda suka tafi din bai dawo nijer ba,hasalima sai ya fara neman gurbin karatu a can,don baijin
zai dawo nijer kuma rayuwa taci gaba da gudanar masa kamar yadda yakeso. duk da yayi murna qwarai
da nafessa ta samu mutum kamar hamani,yayi imani ba ita babu kuka saboda nagarta da kyan zuciyarsa.

Duka duka auren nafessa watanni shida,tana da ciki wata hudu bintou mahaifiyarta ta rasu.
Mutuwar ta girgiza ta ta kuma jijjiga mohmoud,saboda shi kadai yasan irin macen da Allah ya bashi.
Albarkacin samun nagartaccen miji dukan mutuwar yazo mata da sassauci,ya tsaya kai da fata ganin
matarsa bata fuskanci raurawa ba.

Watanni uku da kwana goma nafessa ta haifi SULTANA, yarinyar da ta samu soyayyar da har ta
dara wadda mahaifinta da kuma maina din ya samu,yarinyar data debo kamannin NADEEYA abinda ya
qara adadin soyayyarta a zuciyar kowa da kowa. A sannan tuni dukiya ta fara yiwa aba ambaliya,ya fara
shiga jerin sahun attajiran 'yan kasuwa masu cin gashin kansu,don bai jima da dukiyar ama a hannunsa
ba ya damqa mata komai ya dorata akan turba ya kuma bata cikakken damar kula da dukiyarta kamar
yadda kowanne namiji zaiyi shi kuma ya waiwayi tasa.

Iya bikin suna kawai kudade aba ya zuba masu ciwo yace ayi,duk da hamanin ma ba baya bane
gurin samu,don tun yana lavel one a jami'a ya fara kasuwanci,kawo yanzu kuwa shima ya zama babban
qwaro. Gata iya gata ta kowanne fanni. Ga hamma MAHMOUD jin sultana yake kamar wani yanki na
jikinsa, soyayyarta bata taba boyuwa muddin zaka zauna dashi koda na minti talatinne. Ya zubawa
sultana so wani irin so me tsayawa a zuciya tun tana zanin goyonta. A haka aka fara rainonta kafin me
afkuwa ta afku,mutuwa ta rabata da mahaifiyarta nafessa.

Mutuwar ta daki maina matuqa ta kuma galabaitar dashi,sai kuma a lokacin mutuwar ne ya
fara dora idanunsa akan sultana da a sannan take koyon zama watanni uku da kwanaki a duniya.

Wani irin masifaffen so ya azawa sultana,bama shi kadai ba kusan kowa na cikin gidan,yana ji a
ransa kamar yanzun sultana responsibility nasa ce,kamar shike da alhakin komai nata. Rasuwar nafessa
da samuwar sultana ya sanyashi ajjiye karatunsa ya dawo gida nijer. A hannunsa sultana ta taso,ya zama
shine uwa kuma shine uba a gareta,tsarkin kashi wanka raino rashin lafiyarta dama walwalarta dukka na
hannun maina. Maina ta budi idanu ta gani a matsayin uwarta kuma ubanta tun gabanin ma hamani da
hamma mohmoud din suma subi bayan nafessa sanadiyyar hatsarin motar da suka samu shi da shi a
hanyarsu ta dawowa daga ziyarar kabarin nafessa din. Wannan maraicin da sultana ta sake tsunduma ya
sake ninka soyayyarta,ya kuma sanyashi sake ninka kulawarsa ninkim baninkin a kan sultana,ya ajjiye
karatunsa gaba daya saboda ita,wasu abubuwan tun bai iya ba har ya qware sosai,hatta jakar goyon
sultana yana da ita,yadda yarinyar ta taso tana qulafucinsa sai ya masa kamanceceniya da mahaifiyarta.
Ta dabance sultana cikin gidan kamar yadda komai nata ya zama na daban,tana da farinjinin da kowa ya
shigo sai ya dauketa ko ya tankata,tana da yawan surutu tun shekarunta suna qananu ainun,tana da
kazar kazar irin ta masu cikakken lafiya.

Halasci da sadaukarwar mohmoud ba abune qanqani ba da zaiyi saurin bacewa zukatansu ba,ba
qaramin abu bane da zaiyi saurin shafewa a rayuwarsu ba,a wajen aba hamma mohmoud din uba ne
wanda yayi masa komai a rayuwa,bashi da abinda zai saka masa dashi face ya bawa jininsa qwaya daya
tal da ya bari a duniya dukkan soyayya qauna da kulawa,wannan ta sanya ya fifita sultana akan kowa
cikin gidan,buqatarta ta zama gaba akan buqatar kowa.

Ya koma makaranta a nan maradi amma saboda hankalinsa nakan rainon sultana sai karatun
nasa ya zamana asha ruwan tsuntsaye ne,yaqi ya maida hankalinsa duk da karatunsa karatu ne me tsada
da wahalar samu,yake kuma da buqatar maida hankali akai. Aba da kansa da ya fahimci muddin yana
tare dasu ba karatun zaiyi ba,sai ya maidashi niamy,ya tafi kuma da sharadin sai yayi shekara cur aba
yaga kamun ludayin karatunsa sannan zai barshi ya fara zuwa gida weekend. Itadai ama bata tanka
ba,don zuwa sannan ta zama 'yar don't care game da komai na cikin gidan,ba komai take sanya baki ba
duk da dama ba halinta bane shishshigi,sa'annan har kawo yau aba zafinta yakeji akan hana auren maina
da nafessa. Dukka tulin soyayya da suke nunawa sultana bataga aibu ba,don sultana din jinin mohmoud
ce, MAHMOUD kuma abun asoshi ne,ko ita yana daya daga cikin mutane masu muhimmanci cikin
rayuwarta,abu daya ne ta dinga jiye musu wanda a yanzun ya riskesu,sangarcewa da lalacewar tarbiyyar
da maina keta fadi tashin ganin tafi kowanne yaro cikin gidan,abinda ta dinga gane musu kenan,amma
taja bakinta tayi shuru don tasan ba muhallin da zatayi magana bane,don ba lallai su fahimceta ba. Kaf
yaran gidan ita kanta sultana din tafi shiga ranta,tana tausayinta saboda maraicin da take ciki ta kowacce
fuska,amma hakanan ta barma ranta hakan saboda a qalla dai a samu wanda koda da kallo zaya nuna
mata kuskure idan ta aiwatar cikin gidan,sannan ba lallai su gamsu da ita ba wai don ta nuna tana
qaunarta,duk da cewa tasan kusan komai ya riga ya wuce,family ne da basa da riqo sam sam sam,daya
daga cikin halayensu dake burgeta.

Sanda ya cika shekara ya fara zuwa gidan bai fahimta wani sauyi sosai daga gareta ba. Saidai
bahaushe yace sannu sannu hata hana zuwa saidai a dade ba'a je ba, shekara guda da fara zuwan nasa
ya karanci komai,hankalinsa ya dagu sosai,yayi iya bakin dukka qoqarinsa wajen saita komai amma
inaaaa......wannan shine ya zama SILA kuma SANADIN KADDARAR data samesu a yanzu.........KADDARAR
da zata budewa SULTANA da MAINA qofofi masu tarin yawa.....

_Barkanmu da sauka😄,muje zuwa guwa ga tsakiyar labarin_🤩

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank
_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 09

Numfashi me nauyi ama ta aje tana sake murza tafin hannun sulatana dake tsakiyar hannunta
wanda ya sake yayi laushi sosai
"Ya hayyu ya qayyumu birahmtika astageesu" ta furta qasa qasa tana lumshe idanuwanta. Batasan me
qaddara ta tanadarwa gobensu ba gaba daya,saidai ko meye tana fatan yazo ya wuce sa gaggawa,ko
meye kuma tana fatan yazo ya wuce musu cikin sauqi.

Hannunta ta saje miqawa ta jawo wayarta tana sake lalubar number wayar maina,har yanzu
akwai dacinsa da ciwonsa qasan zuciyarta,tana sake jaddadawa kanta da gayawa kanta ba zata masa ta
sauqi ba,ba zata kuma sassauta masa ba dole tayi masa mafi munin hukunci,saboda ba haka takeso ya
rayu da nashi iyalin ba,ba haka takeso ya soma gina rayuwarsa data zuri'arsa ba,tana da buqatar tsatso
me kyau wankakke daga wajensa tamkar yadda ahali da salsalar mahaifinsa suka kasance.

Babu wani abu da ya canza,har yanzu dai gaya mata akeyi wayar na a kashe ne. Furzar da iska
tayi daga bakinta tana sake gayawa kanta duk nisan kiwon da yayi zaije ya dawo ya sameta.

Sai data duba lokaci taga yadda dare yaketa sake nisa sannan ta fidda hannunta daga na
sultana,ta miqe ta zare yalwataccen mayafinta da kowanne motsi yake fidda qasaitaccen qamshi. Toilet
ta shiga ta dauro alwala don batajin zata iya samun bacci,ta shimfida darduma ta tada salla.

Raka'a shida tayi ta sallame,ta bude ipad dinta tana buda app na qur'ani cikin nutsuwa ta soma
karantawa ko zuciyarta zatayi sanyi daga abinda takeji.

Duk bayan kowannw minti sai ta aza idanunta akan sultana da har yanzu jiya iyau. Tayi nisa
takai gwargwadon izifi biyu ta sake dora idanunta akan sultana,sai taga hannunta da qafafunta suna
wani irin motsi kamar ana jijjigasu.

Da hanzari ta aje qur'anin ta kuma miqe tana nufarta da sassarfa,dab da zata isa inda take
sultana din ta soma fusge fusge kamar wadda aljanu suka yiwa mummunan kamu,kafin daga bisani ihu
ya biyo baya da dakusashiyar muryarta data fara budewa. Gaba daya gigicewa ama tayi da irin abinda
taga sultana din tanayi,sosai take jijjiga tana kuma ihu tare da kiran sunan maina kaika dauka wasu
gaggan mayu ne suka kamata. Rungumeta tayi sosai a jikinta gudun kada ta farke dinkin jikinta ko ta jiwa
kanta rauni,tana rungume da ita din tana kiran sunanta,saidai bisa dukkan alamu bata fahimtar ma
abinda takeyi bare wanda ke kusa da ita,abinda ya sanya hawayen tsananin tausayinta ya sauka a idanun
ama. Tanason ta matsa gaban abun kira ta kirayi nurses amma tana tsoron sakin sultana din,cikin
taimakon Allah kamar Dr chafa'atou tasan halin da ake ciki sai gata ta turo qofar dakin ita da Dr
cha'aibou.
Hannuwanta dake cikin aljihun labcoat dinta ta zare tana nufosu da gaggawa

"Ta farka ne?" Ta tambayi ama tana tayata riqe sultana

"Ta farka Dr amma a mafi munin yanayi" ta bata amsa tana qoqarin dauke qwallar data sauka saman
idanunta. Dr cha'aibou ta yiwa magana ya qaraso ta sanyashi ya duba allura cikin drawer din da suka
ajjiye dukka tarkacen allura ruwa da magungunan da sukasan ciwonta yana da buqata.

Shi ya hada allurar ya kuma yi mata. A hankali sai yanayinta ya fara daidaita,saidai kuma dukka
jikinta ya fara sakewa,kafin daga bisani ta sake komawa wani baccin.

Shuru dakin ya dauka idanunsu dukka a kanta,kafin daga bisani Dr chafa'atou ta furzar da iska
tana maida dubanta ga ama

"Dole zata hadu da attack dama irin wanda aka yiwa rape suke haduwa dashi,saboda wannan abun da
akayi matan kusan daidai yake da rape a tunani da kuma qwaqwalwarta,tunda anyi shine bisa qarfi da
tilastawa,kwanyarta sam batasan meye sahihin ma'anar aure ba bare ta banbance,amma in sha Allah ina
saka ran idan ta sake farkawa zata farka babu dukka wadannan abubuwan,ki kula da kyau don ba dogon
bacci zatayi kamar irin wannan data fark daga shi ba,ko na turo miki nurse hajja ta tayaki zama?" Kai
ama ta girgiza a sanyaye,bata buqatar kowa ya tayata tunkarar wannan,bata da buqatar wani ya aboceta
cikin wannan lamarin,tanason ta tunkari komai ita daya da zuciya da gangar jiki irin ta UWA.

Tunda Dr chafa'atou ta fadi haka ta tattara ta dawo gaban gadon ta tare,qarfe biyu qarfe uku
qarfe hudu dukka saman idanunta suka wuce,bacci ko gezau baibi ta kusa da ita ba bare ya gwada
daukarta,har zuwa sanda sanyin dake bayyana gabatowar asuba ya soma busawa,a sannan sultana din
ta fara bude idanunta a karo na biyu,wannan lokacin cikin nutsuwa,saidai kuma tana jin dukka jikinta
wani iri babu dadi,sannan daya idon nata kuma yaqi bude mata da kyau yadda takeso. Jin hakan ya
sanyata daga hannu da niyyar shafa fuskar taji me ya hanawa idon nata budewa da ganin abu da kyau.
Riqe hannun nata ama tayi da sauri tana fadin
"Bari karki goce qarin ruwan" a nutse ta waiwayo gefanta,idanunta suka sauka kan fuskar ama din,a
hankali kwanyarta ta fara tuna mata abinda ya faru da ita na qarshe. Tunanin da ya sake hargitsata karon
farko cikin hayyacinta,sai wani irin nannauyan kuka me sauti ya kufce mata.

Tana iya tuna sanda maina ya tsiraitata ya yage kowanne tufafi dake jikinta,tana iya tuna sanda
hannuwansa ke kaiwa guraren da ita kanta tana kyautata zaton ma qilan bata taba tabawa ba,tana iya
tuna sanda lokacin da ya sadar da kansa da wajen da ko kallonsa bata yi duk da a jikinta yake......wani
kukan ya sake qwace mata me matuqar sauti fiye dana baya,sai dukka wani qarfin hali da qwarin gwiwar
ama ya kwaranye,ta rungume sultana din sosai a jikinta tana lallashinta.

Sun jima a haka kafin kukan nata ya ragu,sai ta koma sauke ajiyar zuciya kafin ta bude bakinta
cikin hardewar harshe tace

"Ruwa" sakinta ama tayi ta bude carton din ruwan dake aje gefe ta ciro guda daya ta hado da glass cup
din da aka shirya a wata qaramar cabinet a dakin. Ajjiuesu tayi a gefe sannan ta fara qoqarin tadata
zaune don taji dadin shan ruwa. Siririyar qara sultana ta saki tana runtse ido saboda azabar da taji na
ratsata,kowacce gaba ta jikinta ciwo takeyi mata

"Sannu,daure kisha ruwan sai na saka ruwan dumi na gasa miki jikinki ko?" Ama ta fadi a tausashe tana
kallon qwayar idanun sultana cikin matuqar tausayin ta shigo stage din da bai kamata ce ta shigo shi ba.

Tana qananun qwalla tana komai ama ta tada ta,ta zuba mata ruwan ta shanye ta kuma sake
buqatar wani,haka ta dinga zuba mata tana shanyewa har sai da tasha rabin gorar sannan tace ta qoshi.

Da kanta ama ta tara ruwa me dumi qwarai ta dawo cikin dakin

"Muje ki wanke jikinki ko zakiji dadi" a hankali sultana ta kauda kanta gefe kadan tana jin zuciyarta
kamar zata fashe,ganin ama kawai tuna mata yake da maina da abinda ya aikata mata,wai shin ta yaya
zata iya ci gaba da kallon ama?,ta yaya zata iya tubewa ama jikinta tayi mata wanka?. Mutum biyu rak a
rayuwarta suke mata hakan,daga bibi sai tanja,batajin akwai sakewa tsakaninta da ama da har hakan
zata kasance
"Ina bibi ta?" Ta tambaya cikin rauni ba tare data Kali ama ba

"Suna gida,dare yayi yanzunma asuba ce,amma goben nasan da sassafe zaki ganta"

"Zata yimin idan tazo" tace da ama tana jin kamar harshenta take yanka a duk sanda ta buda baki tayi
magana,saboda sam sam a yanzun furta kowacce kalma ta daina bata sha'awa,tafi sha'awar kurumtaka
da bebantaka akan komai,batason jin duk wani sauti ko kuma kalma bare ta tuna mata da ALIYYU
MAINA.

Tsaiwa ama tayi kawai tana nazarinta,har yanzu taqi waiwayowa bare ta dubeta,sai ta taka a
hankali ta isa sashen data maida kanta ta zauna,ta jawo hannunta ta saka cikin nata

"Sultana?" Ta kirata kiran da ya ratsa mata jiki,ta kuma daga kumburarrun idanunta da dayan bai iya
gani da kyau ta kalli ama sannan ta maida dubanta qasa

"Inason ki daukeni daga yau a matsayin bintou mahaifiyarki da baki santa ba,inaso daga yau ki sanya a
ranki ni ba babar maina bace,ban haifi d'a aliyyu ba,ke kadai na haifa,zaki iya daukata a matsayin
mamarki da zaki iya gayawa dukka damuwarki?" Kiran sunan maina din ya saukar mata da wani zafi daga
zuciyarta,amma kuma data dubi ama saita tuna cewar.......matar bata taba takura mata ba,bata taba
shiga huruminta ba bare ta dameta ko ta hantareta cikin gidan yadda sauran matan kawunnanta suke
mata,bata taba mata wata mummunar magana ba,hasalima ko meye zatayi ba ita cikin masu yi mata
caaa. Abinda kuma ta gani idanun ama din a sannan yayi kama da abinda d'a yake gani cikin idanun
mahaifiya,haka kawai taji wata nutsuwa ta saukar mata tattare da ama din,bata daice mata komai
ba,amma kuma bata sake musawa ba,ta kamata ta kaita bandakin ta kuma fara yi mata dukkan wani abu
da tasan zai sanya taji dadi cikin jikinta,cikin hikima kuma tana shaida mata ciwukan dake jikinta don
kada tayi wani abu me qarfi da zai kawo matsala a wajen.

Abun yayi mugun yi mata banbarakwai tare da daure mata kai,dinki a wajen hanyar fitsarinta?,
tabbas kasheta kawai maina yaso yi,bata taba gani ko jin an dinke wajen ba,sai qwalla ta cika mata idanu
ta kuma ga gangaro tabi ta saman kuncinta ta hade da ruwan wankan dake a jikinta,dama koda ama
bata gaya mata ba tasan wajen ba lafiya yake ba,don ita kadai tasan yadda taji gurin yayi mata,tanajin
kamar ba'a jikinta yake ba,zallar radadi da zugin da yake mata ne kadai yake tabbatar mata a jikinta har
yanzu yake.
*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261
*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 10

Kuka sosai ta sakarwa ama saboda kalar azabar da takeji sanda ama din ke gasa mata jikinta.
Tausayinta ya cika zuciyar ama din fal,kamar ta zauna itama tayita mata kuka ko ta barta kawai taji da
ciwukan jikinta,saidai kuma hakan ba zaya yiwu ba,gatan da zata mata kenan hakan kuma shine zai
sanyata ta warware da wuri. Itama ama din bata hanata kukan ba,tana ganin idan tace tayi shuru ko
kada tayi kuka bata yi mata adalci ba,aika aikar da maina din yayi mata ko uwar mata ce ita sai taji
jiki,bare yarinyar da har yanzu rainonta akeyi.
Tsaf ta wanketa ta lullubeta da towel,ta kuma riqeta cikin takatsantsan suka dawo cikin dakin ta
tayata ta shirya,ta fidda simple gown cikin kayanta ta bata tace ta saka,sannan ama din ta matsa gaban
kayan tea dake jere ta fara hadawa sultanar wadda tunda ta gama shiryawa ta maida idanunta ta kulle.
Gaba daya ji takeyi ko duniyar batason kalla,yanzun waye da waye yasan abinda maina yayi mata?,me
zata cewa mutane?,da wanne ido zata kalli 'yan gidansu?,qawayenta dama 'yan unguwarsu?,me ta yiwa
maina haka daya gwammaci ya kasheta ya huta?,bata taba zato ko tsammanin zata farka ta ganta cikin
gidan duniya ba.

"Tashi kisha sultana" ama data gama hadawa ta dawo ta zauna gefanta ta fadi cikin salon lallashi. Bata
iya bude qullallun danunta da hawaye ke ratsasu yana fitowa ba ta girgizawa ama din kai. Batajin akwai
wani abu me sunan abinci da zaya isha shiga cikinta,sam ita bata sha'awar komai ma koda kuwa ruwa
don ya zame mata dole ne ta karba a dazun ta sha.

Duk yadda ama ke tunanin zata lallabeta ta karba tea din amma ta qiya,daga bisani ma daina
amsawa ama din tayi,sai ta koma kamar wadda bacci ya dauka,dole ama ta mayar ta aje,saita koma
kujerar dake fuskantar sultana din tana nazarinta lokaci lokaci,yayin da wani kaso na hankalinta ya tafi ga
ci gaba da karatun qur'aninta ko zata samu sassauci cikin zuciyarta,ta wani bangaren kuma bata gaji ba
hakanan bata sare ba da gwada kiran wayar maina,amma dai duka sammakal,ba abinda ya
sauya,wayarsa a kashe take.

Kafin a kirayi sallar asuba baccin gaske ya sake daukar sultana,wani irin wahalallen bacci da babu
armashi ko karsashi ko kadan a cikinsa. Gyara mata kwanciya kawai tayi ba tare data tasheta ba,ta wuce
bandaki tayi wanka ta hado da alwala sannan ta dawo ta tada salla.

Sallamarta daga sallah yayi dai dai da shigowar aba,ta bishi da kallon mamaki,tamkar wanda
baiyi sallar asuba ba?,ko kuma a nan cikin asibitin yayi?,tafi zaton hakan,don fuskarsa batayi kama da
fuskar wanda ya tashi daga bacci yanzu ba,tafi kama da fuskar mutumin da bai samu cikakken bacci ba.

Da sallamarsa ya shigo,fuskarnan sam babu walwala ko ta gamun gafara sai tarin damuwa da
firgici. Kujera yaja gefan gadon sultanan dake bacci,ama tayi qoqarin shafa addu'arta cikin rashin qwarin
gwiwa ta soma gaidashi. Gaisuwa daya rak ya amsa mata yabiyo bayanta da tambayar

"Yaya ta kwana?"
"Gata nan alhamdulillah"

"Da sauqi jikin nata?" Ya sake jefawa ama tambayar kai tsaye

"Eh,da sauqi,don har nayi mata wanka"

"Yaushe likita zai shigo?" Ya kuma tambaya yatsunsa harda cikin na juna

"Basa wuce shida na safe" sai ya jinjina kai kawai,bai sake cewa komai ba ya zaro wayarsa ya soma
gwada kiran wata number. Bugu biyu ta shiga ya soma magana da wanda ya daga kiran

"Inason ayi cancel tafiyar nan,a maidata sati na sama.....eh yau din gobe dama jibi duka ina da wani
uzuri..... okay yayi Allah ya kaimu" ya fadi qasa qasa.

Maganar da taji aba din yanayi shi ya tuna mata da shirin tafiyarta Nigeria wanda da a yau zata
yishi,sam wannan abun ya sanya ta manta da komai,sai ta ciro wayarta tana dubawa.

Tarin miscal ta gani na masu aikin gidanta na nigeria,musamman bilki miscals dinta yafi na
kowa yawa,sai kuma miscal din yayanta. Dukkansu tasan kowa yanason yaji qarfe nawa ne zata sauka,ta
duba lokaci har yanzu a biyar da rabi suke,idan ta kira yaaya din a daidai lokacin yayi safiya da
yawa,tunda ko banza me iyali ne shi,don haka saita soma kiran bilki.

Dab da zata katse ta daga tana fadi cikin girmamawa

"Afuwa hajiya,bacci ne ya daukeni bayan na idar da sallah,ina kwana?"

"Lafiya lau bilki"ta amsa mata cikin rashin karsashi


"Yauwa dama inata son naji qarfe nawa zaki sauka don nasan me za'a tanadar miki,don tun jiya an gama
kintsa gidan,me gyaran batiran inverter dinnan ne kawai bai iso ba,amma shima yace qarfe bakwai na
safiya zai shigo" Boyayyen numfashi ta saki

"Ya taho a nutse,kada kuma ku dora komai saboda ni,tafiyar nan ba yau ba"

"Toh hajiya,sai gobe kenan?"

"Ba gobe ba kuma jibi ba,kawai duk sanda na shirya sake zuwan zai sanar muku"

"To hajiya,Allah yasa lafiya,Allah ya bamu aron rai"

"Ameen" kawai ama ta amsa mata tana gimtse kiran.

Yadda dakin yayi shuru da yawa saita kasa sakewa,haka kawai takejin wani iri,daga ita har aba
kalma daya game da ciwon nata hadasu ba wai da zummar tattauna,batasan inda ya dosa ba ko kuma
me yake saqawa a ransa ba,sai kawai ta buge da danna wayarta,wanda ita kanta batasan me takeyi
ba,kafin daga qarshe ta shiga sms ta soma rubutawa maina gajeran saqo ta number wayarsa

_"Duk inda kake kada ka kuskura kakai dare baka dawo gida ba,wannan din umarnina ne"_ . Abinda ta
rubuta masa kenan a gajarce ta tura masa.

Qofar aka taba sannan kuma aka murdata aka bude. Dr chafa'atou ce sanye da kayan gida,kai
bazaka taba cewa likita bace ita din. Da alamu sammako itama tayi,kuma duk yadda akayi ta kwana da
abunne itama cikin ranta.

Cikin girmama juna suka gaisa,ta gaida aba cikin matuqar girmamawa shima,sannan ta fara duba
sultana din tana yiwa ama tambayoyin yadda suka kwana. Tun sanda Dr chafa'atou ta shigo sultana ta
farka,amma data fahimci ba su kadai bane cikin dakin harda aba sai ta kasa bude idanunta,saidai
kukanta data dora ta hanyar fidda qwalla,wanda sam basu lura ba sai da Dr chafa'atou tasa hannu ta
juyo da fuskarta tanason ganin yanayin idanunta.

Ta fahimci ta farka kuma kuka takeyi,sai kawai ta yagi tissue tana goge mata hawayen cikin
takatsantsan din kada ta fama mata fuskarta,tasan tana tsananin yanayin da take ciki,so ba buqatar ayi
maganar da zata ji ta takura ko a tilasta mata boye damuwarta ko don gudun kamuwa da depression da
tayi imanin indai ba'a yi da gaske ba tana iya tsintar kanta a ciki muddin ba'a kula da kyau ba

"Dr ina fata komai lafiya" aba ya tambayi Dr chafa'atou kai tsaye. Sai data dan juyo kadan ta kalleshi
sannan ta maida dubanta ga fuskar sultana

"Eh lafiya alhamdulillah,saidai idanun nan nata inajin anjima kadan sai an dubashi sosai,don yaqi sauka
daga kumburin da yayi,sannan da alama ma kamar bata iya budashi da kyau ma ko?" Tayi tambayar tana
me neman amsa daga wajen ama. Kai aman ta gyada mata tana bata tabbaci.

"Oh.....bayan abinda ya aikata kuma har sai daya hada da illatamin idanun yarinya?" Aba ya fadi da wani
irin tune,wanda sai a yanzu ta gama fahimtar inda aba ya sanya gaba akan case din.

"Ba matsala in sha Allah" Dr chafa'atou ta fadi don ta kwantar masa da hankali. Kai ya jinjina da qarfin
gaske hannayensa zube a aljihun wandonsa

"Kuyi mata cikakken bincike,idan da wani matsala inaga zaifi kyau ku bani ita na fita da ita waje ayi mata
dukkan abinda ya kamata" Ya fadi yana hadiye wani abu me daci dake taso masa,tsantsar tausayin
yarinyar da kuma rashin imanin maina qarara yana bayyana a idanuwansa.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*
*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*
09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 11

_______________________________

*_Shin kin isa mace?,don magana akeyi ta ISASSUN MATA_*

*_SUTURA ABAR TUNQAHO_*

*_Ado da kwalliya shine cikar 'YA MACE_*

_Magana akeyi ta_

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*

*UMMU MAHNOOR LUXURIES*


_GIDAN QAWA ADO NA KECE RAINI_

*_INA AL'UMMAR KADUNA ABUJA SULEJA DAMA NIGER......HAR MA FADIN NIJERIA GABA DAYA_*

*_KIN SHIRYA FITA KUNYA?_*

*_MAZA HANZARTA KI LALUBI KALOLIN SUTURAR DA TA DACE DAKE,KAYAN ADO MASU_*

*KYAU*

*QUALITY DA DAUKAN HANKALI*

*LACES NE,SHADDA CE,ATAMFOFI NA 'YAN QWALISA*

*GA KUMA DESIGNERS TAKALMA DA JAKANKUNA NA ALFARMA DA FITA KUNYA*

*_ZAKU IYA SAMUN MAMALLAKIYAR KAMFANIN KAI TSAYE TA WANNAN NUMBER WAYAR_*

08135142610

*INSTAGRAM* UMMU_MAHNOOR_LUXURIES

*FACEBOOK* MUSA GARBA SHIFA

*_Ga wadanda ke cikin garin abuja kuma zasu sameta kai tsaye a_*
*_system property Nefelix estate,near amasco,galadimawa roundabout_*

*_KARKI BARI A BAKI LABARI,KARKI KUSKURA KI ZAMA 'YAR KALLO_*

*TASTED AND TRUSTED*👌👌👌

_____________________________

"karka damu alhaji,in sha Allah zamuyi duka bakin qoqarinmu" kai kawai ya jinjina sannan ya
waiwaya yana duban ama

"Na kirashi yafi sau shurin masaki ban sameshi ba,ban sani bama ko blocking dina yayi?,me yiwuwa
tunda ke uwarsa ce bazai iya miki haka ba,idan kin sameshi ki shaida masa saqon da yabar mana ya
riskemu,munga result kuma a qasa mun gode" daga wannan ya sanya kai ya fice,sai ama ta bishi da kallo
baki sake. Me aba yake nufi ne?,baisan yadda suke nemansa itama hakan bane,ta kirayeshi bata sameshi
ba?,sannan tayi zaton zaiyi maganar ya dawo gida ne ya karbi hukuncin da ya dace dashi,a maimakon
hakan sai taji wata magana ma yakeyi daban wadda a nata ganin a yanzun ba nanata maganar bane ya
kamata a dinga yi,abinda yafi kyau shine asan meye abu na gaba da ya kamata ace an aiwatar.

K'arfe bakwai da rabi sai ga bibi an kawota,ita da matar oncle umar. Jikinta sanye da lallausar
bubu cotton 'yar saudiyya,hannunta riqe da casbahar da kana gani kasan itama ita ta kwana ja.
Dukkansu suna a gaban gadon sultanar suna mata sannu,saidai ba wanda ta tankawa,hasalima ko
qwayar idanuntan taqi ta bude ta kalli koda bibi dinne,sai hawaye da suke bulbulowa ta qasan idanun.
Juyin duniya bibi tayi ta bude ido amma ta qiya,duk da dama daya idon ba wani buduwa yakeyi sosai
ba,koda ta bude dinma bawai ganin komai tarwai takeyi ba.

Da bibin ta gaji ta koma lallabata ta tashi taci abinci,abincin da tafiso ta sanya tanja ta dafa
mata tun sassafe,shima har bibi din tayi ta gama bata ko motsa ba bare ta nuna tasan me sukeyi,daga
qarshe ma sai ta gyara kwanciyarta ta basu baya ta fuskanci bango sanda 'yan dubiya suka fara isowa
dakin.

Ita daya tasan me takeji cikin zuciyarta,wani baqinciki da wani abu me tauri ne tokare tsakiyar
maqoshinta. Kunyar kallon kowa takeji,hakanan kuma haushin kowa takeji. Ta tabbatar inda bibi bata
biyewa umarninsa ba ta sakata a gaba sun tafi yadda suka saba da yanzun babu abinda ya sameta. Kusan
ta tarkata dukka laifin ne ta azawa bibin,tana ganin sassaucin da ta yiwa maina dinne har ya samu qofar
aiwatar da mummunar nufinsa a kanta.

Wasa wasa sai gashi takai har qarfe biyu na rana bataci komai ba,maganinta ma babu wanda
tasha a ciki sai uban kuka data saka gaba. Duk wani motsin sultana din yana kan idanun ama,a yanzun
tana sake jinta ne kamar saddi,tana ji kuma har cikin rai da zuciyarta nauyinta ce sultana,dolenta ce
sultanar.

Biyun da 'yan mintuna su yasmine da aminata suka shigo da abincin rana. Muryoyinsu kadai
suka sake haifarwa da zuciyarta wani sabon rudanin. Yanzun fa kenan itan ba daidai take dasu
ba?,dukkansu sun fita walwala nutsuwar zuciya da kuma 'yanci?,a cikinsun yanzun itace daban kenan?.
Har suka gama leqata suka mata sannu bata motsa ba kaman yadda takewa kowa. Hankalin ama yana
kai,don haka bibi na fita sallah ta sanya kowa yabar dakin,ta maida qofa ta rufe sannan ta tako a nutse
inda sultanan ke kwance.

Kiran sunanta tayi amma bata amsa ba,bata tsaya batawa kanta lokaci ba ta durquso saman
kanta ta kuma sanya hannayenta dukka biyun tana dagota daga kwanciyar tana fadin

"Haba sultanan bibi.....subhanallah" ama ta fadi kuma daga baya bayan taji yadda jikinta ya dumame da
wani mugun zazzabi. Zagayowa tayi ta zauna sosai kusa da ita tana riqe tafin hannunta idanunta akan
rufaffun idanuwanta

"Yanzun da wannan zazzabin a jikinki kike kwance?,sultana kinason kashe kanki ne?,kinaso yayi miki
dariya yace yayi winning a kanki?,kinaso yaji cewa burinsa ya cika na cusguna miki?,kinason sanyawa bibi
hawan jini ne?,ko kinaso aba ya shiga matsananciyar damuwar da zai dinga kasa komai?" Shuru bata
amsa ba,saidai kukanta yanzun ya qaru ya zama me sauti ba kaman daxu da take yinsa silently ba. Tana
jin inama ace ama zata iya farka qirjinta ta cire mata zuciyar daga qirjinta ko zata samu sassaucin abinda
takeji,inama ace mutum yana iya shafe rayuwarsa gaba daya ya sake rubuta sabuwa,inama ace ta rufe
ido ta bude taga ba itace sultanar familyn MAYAK'I ba

"Sultana.....babu ci babu sha babu shan magani,me kikeson yi idan ba kisan kai ba?,kina azabtar da kanki
bayan shi wanda yayi miki laifin har yanzu bai waiwayi gida ba bare yasan kinayi,me yasa kike azabtar d
kanki da kanki?,duba......yanzu lokacin sallah ne amma tunaninki ko kiyi sallar baya baki?" Sake barkewa
tayi da kukan tana cusa fuskarta tsakanin cinyar ama tare da qanqame ama da kyau. Kuka takeyi sosai
me sauti,sautin kukan dake fita da wani irin mugun radadi da ciwo da zukata suka tara. Sosai ta sake
karya zuciyar ama,sai ta dora hannunta saman kanta tana shafa sassalkan gashinta da ya zama kamar na
tsohuwar mahaukaciya tsakanin jiya da yau saboda tsananin firgici da tashin hankalin da take ciki. Sumar
da ake bata lokaci wajen gyarata da qalqaleta amma a yau bata da maraba da radaddagaggen zare cikin
tarin tarkacen bola. Ta yarda da maganar Dr chafa'atou sai anyi da gaske akan sultana din,idan ba haka
ba depression din tsaf zaya kamata. Bata dakatar da ita daga kukan ba,saidai itama tata zuciyar tayi nisa
wajen tunanin yadda zata tafi da yarinyar.

Sai da tayi shuru don kanta sannan ta dagata tana cewa

"Banaso daga yanzu ki sake irin haka sultana,idan maina ya tsaneki ya zalunceki ya kuma cusguna miki
mu dukka nan ke mukeso,mu dukkaninmu walwala da farincikinki mukeso,kuma zaya dawo ya fuskanci
mafi girman hukunci,hukuncin da kuma kece zaki zabeshi da kanki". A duk sanda ta furta sunan Aliyyu ko
maina sai taji wani abu tsakiyar kanta yana mata yawo kamar ana sakatar qwaqwalwarta,ambatar
sunansa kadai yana sake sanya mata wata mahaukaciyar tsanarsa da takejin tamkar zuciyarta zata tsage
ta fado,to amma batun hukuntashi dake hannunta kamar yadda ama ta furta sai ta samu kanta da
laluben amsa,cikin manya manyan hukunce hukuncen da akema dan adam cikin rayuwa batasan wanne
iri zata zaba masa ba,take kuma taji kanta ya sara kamar zai rabe biyu,tunaninsa ko daya bata qauna
cikin kwanyarta,karon farko ta bude bakinta a hankali muryarta na fita da wani irin sarqaqqen amo

"Ama don Allah.....kibar kiramin sunanshi.....kaina kamar zai rabe biyu" ta qarasa maganar dukka jikinta
yana kakkarwa saboda wani sabon zazzabi me cakude da ciwon kai daya sake saukar mata.

Yadda taga jikin nata yana rawa tilas ta kiranyi likita,a sannan dr chafa'atou ta fita sai dr nadra.
Dr nadra tafi Dr chafa'atou fusata da lamarin,ta sake checking sultana da kyau tace a dakatar da
shigowar masu dubiya,idaninta kuma da magariba likitan idanu Dr nouhou zai shigo zai dubata. A barta
ta huta kawai,a qyaleta duk abinda take so tayin,shine zai sanya zuciyarta samun sassauci daga abinda
takeji.
To ba'a sake matsa matan ba,saidai duka ranar ama din tana tsaye akan sultana din,sai yamma
liqis ruwan da suka sanya mata ya qare,ama ta lallaba ta sanyata tayi alwala tayi sallah daga zaune
saboda dinkin da yake jikinta,ta hilaceta da qyar ta samu tasha tea cokali uku,na hudun kuwa dawowa
yayi bai iya shiga cikinta ba. Ganin hakan sai ta qyaleta,tana fatan gobe tasha abinda yafi hakan.

Suna tsaye daga bakin window inda zasu dinga hangota sosai ita da bibi din data gagara tafiya
guda tun safen. Wayarta na hannunta dai still ya zuwa yanzu batasan adadin sau nawa tayi kiran layin
maina ba. Duk sanda zata kira akace mata wayarsa na akashe sai taji ranta ya ninninka baci akan na
baya. Me yaron yake nufi?,ya maishesu mutanen banza kenan?,yayi aika aikarsa ya wuce gararin
gabansa babu abinda ya shalleshi?,baya tunanin a yanayin da ya barta ma ya dawo ya tabbatar da
ingancin rayuwarta ko kuma akasin haka?.

Isowar likita gab da dakin ya sanyasu motsawa,yace a dauko wheelchair a kawota ya duba idanun
nata. Numfashi ama ta sauke tana duban bibi,dukkansu a firgice suke,sannan kowannensu kana kallon
fuskarsa zakaga yayi wata rama tsakanin jiya da yau kawai

"Bibi dare yana yi, inaga ya kamata ki wuce gida hakanan kodon yanayin jikinki,na miki alqawarin zan
bawa sultana dukkan kulawa tamkar yadda mahaifiya zata bawa d'anta na cikinta kulawa"

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*
_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*
09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 12

__________________________________

*_Assalamualaikum warahmatullah_*

*_Kin dade kina neman gurin da zaki siya kaya amintattu masu quality cikin farashi me sauqi?_*

*_ina marabtarku zuwa cikin wannan gida tare da kasancewa da juna,WANNAN GIDANNA HUGUMA
CLOSET NA BUDESHI NE SABODA NA BAKU DAMAR SIYAN KAYA MASU KYAU QUALITY DA KUMA SAUQIN
KUDI CIKIN AMINCI DAGA GURINA,MASU SIYAN D'AI D'AI DA MASU SARI,NATION WIDE DELIVERY cikin
aminci da izinin Allah,Kayan haihuwa na jarirai har zuwa girmansu,ina muna fatan alkhairi ni da ku
gaba_*

https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr

________________________________

Ko daya bibi bata da haufi da ama,kaf yaran gidan a gabanta aka haifesu,kuma babu wani wanda
ya taba kuka da ita. Abu daya ne da ita,bata daukan raini ko qanqani,bata kuma son sakarci,duk wanda
ya santa ya santa da wannan halin,don haka babu haufi bibi din tabar mata sultana,saidai kafin ta tafin
tabar musu tanja saboda ama din kanta ta samu sauqin zirga zirga,sannan kuma tace da ama din
"Kome ake ciki banason ki boyemin,daga maina har sultana dukkansu jini na ne,kuma jikokina ne"

"In sha Allah bazan boye miki komai ba" ama ta furta tana lanqwasa yatsunta tana jin wani nauyi bibin ta
sake aza mata.

Sun kusa a qalla awa biyu harda wani abu kafin Dr cha'aibou ya kammala gwaje gwajensa. Ya
daga result na gwajin da aka yima idanun nan cikin asibitin yana kalla sai ya maida takardar saman
teburinsa yana duban ama

"Ta samu matsalar rainin gani a idonta guda daya,jijiyoyin dake dauko haske sun tabu saboda duka da ya
samesu ko buguwa....." A firgice ta juya tana duban sultana saboda yadda sakamakon ya daketa da kyau.
Idanunta fes ta zubewa sultanar,tana zaune saman lallausan kujerar da Dr din yace ta zauna akai,ko
motsi kyakkyawa batayi ba bare wani reaction,itakam meye wai ya rage mata?,ita a yanzu ko cewa akayi
maina ya kasheta dawowa tayi sam ba zatayi mamaki ba

"Amma ba damuwa in sha Allah,zamu dorata saman magani zuwa wani lokaci mu gani?,idan kuma akwai
buqatar ayi mata glass zuwa lokacin zamu gani" ya fadi yana zaro takarda yayi rubuce rubuce akai.

Hawaye kawai idanun ama keson xubarwa amma tana dannewa,don ta tabbatar muddin ta
zubda hawaye akan maina alhali yana raye ko a macen ma tamnar ruwan masifa ta fidda masa. Tsananin
tausayin sultanar kamar ya fasa zuciyarta. Cikin qasa da awa ashirin da hudu duka yarinyar kamanninta
sun jirkice,tayi wata irin wawuyar ramar da hatta rigunanta basa zaunar mata sosai a jikinta.

Da qyar da daren ta lallabata tasha madararta,madararta ta amana wadda muddin bata shata ba
kaf gidan babu me rintsawa,amma sai gashi wai yau lallabata akeyi tasha din.

Kamar jiya bacci ya riga daukar sultana kafin ita,kaman jiyan dai haka ta zauna,gefe qur'ani gefe
wayarta tana tusa kiran maina amma dai komai bai canza ba.
Batafi awa biyu da zama ba sultanan ta farka firgice tana kiran sunan maina din da qarfin. Da ita
da tanja da itama ta fara bacci batasan waye ya riga wani isa gareta ba. Kuka take sosai dafe da kanta,ta
ture hannuwan ama dake riqe da ita da qarfi,sai ama din ta fahimci kaman batason ganinta. Bataji komai
ba don tasan situation din da take ciki,kuma Dr chafa'atou ta mata bayanin komai,zata iya tsintar kanta
cikin razana da firgita da kuma miyagun mafarkai na abubuwan da suka faru da ita. Don haka ta yiwa
tanja alama taja da baya ta basu waje.

Sun kusa kwashe wata awar tanja na lallabata da hikimomi da dabarun data saba mata kafin ta
samu kukan yaja baya,ta bata ruwa tasha saita maida bayanta kawai ta kwanta hawayen na ratsa gashin
idanunta yana jiqasu da hawayen dake diga har cikin kunnenta.

A wannan daren ma sam ama bata iya bacci ba,tunani ba kalar wanda batayi ba,a haka asuba ta
rusketa.

********Kwanaki bakwai kenan da faruwar abun amma babu abinda ya canza. Al'amarin da ya haifar da
rashin walwala rashin kuzari da karsashi cikin family din MAYAK'I. Kusan dukka sa'aninta dake gidan
tamkar suma sun shiga alhini na abinda ya farun. Cikin dangi kuwa masu zuwa dubiya ne keta
zarya,dadinta daya Dr chafa'atou ta hana shiga wajenta saboda tana buqatar hutu da qarancin hayaniya.
Abinda ya daurewa ama kai shine fitar zancan, saidai bata da tabbacin sunsan ainihin abinda yayi silar
kwanciyartata.

Daga ama har bibi babu wanda bai rame ba,kada ma ama taji labari wadda kullum dare tausayin
sultana yake sanyata a gaba. Kowanne dare yarinyar cikin firgici da kuka take yinsa,idan an dace bacci ya
dauketa kuma tun batayi nisa ba take farkawa a razane,muddin tayi wannan razanar kuma nata baccin
ya qare itama.

Fargaba zullumi da rashin isashen bacci ga jinya suka taru suka yiwa ama din yawa. Gefe guda ga
aba wanda bata sake ganin walwalarsa ba tun daga wancan ranar. Kullum rana zai shigo da safe ya duba
sultana din,ya jima da ita yana tambayarta me takeso?,saidai babu um ba um um,hakan da dare zai sake
dawowa ya kashe lokaci wajenta.

Rashin maganarta ya fara tabashi,tsahon zamanin da aka haifi sultana bata taba zaman
minti.biyar bakinta shuru ba,koda bata da lafiya bata lamunci zaman kurum ba,abun ya soma ganin ya
wuce tunaninsa,yadda takebin kowa da komau da idanu,tana iya yin kwanaki koda nawa ne a hakan ba
tare da buqatar canjin yanayi ba, kodon haka a kwana na takwas ya sanya Dr chafa'atou a gaba yace
lallai ayi mata gwaje gwaje ko bayan idanunta da ya kusa nakasa mata qila ya shaqe mata mafitar
maganarta ma,don wanda yayi hakan babu abinda bazai aikata ba.

Dan dariya maganar ta bawa Dr chafa'atou,itadai tasan lafiya gurin yake,zallar daya daga cikin
illolin da irin wadannan abubuwan suke haifarwa ne kawai data tsinci kanta a ciki. Don dai hankalinsa ya
kwanta ta sanya akayi mata gwaje gwaje,kuma komai ya fito normal,ta bashi gwajin tana cewa

"Kulawa ta musamman kawai take buqata aci gaba da bata,don kamar depression ne take ciki har
yanzu,komai zai wuce in sha Allah,a yawaita faranta mata ranta da dukkan abinda akasan tafiso,tare da
qauracewa furtawa ko tuna duk abinda zai sakata a damuwa". Lafiyar tata da aka tabbatar masa tayi
masa dadi,sai ya qara adadin lokutan zuwansa,ya zauna yayita janta da irin hirarrakin da a baya yasan
tafiso. Kafin wani lokaci dakin asibitin nata ya cika da kayayyaki,kama daga teddies
chocolates,madararta,games kala kala da tarkacen kayan computer. Komai saidai ta bishi da ido,yadda
zai gwada mata ya aje shi a wajen bata sake tabashi. Tana jin bata qaunar komai,bata buqatar
komai,hakanan komai bai bata sha'awa,inda zasu gane su qyaleta ita daya cikin daki,kowa kada ya
kulata,kowa kada ya tanka mata da hakan zaifi faranta mata. Don kusan kowa ta gani da ya danganci
gidansu bata ganin komai tattare dashi sai ALIYYU MAINA,suna Mafi girman da ta yiwa mafifiyar
tsana,sunan da inda tana da hali da daga rana irin ta yau ta shafeshi a doron duniya,halittar da takejin a
rayuwa babu halittar data cancanci azaba irinta.

Sannu sannu komai bai canza ba illa ciwukan jikinta da suka warke din,kumburin fuskarta ya sabe
dai dan tabbai masu launin pink,hakanan dinkin qasanta ma ya hade kasancewar akwai quruciya tattare
da ita,sannan kuma ama ta tsaya tsayin daka tayi bata kyakkyawar kulawar da banda ciwon dake cikin
zuciyarta da babu abinda zai hanata mulka qiba. To a maimakon qibar sai wata mummunar rama da tayi
mara kyan gani.

Kwanansu ashirin cif Dr chafa'atou ta tabbatar da samun lafiyarta ta kuma rubuta mata sallama
tare da bawa ama qarin shawarwarin yadda zata ci gaba da kulawa da ita don a samu rayuwarta ta koma
daidai kamar ta kowa.

Motoci biyu ne cikin motocin gidan iyalin mayak'i sukazo daukarsu. Karon farko da ta fita daga
asibitin tun ranar da ta kawo sultana. Tun dava randa ta koma ta wanke zanin gadonsu bata sake barin
asibitin ba,don duk inda zata motsa sai taga kamar sultana zata rasa wata kulawar,kamar sultana zata
buqaceta,kamar wani abun zai samu sultana din kafin ta dawo.
*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_


09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 15

*_les jumeaux_*(the twins)???


K'arfe biyu da rabi motocin yaran gidan dake jigilar kaisu makaranta suka fara saukesu,a lokacin
ama tana zaune a samanta,tana jin motsi da kai kawonsu,saidai aikin da takeyi ya dauke mata
hankali,batajin zata iya saukowa a sannan,saddi ne yana yima kansa komai don ba qaramin yaro bane
bare tace zai nemi wani abu daga gareta,sai sultananta da tasan ita dinma indai ba wani abu ta buqata
ba ba lallai ta nemi ganinta. Waya ta dauka ta kirayi bilki me aiki tace ta duba mata sultana ta dawo?. Ba
jimawa ta sake kiranta

"Ta dawo hajiya"

"Yauwa to,ki bincika ko akwai wani abu da take buqata,idan babu shikenan,sai la'asar ni zan sauko"

"To hajiya" ta amsa mata a ladabce tana aje wayar. Mintuna biyu rak bilkin ta sake kiranta

"Hajiya qofarta rufe take" dan shuru ama tayi

"Lafiya?"

"Eh kaman lafiya gaskiya don na danji motsinta"

"To yayi,ki rabu da ita wala'alla hutawa takeyi,sai na sauko din"

"To a sauko lafiya" bilki ta amsa mata.

Wayar ta aje tana dan nazari kadan tare daci gaba da aikinta da take gab da kammalawa.
Lissafin shekara shekara ne,wanda bayan ta kammala din take fidda zakka haqqin Allah.

Tana gamawa din yadda taso ta zauna ta huta sai tayi sallar la'asar kuma amma sai taji
hankalinta yayi kan sultana. Kashe mini laptop din tayi,ta zura tausasan slippers dinta ta miqe tana nufo
stairs din.
A nutse ta sauka ta kuma nufi sashen dakunan dake qasa. Tana ratsa falon suna gaisawa da
masu aikinta da yau duka basu samu ganinta ba,tana amsa musu tana dosar dakin,har ta isa qofa.

Murdata tayi har yanzu tana kulle,ta kira sunan sultana din sau biyu bata amsa ba,sai ta juya
yana yiwa fainusa magana kan ta duba store ta ciro mata spare key.

Cikin qasa da minti daya fainusa me aiki ta dawo da key din ta miqa mata,ta karba ta soma
gwadawa har ta samu na dakin.

Dundum yake kamar ba rana ba,cikin mamaki ta kunna fitilar dakin haske ya gauraye,idonta ya
sauka kanta sanda take nade tsakiyar gado lullube da qaton duvet. Mamaki ya kama ama ta kira sunanta
tana takawa ciki hadi da cewa

"Bakijin zafi zaki rufa haka?,wanne irin bacci ne wannan sai an rufe kai?" Ta furta tana janye duvet din.

Razana tayi ganin yadda sultana din ke qudundune guri guda tana rawar sanyi sosai. Farar
fuskarta ta sauya launi zuwa pink color kaman yadda tasan tanayi a duk sanda take zazzabi irin wannan
ko wani ciwo. Tun bata kai hannunta ba take iya jin hucin dake fita daga jikinta gaba daya,duk da hakan
sai ta miqa hannunta da sauri tana taba sassan wuyanta. Saukar hannun ama a jikinta sai taji kaman an
qara mata ciwon,ta maqale wuyan wasu siraran hawayen suna fita daga idanunta

"Ya salam ya Allah" ama ta furta,zafin dake jikinta yayi yawa qwarai,sai ta dauki remote na ac din dake
gefan gadon ta soma da kasheta,sannan ta juyo ga sultana din tana zama sosai a gabanta

"Dama dashi kika dawo daga makaranta?,tun yaushe ne?" Ta tambayeta cikin tsananin damuwa

"Tunda na shiga classe(class)" kai amma ta girgiza tana jin hankalinta yana daguwa
"Bari na kira Dr chafa'atou,zafin zazzabin yayi yawa" ta fadi tana sauka daga saman gadon sannan ta
koma zuwa sassanta da gagggawa.

Qasa tayi da kanta tana lumshe idanuwanta bayan fitar ama. Wasu hawayen masu zafi
kwatankwacin zafin zazzabin jikinta suka biyo kuncinta. Ita daya tasan me takeji cikin jikinta,tanajin
kamar ana kama qasusuwanta ana ballasu daya bayan daya,kowacce gaba ta jikinta ciwo take mata
sosai. Wasu sabbin hawayen suka kuma biyo idanunta,tun daga wancan ranar...... tun daga randa yayi
mata fyade......tun ranar da ya zalunceta ya cuceta bata sake samun lafiya ba......bata sake jin qarfi cikin
jikinta ba,ya tafi da dukka kuzarinta,ya tafi da walwalarta da kuma farincikinta,tana jinta a cikin jikinta ita
karan kanta kamar ba sultanan bibi ba,kamar ba itace ke rayuwa a wannan gangar jikin ba.

Dukka wayoyinta ta debo ta dawo dakin tana gwada layukan wayar Dr chafa'atou. Bude qofar
dakin ya sanya sultana bude fararen idanunta da suka sauya kala saboda tsabar zafin zazzafin dake fita a
jikinta

"Sannu sultana.....sannu" ama ta fadi cikin kulawa ainun tana zama saman bedside drawer tana kuma
sauraren wayar Dr chafa'atou dake ringing.

Dab da zata katse ta daga,cikin girmama juna suka gaisa

"Jikin patient dinki ne ba lafiya médecin(Dr)"

"Tofa,me ya sameta kuma?" Dr chafa'atou dake shirin zama saman kujerarta daga can cikin office dinta
ta tambaya

"fièvre ne me zafi,dashi ta dawo daga école(school)"

"Subhanallahi,idan yayi zafi da yawa ki samu mouchoir(handkerchief) me kyau da ruwa a goge mata
jikinta,gani nan na tashi gida zan wuce dama,zan qaraso na dubata"
"d'accord(okay),amma ina neman alfarma,zan saka motocin mayak'i yanzu suzo su taho dake,je ne veux
pas de retard(banason jinkiri)"

"Hakan yayi ba damuwa" wayar dukka suka ajjiye.

Idanunta a lumshe,yadda jikinta ke zafi da quna haka zuciyarta,tana jin sanda ama ta iso da
ruwan da qaramin towel ba tare data nema kowa ba

"Tashi a goge miki jikin sultana la fièvre est si élevée(zazzabin yayi yawa)" kai ta girgiza a hankali sannan
tace

"A kiramin bibi,bibi nakeson gani"

"Za'a kirata,amma a ragewa jikin naki wannan zafin kada tazo ta gani hankalinta kuma ya tashi,ko kinaso
hankalinta ya tashi kuma?" Kai ta girgiza a sanyaye,sannan ta yunqura ama na riqe da ita ta zaunar da ita
sosai ta rage mata uniform din,ya zamana daga half vest din da ta soma kare martabar qirjinta da su,sai
gajeran wando mahadin vest din. Sam ba wani kunya tsakaninta da ama,don ta zama tamkar uwar da
babu shamaki a tsakaninsu. Tana goge mata din ta kirayi layin tanja donta kira bibi din bata sameta
ba,tace ta shaida mata sultana ke rigimar son ganinta yau kuma,ta tashi da wani dan zazzabi. Tanja din
ta amsa mata sannan ta kashe wayar ta maida saman drawer.

Tana gama goge matan akayi knocking qofar sannan aka turo. Bibi ce sanye da lallausan abaya
cotton 'yar marocco ta mata me hade da mayafi.

Ama ce ta amsa mata tana miqewa hadi da tattare towel da roban ruwan,ta kuma jawa bibi
kujera zuwa gaban gadon da sultana ke zaune.

Idanun bibi qur cikin na sultana bayan ta daidaita zamanta saman kujerar,sannan a hankali ta
maida dubanta ga qirjin sultanan wanda ba baqonta bane.
Wata mummunar faduwar gaba ta samu kanta da ita

"La haula wala quwwata illa billa" ta fadi qasan zuciyarta,sannan ta janye idanunta ta juya zuwa ga ama
dake qoqarin saqale towel din jikin qofar toilet

"Me ya sameta?"

"Zazzabi ama,daga tafiya makaranta"

"Zazzabi kawai?,kuma iya yau?" Ta tambayi ama cikin mamaki a sautin muryarta

"Wallahi bibi,kuma koda safen lafiya lau ta shiga ta miki sallama nima tayimin sallama,sun dawo nasa
azo dubata su bilki suka samu qofanta a rufe,sai da na sauko dubata na sameta kwance" aman ta yiwa
bibi bayani dalla dalla. Kai kawai bibi ta jinjina jikinta yana wani irin sanyi,dukka gwiwoyinta kamar an
bubbugesu,wani irin fargaba ya cika mata zuciya,ta samu kanta tana furta addu'a can qasan
zuciyarta......dai dai lokacin aka shaidawa ama isowar Dr chafa'atou wadda drivern mayak'i mansion ya
daukota.

"Kiyi mata iso ta shigo" tace dame aikin nata tana komawa opposite bibi tana zama itama,jikinta yana
sanyi da ganin sauyawar reaction na bibi cikin tambayoyin da tayi mata.

Har qasa Dr chafa'atou ta tsugunna ta gaida bibi. Sannan ta qarasa gaban sultana tana kallonta.

Kallo na kusan minti guda,kallon da ya sanya sultana janye nata idanun daga kan Dr
chafa'atou,haushi yana cikata duk da ciwon da takeji a dukka gabobinta,don meye zata sakata gaba da
kallo kaman taga wata dodo?.

"Bayan zazzabin kinajin wani abu dabanne?" Dr chafa'atou dake qoqarin bude dan akwatin aikinta ta
fada. Da qyar ta motsa lallabanta ta bata amsa a gajarce
"Babu"

"Okay.....yaushe rabon da kiga period dinki na qarshe?" Tambayar da ta sake sanya razani me yawa a
zuciyar bibi,ta kuma saka ama barin abinda takeyi tana duban Dr chafa'atou da batasan ma duka suna
kallonta ba,don ita nata zargin yayi wani waje daban,don haka ta yankewa kanta yin abu guda daya da
take da babban zato a kansa ba tare data batawa kanta lokaci ba.

"Bana tunanin zata iya riqewa,don kwata kwata al'adarta ma ina jin batayi yakai sau shida ba,niketa
qoqarin tsara mata calendar dinta da sanar da ita lokaci donta dinga kiyayewa" bibi ta yiwa Dr
chafa'atou bayani tana dubanta

"Okay ba matsala" ta amsawa bibi bayan ta gama fidda container dinta

"Kina Jin fitsari?" Ta tambayi sultana tana kallonta

"Kadanne"

"Yimin shi a nan koda dan kadan dinne" sai ta miqawa sultana container din.

Daga bibi har ama bin container din sukayi da.kallo,dukkansu sunsan gwaji akeyi da ita,kuma
batun gwajin fitsari wani al'amari ne me zaman kanshi

"Amma ba fièvre du paludisme(zazzabin malaria) bane Médecin?(Dr)"

"Yanzun zamu gani in sha Allah hajiya" ba wanda ya iya sake cewa komai. Dr chafa'atou dince ta riqe
hannun sultana har qofar toilet sannan ta dawo tana fidda kayan gwajinta. Duka duka bata wuce minti
daya ba ta miqawa Dr din kwalbar ta koma saman gadon ta lafe tana rufe idanunta,don a yanzun babu
abinda takeso da qauna irin ta ganta a kwance,cikin daki me qarancin hayaniya irin haka.
Duk motsin Dr chafa'atou suna biye da ita,har zuwa sanda ta kammala tsatsube tsatsubensu na
likitoci,ta daga pt strip din da ya bayyana komai dara dara yana sake bata haske.

Saukeshi tayi tadan saci kallon ama da bibi,akaci sa'a dukkansu idanunsu yana kanta. Ajiyar
zuciya ta sauke ta koma ta zauna,ita kanta tana jin fargabar bayyana sakamakon gwajin,amma kuma har
kusan hada baki ama da bibi sukayi wajen tambayarta

"Ya dai?,an kammala?" Kai ta gyada musu,ta aro dukka jarumta da dauriya irin ta likitoci sannan tace

"JUNA BIYU GARETA!" Dif wutarsu ta dauke na dan wani wucin gadi,haka kunnuwansu suka tsaya da aiki
na wucin gadin,kamar yadda kwanyarsu ta daina banbance saqon da aka aika mata dashi na wasu
daqiqu. SULTANA dake a kwance kuwa taji dukka kalmomin Dr chafa'atou,amma abu daya zuciyarta da
kwanyarta ta gaya mata

"Bafa dake take ba,magana take akan wata" wani sashe na zuciyarta ya gaya mata zuciyar na wani irin
mugun bugu kamar ta balle daga qirjinta

"Kin duba da kyau kuwa Dr?" Ama data tattaro dukka sauran maqalallen busashen yawun dake saman
halshenta ta fadi

"Na tabbata,a yadda kuma ya nuna shi sosai bana tunanin ma yana qasa da wata daya ne"

"Mun gode kawai Dr,tattara kayanki kije,banda rainin wayo ta yaya zaki kalli kaman sultana kice tana da
ciki?, shekara sha ukun?,lallai na yarda da akace wani lokaci qwqwalwarku tana tabuwa" bibi ta fada da
wani irin yanayi da zai gaya maka lallai ba cikin hayyacinta sosai take magana ba.

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 page 16

"iya abinda na gaya muku hajiya bana tunanin akwai son rai a ciki ko kuma ba dai dai
ba.....dukkanmu munsan me ya faru,ina ganin ba abu bane na mamaki don ance ciki ne da sultana
ba......" Ta qarashe fadi cikin tausasa harshe da kuma dukka yunqurinta nason ganar da bibi abinda ke
wakana.

Wani irin gumi ne yake yanko musu su dukka. Yayin da sultana dake kwance taketa qoqarin fasa
maganar Dr chafa'atou cikin kanta. Wanne irin ciki take nufi tana dashi?,shin mene ne ma cikin wai?.
Wani muguwar razana tayi sanda tunaninta yakai inda ya kamata yakai din,ita kanta batasan yadda akayi
ta isa gaban Dr chafa'atou ba bare bibi da ama dake zaune kowanne jinin dake jikinsa nason daskarewa.

Kyakkyawan riqo ta yiwa Dr chafa'atou, muryarta da wani irin galabaitaccen amo......fararen


idanunta da suka sauya launi dukka sun fito waje tana duban Dr chafa'atou,hucin da jikinta ke fitarwa
bai damunta ko kadan

"Ba Bibi tace ki tafi ba?,me yasa kikeson sake jefani cikin halaka?" Ta jefawa Dr chafa'atou tambayar

"Don Allah medicin kice ba haka bane.....kice kuskure kikayi......me nayi miki zaki jawomin wannan
abun?,ta yaya zan iya haihuwa?,kinga cikina fa dan qarami ne amma kike cewa wai ciki ne dani?" Ta sake
fada tana sakin Dr chafa'atou,sannan taja da baya da wani irin hanzari tana tattare rigar jikinta har
saman qirjinta,plate tummy dinta wanda ke shafe hade da bayanta ya bayyana. Daga jajayen idanunta
tayi tana maida dubanta ga Dr chafa'atou dake tsaye tana karantar yadda kwanyar sultana din ke shirim
birkicewa

"Kinga cikina?,ko plate din abinci daya bazan iya cinyewa.....amma kikayi qarya kikace ciki......." Bata
barta ta qarasa ba ta sanya dukka hannunta a tausashe ta jawo sultana cikin jikinta ta rungumeta tsam
"Kiyi haquri......wasa nake miki,kinyi qanqanta sultana,har yanzun ke yarinya ce" ta fada muryarta na
rawa,tsananin tausayin sultana yana taba zuciyarta yana ratsa jikinta.

Daga bibi har ama gaza riqe hawayensu sukayi. Hawayen tausayin sultana,ta yaya zata iya karbar
wannan qaddarar da qananun shekaru irin haka?,ta yaya zata iya fuskantar wannan qaddarar cikin
rayuwarta?,ya rayuwarta zata zama?,ciki a shekarun da duka duka basufi sha uku zuwa sha hudu ba.

Sun jima a haka dakin tsit,bakajin komai sai sheshsheqar kukan sultana,wanda tun tanayi da
ragowar qarfin da ya ragewa jikinta har ya zama bata iya koda motsi saboda wani mahaukacin zazzabi da
yafi na baya daya sauko ya rafketa.

Cikin hanzari Dr chafa'atou ta fara bata taimakon gaggawa don kada zafin zazzabin ya kaita ga
convulsion musamman da yake ba ita kadai bace,zazzabin zai iya zama illa ga abinda ke mahaifarta,duk
da cewa ta lura har yanzu bibi ko kadan bata yarda da abinda ta gaya musu ba.

Kimanin awa daya kafin bacci ya dauketa,don Dr chafa'atou ta sanya ruwan allurar bacci cikin
ruwan,saboda a yanayin da take ciki yanzu bacci ne kawai maslaha.

"Zan wuce,Allah ya bata lafiya,saidai koda baki yarda da abinda na fada ba yana da kyau a kula da
lafiyarta,a sake gujewa sanyata damuwa" tayi musu taqaitaccen bayani dukansu da ama da bibi din.

Qwaqwwaran motsi aka rasa wanda zaiyi a cikinsu,ta tafi ta barsu da tarin tunane tunane qulle
qulle da kuma kwancewa. Ita dai ama bata da abinda zata iya cewa bibi,maina ya tafi ya barta da dukkan
wani nauyi da kuma kunya. Yayin da Bibi take juya maganar Dr chafa'atou wadda take jinta kamar a
duniyar mafarki.

Shigowar aba dakin shi da goumar shi ya katse shurun da yake wanzuwa a dakin tsahon wani
lokaci. Dukka suka daga kai suna amsa sallamar tasa yayin da nashi idanun suke kan ledar ruwan dake
shiga jikin sultana.
"Dama bata da lafiya?" Yayi tambayar wa bibi. Da qyar ta iya buda fatar bakinta guda biyu tana gyara
qafafunta da sukayi tsami

"Dazune kawai bayan fitarta makaranta"

"Subhanallah" aba ya furta bayan ya isa gaban gadon yana taba temperature na jikinta wadda ta fara
sauka

"Allah ya sawwaqe ya taqaita gaba......amma ba damuwa bace har yanzu a ranta bibi?" Ya sake yin
tambayar yana waiwayowa hadi da duban bibi.

Kai ta girgiza da qyar kamar me ciwon wuya alamun a'ah

"Wannan abinda ke damun nata a yanzun yafi qarfin damuwa muddin abinda Dr chafa'atou ta fadi
gaskiya ne......muddin abinda tace yana damun nata da gaske ne dukkanmu muna cikin tashin hankalin
da bamusan inda zamu ajeshi ba,bakuma musan da wanne ido mutane wadanda basusan sultana matar
maina bane zasu kallemu" tamkar an doke masa gwiwa haka yaji,sai ya qaraso gaban bibi din ya zauna
sosai saman qafarsa yana kallonta. Tun daga zuciya zuwa ruhinsa addu'a yakeyi, ubangiji yasa ko meye
kunnuwansa zasu jiye masa yanzu su jiye masa sassauqar qaddara

"Ya salam.......wani mummunan ciwo ya shafa mata?" Tambayar da yayin sai data motsa ran ama. Tayi
qasa da kanta tana jin babu dadi,yaronta kamammen mutum ne wanda tsahon zamanshi dasu ko sau
daya basu taba gani ko jin labarin ya tsaida yarinyar kowa bama,amma me yasa tunanin aba koda yaushe
ke zarga masa mummunan zato game da maina din?,dan cikinsa?,me matuqar masa biyayya?,don kawai
Allah ya kawo tsausayin faruwar wannan abun?.

"Ba ciwo bane,juna biyu gareta wai" qas aba yayi da kansa zuciyarsa na cika da wasi wasi. Ko kusa ko
alama baiyi tunani ko tsammanin jin haka ba. Maganar shima sai tayi masa nauyi,bakinsa kuma ya
sarqafe ya kasa furta komai.
"Inaso gobe ni dakai da ita muje wani asibitin a sake gwadata,don inason sanin gaskiyar batun" ta fadi
da alamun da gaske take maganar tun daga zuciyarta har harshenta

"In sha Allah".

Dukka sauran maganganun ama tana ji batace komai ba,nata tunanin yayi nisa ne kan yadda
rayuwa zata kasance a garesu gaba daya. Batasan ME GOBE TA TANADAR MUSU BA.... BATASAN ME
K'ADDARA TA AJIYE MA GOBENSU BA......yadai tabbata GUDUN K'ADDARA GUZURIN TADDATA CE.......

**********Dogon lallashi wayo da dabaru tayi kafin ta samu nasarar da sultana tayi wanka. Ta tabbatar
a yadda jiya aba ya kwana da zancan cikin ranshi zaiyi wuya basuyi fitar safiya da ita yawon gwadata ba.

Breakfast me kyau kamar kullum ta shirya mata da kanta. Ta sameta zaune tsakiyar gadon. Gaba
daya ta jeme ta lalace,tun daga wancan lokacin sultana bata sake kyawun gani ba,ta firje ta
firgice,tsakanin jiya zuwa yau kuma gaba daya ta sake zama kamar wata susutacciya.

Da kanta ta zauna ta fara bata breakfast din bayan ta sha kanta. Saidai loma daya kacal ta fara
kelayowa ama amai kamar me shirin amayar da dukka kayan cikinta. Hankalin ama din ya tashi qwarai
ganin yadda take maida numfashi kamar wanda ke shirin qwace mata. Ita ta gyara wajen tas ta kuma
gyara mata jikinta,sannan ta sauya mata wasu kayan.

Zaune tayi kawai gaban sultanar wadda keta rera kuka da galabaitacciyar muryarta. Abinda
takeji din tunda aka haifeta bata taba jin makamancinsa ba,wani irin ciwo takeji da rashin dadi da
sukuni,dukka duniyar takejin ta mata wani irin zafi kamar ma ta mutu ta huta,ba abinda takeso,babu
kuma abinda yake burgeta.

Sau uku tana bude bakinta da zummar baiwa sultana haquri sai kuma taga na meye?,me zata
cema sultana din?,babu wata kalma a yanzu da zata gayawa sultana da zata cire mata radadin da takeji
yanzu a qirjinta. Laulayin cikin ba qaramar masifa bace ga duk macen da Allah ya jarabceta dashi. Inda
idanun bibi a bude suke bata makance da son jin akasin gaskiya ba tana tunanin yaci ace ta fahimci da
gaske ciki ne da sultana. Jiya bayan duk sun fice sun barta daga ita sai ita ta qarewa sultanar kallo. Komai
nata ya canza,hatta qirjinta da suke matasa zuwa yanzu sun fara cikowa,abinda dukkansu suka makance
idanuwansu basukai ga ganinsu ba. Dukkansu ubangiji ya kauda hankalinsu daga ganin wannan,sai a
yanzu da yaga dama ya bayyana abinsa.

Saddi ne ya shigo a hankali idanunsa akan fuskar sultanan. Shi kansa mugun tausayinta
yakeji,yakan kuma tambayi kansa kuma ME YA MAINA YAYI MATA NE WAI?,ME YASA YAYI MATA
ABINDA YASAN BATASO?.

"Aba yace sultana ta fito" kai ta daga ta kalleshi

"Kace masa gata nan zuwa,zataci abinci ne" amsawa yayi ya juya ya fita. Shuru tayi tana tunanin me zata
bata?,kaf tunaninta a yanzun bawai gudu yakeyi ba,batasan me zata bawa 'yar marainiyar Allahn da zai
riqeta ba. Wani tunani ne ya fado mata,ta tuna abinda nafessa tafi yawanci sanda tana da cikinta,may be
idan tayi gado itama ta iya ci din.

Cikin mintuna ta kammala ta dawo ta sameta,har yanxu kukan takeyi da wani irin rashin kuzari.

"Taso kiji sultana" ama ta fadi tana zama kusa da ita tare da dagota. Sanda takai spoon din kusa da
bakinta kai ta girgiza tana kauda kai

"Don Allah ba don ni ba ki karba" karon farko da ama tayi mata magiya tsahon tarayyarsu,sai taji
nauyinta ya kamata. Hidima take mata tsahon dare da wuni,duk da tarin 'yan aikin dake sassanta amma
ta maida hidimarta saman wuyanta kamar yadda hidimar aba ta zame mata dole,batajin koda su saddi
da suka fito daga tsatsonta sun samu nau'in kulawar da take samu cikin wata ukun daga wajen
ama,wannan ya sanyata bude bakinta zuciyarta na mata nauyi.

Batayi tunanin ko Loma biyu zata karba ba,amma sai gashi har takai biyar,ata shida ta kauda
kanta hawaye naci gaba da tsartuwa daga idanunta. Ko iya hakan da taci ya yiwa ama dadi,tasan dai
aqalla dai ba za'a ce babu komai cikin cikinta ba.
Hijabi me kyau a tsaftace ta fiddawa sultana,ta sanya mata sannan ta bata takalmi ta saka ta
sakata a gaba zuwa parking lot na gidan.

Acan ta samu oncle bashar oncle umar da matansu. Batace komai ba ta budawa sultana bayan
motar inda bibi ke zaune ta sakata

"Duk inda kikaji kin gaji ki samu waje ki zauna har sai jikinki da yanayinki ya daidaita" abinda ta cewa
sultana kenan kawai ta juya tana barin wajen ba tare da tace da kowa komai ba,ba kuma tare da tayi
tayin binsu din ba,saboda tasan yawo ne kawai zasuyi tare da batawa kansu lokaci.

Abu daya data sani shine,ko kadan a zuciyarta bataji tana qyamatar cikin da sultana ta samu
ba,bata kuma ji baqinciki ba,kawai dai ta razana da jin sakamakon......tana kuma tsananin tausayin
sultana da ciki a qarancin shekarunta.

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_**H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 17

Tunda ta koma ciki wayarta ke hannunta,sai tayi kaman zata kira bibi ko aba din sai ta fasa. Haka
kawai takejin zafin yadda suka dauki abun da zafi suka girmameshi haka,a nata zaton yau ko fyaden da
babu aure maina ya yiwa sultana,sannan har rabo ya shigo ciki,tayi zaton zasu karbi abun da sunan
qaddara,su kuma rufa abun don yiwa juna halacci da kuma kyautata alaqar juna tare da girmama tsatso.

Daga qarshe data gaji da kai kawon da bashi da amfani sai kawai ta shiga kitchen da kanta. Dukka
masu aikinta suna ciki,kowacce na hidimar da take alhakinta ce. Cikin girmama suka matsa suna bata
hanya. Bilki ce ta fara tambayarta

"Ko akwai abinda kike buqata?" Kai ta girgiza


"Ba komai,zan dan gwada wasu qananun abinci ne ko za'a dace sultana ta samu wanda zata iya ci a ciki
kafin su dawo" . Bata bawa kowa aiki ba,tace dai kowa yaci gaba da aikin dake gabansa.

Tana aikin amma sam ko qananun hirarrakin dasu bilki keyi a tsakaninsu bata iya
tantancewa,saboda tsabar nisan da tunaninta yayi. INA MAINA YA TAFI?,wasa wasa kwanaki nisa suke
suna kuma jirkicewa zuwa watanni,a ina yake?,ina yaje?. Ba qaramin damunta abun yakeyi ba cikin rai,a
duk sanda ta sanya haqarqarinta a qasa zata kwanta maina dinne yake soma fado mata. Abinda ta lura
ko sau daya aba bai taba tada maganarsa ba,sau biyu oncle umar da oncle bashar suna masa maganar
sai yace dasu

"Ai ba yaro bane shi,ya fita sahun yara ko samari,magidanci ne yanzu,duk inda yaje ma zai dawo da
qafafunsa,bani da lokacin bata lokaci wajen nemansa" itadinma ko sau dayan batayi gangancin masa
maganar ba,tana iya nata qoqarinne kawai a bangarenta wajen samun koda labarin inda yake.

Shuru office din likita na uku da suka ziyarta a ranar yayi. Asibiti na qarshe da dukkansu sukayi
yaqinin ba inda za'a gaya musu sama da abinda zasu gaya musun,saboda qwarewa da ingancin asibitin
da har takai bayan ainihin asibitinsu Dr chafa'atou shine asibiti na biyu da ya samu lambar yabo daga
qasar France,suke kuma da qwararrun likitoci da wasunsu 'yan asalin qasar France dinne.

Kanta na kwance saman kafadar bibi tana wani irin kuka kamar numfashinta zai dauke. Aba
dake zaune ya gaza cewa komai,saidai dukka hankalinsa yana kan mahaifiyarsa saboda dimbin tashin
hankalin da ya gani saman fuskarta. Shekarunta sun fara jaa,yana tsoron kada wani ciwon ya sarqafeta.

"Wannan kukan da takeyi yayi yawa,yanzu haka da na duba awon jininta,jininta ya hau daga qa'idar
yadda ya kamata ya kasance,tana buqatar kulawa ta musamman,saboda shekarunta sunyi qanqanta
qwarai da iya rainon juna biyu,muddin anason ta rayu lafiya ita da abinda yake cikinta dole a kula da
damuwarta" kai bibi ta girgiza

"Ba zamu taba iya hanata wannan kukan ba.....mu dinma inda da hali barin namu idaniyar zamuyi ta
zubda qwalla....... abu daya kawai na sani......bazan bari rayuwarta ta galabaita ba muddin ina numfashi"
bibi ta fada da qwarin gwiwa.
"Yanzun zamu dan riqeta saboda tana da buqatar kulawar likita gaskiya qwarai da gaske,zamu sanya
mata ruwa saboda jikinta babu isashen ruwa,sannan hawan da jininta yayi ma banajin yana da kyau a
qyaleta ta tafi gida,akwai gwaje gwaje da dukka za'a yi mata a ajjiye koda buqatar gaggawa zata taso".
Yana kaiwa nan nurse din ta shigo cikin harshen faransanci take gaya masa sun gama shirya komai

"Ku rakata dakin" ya fadi yana hada tarkacensa dake saman table din.

Tashin hankalin da takeji ya zarta duk yadda zata misalta. Sanda ta miqe nurse din ta kama
hannunta sai taji ba zata iya sakin hannun bibi ba,a hankali taji idanunta sun soma rage kaifin
ganinsu,wanda guda dayan da aka yi mata glasses saboda shi zuwa sannan ya sake samun raunin gani
sosai sakamakon hawayen da take wuni ta kwana tana zubdawa. Babu wata ranar banza a gareta da zata
fito har ta fadi hawaye basu fita daga idanunta ba.

"Muje ko?" Nurse din ta fadi cikin kwantar da murya. Qoqari take taga ta taka amma sai taji qafafunta
kamar an riqesu,qirjinta kamar an aza masa wasu kaya masu nauyi,kanta kamar an daketa da wani
qaqqarfan abu,duhu kuma ya soma mamaye hasken tarwai da office din yake dashi,ba tare data shirya
ba hannayenta suka zame daga cikin na bibi,babu abinda taji sai salatin bibi da wani irin qaqqarfan sauti.

**********Tamkar wadda ake tasa daga bacci ta soma bude idanunta,wanda tun kafin takai ga gama
bude idon gaba daya ta danji muryoyin qasa qasa. Sannu a hankali ta gama bude qwayoyin idanunta,fes
suka sauka cikin dakin.

Mutum biyu ne zaune gaban kujeru ukun dake gaban gadon nata,sai kuma oncle umar da oncle
bashar dake tsaye daga saman kanta. Saitin qafafunta kuma mamma kausara ce(qanwa ga mahaifinta
hamani uwa daya uba daya).

Kusan kowa yunqurin mata sannu yakeyi,yayin da ama da mamma kausara suka matso suna
qoqarin tadata zaune ganin tana mutsu mutsu

"Dole ki gaji,kwanciya ace tun jiya?" Ta danji mamaki cikin ranta,to amma kuma a yanzun ita duka ba
wannan bane gabanta ba.
Duk sai da suka gama mata sannu da jiki sannan ama ta kawo ruwa ta bata. Tasha da yawa
sosai,sannan ta kamata ta sauko da ita zuwa bandaki

"Kiyi wanka kizo ki rama sallolin da ake binki ko da a zaune ne" ama din ta fada.

Tayi wankan ta kuma rama kuma sallolin,saidai daga haka ba abinda ta iya qara yi,tana daga
zaune saman abun sallar kawai. Ita ba tunani ba ita ba bacci ba, hakanan ita ba ido biyu ba,a haka
'yammatan gidan sa'anninta sukayi sallama suka shigo.

Aminata,yasmine,najma almu sai atta biye dasu. Sai da suka gama gaida iyayensun sannan suka
qaraso inda take zaunen. Zagayeta sukayi kowa yana mata sannu cikin nuna kulawa da qauna ta 'yan
uwantaka.

Banda kalmar DA SAUQI ba abinda ta iya sake furtawa. Da idanu kawai take binsu wani abu
yana kai kawo cikin zuciyarta,sai kawai ta hade qaffaunta waje guda tana cusa kanta tsakanin
cinyoyinta,don kuka take da buqatar ta sakeyi. Wannan kukan batasan yaushe zata daina yinsa ba tsayin
rayuwarta,su aminata sha'awa suke bata,tana jin dama itace su,su dinma kamar haka rayuwarta take a
baya ba?,tashi daya zallar zalunci irin na maina ya kutsa rayuwartata ya wargaza mata komai ds komai,ya
rusa farincikinta da walwalarta,yayi rugu rugu da mafarkinta,a yanzun bata da wani sauran mafarki ko
buri na rayuwa,tana jin rayuwarta dai dai take da fanko,tana kunyar kallon idanun su aminata su hanan
da sauran qawayenta su ganta dauke da wani abu waishi CIKI!,cikin da suke gani jikin yayyensu?,cikin da
suke ganin jikin iyayensu?. Batasan ya akayi sautin kukanta ya fita ba,saiji tayi su yasmine suna rungume
da ita suna bata haquri,dukka muryoyinsu suma a karye,abinda ya sanya bibi miqewa kawai ta fice a
dakin.

**********Dukkan iya abinda likitoci zasu yi mata na taimakon da ya dace sun bata,saidai kuma jigon
samun sauqinta yadda ake da buqata yana hannunta.

Nutsuwa kwanciyar hankali da taqaita damuwa,abubuwa ne kuma da zasuyi wuyar gaske ace an
samesu daga wajenta a yadda take ciki a wannan lokacin.

Wani irin matsanancin laulayi mai matuqar azabtar da ruhi da gangar jiki. Ta fita hayyacinta
ainun,tayi wata irin rama da bata taba kwatankwacinta ba,har takai jallin da dukka suturunta sunyi mata
yawa basa sanyuwa a jikinta. Bata iya cin komai,hakanan bata iya shan komai,kusan qarin ruwa shine
abinda akafi yi mata duk bayan kwana biyu saboda samarwa jikinta abinci.

Wannan yanayin ya daga hankalin bibi matuqa,ta dinga jin kamar lokacin da zata rasa sultana
ne yayi,kaman yadda ta rasa MOHMOUD ta rasa BINTOU ta kuma rasa NAFESSA. Wannan tunanin yayi
matuqar razanata,ya kuma sanyata tattara dukka 'ya'yanta harma da ama da kuma mamma kausara ta
shaida musu hukuncin da ta yanke ba kuma tare da neman shawararsu ba. Shawarar da take ganin ita
daya ce MAFITA,ita kadai ce kuma hanya ta yankewa wannan AZABA da sultana ke sha, sa'annan qilan ta
zama silar warwarewar bakin zaren komai.

*******A ranar data nemesun ta shaida zamanne bayan sallar isha'i. Cikin daya daga cikin falukanta
masu kyau da tsari,wanda sam basu cika girma ba,sannan bata fiya wani zama cikinsu ba saboda ba falo
bane dake a farko farkon sassanta ba.

Ama ce qarshen shigowa,sai data tsaya ta tabbatar abu me ruwa ruwa ya shiga cikin sultanan
bayan wunin da tayi a wunin yau sur bata sanya komai a cikinta ba,sai uban amai da ya galabaitar da ita
liqis. Duk sanda ta tashi da rikicewar yanayi irin hakan wuni ama din takeyi itama cikin tashin hankali.
Tuntuni ta sauke dukka wasu harkokin business dinta ta damqawa wasu daga cikin mataimakanta,sai
kuma saddi da yake yaayan atta da almu data dora masa wani nauyin shima,duk kuwa da cewa
shekarunsa ba wasu masu yawa bane,duka duka sha bakwai yake amma lalura ta sanya dole ta fara
dorashi bisa hanya.

Ta samu tasha oat da madara dan qaramin cup da baifi cup din yaro dan yaye ba,saidai duk da
haka ama murna takeyi da ya zauna acikinta har ma bacci ya dauketa.

Tun jiya da bibi ta shigo wajen sultana,ta kuma buqaci ama ta basu waje zasuyi magana taji
hankalinta bai kwanta ba. Duk wani kuka da damuwa da take ciki babu shi daga jiya zuwa yau din,sai
laulayin kadai dake hanata sukuni. Maganar qarshe da taji bibi na fada bayan ta dawo canzawa sultana
beadsheet ta tsaya mata a rai,ta kuma dinga juyata cikin ranta. Ta qure dukka maqurar tunaninta wajen
son gano abinda maganar ke nufi,amma mahanga daya kwanyarta ke kaita,a ma'ana daya duk wani
ma'aunin fassara yake zuwar mata,ma'anar da taqi gamsuwa da ita,zuciyarta taqi aminta da hakan.
"Karki damu,kwana uku kawai zakiji sauqi ki koma rayuwa kamar 'yan uwanki,duk wani ciwo zai wuce"
to meye qarshen maganin laulayi haka da gaggawa?,laulayin da ba abu bane me yankewa yau ko gobe
ba?,har sai sanda rabbi ya dauke maka,ko kuma zuwa sanda ka haife abinda yake cikinka?.

Da sallama ta shiga falon,sai taga kamar dukka idanu sunyo kanta. Bata wani bada
muhimmanci ba ta qarasa daya daga cikin kujerun dake daura da aba,ta dauke filon kai ta zauna,ta kuma
gyara zamanta sosai tana fuskantarsu

*_Tofa!,taron na meye?,me karatu muje zuwa,akwai sauran tirka tirka_*

*_wai ina Aliyyu haidar ya shiga ne?,ko team SULTANA NE SUKAYI MASA KURCIYA?_*🫣🫣🫣

*HUGUMA CE*

*H U G U M A*

Book 02 page 18

"Tom,nasan dukkanku kuna mamakin abinda yasa na taraku a nan wajen?......a taqaice ba wani doguwar
magana bace me tsaho,sannan kuma ba shawara na taraku nayi daku ba,na kiraku ne don na shaida
muku,babu buqatar cikin dake jikin sultana a yanzu,saboda dukkaninmu munsan abinda likitoci suka fadi
gami da hatsarurrukan dake tattare da lafiyarta,kuma ita din munfi buqatarta akan abinda take dauke
dashi,saboda haka na yanke shawarar aje A CIRE CIKIN JIKINTA ma'ana A ZUBAR DASHI! don ta tsira da
rayuwa da lafiyarta" Dif dakin ya sake yi,kowa ya zubawa bibi idanu sona son gano wasa takeyi musu?,ko
tana fadin maganar ne da gaske.

Kaf dinsu babu wanda yaga digo ko alamun wasa tattare da bibi din, fuskarta ta sauya zuwa wani
yanayi da yake sanya musu shakka a duk sanda wani ya yunqura zaiyi jayayya da umarninta. Ba wanda
baiji saukar maganar har tsakiyar zuciyarsa ba. Kusan daqiqa uku kowa ya gaza tofa komai kafin daga
bisani oncle oumar ya motsa yana matsowa gaba kadan daga kan kujerar da yake zaune

"Amma bibi......" Hannu ta daga masa tana cewa

"Dakata oumar,ya isa,bana buqatar qarin bayanin kowa,inajin dukkaninku ba wanda yasan ciwon sultana
sama dani......."

"Sai kuma maina.....wanda shine yaci kashinta yaci fitsarinta,shine wankanta shine wankinta,tare suke
jinya kukanta nashi ne damuwarta tashi ce....... shine cikinsa yake a jikinta a yanzu.....cikinsa na halak ba
shege ba.....cikin da baya biya sadaki da albashinsa na dan makaranta.....shine cikin da ake cewa yanzu a
cireshi?" Ta qarashe maganar tana jefawa bibi tambaya

"Hamdiyya...... meye haka?,kinsan a gaban wa kike a tsaye?,kisan me zaki fadi......"

"Me zan fada?,me zan fada ma?,to ban qarasa ba.......indai nice mahaifiyar Aliyyu,kuma akwai haqqinsa
a wuyana,akwai kuma nawa haqqin a wuyansa.....ina fada da harshensa da nawa......ban yarda a fidda
abinda yake tare da sultana ba,ban yarda ba har abada........!" Saita qarashe da wani kukan da bata
shiryawa ba ya kufce mata,sai ta juya da gudu gudu sauri sauri tana fita daga falon,tana jin qirjinta yana
mata nauyi,wani abu ya tokare mata qirjinta.

A gurguje a gurguje ta dinga ratsa farfajiyar gidan har ta isa sassanta. Can cikin dakinta ta yiwa
kanta masauki,ta zube daga bakin gado a qasa kuka yana qwace mata.

Shin ta yaya?,ta yaya ma zata bari a zubda cikin aliyyu?,da wanne dalili zata bari hakan ta
faru?,koda cikin shege bare na halak?,idan su dukka tunaninsu ya toshe hankalinsu ya gushe da soyayyar
sultana don kawai su sama mata mafita to ita din tana a dai dai cikin hayyacinta.

Tayi kukan data jima batayi irinsa ba,ta kuma jima a nan zaune tana tunanin hanyar ra zata
hana faruwar abinda bibi ta qudurta. Ta sani ta kuma yankewa ranta ko a mutu ko ayi rai,koda igiyar
aurenta zata girgiza ba zata taba bari wannan abun ya faru ba.
Sanda ta kalli agogo sai ya nuna mata qarfe biyu da rabi na dare. Ta share sauran qwallar da
suka rage mata cikin idanunta tana miqewa. Mafita guda daya ce yanzu tak ta rage mata ta amintar da
sultana takuma sauketa daga doron amincewar da bibi ta sanyata tayi kan a zubda cikin.

Bandaki ta nufa ta daura alwala saboda ta samu sassaucin abinda takeji tsakiyar qirjinta,sannan
ta fito ta dauki medium veil me santsi mahadin rigar jikinta ta yane kanta,ta jawo wayarta ta kunna data
sannan ta nufi qofa ta buda a nutse ta fice a dakin.

Sau daya tak ta murda qofar dakin ta bude,saita tura a hankali tana shigewa. Fitilar gefan gado
ne kawai a kunne,saman gadon kuma babu kowa alamun sultana din ta tashi,sai ta zauna saman sofa
bed din dake daura da ita tana jiyo motsin ruwa a bandaki,sai ta tattara hankalinta akan wayar tana ci
gaba da research kan abinda take da buqatar

A nutse ta kammala fitsarin tayi tsarki,saita matsa gaban wall mirror dake jikin bandakin,ta
murda famfo ta wanke fuskarta da kyau,bayan ta gama taja qaramin towel ta soma goge fuskarta,a
sannan ne idanunta suka fada kan fuskarta data fito tarwai ta cikin madubin kamar rana saboda wadatar
haske da bandakin yake dashi.

A hankali take qarewa fuskartata kallo,fuskar da aqalla ta dauki watanni sama da uku rabon data
kalleta. Lumshe idanunta tayi tana jin ciwon yadda dukka kamanninta suka canza,ta sanya hannu a
hankali ta shafa gefan idonta da har yanzu akwai sauran tabo na bahagon marin da ya kaiwa fuskarta har
ya zame ma idanunta illa. Janye hannun tayi tana jin wata irin mahaukaciyar tsanarsa tana ambaliya cikin
zuciyarta,nau'in tsanar da tunda tazo duniya bata taba jin digo ko kwatankwacinta cikin ranta game da
wata halitta ba.

A hankali sai kuma takai hannunta saman shafaffen cikinta. Itakam har yanzu bata yarda da
zancan wai ciki gareta ba,bataji cikinta ya dago ba,bataga ya qara girman komai ba,hakanan batajin
komai banda qinson cin abinci da dan banzan fitsari da take yawaita tashi cikin dare,sai kuma rashin
lafiyar da ai ita dai tasan normal ne kowa yana iya cuta.

Kamar kuwa jira akeyi takai qarshen tunanin nata taji wani abu ya harba sau biyu a marartata
kwatankwacin bugun zuciya. Ta miqa hannu da sauri dai dai gurin ta danne tana zare ido tare da saka
ran sake jin wani abu. Saidai kuma tsayin sakanni shuru bataji komai ba,wannan ya sanya ta saki hannun
nata hawaye na cika mata idanuwa.

Indai da gaske ne cikinne ita wallahi babu abinda zatayi dashi,d'an maina ne fa kenan ko?,ita zata
haifawa baqin mugu azzalumi yaro?,sun hada jini kenan kamar yadda taji ana fada?,Allah ya kiyaye ya
kuma sawwaqe ta hada jini da maina,la shakka shawarar bibi itace dai dai,bibi din masoyiya ce ta
gaske,wadd bata qaunar kukanta ko damuwarta,batason dukkan wani abu da zai zamewa rayuwarta
barazana,tsahon shekaru tana akan haka. Towel din ta maida cikin zafi tana jin cewa gari yana wayewa
zata buqaci bibi ta kaita a cire d'an aliyyu daga jikinta,ta tako da kuzarinta daga bandakin tana fitowa.

Tsaiwa tayi daga bakin qofar cikin mamaki tana kallon ama wadda ke zaune sosai cikin dakin,ta
kuma qarawa dakin haske da qwayaye biyu dake manne a bango gudun kada sultana din ta tsorata.
Idanu ta daga daga inda take zaunen tana duban sultanar,sai ta gyara zamanta tana cewa

"Qaraso ciki,nazo dubaki ne na tarar bakya ciki" sakin qofar tayi tana takowa cikin dakin,har cikin ranta
tana jinjina tsantsar kulawar da ama ke bata,ta yadda da wannan dari bisa dari, kowanne motsinta ama
na dame dashi,ko yaya kuma ta sauya tana riga kowa fahimta ta kuma bi ba'asin matsalar ta maganta
mata.

Wayar hannun nata ta ajjiye bayan sultana din ta zauna tana dubanta

"Sultana,magana nazo muyi dake,ki nutsu sosai ki fahimceni kinji?" Kai ta gyada a hankali tana kallon
qwayoyin idanun ama

"Me yasa kikeso ki MUTU?" Ama ta jefa mata tambayar kai tsaye,tambayar data saka sultana zaro
fararen idanunta tana duban ama a rude

"Ni kuma ama?,ni nakeso na mutu?,banaso na mutu ama......"

"A'ah,qarya kikeyi,keda bibi duka so kukeyi ki mutu" sake rudewa tayi ainun,saboda kalmar mutuwar
girma take mata
"Allah a'ah ama,banaso"

"Amma kikeso a zubda miki ciki?,bakisan duk wadda aka zubarwa da ciki mutuwa takeyi ba?" Tsam tayi
tana duban ama hawayen nan nata da basu da wuyar fita tana zartowa daga idanunta. Tsaf ama ta
karanceta,da alama abu ya fara tabata,saita dora da cewa

"Ungo wannan ki gani,ki kuma karanta,adadin mata nawa ne suka mutu duk akan silar zubda ciki" hannu
tasa ta karba din,ta shiga folder din da ama ta shirya komai ta soma kalla wani kuma ta karanta bayanan
da suke da harshen France.

Bata iya qarasawa ba cikin matuqar tsoro da razani ta miqawa ama wayar hannunta yana
rawa,ama tasa hannu ta karba tana dorawa da cewa

"Dukansu KARUWAI ne sultana, ba'a daura musu aure da ubannin masu cikin ba,me zai kaiki layin
karuwai?,don kawai kin tsani MAINA......"

".......ama don Allah,daina kiran sunansa" ta fadi da sautin kuka sosai,tana jin mafitar da take hango
qofarta a bude qofar ta ida rufewa ruf,gaba kura baya sayaki,ashe sauqin da take hasashen samu babu
shi,ta tsorata da irin bayanan data gani,itakam ya za'a yi taso ta mutu haka?,da irin wadannan shekarun
qanana?.

"Na daina kiran sunansa sultana,kiyi haquri......amma.......ki share hawayenki,ki kuma bani aron
hankalinki nan" shuru ya ratsa dakin na wasu mintuna sultana na qoqarin saisaita kanta sannan tadan
samu 'yar qaramar nutsuwa

"Kin yarda bakison ki mutu?" Ama ta tambayi sultana. Da sauri ta daga mata kai

"Amma tunda bibi tayi zancan bansan ta yadda zance mata kada a zubar ba"
"Ni nasan yadda zan hana haka faruwa don banason ki mutu,abinda nakeso kawai shine,kibar cikin ki
haihu,zan karbi ko meye kika haifa ke kuma kiyi tafiyarki kiyi rayuwarki babu me takuraki,kinga shikenan
babu ke ba mutuwa"

"Amma wajen haihuwar ai ake mutuwa ama" ta fada da sautin quruciya fal muryarta

"Inji wa?,inda haka ne suk da bamu haifeku ba ai ko?,waye a cikin gidannan kika taba gani ya mutu don
zai haihu?" Shuru tayi tana son tunawa. Babu,babu wadda ta gani ko ta sani iya wayonta da akace ta
mutu wajen haihuwa,amma wajen zubda ciki kuwa gasunan yanzun ta gansu da idonta bila adadin.

"Kin yarda zakibi dukka tsarina ni kuma na tsallakar dake daga fadawa mutuwa?" Duk wanda zai kauda
maka mutuwa aiba abun gudu bane,bare ama din da zuwa yanzu take jinta kamar mahaifiyar data
haifeta,don haka ta gyada mata kai

"Da kyau,amma abinda nakeso fa dake shine,kada ki gayawa kowa wannan maganar da mukayi dake
kinji ko?,idan ba haka ba zasu daukeki sukaiki gun cirewa da wurwuri kafin na gama nawa tsarin"

"To ama"

"Yayi kyau,maza kwanta sai da safe,kada kuma kiqiyin bacci kinji ko?komai zai wuce in sha Allah" Kai ta
jinjina mata. Ama bata bar dakin ba sai data tabbatar ta kwanta,ta kuma lullubeta ruf sannan ta kunna
mata karatun qur'ani da madaidaiciyar qira'a ta kashe hasken dakin sannan ta fice.

A daren bata kwanta ba sai data ci rabin plan dinta,don tana ganin tana kwanciya kamar lokaci
zai qure mata,don bata da isashen lokacin gama komai da komai da takeso.

*_KWANKWASON JIMINA_*
*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*
09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 19

A daya daren kuma ta kammala shirinta gaba daya,cikin daren da kowanne ya kwanta a cikin
gidan,daren da suke sanya ran washegarin safiyar ranar za'a fita da sultana a zare tayin cikin......a daren
ta shammaci kowa a cikinsu,harda 'ya'yan cikinta saddi da almu,a daren dai ta fice daga gidan,ITA TANJA
DA SULTANA ba tare da sani ko ankarewar kowa ba.

K'arfe sha biyu na daren ranar amma tamkar rana ce cikin zuciyar ama. Mace mai kamar maza
wanda ko sau daya tun daga quruciya zuwa girma zuciyarta batasan karaya ko tsoro ba. Ita ke tuqa
motar da hannuwanta ba tare data dorawa kowa nauyin tuqata ba bare a buqaci sanin ina ya kaisu?.

Gudu kawai take shimfidawa cikin lafiyayyar motar tata,sultana na bacci abinta lakadan a
baya,tanja na zaune daga gefan ama din tana rarraba idanu. Har yanzu cikin fargaba ita take,ga tsoron
daren da suke ketawa saman shimfidaddiyar kwaltar da zata sadaka har cikin qasar nigeria.
"Ki saki jikinki tanja,ba abinda zai biyo baya sai alkhairi,ba kuma abinda zaya faru" ama ta fadi idanunta
nakan kwalta data cika da full light na fitilun motar masu tsananin haske. Ajiyar zuciya ta saki tana gyara
zamanta

"Amma hajiya,bakya tunanin dole zasu bibiyi inda muke?"

"Ta yaya?,na cire duka layukan wayata,sannan koda yayyena da muke uwa daya uba daya basusan inda
na nufa ba,tanja......zan iya sadaukar da komai nawa saboda na kubutar da cikin maina......zan iya
sadaukar da numfashina dama rayuwarta,JINI NA NE......jinin maina ne" ta fada zuciyarta na
tsinkewa,rauni yana son saukar mata don batasan a nahiyar da mainan yake ba,bata kuma san a wacce
duniya yake ba a yanzun.

Dai dai sanda saqonta ke sauka ga wayoyin dukkan mutanen dake da muhimmanci a gareta,suka
kuma cancanci tayi musu bankwana dai dai lokacin tayoyin motocinta ke shiga qasar KANO. ta zabi kano
dinne saboda tasan zaiyi wuya hankali yakai can,asalima ta zabi kano ta zama hanyar fitarta daga nijer da
nigeria din gaba daya, saboda batasan kowa ba acan,basu da kowa ballantana a samu fargabar wani da
suka sani ya gansu.

Ba bata lokaci tabi cikakken kwatancen da dillalin data kama hayar gidan na sati biyu a
hannunsa ya turo mata. Cikin kwanciyar hankali ba tare da kuskure ko batan kai ba sai gasu sun isa qofar
gidan dake jerin rukunin gidajen SHARADA NNDC QUATERS.

"Alhamdulillah,alhamdulillah,allahumma inni as'alukal birru wattaqwa" ama ta furta tana zare belt din
jikinta sannan ta buda murfin motar tana fita.

Seat din baya ta bude,sultana dake zaune kawai ba tare da sanin ainihin meke faruwa da ita ba ta
daga kai suka hada ido da ama. Murmushi ama ta sakar mata

"Sannu daughter,fito mu shiga ciki ki huta" tayi maganar da sakakken murmushi akan fuskarta hadi da
miqa mata hannunta. Ba musu ta kama hannun aman ta fito da ita,sai ta miqawa tanja key tana cewa
"Ki bude ku shiga ciki,zan daidaita parking motar sai na biyoku". A ladabce tanja ta karba,tana gaba
sultana dake takawa da qyar tana biye da ita,don bata tana kusan doguwar tafiya irin haka a mota ba.
Duk inda zasu muddin yanabda airport to tabbas jirgi zasubi suje su dawo,zata iya cewa wannan shine
karon farko data taba shigowa nigeria ta mota.

⚜️⚜️Ya sani har ya kwanta bacci bata shigo dakin ba,to amma yayi tsammanin taras da ita bayan ya farka
sallar asuba amma sai yaga lokacinma wayam. Yayi tsammani dukka fushi takeyi dashi akan maganar da
Bibi tun ta shekaran jiya,to amma shi ya dauka zata yi masa uzuri,ta dauki bibi a mizanin mahaifiya
wadda bazai iya musanta mata ba,saidai yayi mata gyaran kusakuranta cikin hikima idan buqatar hakan
ta taso. To a lokaci irin wannan,matsalar sultana da maina matsala ce me matuqar sarqaqiya,dukkaninsu
daga maina har sultana babu wani wanda zaiqi a cikinsu,babu kuma wanda bayaso,saidai dole yayi kaffa
kaffa game da duk lamarin da ya shafi maina,saboda gudun son zuciya ya shigo ciki,ko kuma duniya tayi
masa kallon maras adalci meson kansa da d'ansa,dole ya sanya buqatun sultana da maslaharta a gaba
data maina,kodon maraicinta.

Bayan ya gama addu'o'insa ya jawo wayarsa da zummar kiran ama din ya nuna mata kulawa ko
yaya ne,ko ba komai ita din uwa ce,itama tana jin yadda kowa yakeji a ransa game da d'ansa,saidai kuma
saukar saqon da sunanta saman screen din wayarsa ya katse masa dukka wani hanzari nasa.

_amincin Allah ya tabbata a gareka,nayi imani a sanda saqonnan zai riskeka tuni na jima da yi muku nisa
ni da d'iyata kuma surukata,inason shaida maka cewa munyi nisa ni da ita domin tseratar da abun
farautarku,nisan da banajin nemanku zai iya cimmana,ina rubuta maka wannan saqonne don baka zabi
guda biyu......ko ka jirani har na dawo daga balaguron tseratar da rai nayi.....ko ka sawwaqe igiyar
aurenka dake kaina idan kaji ba zaka iya zaman jiran hamdiyya ba,ga yarana nan zasu iya kulawa da
kansu na sani haqiqa.......ina muku fatan alkhairi......ina kuma fatan saduwarmu ta gaba ta zama da
alkhairi,bissalam_.

Hannunsa ya sanya ya sharce gumin dake goshinsa yana jin wani tashin hankali yana sauko
masa. Babu MAINA babu HAMDIYYA sannan kuma babu SULTANA gaba daya,duka cikin wat uku
kacal?,wannan wacce irin jarabawa ce haka ke tunkararsu?,wacce irin musiba ce haka?. Kaman an
mintsini aba sai ya miqe cikin hanzari,ko slippers din qafarsa bai maida ba cikin sassarfa ya nufi sashen
ama.
Loko da saqo na cikin sassan ya fara bincikewa kamar wani zautacce,kaf ya karade sannan ya
koma kewayen gidan ba ama ba dalilinta,sai ya sake komawa bedroom dinta a nan yaga shaida. Ta
kwashe duk wani abu nata me muhimmanci kamar yadda maina yayi. Haka dakin sultana an kwashe
kusan komai nata me muhimmanci,a farfajiyar gidan kuma da ya duba yaga babu motarta guda daya,a
nan ya saddaqar da cewa lallai abinda ta fada din da gaske ne.

Bai tsaya duba qarfe nawa ba a sannan ya soma dokawa abdulhakeem kira. Da alama yana
kusa da wayar,don bugu daya ya dauka. Abirkice aba ke tambayarsa hamdiyya ta iso?.

"Ta iso ina?" Ya tambayeshi cikin daurewar kai

"Don Allah idan ta iso kada ku bata dama ta sake fita ko ina"

"Akan me kake magana ne hamidou?,ina hamdiyya din tace zata je?,ina cewa ko jiya munyi waya tana
nan nijer,bata kuma cemin zata zo Nigeria ba" komawa da baya aba yayi ya zauna,sannan ya warwarewa
abdulhakeem komai.

Shi dinma ya rude,don har yanzu ana ju da auta,wanann gatan da soyayyar ba inda suka
je,musamman mutuwar iyayensu ya sanya sun sake dora mata gata

"Kada ka damu aba,muddin tana cikin Nigeria dinnan ba zata fita ko ina ba,zamu dubata kuma zamu
tabbatar ta dawo dakinta" abdulhakeem ya fadi cikin fargaba xa kaduwa,duk da yana boye hakan a zahiri
gudun sake jefa aba cikin wata damuwar.

Ya jima zaune a wajen,baisan ta yaya zai tunkari bibi yace mata ama ta dauke sultana ba, ba'a
san kuma ina suke ba,ina suka dosa?,sanda kuma zasu dawo din kwanaki ne da suka tasamma watanni
sha biyu qila harda doriya.

Yana wannan tunanin sai ga Omar kamar an jefoshi,wayarsa a hannu,ya tsaya gaban aba yana
miqa masa Wayar. Hannu ya sanya ya karba yana dubawa. Saqo ne dai daga hamdiyya tana dora ma
Omar din alhakin yiwa bibi bayani
_"Ka gaya mata Omar ta kwantar da hankalinta,nayi alqawarin dawo mata da sultana cikin aminci"_
wannan shine statement dinta na qarshe.........

⚜️Komai akwai cikin gidan,kusan ba abinda suka shiga dashi sai kayan sawarsu da ba wani masu yawa
ba,sai kuma kayan abincin gida da tayi order ta wani app suka iso gidan babu dadewa suka dire mata
komai.

Sai bayan magariba ta nutsu,wunin ranar suna dan gyare gyare cikin gidan ita da tanja,sultana
na baccin gajiya,zuwa magariba din har abincin dare tanja tayi,bayan sallar isha'i dukkansu suka hadu
cikin madaidaicin falon da duka duka baifi girman toilet din ama ba nacan nijer da kuma gidanta na nan
dake abuja ma.

Zuwa magariba tanja da ama sun kintsa gidan tsaf,duk kuwa da cewa bawai zama zasuyi ba
gaba zasu qara nan da wasu 'yan kwanaki amma ama ta tanadi komai da zasu buqata a kwanakin,ciki
harda abincin ci ruwan sha da drinks.

Zuwa magariba har girkin dare tanja ta gama. Ama na gama sallar magariba din ta fito falon tana
cewa tanja

"Shiga ki duba sultana,tun yamma data kwanta banji motsinta ba" ta fadi tana zama saman kujerar falon
hadi da kunna tv plasma din dake zaune saman TV stand.

Bata da wata sanayya da gidajen tv sosai,don ba ma'abociyar kallo bace,don haka tabar tv din
saman channel din dake haska labarai a dai dai lokacin.

Bata gama maida numfashinta ba tanja ta fito a dan rude

"Hajiya zazzabi ne ya saukarwa sultana fa,kuma irin me zafinnan da likita yayi magana akai" ajjiye wayar
hannunta da zuwa yanzu ta sauya layi zuwa na Nigeria,shima temporary ne,don dole tana da buqatarsa
wajen neman visa dinsu da kammala komai na tafiyarsu,uwa uba kuma ita din ma'abociyar hawa social
media ne duba labaran kasuwanci da sauran al'amuran da suka shafi rayuwa

"Subhanallah,ya salam,muje na gani" ama din ta fada hankalinta yana dan daguwa.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank
_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/05, 2:33 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*
*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107
*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[06/05, 5:17 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 20

Riris ta sami jikin nata,dole ta soma laluben asibiti dake kusa da GRA din ta hanyar taimakon
MAP. Allah ya taimaketa ta samu wani private hospital nan kusa dasu wanda ko a qafa ma kana iya
takawa.

Ta sani dama babu makawa,qarin ruwa ne dole shi za'a mata,saboda irin wannan zazzabin gaba
daya sanyawa yake lokaci daya ruwan jikinta yayi qasa. Nan gabanta suka kwana, tausayin sultanan yana
ratsa ama. Ta hadu da azababben laulayi me zafi,bata sani ba ko harda quruciya a ciki?.

Cikin taimakon Allah washegari taji qwarin jikinta sukayo gida.

Sai yamma sannan suka zauna cin abinci. Cakula abincin kawai takeyi,hankalin ama duka yana
kanta. Ta yaya wannan dan tayin dake manne da ita zai zama yadda akeso?,bayan kwata kwata bata
wani iya cin abinci?,duk irin lokacin da ama ke kashewa tayi mata nau'ikan abinci kala kala. Bata taba
damuwa da bata lokacin da takeyi ba,duk da aba kadai take kashewa lokacinta a
kitchen,aah.....damuwarta na rashin cin abincin sultana dinne.
Afakaice bayan rashin cin abincin ta karanci kamar akwai damuwa boye qarqashin zuciyarta,don
haka ta kirayi sunanta a hankali. Kai ta daga tana kallon ama da zugaggun idanunta da a yanzun kullum a
kode suke tasss kamar danyen nama

"Banason ganin wannan damuwar sultana,zan cika miki alqawarinki......zan maidaki wajen bibinki,zan
kuma karbi ko meye kika haifa,idan kinso kice ma ba kece mamarsa ba dukka na yarda......amma muddin
kina son hakan ta kasance sultana sai kina sakin jiki kina cin abinci" wasu hawaye ne masu sanyi suka
gangaro daga idanunta

"Basa ciyuwa abincin ama.......sai naji ko kallonsa bana sonyi,bazan iya ci ba amma yadda kikeso" sake
sassauta murya ama tayi

"Shikenan,calme-toi(kwantar da hankalinki),ba lallai bane sai kinci duk abinda aka dafa din ba.....duk
sanda kikaji akwai abinda kike sha'awar kici to komai rana kome dare ki gayamin ko ki gayawa
tanja,zamu tabbatar an dafashi kinji?" Kai ta gyada mata a sanyaye

"Yauwa,madalla......yanzu wacce qasa kikeso mu wuce?,don banaso mukai sati uku a nan,inason na kaiki
inda za'a kula dake,ba zaki sha wahala ba" har qasan ranta taji danji sanyi ya saukar mata,abinda zata iya
cewa ta jima rabon da ta jishi. Ta dan lumshe idanunta tana jin yadda zuciyarta ta gamsu da tayi nesa da
NIJER qwarai da gaske,tayi nesa da qawayenta dama idanun da suka santa,tayi nesa da dukkan
cakwakiya,a yanzu idan ka debe bibi da aba bata qaunar ganin duk mutumin da ta sanshi a baya,tanaso
ta nesanta kanta da kowa,da da halima zataso ta rayu ita kadai

"Wacce qasa kikeso?" Ama ta datsi tunaninta tana sake tambayarta. Abaya dukkan burinta shine aba ya
kaita France,kullum zancanta kenan,har yana tsokanarta

"Tunda kikaje makka kikaje madeena aikin gama yawo sultanan bibi.....amma itama France din zan
kaiki,amma fa sai ranar da kika gama école secondaire(secondary school),naga kuma
résultat(sakamako)nki yayi kyau,zan hadaki da ama idan an dace zata shiga ta can ku tafi tare har sai kin
gaji sannan ki dawo".
A wannan karon sai taji kamar an zare qasar fit daga zuciyarta,maimakon ta cewa ama itace
zabinta sai ta buda baki a hankali tace

"Austria"

"Austria?" Ama ta sake tambaya,don itama France ta tsammaci zata ce. Kai ta gyadawa ama din tana me
tabbatar mata,sai ama din ta sauke ajiyar zuciya tana cewa

"Très bien(ba laifi)" sai ta jawo wayarta ta kunna data ta soma danne danne.

*********Sati biyun da sukayi cikin garin kano sunyi shine cikin gida ba tare da zuwa ko ina ba,idan ka
gansu sun fita din to tabbas zasu miqa sultana ne asibiti. Sultanan da ko yaushe jikinta ke qara zafi da
rikicewa.

Wani irin bahagon laulayi takeyi mai bala'in zafi da wahala. Duk yadda ama tayi shekaru a
duniya,taga kuma masu ciki kala kala,itama kuma tayi kalar nata cikin har sau uku ta jima bataga
masifaffen laulayi irin na sultana ba. Sosai take a galabaice,bata iya komai sai kwanciya,sai kuma kuka
daya zame mata tamkar sallolin farilla guda biyar.

Kullum gari ya waye rana ta fito bawa kanta mutuwa takeyi,azabar da takeji a kowacce gaba ta
jikinta tana jin ba irin nau'in azabar da zakaji ka rayu bane. Ta sake zama 'yar firit da ita,sai wani
mahaukacin haske da tayi,idanunta suka sake fitowa tare da yin wani irin haske me sheqi. Saidai kuma
duk yawan gashin nan nata da sumar nan babu su,yanzun haka qaramin ribbon ya isa ya riqe 'yar sumar
dake kanta. Bata um bata um um,kuka a yanzun ya fiye mata komai cikin rayuwarta.

Yanayin sultana din ya sake cirewa ama nutsuwa,tausayinta takeji kamar kamar me,inda tana
da iko da kuma me yiwuwa ne da tuni ta fidda cikin daga jikinta ta dawo dashi nata jikin ko zata samu
hutu koda na kwana daya ne tak.
*_AUSTRIA_*

*VIENNA*

*_VIENNA INTERNATIONAL AIRPORT_* _(flughafen whien_schwechat VIE)_

A nutse suke saukowa daga jirgin Ethiopian airlines wanda yayi jigilarsu daga kano ta dabo suka
yada zango a Addis ababa,daga addis ababa din suka sauka London,daga london kai tsaye zuwa Austria
babban birnin Austria din wato Vienna.

Hannun sultanan wadda tayi wani dan qaramin kyau cikin wasu skirt and blouse da suka dace
da jiki da kalar fatarta,sai headscarf data nannade kanta dashi,wanda hakan ya bayyana fuskarta data
bayyanar da rama quru quru.

Backpack bag ne a kafadarta guda daya, sauran duka luggage dinsu yana hannun tanja. Shima
ita ta dage kan zata iya amma aman hanata tayi.

Hannunta cikin na aman,wadda ke saye da wata doguwar riga me rubi biyu beig color saqar
qasan oman,sai rufaffen takalmi data saye qafarta dashi. Qwayar idanunta lullube da wani sun glasses
baqi da ya qara mata kwarjini ainun. Kana kallonta kaga classy maama,muddin baka santa ba ba zaka
taba tsammanin ita ta haifi saurayi haka kaman aliyyu ba, zakayi tunanin almu shine yaronta na fari.
Tana da kyan jiki,tana da son ado,idan akace ado ado me aji wanda bai fiya daga hankali ba,irin adon da
duk wanda ya kalla zao burgeshi ya kuma ga cewan ya dace da age dinta.

Duk da ba kasafai ta fiya zuwa Austria ba,to amma abune na aiki da ilimi,don haka tun kafin su
tsoma qafarsu cikin qasar hatta da inda zasu zauna tsahon wadannan watannin ta gama dashi,don haka
suna sauka taxi suka dauka kai tsaye suka wuce masaukinsu.
*_SECOND DISTRICT Leopoldsdadt_*

Unguwace dake da wani irin tsari me kyau tare da saukar da nutsuwa, nutsuwar da tunda suka
shigo unguwar har qasan rai da zuciyar sultana taji yanayin unguwar yayi mata. Suna da wasu irin jerarru
kuma tsararrun Street da aka cikasu da bishiyu dake bada wadatacciyar iska da inuwa me kwantar da
hankali.

A nutse suka isa second floor,inda anan apartment nasu yake. Babban falo ne yalwatacce dake
dauke da dining area,budadden kitchen,balcony daga gaban gininsu da zai baka daman samun iska me
kyau da ganin yanayin ginin unguwar,sai dakunan bacci guda uku madaidaita dake manne da toilet
kowannensu. Yanayin ginin gini ne me matuqar tsari wanda ama tayi amanna zai dace da tsarinsu,komai
an zuba,hatta da kayan abinci basu da abinda zasu buqata.

Tun daga daren har zuwa wayewar gari ama bata zauna ba. Kwanaki biyu tayi a tsaye,sai data
tabbatar duk wani da zai zamewa rayuwarsu tilas na su nemeshi ta gama da matsalarsa a tsahon shekara
guda da take sanya rai zasu kwashe a qasar. Tun daga booking na asibitin da sultana zata dinga zuwa anti
natal,tayi mata register da wani center na bawa mata masu juna biyu kulawa da kuma shawarwari,ta
sake mata register da cikakken likitan dake lura da matsaloli da qwaqwalwa kamansu depression anxiety
da sauransu. Center ce me kyau data jima tana bin qwaqwafi da bincike a kanta,tanason duk wani
damuwa ya gushe daga zuciyar sultana din,tana sha'awar taga sultana ta fuskanci rayuwa da
kyau,tanaso ta haihu successful ba wani matsala da zata shafeta ko ta shafi abinda ke cikinta. Ta canza
layukan wayarta,ta kuma canza dukka accounts nata da take amfani dasu,kama daga Facebook page
dinta,instagram dinta da watsapp dinta,daga ita har sultana suna buqatar nutsuwa,suna da buqatar su
manta da kowa da komai na wani dan lokaci.

[06/05, 5:17 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 21
Hutun sati guda kacal sukayi duk wani abu data biyawa sultana din tayi qoqari taga ta fara
zuwa. Duk da zuwan nata sai ya zamana asha ruwan tsuntsaye saboda yanayin jikinta na yau lafiya gobe
babu.

Cikin nasara da taimakon Allah sannu sannu tana zuwa ganin likitanta sai aka fara samun
sassauci,don an samu ci gaba tayi katari da irin abincin da takeso a wata fita da ama tayi dasu cikin
unguwarsu. Street food ne da sukeyi a wani kebantaccen waje,ama din bata taba tsammanin sultana
zata iya cin abincin ba,don har ta kira waitress tace a maida,sai ta buda baki da muryar nan tata data
zama sasaanya tace

"Ama ni zanci" a mamakance take kallonta,cikin harshen German tace su ajjiye. Kaman wasa ta koma da
baya ta zubawa sultanan idanu,sannu sannu sai gashi ta tashi dashi. Abun ya yiwa ama dadi,sai suka
maida wajen gurin zuwansu duk dare,don acan ne kadai sultanan ke iya ci ta qoshi,koda zataci tayi
amai,amma tanaso,hakanan ana samun wani yana zama a cikinta.

Kaman yadda taci burin sadaukar da komai nata ta sadaukar din,don lokutta da yawa tanja na
girmama girman qaunar data karanci ama na yiwa cikin dake manne jikin sultana,ko kadan batajin kudin
dake fita a jikinta,duk da cewa ita din ahalin abunne,ta tara da yawa an kuma tara mata,amma saidai
daga qasar har zuwa unguwar da suke zaune din tana cikin nau'in gurare masu tsadar rayuwa a
duniya,amma tanja bataga alamun hakan sam sam yana damun ama ba.

Sannu sannu suka kwashe watanni uku a Austria......daidai watannin cikin sultana shida cif,ba
labarin gida a kunnuwansu kamar yadda gida basusan wacce duniya AMA TANJA DA SULTANA suke
ba.....bare maina da tun daga wancan ranar ko me kama dashi basu sake gani ba,basu sake jin komai da
yayi kamanceceniya dashi ba..... tun uncle abdulhakeem suna cigiya har gwiwoyinsu ya sare.......tun suna
cigiyar maina kadai har suka koma hadawa da cigiyar ama......tun hankalin aba bai tashi da yawa ba,yana
ganin kamar adadin Tex naban haqurin da yake tura mata yana riskarta......girman soyayyar dake
tsakaninsu zata hanata yin nisan zango.......zata kuma waiwayeshi.....har ya sare ya fara tunanin ta ina zai
nemo hamdiyya?,ta yaya zai maidowa da bibi farincikinta?. Duk wani kuzari da walwala na family din
MAYAK'I yayi nasa guri sai abinda ba'a rasa ba. BA MAINA BA AMA BA SULTANA wadannan abubuwa
dasu suke kwana kuma dasu suke tashi cikin zuciyar duk wani ahalin mayak'i.

********K'arfe takwas na dare agogon qasar Austria,daidai lokacin da ama ke tsaye gaban cupboard din
sultana tana zaqulo mata kaya.
A qalla kayan dake zube saman madaidaicin gadon sultana din sun kusa kala ashirin,saidai
kowanne a ciki sultanan ta gaya mata baya shigarta.

Daga qarshe hannunta ya damqo wata free size gown,golden brown ce da ratsin baqi,ama ta
dagata tana kallonta hadi da sauke ajiyar zuciya.

K'ofar toilet din dakince ta bude,sultana ke takowa a hankali daure da babban towel.

Idan a watanni biyun baya kaga sultana a yanzun zaka iya rantsewa ba ita bace,ko kuma kace

"Wanne irin ci takewa abinci haka?" Zaka kuma iya qaryata duk mutumin da yace maka baqar wahala
takesha,bata iya bacci da dare sosai,bayan dukka 'yan kwanaki sai ta ziyarci likita ya qarawa jijiyoyinta
ruwa.

Kamanninta tun daga jikinta zuwa fuskarta sun dauki hanyar bacewa. Tana takowa gaban ama
ama din na kallon idanunta

"Kuka kikayi cikin bandaki sultana?" Ta jefa mata tambayar data sanya sultana ala dole kauda kanta.
Kukan tayi,kukan data kwan biyu batayi irinsa ba saboda rashin qwarin jikinta. Fuskarta ta kalla taga
yadda ta koma,gaba daya kaman ba sultanan bibi ba?,me yasa ama ta tilastata akan tabar cikinnan?,me
yasa bata yarda da shawarar bibi ba?,kullum rana ji takeyi kamar ruhinta zai fita daga gangar jikinta,wani
lokaci ma sai taji numfashi kamar na mata wahalar shaqa,wani abu ya yiwa cikinta qabe qabe,yayita
mata motsi kuma yana dukan bangon cikinta,wani lokaci ta tashi ta zauna a firgice cikin dare,wani lokaci
ta dafe gurin ta saki kuka me tsuma zuciya.

Tunda uwarta ta haifeta bata taba jin ana motsi cikin mutum ba,a ranar data fara ji din kusan
haukacewa ama tayi da kuka da firgici. Ita sa tanja sai da suka kusa kwashe awa guda suna mata bayani
suka kuma kwatanta mata kafin su samu ta sassauta,saidai har yau idan cikin zai motsa to yana motsawa
ne da wani irin miki a zuciyarta.
Ganin tayi namijin shanye damuwarta sai ama din bata kuma tuhumarta ba,ta zauna tana miqa
mata kaya tana shiryawa. Gaba daya girman cikin ba zakace na haihuwar fari bane,bayan haihuwar fari
ma ace cikin yarinya kaman sultana?. Duk da a yanzun wani girman dole yazo mata,ta cika ta zama
mace,amma idan ka qare mata kallo tsaf idan kana da nazari zakazan yarinya ce danya shataf.

Ko a jiya sai da sukayi zancan girman cikin da tanja

"Next month zamu koma ganin likita,zan masa complain naji me zaice" ama ta cewa da tanja

"Amma hajiya anya baki tunanin tagwaye ne a cikin nan na sultana?" Sai da gaban ama ya fadi

"Tagwaye a cikin sultana kuma?,ina zata kaisu?" Ta tambaya da fargaba,sai kawai tanja tayi murmushi

"Shikenan,Allah dai ya raba lafiya kawai zamuce cikin amincinsa"

"Allahumma ameen" ama ta amsawa tanja,saidai cikin ranta tana nazarin maganganun tanja din

A nutse ta gama shirinta tsaf sannan ama ta sanyata a gaba suka fito. Yau din tanja tace zata
zauna cikin gida,ita ta soma gajiya da kallon masu jajayen fatar nan. Sosai maganar ta bawa ama
dariya,sultana kuwa murmusawa tayi qasan zuciyarta ba tare da fuskarta ta nuna ba.

Hakan kaman qa'ida ya zamewa ama tun sanda likitan ya basu shawarar fita strolling da sultana
din saboda sake samun qarin lafiya da kuma gujewa qaruwar hauhawar jininta. Tare suka jero ta layin
unguwar da yafi kama da titi sabooda shimfidaddiyar kwalta data maye gurbin qasa da mu muke fama
dasu cikin layukanmu. Idan ka hangesu daga nesa zakayi tunanin yaya ce da qanwarta,idan suka kusance
ka kuma sai kaga UWA da 'YA sak.

Yau din shuru ne ya soma ratsa tafiyar tasu,har sai da ama tayi gyaran murya
"Yau bakison kowanne labari ne?" Ta fadi tana dan satar kallon sultana,wadda tun sanda ta fara zuwa
center din data mata register ake samun sauqin wasu abubuwan,koda ba zaka ganta tana dariya ba
amma a qalla akwai raguwar dakuwa kaso sittin cikin saba'in data dawwamarwa fuskarta,to amma yau
din da alama akwai wani abu da ya taba zuciyarta

"Inaso" ta fadi a taqaice,sai ama ta dage dukka kafadunta

"Shikenan,zan baki labarin qasar Germany,sanda mukaje da abbana duka duka shekaruna goma sha
hudu......amma saikin gayamin meye yake damunki,karki manta......munyi alqawari dake kin daina
boyemin komai" ama ta fada taba nuna fuskar sultanan da dan yatsa.

Duk yadda taso jurewa saida hawaye suka taru a idonta,tasa bayan hannunta ta matsesu sannan
bakinta yana dan rawa tace

"Na gaji da cikin ama,don Allah yaushe zai baki na huta?" Tausayi da dariya dukka suka kama ama
din,amma tausayin ya rinjayi dariyar. Tsabar sangarta da gata batasan ma wata nawa ne ciki yakeyi a
jikin mace ba kafin ta haihu,tsabar qanqantar shekarunta ma batasan yadda zatace Mata yaushe zata
haihu ba,sai ta kama hannunta suna dab da wani shop na Shan coffee da snacks don haka suka qarasa.
Kujera taja mata ta kalleta,ko batayi magana ba tasan me take nufi,don haka sai tayi taku biyu,ta isa
gaban kujerar ta zauna,fararen idanun nan a narke.

Murmushi ama din ta sakar mata,ta daga mata yatsanta guda sannan ta shiga shop din. Da kallo
sultana ta bita harta bace cikin shop din,sai ta zuqi numfashi wanda yakai mata har tsakiyar hunhunta.
Da sauri tare kuma da wani irin gaggawa ta saki numfashin hadi da fesar dashi waje tana zare idanunta.

Cikin kowacce kafa ta numfashita.....cikin kowanne sasanni na shiga da fitar numfashinta


qamshin yakai. Qamshin da tafi tsana a duniya,qamshin da batajin ko da tana kwance ne a kushewarta
muddin qamshin zai gitta ta gurin zata iya jiyoshi,qamshin da jikin mutum daya ta sanshi,ta kuma yi
masa mummunar hadda me wuyar mantawa a baqar ranar da tayi silar jirkita dukka farinciki walwala da
tarin mafarkan data tanadarwa rayuwarta.
Tsam ta miqe tsaye dukka jikinta yana rawa,ta ware idanunta tana duban kowanne sashe na
wajen. Ba kowa,bata ga kuma kowa ba,hasalima kaf wajen kamar ita daya ce baqar fata,sai kuma ama
data shiga ciki.

Dafa kafadarta taji anyi,abinda ya sanyata wani irin bahaguwar juyowa,sai idanunta ya fada cikin
na ama. Kallon kallo suka tsaya yiwa juna,ama tana kallonta cikin mamakin abinda ya firgitata daga shiga
ta fito bayan wajen safe yake,yayin da ita kuma razanar da tayi da kuma tuna mata da mummunar ranar
da sanadiyyar wanzuwar qamshin ya haifar mata ya sanya zuciyarta raurawa,kawai saita aza fuskarta
saman kafadar ama ta saki siririn kuka.

Tasan dama akwai sauran qunci cikin zuciyarta,wanda babu wata hanya da zata samu
sassaucinsa saita hanyar kukan,don haka batace komai da ita ba,ta jata jikinta sosai tana bubbuga
bayanta,har sai data nutsu don kanta sannan ama din ta maidata saman kujerarta,ta kuma tura mata
daya daga cikin nau'in abin shan da shima akan dace ya zaunawa cikinta.

Bata tambayeta ba hakanan batace mata komai ba sai da taga tana diba da kadan da kadan
kamar me ciwon baki tana sha sannan ama din tayi gyaran murya tana gyara zamanta

"Next month zamu koma asibiti,zan tambayeshi wacce rana ne zaki haihu,zakiji in sha Allah,amma kinsan
zai iya ce miki ba yanzu ba?" Da sauri ta daga kai tana wulqa idanu,idanun nata cikin na ama, fuskarta ta
narke sosai cikin nuna zallar fargaba. Sai ama ta dage mata dukkan girarta

"Eh mana,ya hana wannan koke koken,sannan yace ki dinga daurewa kina cin abinci sosai haka ne?" Kai
ta gyada mata a hankali

"To me kike tunanin zai faru idan mukaje ya gwadaki yaga babyn baiyi girman da zaki haihu ba?"

"Zanci ama,don Allah kice masa kada yacemin ba yanzu ba,bana iya bacci ama,bana iya komai,dukana
kawai yakeyi a ciki na,kullum dare a zaune nake....." Ta qarasa fada tana saka tafin hannunta guda tana
share sabbin hawayen dake sauko mata. Tsananin tausayinta sai da ya sanya ama din taji qwalla sun
sauko mata amma ta daukesu cikin dabara,saita miqa hannu tana dan bubbuga bayanta cikin dabara.

[08/05, 9:28 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*


*H U G U M A*

Book 02 page 22

Ganin ta zage tasha abun sosai sai ama ta yanke shawarar su qara nisan zango a tafiyarsu don
ya saukar mata sosai,kada su koma gida da wuri ya dameta ko ya sanyata amai.

Cikin salon jan hankali ama ke bata labarin Germany,har zuwa sanda sukazo giftawa ta wani
baby shop. Har sun gota amma ta tsaya,sai a sannan ta tuna babu koda qyallem handkerchief da ta siya
da sunan kayan haihuwa. Juyawa tayi ta dubi sultana

"Mu shiga nan ki jirani nayi siyayya" bata musa ba ta sanya kai tana biye da ama din.

Guri ta sanya ma'aikatan gurin suka bawa sultanan tace tayi zamanta,gudun kada tace tazo ta
tayata zabe taje ta jangwalowa kanta,qilu ta jawo bau.

Sosai ta nutsa cikin shagon,ta dinga zaben kaya designers masu tada da sukaja pounds sosai.
Samun kanta tayi da daukar duk abinda ya bata sha'awa,musamman kayan baby girl.

Har yanzu akwai wannan qawa zucin a jikinta da kuma zuciyarta,har yanzu tanason baby
girls,don dai kawai lokacin haihuwarta ta fuskanci ya wuce ne.

Sanda ta shiga bangaren overalls 'yan ubansu,saita tsinci kanta da zaben komai pink,haka kawai
cikin zuciyarta taji tana da burin inama ace babyn ya zama mace?, murmushi ya subuce mata ba tare
data shiryawa hakan ba.
Daidai bangaren teddies ama ta ajeta. A nutse takebin wajen daki daki da kallo,komai na wajen
me kyau ne,alamu dake nuna cewa komai na cikin shagon zaiyi tsada kenan.

A hankali wani tsohon emotion nata ya fara taso mata. Nini dinta ta fado mata wadda har
kwanan gobe batasan inda tayi ba. Allah ya zuba mata qaunar teddy,duk da wannan emotion din nata
yaso mutuwa murus daga gangar jiki harma da ruhinta.

Har ta zare idanunta daga kansu sai hankalinta ya fusgo mata wata kyakkyawar pink teddy. Maida
dubanta tayi,ta miqa hannunta tana shafata. Sosai jikin teddy din yayi mata,haka ma fasalin da akayi
mata

"Ki dauka idan tayi miki" ta tsinci muryar ama daga bayanta. Da sauri ta waiwaya ta kalli ama dake riqe
da wani babban kwando da ta cikashi taf da suturu,saita maida dubanta ga fuskar ama din tana girgiza
kai alamun a'ah,sannan ta miqe a hankali da zummar barin wajen. Da kallo ama ta rakata sai kawai ita ta
saka hannu ta zaro teddy din ta jefata a kwandon kayan. Har tayi gaba ta dawo da baya,ta zake zabar
wasu guda biyar suka zama shida cif,sannan ta wuce wajen lissafi.

Mamaki ne kawai ya kashe sultana sanda taga uban kayan da ama ta diba,ashe kwandon
hannunta na daxun sauran kayanne kawai. Kamar ba da guminta take neman kudin ba,ta zare Pounds
masu ciwo ta biya kudin kayan tas,sanann ta bada Adress din inda za'a kai mata suka fice abinsu daga
shagon.

Har ranta bataji komai ba,jinin maina ne kuma tsatsonta itama.......inda ana kyautar rai tabbas
zata iya sadaukarma ahalinta,xata iya komai domin jininta,ita a yanzun ma da kwanakin cikin ke qara
nisa sai takejin zumudi qauna da kuma soyayyar abinda ke cikin na sake kamata,taji ta dokanta da son
ganin abinda ke cikin sultana din,ta matsu ya iso duniya.

********Sake duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta ama tayi,mamaki ya sake kamata,me
sultana din keyi shuru bata fito ba har yanzu?,bayan tasan inda zasuje din da kuma muhimmancin wajen.
Kamar ta aika tanja sai kuma ta fasa,ta miqe tana ajjiye medium veil din hannunta mahadin
doguwar rigar jikinta ta gyara zaman agogon hannun nata tana wucewa dakin sultanan.

Zaune ta sameta saman stool a gaban madubi,daure take da babban farin towel,sumar kanta
na nannade tsakiyar kanta. Tuni ta jima da zama qazama ta wannan fannin,bata yarda da abinda zaya
taba mata kanta duk qanqantarsa,sai ama tayi da gasken gaske sannan ake wankeshi a kuma maidashi
yadda yake.

A nutse tare da sallama ama ta shiga dakin,waiwayowa sultana din tayi,hawaye ne shabe shabe
kwance a fuskar tata

"Ya salam" ama ta furta qasa qasa. Itadai tunda take bata taba ganin mutumin da kuka baya damunsa ba
baya kuma yi masa wuya ba irin sultanar

"Yanzun kuma kukan meye?" Ta tambayeta tana isa bayanta ta tsaya tana duban fuskarta cikin mudubi.
Cikinta ta kalla,sai a sannan idanun ama yakai kai,ta yaye towel din dake jikinta,sai turtsetsen cikin a
gaba kai kace saura satittika ta haihu

"Menene?" Ama ta sake tambayarta cikin fargabar kada ta bata amsar wani abu ne ya samu cikin

"Fasamin ciki zaiyi ama......sai dukana yakeyi nan da nan" ta bata amsar tana rushewa da kuka tare da
nuna mata gefe da gefen cikinta da yatsanta. Ga dariya ga kuma tausayi,da gasken gaske sultana danya
ce shataf,babu wani abu data sani dangane da ciki ko haihuwa,uwa uba auta kuma 'yar fari,wautar tata
tayi yawa.

Gaban sultana din ama ta zauna tana qoqarin fahimtar da ita cewa alama ce ta lafiyar abinda
yake cikinta

"Ni na tambayeshi yana lafiya?,ya mutu mana" ta fada tana buntsuro baki gaba
"Subhanallahi" ama ta fadi tana zaro idanu,don sosai maganar ta daketa, jikinta yayi wani mugun
sanyi,tsoro kuma ya shigeta. Kada dai ace zuciyarta ta taso da qeqashewa da qiyayyar abinda zata haifa
din kamar yadda ta yiwa mahaifinsa muguwar tsana?. Wannan tunanin kadai ya sanya zuciyarta
rawa,bata fatan kuma wannan ya zama qaddararta ta gaba,batasan yadda zata fuskaci wannan qaddarar
ba kuma

"Sultana?" Ta kirayeta a sanyaye tana kallon tsakiyar qwayar idanunta. Duban aman tayi amma sai ta
janye kallonta daga kanta,karon farko da taji wani nauyi na aman,taji kuma nauyin kallon idanun
aman,jikinta itama ya sanyaya,taji a jikinta kamar ta furta wani abu da ba dai dai ba.

"Kinaso muyi fada dake?" Ta sake tambayarta with seriousness. Da sauri ta girgiza kai tana jin zuciyarta
tana karyewa

"To kada ki sake fada,kada na sake jin kinyi wannan furucin,akan kowa ma bare d'an cikinki,da yake
kwana ya tashi a jikinki,bashi da wata uwa sai ke,ke kadai kika dauki cikinsa kikasan wahalarsa,mu nan
dukka tayaki kawai mukeyi kinji ko?" Kai ta jinjinawa aman,sai tayi saurin kauda zancan ta hanyar cewa

"Oya.....tashi ki qarasa shiryawa,idan munje wajen likita saiki kai masa qararsa,zai masa fada nasan,zai
daina kuma dukanki" wannan 'yar maganar ta sanyayawa sultana rai,ta kuma miqe din ta shirya tsaf a
gaban ama din kamar yadda ta saba shiryawar,ba wani nauyi ko kunya ko digo da takeji nata.

Yauma sai da sukayi tattaki subway,sannan suka hau train zuwa asibitin.

Dr abdur'razaq mansoor,cikakken likita dan asalin qasar Egypt shine likitan dake duba
sultana,likita ne me matuqar kirki da kula da addini,yana da tausayi da kulawa sosai. Tun ranar farko da
ya fara ganin sultanan tausayinta ya cikashi,ya fahimci yarinya ce qarama sosai da bata gama sanin
rayuwa ba.

Yanayin nutsuwar likitan da tausayin da ya gwada ma sultanan ya sanya ama bata boye masa
komai ba
"Zan bata kulawa in sha Allah,zata haihu kuma lafiya" a boye ya baiwa ama addu'o'in da zata dinga
tofawa sultana din a ruwa,kuma ko sau daya aman batayi fashin tofa mata din ba ba tare da sultana ta
sani ba. Duk wani gorar ruwa na gidan da tasan sultanan zata iya sha sai data budesu ta tofa din,daya
daga cikin sirrikan abinda ya kawowa zuciyarta nutsuwa ya kuma sake tanqwara ta ya sanya mata
dangana.

A irin qasashe dake da ci gaba irin haka,zaiyi wuya kaje ganin likita ka samu cinkoson marasa
lafiya suna jiran likita,hasalima lokuta da dama saidai ka samu likitan yana zaune kawai yana hutawa ko
wani research da ya danganceshi. Don haka mace daya ce ta fito number dinsu tayi appearing jikin board
na office dinsa don haka suka wuce ciki kai tsaye.

Da fara'arshi da kuma sakin fuska ya musu maraba. Ya saba sam sultana bata magana har su
gama ganinsa su tafi,amma hakan baya hanashi dan tsokanarta janta da wasa kadan don ta saki jiki da
kuma tambayarta yanayin lafiyarta.

Sai da ya gama mata dukka tambayoyin da aka saba,ya nemi jin ko akwai wata matsala da take
fuskanta?. Murmushi ama tayi sannan cikin harshen France don sultana din taji ta gaya masa

"Tace dukanta cikin yakeyi,ta gaji dashi yaushe zan karba?" Qaramar dariya Dr abdur'razaq mansoor ya
saki

"Yau zamu duba muga me yake faruwa sai a gaya masa ya fito haka momy ta gaji" shi da ama suka dan
saki dariya,banda sultanan da take binsu kawai da kallo.

Komai ya hada sannan ya bata umarnin hawa gadon scanning. Karon farko da za'a yi mata
scanning din tun bayan wanzuwar cikin.

Kusan daskarewa Dr abdur'razaq mansoor yayi yana ci gaba da yawo da na'urar saman cikinta

"Subhanallah" kawai yake furtawa lokaci lokaci idanunsa qur bisa allon computer din.
Subhanallah din da yake fada ta sanyawa ama fargaba,amma ita dinma saita dinga ambaton
sunan Allahn kawai,don tunda taji baice komai ba qila babu buqatar yin maganar gaban sultana.

Yana kammalawa ya danna wani madanni na kiran nurse,ba jimawa nurse din ta shigo,cikakkiyar
baturiyar Austria,saidai ita dimma da alama macace me kirki da yawan fara'a.

Cikin harshen German yace da ita ta kaita garden na masu juna biyu,sannan ya sake juya
harshen nasa cikin yaren France ya yima sultanan magana. Ba musu ta miqe ta saki doguwar rigarta,ta
kuma gyara yafen mayafin nata tabi bayan matar.

Da idanu ya bisu,sai daya tabbatar da fitarsu sannan ya dawo da dubansa ga ama wadda ta
tsurawa hoton scanning din dake jikin allon computer din idanu,kwanyarta nason rarrabe mata gaskiyar
abinda idanunta ke gane mata.

Hannu kawai ya miqa ya juyo mata da fuskar computer sosai yana kallon idanunta,cikin yaren
faransanci yace mata

"Ina tayaku murnan samun 'yan biyu,yarinyarki tagwaye ne a cikinta kamar yadda na jima ina zato"
maganar tazo mata a mugun ba zata,cikin hanzari ta maida dubanta ga Dr abdur'razaq. Ya fahimci she
was shocked,sai yayi murmushin nan nasa yana dora dukka hannuwansa kan computer din.

Kai tsaye ya canza hoton da take gani zuwa 3D scanner,take fuskokin yaran dake kwance cikin
mahaifar sultana din suka bayyana tarwai.

Ko ina a jikinta ya dauki rawa,ta sanya hannuwanta dukka biyun tana rufe bakinta,bakin nata
dakeson kama sunan Allah amma rawar da yakeyi ya sanya ta kasa,Dr abdur'razaq bai waiwayo ya
dubeta ba yaci gaba da mata zooming fuskokin guda biyu da suka zama cikakkiyar fuskar
bil'adama,fuskokin da suka cika suka kuma bayyanar da kamanninsu,suna rungume da junansu

"Bacci sukeyi,inda idanunsu biyu zaki iya ganin motsawar kowannensu,kukansu ko walwalarsu"
"Subhanallazi lam yattakiz waladan walam yakun lahu sharikun fil mulki walam yakun lahu waliyyun
minazzull" ta furta wasu hawaye masu sanyi suna sauko mata. Tayi tunanin zasu tsaya amma basu tsaya
din ba,haka suka dinga sauko mata daya bayan daya. Bai hanata ba Dr,yadai miqa mata tissue yana duba
wasu ayyuka nashi har sai da zuciyarta tayi sanyi sannan suka dakata,ta gyara fuskarta ta kuma gyara
zaman mayafinta sannan tace

"Amma Dr ina tsoro,ta yaya sultana zata iya haifan tagwaye da kanta?" File din gabansa ya rufe yana
dubanta

"Bayanin da nakeson miki kenan,tayi qanqanta qwarai,don ko a yanzun girman da yaran keyi a cikinta ya
bani mamaki,nauyinsu da na gani,lallai ita kanta ba qaramin qoqari takeyi ba,kuma tana da jarumta duk
raunin nan nata da yawan koke koke,bakinta kuma na tabbatar duk da yawan qorafinta akwai abinda
bata iya gaya miki,so ina kyautata zaton cikin yana shiga sati na talatin da shida za'a yi mata CS a
cireshi......amma banason ki gaya mata hakan,saboda a yanzun dole a dinga monitoring blood pressure
nata,a bata kwanciyar hankali sosai da nutsuwa don komai yazo yadda akeso". Sosai jikin ama ya qara
sanyi,ya lura da hakan sai ya bata gwarin gwiwa sosai,qwarin gwiwar da ta sanya taji eh tabbas zasu iya
fuskantar komai,kuma komai zaizo ya wuce da qudirar Allah kaman bai faru ba.

A karo na Babu adadi bayan fitowarta daga office din Dr abdur'razaq ta ciro wayarta,kamar
kowanne lokaci da idan abu irin hakan ta faru zatayi gajeran tex wa maina

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[08/05, 9:28 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 23

A duk sanda wani abu ya faru sai ta rubuta ta tura masa tare da gargadinsa kan duk inda yake ya
dawo. Ko sau daya bata taba samun tabbacin saqon yana isa ba,bata taba ganin alamu na maido amsa
ba koda da digo,amma hakan bai hanata aika saqon ba.

Cikin hanya kaf tunaninta na yadda zata sake dauke hankalin sultana,tare da yin handling komai
idan lokaci yayi.

Dukka qarfi da basirarta ta sanya don tabbatar da farincikin sultanan. Ta sake qirqirar abubuwan
da tasan zasu dauke mata hankali. Tilas ta dinga siyan ticket na zuwa qasashen da suke maqwaftaka da
Austria duk don ta faranta ranta,ta kuma sake don a samu a cimma nasara.

********Misalin qarfe tara na dare ta fito daga toilet din. Daure da babban towel take amma sam ya
kasa ratsata saboda girman uban cikin dake gabanta. Da qyar take daga qafafunta,duk ta qarasa zama
wata babba ta kuma kumbure har fuskarta. Dazu daxu kafin ta shiga wankan ta gama cikin
kukanta,abinda ya ruruta idanunta kenan,ya kuma sanya fuskarta ta sake yin jazur.

Kai tsaye ta isa gaban mudubin ta tsaya tana kallon kanta da kanta,wani zazzafan hawayen ya
zake silmiyo mata,ganin kanta takeyi kamar ba ita ba,sau tari idan ta kalli fuskarta takanji kamar ba itace
sultana ba,itakam a rayuwa tana jin hatta da shaidan saidai maina ya biyo bayan qiyayyarsa a zuciyarta.
Batajin har abada zata iya yafe masa,batajin akwai wani wahala ko Azaba da zata ganshi a ciki da zai
karya zuciyarta taji zata yafe masa. Kullum kwanan duniya fadi take fili da zuci
"Allah ka sakamin". Hannu ta saka ta yaye towel din,tulelen cikinta dake rinjayarta ya bayyana,yayi girma
qwarai ya kuma yi tsini sosai,ta dafe qasan mararta da nauyin da takeji yafi yawa a nan akan ko ina,Allah
Allah takeyi kwanan watan da ama tace mata zata karbi babyn yayi,Allah Allah take a cire mata shi,ta
hanci ne?,ta baki ne?,ta kunne ne oho itadai ba matsalarta bane. Matsalarta daya ta wayi gari ta jita
wayau,ta jita ta tashi babu wadannan lalure laluren da uban nauyin da yake damunta.

Turo qofar da akayi ya sanyata saurin sakin towel din. Ama ce ta kuma ga abinda ta tsaya din
tana kalla amma sai tayi kamar bata gani ba,ta dauke kanta ta shigo dakin tana fadin

"Bakijin sanyi sanyin garin nan daya fara busawa?"

"Yanzu zan shirya" ta fadi da dakusashiyar muryar da har yau bata bude qwarai ba don ba maganar ma
ta fiya yi ba bare ta bude yadda ya kamata.

Tana kallon ama ta gefen ido ta jawo akwatin da kusan kullum sai taga tazo ta shiryashi,ta kuma
sake zuba kaya,ita kadai cikin ranta take mamakin kayan da ama din keta narkawa akwatin,bayan tace
mata dashi zasu tafi asibitin,to tabbata zasuyi cikin asibitin da aketa loda ma akwati kaya?,oho bata da
wannan amsar,sai kawai ta jawo lotion ta fara shafawa a jikinta.

*********Sanye da kayan theatre Dr abdur'razaq mansoor ke fitowa daga office dinsa. Gefansa wani
gajeran likita ne baturen qasar Austria din,yana riqe da files a hannunsa suna magana da Dr abdur'razaq
din cikin harshen German.

Ama dake zaune saman kujerun dake daura da theatre room din ta miqe tsaye tana jiran
qarasowarsa. Dab da zasu iso din ya sallami likitan ya shige dakin theatre din shi kuma ya amshi file din
hannunsa yana qarasowa.

Yaga fargaba,sarewa da kuma tsoro a tattare da ita,abinda bai tana gani ba kenan daga gareta
tsahon watannin da sukayi suna zuwa gurin nasa. Tsayyayyar macace da ba komai ke firgitata ko kuma
ya bata tsoro ba. Ya sani a irin situation din sultana dole ta fuskanci fargaba da tsoro,don haka ya sakar
mata murmushin dake bada qwarin gwiwa,ya miqa mata file din yana kallon agogon hannunsa
"Ki kiranta a nutse ki sanya hannu,sanya hannun shi zai bamu damar fiddo miki jikokinki nan da mintuna
talatin kacal in sha Allah". Hannu tasa ta amsa,ta koma ta zauna kusa da tanja gwiwa a matuqar
sanyaye,ta buda page din ta fara karantawar tana sanya hannu,saidai a duk inda ta sanya hannun,sai
zuciyarta ta jaddada mata.....muddin aka samu akasi la shakka itace ta kashe sultana

"Hasbunallahu wani'imal wakil" take bin mummunan tunanin da shi,har ta kammala ta rufe ta miqawa
Dr abdur'razaq. Amsa yayi yana sake murmushi

"Compte à rebours les minutes(ki irga mintunan)" ya fadi yana bata qwarin gwiwa cikin idanunsa,sannan
ya taka zuwa qofar dakin theater din ya sanya kai bakinsa dauke da bismillah.

Ragwaf ta koma ta zauna,ta dunqule dukka hannayenta cikin na juna tana jin jikinta yana mata
wani yaarr,ta dinga maimaita kiran sunan Allah data samu bakinta ya fuzgo sanda tanja dake riqe da
carbi take maimaitawa a fili don ta samu ama din ta kama kuma nutsuwarta ta dawo.

Mintina biyar kacal ambaton sunan Allah ya saukar mata da nutsuwa,saita zaro wayarta as usual
ta turawa maina tex akan current situation din da ake ciki,ta maida wayar tsakanin cinyoyinta kawai tana
ci gaba da kiran Allah.

Da ita da bibi batasan waye ya riga wani miqewa ba sanda qofar theater din ya bude ba,saboda
mintunan da Dr abdur'razaq mansoor ya basu sun cika harma sun gota da wajen qarin mintuna wasu
talatin din akai.

Dr dinne da kansa,iya fara'ar saman fuskarsa kawai ta bayyana musu labarin me dadi ne,ya
qaraso gabansu yana cire facemask din fuskarshi

"Alhamdulillah,anyi nasara,an ciro mata tagwaye dukka YARA MATA" ya fadi yana duban tanja da ta
qame cikin zallar farinciki.
Batasan yaushe bane,ba kuma tasan ya akayi ba,itadai taji dukka gwiwoyinta sun zube izuwa
qasa,kafin daga bisani fuskarta da goshinta su kafu a qasa

"ALLAH kaine Allah,Allah ina me tuba izuwa gareka,Allah na tuba bisa dukka laifukana,Allah na tuba bisa
dukka zunubaina,Allah na tuba bisa karan tsaye da nake yiwa al'amuranka, ubangiji a yau ka tabbatar
min da qarfin ikonka,Allah ina godiya a gareka,Allah na gode mahaliccina na gode,ya hayyu ya qayyumu
kasa yarannan rayayyu ne,duk wani dake boye da wanda ke a zahiri Allah ya daidaitashi cikin izza hikima
da buwayarka,Allah ka bawa mahaifiyarsu dangana,ka bata haquri,ka taushi zuciyarta,ya hayyu ya
qayyumu ka karkato da hankalin mahaifinsu gida,Allah kaine mafi sani,kafi kowa sanin hikimar data
sanya ka wanzar da wannan al'amari,ya arhamar rahimeen ka sanya qarshen komai ya zamana da
kyakkyawar cikawa" sannan ta cikashe da maimaita alhamdulillah har sau babu adadi.

Itama tanjan sumbatun addu'a kawai ta dinga yi,hawaye ne itama cikin idanunta,yau 'yar lelen
bibi ta zama uwa,yau 'yar lelen bibi da yara har biyu?,tabbas wannan haihuwa inda cikin gida nijer
akayita batasan wanne irin cika yau asibitin nan zaiyi ba,batasan adadin farincikin da fuskokin mutane
zasu nuna ba.

Da suka buqaci ganinta ba'a hanasu ba,wata nurse ta musu jagora zuwa dakin hutun da aka bata
wanda suna ciki ita da yaran da aka dawo dasu daga sashen yara yanzu yanzu bayan anyi musu gwaje
gwaje da bin qwaqwafi irin na bature. Sakamakon da suka gani ya basu mamaki kodon qarancin
shekarun uwar yaran. Sun jima basuga lafiyayyun yara irin yaran ba,ga wani irin girma kai baka ce daga
cikin qaramar yarinya under 14yrs suka fito ba.(ai addu'a ba wasa bace,duk wanda ya gaza ganin tasirin
addu'ar da yakeyi to baiyi addu'ar da kyau bane,ko bai cika sharuddanta ba,ko kuma baiyi addu'ar yana
bawa Allah dukkan yaqininsa ba da yardarsa ba).

Duk yadda taso taje ta fara ganin fuskar sultana dake bacci daga ita har tanja sun kasa,gaba
dayansu gadon babies din suka nufa,hannun kowa yana rawa yana saurin isa garesu.

"Ma sha Allahu la quwwata illa billa,ma sha Allah....tabarakallahu ahsanul khaliqeen....." Ama ta dinga
maimaitawa bakinta yana rawa.

Wasu irin fararen yara masu cikar zati da kyau,wasu irin jarirai masu tsananin kama da
juna,kyawawan jariran da batasan ma kamannin waye zatace sun dauko ba. Farare tasssss tamkar
iyayensu haifaffun Vienna ne ba nijer ba,nannade cikin fararen kaya masu tsananin taushi da daukan
idanu.

Yadda hannunta ke rawa ta tabbatar muddin ta daukesu tana iya yada su,hasalima bata iya gani
sosai saboda uban hawayen dake narke cikin idanunta,saita sanya dogayen yatsunta ta riqe siraran
yatsun yaran dake nannade cikin safar hannu. Duk yadda taso riqe kanta sai ta kasa,kuka ya balle
mata,tayi qas da kanta tana kokawa,tanja tana bata baki.

Ina maina ya tafi?,ina aliyyu yaje?,yazo ya gani a yau shima ya zama uba,a yau yabar yabanya,a
yau ubangiji ya cika masa burinsa,mafarkinsa,kuma fatansa,burin da a sansa yake furtawar yana fada ne
kawai ba tare da samun tabbacin fatansa zai cika ba

_"duk randa nayi aure,matata ta haifami 'ya mace haihuwar fari ama ke zan bawa,in sha Allah sai na
share miki kukan rashin haihuwar 'ya'ya mata,sai na dauke miki takaicin da ake sakaki na hanaki riqon
'ya'yan wasu"_ wasu daga cikin kalaman maina kenan a duk sanda yaga tana neman 'yar budurwar da
zata riqe,ko kuma taje ta daukota akazo aka karbeta,ko kuma ta fara riqon taje hutu taqi dawowa. Yau
gashi burin maina ya cika,bama yarinya daya ba,yara biyu reras a lokaci guda,itakam batasan me zata
cewa Allah ba.

Ko sau daya ama ta kasa motsawa daga gindin gadon,ta kasa dauke idanunta daga kan
yaran,duk wani motsi da zasuyi saman idanunta ne,kamannin yaran sun baci ainun. Wata irin
mahaukaciyar soyayyarsu ce ke ratsata tun sanda ta dora idanunta saman fuskarsu,sai takejin kamar a
duniya bata taba son wata halitta ba tunda Allah ya halicceta sai a kansu.

[11/05, 10:00 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 page 24
A hankali ta zare hannunta daga nasu bayan sunsha hoto,sun sha videos har batasan adadinsu
ba,ta matsa kusa da sultana karo na biyu taga kota farka a baccin?. Har yanxu dai baccin takeyi
lakadan,fuskarnan ta fada tayi kuyas,hakanan duk girman jikinnan ksmaryan zugeshi tare yaran,ta ragu
sosai,qanqantarta ta soma dawowa.

Sai data fuskanci lokacin sallar azahar yayi sannan ta tashi a wajen,ta shiga bandaki ta daura
alwala tabar tanja a wajen.

Sanda take idar da sallar sultana ta motsa,ta shafa addu'ar da sauri ta miqe ta nufi sultanan.

Tun daga idanunta zuwa jikinta take jinsu wani iri,batayi yunqurin miqewa ba saboda nauyin
da jikinta yayi mata,kanta ta mirgina gefe guda tana kiran Allah can qasan zuciyarta,zuciyar tana bata
zaiyi wuya idan ba mutuwa tayi ba,don ba abinda zata iya tunawa,tadai jita daga qarshe kamar tana
yawo cikin iska.

Ama data hango tana tahowa ta tsurawa idanu. Da murmushi a fuskarta ta taqaraso,ta jawo
doguwar stool dab da gadon nata ta zauna. Idanunsu cikin na juna

Hannunta ta miqa ta riqe hannun sultana wanda babu qarin ruwa a jiki

"Kin tashi?" Kai gyada mata tana ci gaba da duban ama din

"Sannu" yauwa tace da ama,amma sautin baya fita sosai.

"Me yake miki ciwo yanzu?" Kai ta girgiza alamun ba komai,hakan ya yiwa ama dadi,sai taci gaba da
zama a nan din bata sake cewa komai ba kaman yadda sultana din itama bata sake magana ba,sai
idanunta data mayar ta lumshe. Tana jin alamun cikinta empty babu komai,duk uban nauyin dake jibge
tana jin ba komai a cikinsa,tasan dai kenan tabbas an cire baby din kamar yadda ama tace mata,to amma
yana ina?, Ta yiwa kanta tambayar
"Oho" ta sake baiwa kanta amsa

"Kome meye na cika umarnin ama,nima ama ta cikamin alqawarina,ban mutu ba gani ina raye,baby
dama nasu ne,na gama nawa aikin" ta gayawa kanta da kanta,don haka tayi relax daga kwancen,duk da
tanajin ta soma gajiya da kwanciyar.

Qushin qushin din qananun kukan jariri shi ya sanyata bude idanunta a hankali,saidai kuma bata
yarda ta juyar da kanta sashen da take jiyo kukan ba

"Hajja yaran nan fa da alama maciya ne,tun dazu sun kasa nutsuwa sai mutsu mutsu sukeyi,ya kamata a
nema wani abun a basu,tunda naji kince likita yace idan sun nema din a basu" tanja dake rungume da
daya daga cikinsu ta fada

"Eh,ai bari nazo nayi musu addu'a cikin kunnensu" ta fada tana zame hannunta daga na sultana.

"Har su nawa ne?" Sultana ta yiwa kanta tambayar can qasan zuciyarta,duk takun ama zuwa wajen yana
qididdige a kunnenta

"Wacece babba ne?" Tanja ta tambayi ama tana duban fuskokin yaran

"Akwai alama da suka sanya a qafafunsu"aman ta fada tana duban qafafun yaran.

"Ga hassana ga usaina" ama ta furta tana murmushi hadi da duban fuskansu.

"Anya wannan nan gaba za'a dinga banbancesu?" Fuskokinsu ama ta duba sosai

"Subhanallah subhanallah" aman ta fadi da sauri tare da yiwa tanja nuni da hannu. Daidai gefen kunnen
hassana,wani digon baqi sak irin na maina
"Tanja kin gane wannan?" Ama ta fadi muryarta tana dan rawa,abinda ya sanya sultana bude idanunta
da sauri,ta kuma juyar da kanta sassan da su ama ke tsaye tana ware idanunta cikin fargaba

"Allah hakimu,Allah me iko,irin digon baqin dake kunnen maina" da sauri sultana ta runtse idanunta
saboda kiran sunan maina din, tsakiyar qahon zuciyarta taji kamar an caketa da wani qarfe. Tanason
saka hannuwanta ta toshe kunnenta don kada ta sakeyin kuskuren jin sunansa ko wani abu da yayi
kamanceceniya da shi,saidai a daidai lokacin ama ta yiwa tanja alama da idanu na kuskuren kiran sunan
nasa da tayi,don haka tanja din bata sake cewa komai ba,sai ama data miqa hannu ta karbi yaran ta
sanyasu cikin jikinta sosai,dumin jikinsu yana haduwa,wani irin qauna ta jini tana ratsata.

Dukka addu'o'in da musulunci ya tanada tayi musu,ta kuma yi musu huduba cikin
kunnuwansu,sannan ta basu suna kanta tsaye ba tare da shawara da kowa ba FATIMA BINTOU DA
NADEEYA (mahaifiyar sultana da kakarsu aba). Hadasu tayi dukka ta sake rungumesu a jikinta tana sauke
ajiyar zuciya. Ko yau ta mutu burinta ya cika,babu kuma abinda zata cewa ubangiji face godiya mara
qarewa.

"FATIMA BATOUL da NADEEYA BENAZEER" Ama ta fadi idanunta akan fuskarsu. Masu cikakken gata irin
gata da ba kowanne bawa Allah ke tsagawa da rabonshi ba,amma sai gashi sunxo tsakiyar wata irin
cudewa rikita rikita da kuma cakwakiya,saidai koma meye ita din ba zata bari komai ya shafi rayuwarsu
ba,zata basu cikakken gatan da suka cancanci dashi,zata basu dukkan wata rayuwa da duk wani me
tutiya da tunqahon gata zai sameta.

Har likita ya bada umarnin sultana zata iya zama zata kuma iya miqewa,sannan ya bada
umarnin duka a ranar za'a iya goge mata jikinta,za'a kuma iya nema mata wani abu me ruwa ruwa tasha
bata tambayi yaran ba ko sau daya. Duk ama na ankara da ita,ko sashen da suke bata kalla,sai tayi mata
shuru batace da ita komai ba,har sai data gama goge mata jikin,ta zaunar da ita tana bata abu me dumi.
Dab da sultana din take zaune,ta miqa mata spoon bakinta sannan tace

"Baki tambaya baby ba sultana uhmmmm" shuru ta danyi,sannan ta bude bakinta a hankali
"Naki ne ama,dama kince ke zan bawa,na bakin ai" kai ama din ta jinjina tana jin ba dadi,kada dai ya
zamana su rasa soyayyarta kamar yadda taketa tunani tun dazu.

Rabuwa tayi da ita har sai data gama batan sannan ta maida bowl din. Ta qarasa inda yaran
suke ta dauki batoul sannan tanja ta aza mata benazeer ta rungumosu a kafadanta.

Da idanu sultana ta bita sanda take aza mata yaran saman cinyoyinta,bata budesu ba ta kalleta
tana murmushi

"Budesu ki gansu" cewar ama. Idanu biyu dukka sultana ta fiddo,sai kuma ga hawayen nan nata da bata
gajiya da xubdashi

"Har biyu ama?,ni ba guda daya kikacemin bane?,har guda biyu?, gaskiya ni guda daya ne.....guda daya
ne Allah" mamakin tarin quruciya irin ta sultana da bata rabuwa da ita ya kama ama

"To biyu Allah ya baki,yanzu a ciki wanne ne bake kika haifa ba?,wace bakyaso?,bude ki kalla ki zaba na
zaba a bada dayan,dayar kuma saiki bata nono kinji kinga duk yunwa sukeji" kuka ne ya qwace mata

"Ni banaso duka,banaso ama,kuma ba Wanda zan bawa......." Sai ta kasa qarasa fadin nonon ta sanya
hannunta mara qarin ruwan tana janye zaninta,abinda ya sanya batoul ta gangaro sosai jikin
benazeer,nauyinta kuma ya sanya benazeer ta gaza riqeta suka fara gangarowa.

A gigice ama ta sanya hannayenta ta fada tallafe yaran zuciyarta na bugawa da tsananin
tsoro,saboda ba qaramin shammatarta tayi ba,dukkansu yaran suka tsanyare da kuka a lokaci guda,da
alama suma din sun tsorata dinne.

Wani irin mummunan baci ran ama yayi,bata tabajin haushin sultana ba irin yau,bata taba jin
rayukanta sun baci dama ko meye takeyi ba irin yau.
"Ke sultana!" Ta kirayeta cikin tsawa,tsawar data kada zuciyar sultana din. Karo na farko a rayuwarta da
tsawa ya taba hadasu da ama

"Ashe baki da hankali?,don baki sonsu sai akace ki kashesu?,yaran da kika haifa a cikin cikinki?,ke haka
kika ga bibi tana miki?,haka kika ga aba yana miki?, oncle bashar oncle umar?,uwa uba mahaifin nasu da
kikaqi jini?,shi ya goyeki a gadon bayanshi,ya baki abinci da hannunsa,yayi maka wanka,wankin kashi da
na fitsari,shine yanzun zaki gangaro qananun yara da ko kwana daya basuyi ba duniya?,to ke kika haifesu
duka 'ya'yanki ne,idan ke kika haliccesu ki maidasu inda suka fito" ta qarasa fada cikin bacin rai tana
debe yaran.

Wani mugun mutuwa jikin sultanan yayi,dukka gabbanta sukayi sanyi,idanunta suka cicciko da
sabbin hawaye,ranta ya dinga yi mata ba dadi da ganin bacin ran ama. A yau zuciyarta ke mata fadan da
ya dace,bai kyautu ta yiwa ama haka ba,matar data tsaya da ita cikin wuya rintsi da dukka tsananin data
fuskanta tsahon watanni goma,bata tana gajiya ba,bata taba sarewa ba,bata kuma taba ja da baya
ba,bai kamata ta saka mata da wannan ba.

Tana jin sanda ama ta fita ta siyo madara tazo ta hada ta bawa yaran,babu jimawa sukayi
luf,bacci yayi awon gaba dasu.

Ama bata sake saurarenta ba,iyakaci ta barta da tanja,tana ji tana gayawa tanja ita yanzun ta
koma rainon jikokinta,ga diyarsu nan. Abun sai ya quntatawa sultana,a fakaice dai ama ta rabu da ita
kenan?. Ko a washegari da mutane sukayita shigowa ganin twins duk wanda ya tambayi mamansu sai
tace bacci takeyi,duk kuwa da idanunta biyu. Sosai turawan suka dinga shigowa ganin 'yan biyu,abinka
da bature wanda baya raina abun kallo. Hotuna suka dinga yi da yaran,gif kuwa sai gashi sun cika wani
sashe na dakin da gifts,har sai da ma'aikata suka kwashe aka kai musu ajiya dakin ajiya dake cikin
asibitin. Wani irin kyau da murjewa yaran sukeyi,kusan kullum Allah ne da kullum amma indai rana zata
fito ta fadi sai masu son ganin yaran sun shigo,kuma dukkansu turawa ne,duk wanda zai shigo kuma da
gift dinsa,suna son yaran kamar su lashesu,akwai cikin ma'aikatansu da kullum a rana sai sun shigo kusan
sau uku kawai saboda yaran,tamkar wadanda aka yiwa yayyafin farinjini,ita dai ama ta sani muddin suka
dauko farinjinin iyayensu to lallai sai ta hada musu da addu'ar baki.

Kwana uku kacal suka sallamesu,har a ranar aman bata sake mata maganarsu ko tayin basu
nono ba,hasalima ita da yaran saidai taji muryoyinsu daga nesa,suna qushin qushin din kuka ko wani abu
daban.
Bata yarda ankai yaran ko ina na,cikin nan dakinsa tasa aka shirya musu gadajensu da komai da
komai,komai nasu pink hot pink da baby pink,komai nasu designers ne,hatta da turaren jarirai na
kamfanin Dior ta siya masu yawa ta ajjiye. Dukka kayan sawarsu kuwa cotton kaya ne masu kyau qwarai
'yan turkey,channel brand,h&m brand,zara brand,Lacoste fendi Balenciaga da sauran manyan brand.
Tanason a san cewa tabbas daga tsatso da ahalin manyan iyali suka fito MAYAK'I FAMILY sannan jinin
babbar 'yar kasuwar qasar nijer da kewayenta hamdiyya ABDU ME KANO ne.

Tsaf ta shiryasu cikin wasu long sleeve body suit masu kyau da taushi na kamfanin channel,ta
nade kowannensu cikin shawl me taushi sannan ta rungumosu kowacce ta kwantar da ita saman
gadonta,ta daidaita qarfin AC din dakin,sannan ta fita zuwa kitchen don ta zuba ruwan zafi a flask dinsu
ta hada musu madara.

NADEEYA ALIYYU MAYAK'I (BENAZEER)

FATIMA ALIYYU MAYAK'I (BATOUL)

_SAI MUCE BARKANKU DA ISOWA TSAKANIN CAKWAKIYAR DADDY MAINA DA MOMMY SULTANA_😂
😂😄

[11/05, 10:00 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 25

Ta dade a tsaye gaban madubi daure da towel,ita bata shirya ba ita bata zauna ba,haka kawai
takejin zuciyarta wani irin empty,sai tarin karaya da rashin confidence. Sake shafa fuskarta tayi a karo na
babu adadi tanason tuna fuskokin yaran,batasan me takeji a kansu ba,soyayya ko qiyayya?,har yanzu
bata tantance ba,abu daya ta sani har yanzu tana iya tuna wahalar da tasha a kansu,ko yanzu da take
goge jikinta sai data kalli wajen da aka yanka cikin cikinta saboda yaran

"Mene makomata?" Tambayar da taketa yawaita yiwa kanta kenan,zata koma nijer ne taci gaba da
fuskantar mutane?,taci gaba da fuskantar qawayenta a haka?,da wacce fuskar?,ita sultana me 'ya'ya har
guda biyu?,duk da ama ta karbesu,duk da ama tace nata ne amma ta sani hakan bazai canzasu daga
sunan 'ya'yanta ba tabbas!. Wanne bigire ta kama?,ina rayuwarta ta fuskanta?,bata sani ba!,bata sani ba
sam sam sam......wannan itace amsar da take bawa kanta.

Qas tayi da kanta, hawayen da batasan ranar daina zubarsu ba suka fara tsiyaya daga idanunta
suna diga saman madubin.

Sautin kukansu cikin muryar rigima sosai ita ta sanyata daga kan nata tana duban fuskarta ta
cikin mudubin tamkar su din zata gani ta ciki. Idanunta ta maida ta lumshe kukan nasu na isketa har inda
take,dukansu su biyun sun dage sai qyaqyata kuka sukeyi. Idanunta ta lumshe,batasan me yasa sam
batason jin kukan ba,ta matsa daga gaban madubin,saita samu kanta da jawo babban mayafinta ta
lullube dukkan jikinta,sannan ta taka a hankali ta murda qofarta ta fice.

Daga dakin ama ne kukan ke fita,ci gaba tayi da nufar dakin amma gabanta yana dukan tara
tara,wata zuciyar kuma na hanata zuwan,sai ta kasa dakatawa,har ta isa qofar dakin ta tura ta bude.

Kanta ta fara zurawa tana leqensu,ba kowa cikin dakin sai su kadai,sun rude da kuka abinsu suna
jejjefa qafa kamar zasu tashi sama

"Ya salam ya Allah" ta fada qasa qasa saboda yadda taji zuciyarta na motsuwa. Batayi tunanin komai ba
ta sanya kanta cikin dakin,ta taka a hankali zuwa gaban gadajensu.

Fes kyawawan fuskokinsu suke,ba hawaye ko wani abu,harararsu tayi tana tura baki gaba,kamar
an gaya musu wacece ita,kamar an sanar musu da matsayinta garesu sai kukan nasu yana baya sosai,da
kadan da kadan yana ja baya,yayin da duk su biyun suka kafeta da idanunsu.
Itama nata idanun ta zube musu, zuciyarta na ayyana mata abubuwa iri daban daban. Banda
wahalar da ita daya tasan kalarta da tasha, tabbas da zatace ba yaranta bane. Dan mutum guda guda har
guda biyu?. Murmushi ya subuce a saman fuskarta karon farko bayan shudewar watanni d'ai d'ai har
kusan wata goma sha daya rabon da ya fita a fuskarta. Miqa musu yatsuntsa tayi d'ai d'ai kowanne ta
cusa shi tsakiyar tattausan tafukan hannunsu. Mamaki ya kamata yadda taji caraf kowacce ta riqe suka
sakeyin relaxing suna kallonta zaka rantse ba jariran kwanaki kadan bane.

"Batoul?, benazeer?" Ta furta qasa qasa tana nuna kowacce da yatsa daidai,tanason ganin ta banbance
sunayen kowaccensu?. Kai ta girgiza tana ganin kamar bata fadi dai dai ba,amma ta tuna taji ama tana
cewa gefan kunnen babbar akwai alama irinta aliyyu. Wani daci ya ratsa harshenta da tuna sunansa
kawai da tayi, qirjinta na quntata ta sanya hannu ta duba gefan fuskokinsu. Taga alamar da ama din ke
fada,kuma haka yake,sak irin nashi,tawadar Allah,tasha tambayarsa meye wannan tare da nacin sai ta
kankare masa

"Nadeeya BENAZEER fatima BATOUL" ta sake maimaitawa kamar me gudun kada ta mance sunan. Sai
taji sunan kuwa ya zauna daram a kwanya da zuciyarta.

A nutse ama ta maida qofar ta rufe bayan ta gama kallon duk abinda takeyi. Sautin rufe qofar
ya sanyata waiwayowa a dan razane gabanta yana faduwa. Ya akayi ta shigo haka ta sakankance ba tare
da tunanin ama ko tanja wani cikinsu zai shigo ya ganta ba?. Kauda kai ama tayi sam kamar bata ganta
cikin dakin ba,ta fiddo kyawawan feeders dinsu guda biyu ta dora saman bedside table tana nufar gadon
nasu tare da fadin

"Bansan kun qagu kusha ba,ashe yunwa kukeji my babies" ta fadi tana fara dauko benazeer da kukanta
yafi na kowa,sannan ta dauko batoul ta iso dasu gaban gadon.

Dole saidai ta fara bawa mutum daya,don tanja ke tayata bawa dayan tanjan kuma yanxu ta
fita,don haka ta fara bawa benazeer sai kuma batoul ta fara qushin qushin. Da idanu sultana dake qame
take satar kallonsu,shan madarar takeyi yarinyar sosai kamar zata hada da feeder din,da alama me cice
sosai

"Wai mutum mutumin sultana aka shigomin da shi ne?,zonan ki zauna ki taimakawa batoul idan zaki iya"
ama ta fadi tana gyara zamanta. A kunyace a kuma mugun darare ta tako ta zauna. Sau biyu tana miqa
hannu zata dauki batoul sai ta fasa
"Har yanzu baki sonsu dinne?" Ama ta jefa mata tambayar da ta sanya babu shiri ta dauki BATOUL din ta
aza saman cinyarta. Dumin jikin yarinyar ya sauka a dukka cinyoyinta,yarinyar kuma ta sake zuba mata
idanu sosai kaman dazu,tamkar tasan yau ne ranar farko da mahaifiyarta ta azata zaman cinyarta,zata
kuma shayar da ita da madara bawai da nonon jikinta ba.

Dukka yadda taga ama tanayi haka tayi,har sai da ama din tace ta zare ya isa haka,ta basu ruwan
zam zam da shine ya ruwam shansu,kuma shi zaici gaba da zama ruwan shansu cewar ama har sai sanda
suka buda baki sukace sun gaji dashi muddin tana raye.

"Sakata a kafada har sai tayi gyatsa" cikin tsoro ta dagatan ta sakatan,suka shiga shafa bayansu ita da
ama din,sai a sannan ama ta magantu

"A qalla idan baki sosu ba ko kulawa ki nuna musu,mafi qaranci dai zasu tashi da ganin kallon rahama
daga idanun uwarsu.......maraici bashi da dadi,ke baki sanshi bane saboda an baki cikakken kulawa da
gata,to kiyi qoqari su dinma koda sun rasa uba susan cewa suna da uwa a raye". Kasa cewa komai
sultana tayi sai qas da tayi da kanta,wani abu yana dawainiya da zuciyarta.

Sanda ama ta lura batoul din tayi bacci tace ta kwantar da ita,lokacin da zata kwantar da itan
kusa da 'yaruwarta ji tayi kamar kada ta kwantar da ita din

"zo ki zauna" ama ta sake fada kanta tsaye da daure fuska,daure fuskar da take sanya ma sultana
shakkarta da kuma d'ari d'ari. A dararen ta zauna

"Ki saki jikinki sosai mana,ki manta ni momynki ce?" Maganar tayi mata dadi sosai,amma sai taji
zuciyarta ta raunana,inda ace uwa mahaifiya a gareta tana raye wala'alla zatafi fahimtar duk wani rauni
da quncinta ko?.

Kamar ama tasan abinda take tunani sai tace


"Zuwa yanzu banajin akwai wanda ya fahimceki kamar ni,akwai wanda zaisan ciwonki da zaqinki kamar
ni......daga yau inaso sultana ta fara sauyawa,inason na daina ganin wannan sultanar,me musu da taurin
kai,inason sassauqar sultana me cewa "eh to" a dukka lamuranta,inaso ki canza zan tallafa miki duk wani
ciwo na zuciyarki ya gushe idan kin shirya" kai ta gyadawa ama tana share hawayenta

"Na shirya,kiyi haquri ama" ta fadi kuka yana tsinke mata. Cikin jikinta ta rungume sultana din tana
rarrashinta. Sai takejin inama komai yazo ne a LOKACIN da ya dace,inama ace aliyyu baiyi gaggawa
ba?,saidai idan ta tuns cewa rabonsu batoul......lokacin wanzuwarsu a duniya ne yayi shi yasa komai yazo
a gaggauce irin haka,sai taji ta sake sallamawa lamarin ubangiji.

Hamdiyya abdu kano,jajirtacciya uwa kuma tsayayya. Itace ta shimfida dukkanin tafukan
hannayenta......ta sadaukar da dukkanin dukiyarta........ta bada lokacinta da rayuwarta ma rayuwar
SULTANA BATOUL DA BENAZEER.....ta sadaukar musu da dukka komai nata,ta kula da yaran ta kuma kula
da uwarsu.

Dukkaninsu babu wanda ya samu naqasun kulawarta. Sau tari tanja kan zauna tayi shuruuu.....
Eh lallai baka taba gama sanin halin mutum sai ka zauna dashi. Ashe wannan itace hamdiyya wato ama
da sukewa kallon me izza,miskila saboda ganin ta mallaki maqudan kudade,wadda bata shiga shirgi ko
sharafin kowa,ashe ita din me sadaukarwa ce,ashe ita din me sassauqar zuciya ce?.

Kulawa da sultana kusan itace ta kwashe mafi yawancin lokutanta. Fitness center ta kaita me
kyau da suke bawa jikin sultana kulawa cikin kula da CS dinta ba tare da ya samu matsala ba,tanason
sultanan ta koma sultana dinta,harma tafi da,tunda zuwa yanzun idan ka ganta zaka tsammaci ta shiga
shekara ta sha bakwai ne bawai sha hudu ba. A gida kuwa lafiyayyun abinci da dukka nau'in ganye da
tasan zai maida sultana mutum,ya murje mata jiki kullum cikin research da hade hadensu take,ruwan
ganyen gwanda daya zamewa ama aboki a baya yanzun ta tilastawa sultana shanshi sau biyu a rana(yana
hada nuna tsufa,yana maintaining jiki,kiyi looking younger akan shekarunki)daya daga cikin sirrikanta da
take taqama dasu.

Sannu a hankali saiga sultana ta fara dawowa SULTANAN BIBI DA ABA,fatarta ta fara ninka
kyanta,duk wata rama tata tana yin nata waje,komai yana komawa kan saitinsa. Tun usul dama
damammen ciki gareta,don haka ko yanzunma ba zace ta taba daukan ciki a cikinta ba, stretch marks ne
yaso fito mata dan kadan a fatar cikinta ama tace bataga ta zama ba. Kudi ta zuba sosai ta siya mata
mayuka masu kyau da dan Karen tsadar da ko a can dimma saika ciza sannan zaka siya,sai gashi sun bace
bat,babu su babu alamunsu,tunda dama bana halitt bane na ciki ne.
Gyaran kai, manicure da pedicure akai akai,so take ta koma sultana cikakkiyar 'yar gayu,cikin
kwana talatin da biyar cif da haihuwar sai gata ta canza,ba zakace itace me jego ba.

Wani irin girma yaran sukeyi tamkar ba madara suke sha ba,wani irin wayo kai zaka ce sun
doshi watanni uku ma. Bul bul dasu kamar ana hurasu, weather din Austria tamkar don saboda su aka
halicceta. Wayo na masifa a cikinsu,sunsan idanun ama sunsan na tanja,don na sultana bai fiya ganuwa a
garesu ba. Bata kyararsu,amma ba kasafai take shiga shirginsu ba,idan suna kuka dai takan daukesu idan
ama bata wajen,amma indai tana wajen saidai ita ta dauka ko tanja.

Cikin kwanakin talatin da biyar din taji dukka hankalinta ya fara komawa gida. Ta yita duba
saqonninta na layinta da email ko zata ga saqon sakinta daga hamid(aba) duk da tasan abune me wuya
amma bata gani ba,sai saqon roqon ta dawo ta email dinta har babu adadi daga aba,saddi atta harma da
almu.

Visa kawai ta shiga nema musu,tana ganin zuwa yanzu lokaci yayi da zasu koma. A yanzun zata
koma da dukka qarfinta ne,zata sanya auduga ta toshe kunnuwanta,ta sanya duk wani effort nata ta
nema inda maina yake,tana da buqatar danta,ba don komai ba kodon yaran da ya dasa baisan da
wanzuwarsu ba,ya kamata su tashi da dumin ubansu. Ba zata sanya kowa neman maina ba,ita daya zata
fuskanci komai,ita daya zatayi fadi tashinta,yadda suka dauki zafi dashi saidai suga dawowarsa
gida......amma kuma hakan ba yana nufin itama ba zata hukuntashi ba bisa laifinsa,amma hukunci ta
hanyar da ya dace.

Sultana batace komai ba bayan ama ta miqa mata passport dinta dake dauke da visa din
Nigeria. Ta danji sassaucin ganin qasar nigeria zasu fara shiga,kwata kwata nijer ta fita a kanta, batasan
ma ta yaya zata fuskanci rayuwa ba a can. Zaman gida zatayi tayi rainon yara?,ko makaranta zata koma
cikin qawayenta da a yanzu ita kanta tasan tabbas ta banbanta dasu?,dukka dai bata sani ba.

********Sun baro Austria cikin matuqar kewa, Vienna garin da suka shuka tarihi a ciki suka kuma
binne,sun fito da benazeer da batoul da a yanzun suke da shaidar zama cikakkun 'yan qasar Austria halak
malak,wanda sanadin haihuwarsu qasar ya basu wannan damar.
Transit ne na kwana guda a Egypt cairo,sun sauke luggage dinsu a gajiye,amma ama tace su shirya
su fita su zagaya,akwai guraren tarihi me kyau da yake da kyau suje din. Tanja na murna ta gama
shirinta,ta kamawa ama shirya su benazeer daketa wutsil wutsil abinsu,kamar sunsan suna kan hanyar
komawa qasarsu ne.

[13/05, 2:25 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 26

Sanda ama ta fito sultana na zaune ta saka tv a gaba tana kallon news,wanda ama tayi imani ba
wani fahimtar me akeyi takeyi ba,kawai tsabar zama miskilar qarfi da yaji da tayi ne duk ta koma
haka,bata doguwar magana bare doguwar hira,dukka kalmominta taqaitatattu ne

"Baki shirya ba sultana,ya kamata muje mu dawo da wuri mu kwanta don mu samu gobe mu tashi da
wuri,jirgi baya jira" ama ta fadi tana taje doguwar sumarta

"Ama na gaji,saikun dawo" waiwayawa tayi ta dubeta

"Ahaaa?......kina da tabbacin sake samun dama irin haka?,baki da tabbas zaki sake ratsa qasarnan,oya
tashi ki shirya" ta fadi tana dan dakewa. Tsam sultana din ta tashi,ama ta bita da kallo har ta shige
bandaki.

Sanda ta fito cikin ido sai ama taga tayi mata kyau ainun. Cikin doguwar rigar Dubai,tayi rolling
kaman yadda ta saba shekarun baya. Ta cika tayi tsaf tamkar babu wani abu dake damunta.

Yawo sukayi sosai gidajen tarihin dake cairo,sannu a hankali sai ta dinga jin zuciyarta na
sakewa,damuwarta dake cunkushe a qirjinta tana raguwa sosai. Saidai duk inda duka gifta sai an tanka
benazeer da batoul,abinda ya sanya dole ama ta sake lullubesu da kyau.
Koda suka shiga daya bangaren na kayan tarihi sai ama ta miqawa sultana batoul. Waiwayawa
tayi ta dubi ama din,sai kuma ta sanya hannunta ta karbi yarinyar ta rungumeta a kafada. Ajiyar zuciya ta
saki a boye,wani abu taji ya zarta ta jininta sanda dumin jikin yarinyar dake cakude da daddadan
qamshin turaren Dior ya sauka a hancinta. Sau tari cikin zuciyarta takanji yaran suna burgeta,irin
burgewa da kake iyaji ga yaran da suke ba naka ba ko kake ganinsu daga nesa. Tun daga ranar da suka
iso duniya cikin ado suke da kwalliya,koda a gida suke babu inda zasu fita to tabbas adonsu na
dabanne,hatta kayan bacci idan ka gansu a cikinsu saisun dauki hankalinka.

A asirce tanja ta saki murmushi tana kauda kai,wato dai so sone amma son kai yafi. Tuni ta lura
da abinda ya sanya ama ta maqalawa sultana batoul,idanuwa ne sukayi yawa akan sultanar,duk da cewa
ba wani sakewa a tattare da yanayinta ko fuskarta,amma ta fuskanci tana ta fusgar hankulan mazaje
dake wajen.

Duk inda ama taga wulgawar kayan yara saita saiwa su benazeer,kayan qyale qyale masu
yawa,su kadai take tunawa,komai ta siya nasu ne.

Sai cikin dare suka koma gida a gajiye,duk da haka ama bata gaji ba sai sata wanke yaran
tsaf,nan suka shiga baccin gajiya.

**********K'arfe daya na rana dai dai motar mallakin hajiya hamdiyya abdu me kano ke shiga
makekiyar harabar gidanta dake garin abuja. Dukkansu ita da sultanan ba wanda bai saukar da boyayyar
ajiyar zuciya ba.

Kafatanin masu aikinta maza da mata dukkansu suna tsaitsaye a harabar gidan domin yi mata
barka da isowa. Sanda motar ta tsaya bakin motar sukayo,kowanne zuciyarsa fal farinciki da
annashuwa,tsoro da fargabar data mamayesu na bacewarta tsahon watanni tuni suka bar zukatansu
daga jiya data shaida musu isowarta,tare da isowar ma'aikata sukayi musayen furniture na gidan,suka
kuma shirya lafiyayyen daki wa benazeer da batoul.

Bilki ce ta karbi batoul,uwa ta karbi benazeer kowa bakinsa fadi yake


"Masha Allahu,ma sha Allah,barka da arziqi sultana" a lokacin da sultanan ke fitowa daga motar cikin
wata baqar doguwar riga me azabar sulbi da daukan idanu. Fatarta da jikinta dukka sunyi kyau,ta dan
murje,saidai qiba ce har yanzu babu ita ba dalilinta,ta zama slimy.

A hankali idanun ama suka sauka kan baqin motoci da take gani a rumfar gidan,sai ta maida
dubanta ga tasi'u

"Malam Tasiu wadannan motocin fa?" A ladabce ya rusuna yana cewa

"Yallabai ne suka zo shi da hajja bibi,yau kinsan ake bikin bude kamfaninsa na nan abuja" kai kawai ta
gyada,ta san da company din,wanda ya dauki shekara da shekaru yana gininsa tare da tanadin ranar
budesa,tabbatuwar kamfanin kuma zai iya sanyawa zamansu yafi yawa a Nigeria ne garin abuja saboda
yawan hada hadar da a kullum aba din zai dinga gudanarwa.

Ciki dukkansu suka dunguma,tana jinsu bilki sun barke da hira da tanja hirar yaushe
gamo?,sunata kwasar tanjar wai ta sauya quruciyarta ta dawo,itakam sai dariya kawai take musu.

Dukkan wani abu da zaiyi cikin watannin da sultana da ama sukayi baton dabo yana yinsu ne
tuquru don wanke duk wani ciwo da radadi na batan sultana a zuciyar bibi. Ko a yanzun da duke
dawowa su biyu rak cikin motar bayan ya karbi tuqin daga hannun driver dinsa ajiyar zuciya ta saki

"Har yanzu hamidou zuciyata ta kasa nutsuwa,har yanzu ina ganin cewa nice silar faruwar komai,inda
nasan sultana na buqatar cikin,inda nasan da gaske hamdiyya take tana da buqatarsa itama,da na ajjiye
nufi na,ba hamdiyya ba sultana..... shima maina tunda ya tafi....."

"Ki ajjiye batun maina,ba mune mukayi masa laifi ba,shi yayi mana laifi,sannan ya zabi tafiya ya
barmu,koda kasheta yayi a yanayin da ya barta bashi da asara" ya furta maganar yana ciro wayarsa da
yaji alamun kira ya shigo. Baikai ga daga wayar ba kiran ya katse,sai text din hamdiyya da ya shigo kusan
awanni biyu baya,rububin taro ya sanya bai gani ba sai yanzun da ya samu ya sullubewa jama'a yayi bad
da bami a mota daya ya taho gida kawo bibi ta hut sannan ya koma.
Hannunsa har rawa yake sanda ya karanta layi guda kacal na saqon,ita dai bibi batasan me
yake faruwa ba,taga dai ya qarawa motar uban gudu bayan ya aje wayar da hanzari a gefensa

"Lafiya hamidou?" Bibi ta tambayeshi tana dubansa

"Hamdiyya ce ta dawo,ina kyautata zaton suna nan cikin abuja" ya bata amsa yana sake bakwa kwalta
hankalinsa sosai. Idanu bibi ta fidda cikin wani mugun zumudi da ba zata

"Hamdiyya?,ita da sultanan?"

"Eh na tabbatar tare suke" ya amsa mata yana sake qara tsula gudu abinda sam ba al'adarsa ba

"Allahu qadiran Ala man yasha'u" bibin ta furta hankalinta yana daguwa,jinta takeyi kamar tayi
tsuntsuwa ta isa gidan,sai kawai tayi luf jikin kujera tana kiran sunayen Allah a jejjere.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN K

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 27

"a hankali bibi" aba ya fada lokacin da yake tsaida motar tasa bibi na qoqarin budewa ta sauka. Ai bata
saurareshi ba sai data tabbatar qafafunta sun taka qasa. Da sauri ya fita a motar yabi bayanta,yasan tana
da ciwon qafafu,a yadda kuma take gaggawar kaiwa ga sultana yana gudun kada ta sarqe.

Dukka muryarta ta ware tana doka sallama kamar baquwar gidan,ta daburce gaba daya,saboda
batasan ta inda zata fara ganin sultana ba.

Tana shirin shiga wanka taji kamar muryar bibinta,kamar muryar da kullum take mafarkin ji,sai
kawai ta jawo babban mayafi ta yafa a kanta tana nufar qofar fita.

Qarar bude qofar ya sanya bibi maida kallonta gurin,sultanarta ce,itama sultanan bibin take
kallo,kallo kallon suka hau yiwa juna kamar wasu baqin juna,sai kuma daga bisani sultana din ta nufo bibi
cikin sassarfa tana kiran sunanta da rawar murya.

Jikin bibi ta fada bibi din ta maida hannayenta ta rufeta gam

"Sultana?" Itama bibin ta dinga maimaitawa tana jin wani irin abu cikin zuciyarta,abinda ya karyar da
zuciyartata kenan hawaye masu sanyi suka saukar mata.

"Bibi" itama ta sake maimaitawa kowannensu hawaye yana fita a idanunsa. Da kyau bibi ta riqeta suka
qarasa saman kujera,sai kawai sultana din ta kifa kanta saman kafadarta tana sakin sabon kukan.
Ya zata iya kwatantawa bibi abubuwan data fuskanta?,baki bazai iya bayyanawa ba,
gwagwarmayar data ratsa har ta kawo yau din ita kadai tasan abinda taji,ba mahalukin da zai iya
fuskantarta,wannan din wani abune da yake tsakanin zuciya ruhi da kuma gangar jiki ne kawai.

Kasa cewa komai da ita bibi tayi,sai sharar hawayen itama da takeyi aba yana tsaye a kansu yana
basu baki,saidai fiye da rabin hankalinsa shima yana tsakanin falon da kuma qofofin da falon ke dauke
dashi,yana son ganin ta inda ama zata bullo.

Dukkaninsu taga shigowarsu ta cctv camera din dake hade da system din gefan gadonta,amma
bata motsa ba,sai data kammala shirya yaran tsaf bayan ta musu wanka,ta nadesu cikin overall set da
wasu irin huluna masu kyau da suka boye tattausan sumarsu me azabar baqi da sulbi,fuskokinsu sun fita
tarwai da wani irin haiba da annuri.

Nannadesu tayi cikin tausasan shawl sannna ta sanyasu a kafadarta hagu da dama,ta zura
slippers dinta ta taka zuwa hanyar fita.

Duk da cewa takunta baya bada wani sauti amma sai fitowarta din taja hankalin bibi da aba tamkar
wadanda aka jonawa mayen qarfe. Kasa miqewa bibi tayi,daga ita har aba bin ama sukayi da kallo har
zuwa sanda ta qaraso ainihin cikin falon da sallama a bakinta.

Wuce aba tayi kaman ma bata ganshi ba,ta isa gaban bibi a nutse ta sauke yaran daga kafadarta
tana kwantar dasu a gaban ama tana jeresu daya kusa da dayar,sannan ta miqa hannunta tana yaye
shawls din da suka lullube fuskokinsu.

Dukkaninsu suka kai idanunsu kan yaran,tamkar an jona musu shock haka sukaji cikin jikinsu

"Subhanallahi wabi hamdihi, subhanallahil azeem" bakin aba ya furta yana tasowa da gaggawa daga
tsaiwar da yayi daga jikin bango.

Gaban yaran ya qaraso ya zube,yasa hannu ya tallafawa bibi da hannuwanta ke rawa tana son
karbar yaran,ya dauki benazeer ya dora mata ita saman cinyarta.
"Ya Allahu,ya assamadu" shine abinda take maimaitawa tana juya yaran qwalla na sauko mata

"Astagfirullah, astagfirullah....." Ta sake maimaitawa tana jin qirjinta na mata nauyi,har cikin jini da
zuciyarta takejin wani irin nauyin ubangiji,har ruhinta takejin wata irin kunya tana saukar mata,yanzu
wadannan halittun da taso a murqushe?, yanzu wadannan ruhin taso a niqeshi yabi rariya?.

"Allah na tuba,Allah ka yafemin,Allah kada ka barmu da soye soyen zukatanmu" ta dinga maimaitawa
hawayenta yana qara yawa

Hannu ta miqa tana shafa fuskokin yaran,idanuwanta a kansu tana sake tsarkake girman zatin
Allah.

"Ga jikokinku nan,kuma 'ya'yan jikoki,wadanda kukaso gushewar rayuwarsu kafin isowarsu duniya,nayi
dukkan abinda nakega ya dace nayi,ga sultana nan na dawo muku da ita,yaran kuma zan riqesu,Allah ya
rayaminsu" ama ta fadi hawaye yana cika idanunta taf ta sanya tafin hannunta tana sharewa

"Inaaa hamdiyya,kece kika cancanci mu bawa haquri,kece kika cancanci wannan yabon,abinda ya
kamata tunaninmu yakai kai ya gaza kaiwa kece naki tunanin yakai,kika fiddamu daga halaka zuwa
hanyar tsira,inda ace na aikata abinda son zuciyata ya gayamin a sannan tabbas da zuwa yanzu ina cikin
fushin Allah,ku yafemin 'ya'yannan da naso kasheku tun baku shaqi iskar duniya ba" bibi ta fadi tana
sake kuka.

Iya yadda bibi ta rame kadai ya isa ya gayama ama ba qaramin tashin hankali take ciki akan
tafiyarsu ba. Cikin zuciyarta wani abu ya darsu me kama da tausayin bibi cikin ranta

"Zo nan hamdiyya,yaki" Bibi ta furta tana miqawa ama hannu. A nutse ta qarasa gaban bibin,ta
tsugunna,har a yanzun tana jinta a matsayin suruka,kuma har yanzu babu abinda ya sauya. Ta sani
dukkan wata zuciya cike take da son rai,saidai idan Allah ya baka ikon fin qarfin zuciyar taka.
"Allah yayi miki albarka,kiyi afuwa a gareni" bibi ta fadi tana dafa hannuwan ama. Qas tayi da kanta tana
jin nauyin bibi din

"Ya wuce bibi,ya wuce har abada"

"Na gode hamdiyya" ta sake fadi tana sake duban fuskar yaran daya bayan daya,tare da tunanin da waye
sukayi kama

"Wanne suna kika basu?" Bibi tayi tambayar sanda ama ke tashi ta zauna sosai saman kujera kamar
yadda bibi ta buqata a tare da ita

"Nadeeya BENAZEER da Fatima BATOUL" a nutse aba ya daga kai ya dubeta karo na biyu yana jin kimarta
na daduwa cikin ransa,yayi tsammanin zatayi zuciya ne,ta saka sunanta da kuma sunan duk wanda taga
dama,sai gashi ta watsa komai a baya,ta sanya musu sunayen mutanen da suka kasance tsani na
samuwarsu.

A hankali aba yakai bakinsa kunnen kowaccensu yayi mata addu'a,ya sauke batoul a nutse
saman cinyar ama sanda ta fara mutsu mutsu yana miqewa idanunsa suna satar kallon ama. Ya sani
akwai zantuka da yawa wadanda a yanzun ba zasu fadu ba,ba kuma zasu yiwu a tattauna ba,zai jira
lokacin da ya dace.

Ta sani abinci suke da buqata a yanzun,don tunda suka taho daga Egypt bacci sukeyi abinsu
basu buqaci madara ba,sai ama ta juya tana kallon tanja data rabe tana jin nauyi nauyin ama

"A sama musu ruwan zafi zan hada musu madara" dubanta bibi tayi

"Madara kaman yaya hamdiyya?,ko zasusha madara nono ai ya kamata a fara basu ko tukunna,idan
basu qoshi ba saisu qara da madarar"

Ama bata dubi bibi ba tace


"Madarar sukesha,itace abincinsu" ta maidawa bibi amsa tana gyarawa benazeer kwanciya.

"Ina nonon uwarsu?" Maganar ta zowa sultana a bazata saboda ta tsammaci bibi zata bar maganar
ne,sai gashi kuma ya jefo da wata tambayar.

Waiwayawa bibin tayi tana duban sultana,a hankali sultana din ta jawo gaban mayafin jikinta
tana sake suturce qirjinta da bibi ke kalla

"Hamdiyya kada dai kicemin hanasu nono tayi" bibin ta fada da wani irin zafi a muryarta abun yana
tabata. Kai ama ta girgiza

"A'ah,kawai dai bata taba gwadawa bane"

"To yau kuwa zata gwada yau dinnan" bibi ta furta da gaske tana zunkudawa gaba.

Dukka idanunta sultana ta fidda waje tana zarosu,nonon nata za'a zuqa kuma?,tashin hankali.

"Aje a nemo min wannan maganin duk inda yake a garin abuja,a fiddo da dukka bournvita din dake gidan
nan da madara,daga yau zuwa safiya nakeso ruwan nono yazo yara su kama abinsu" sosai sultana ta
sake gwalalo ido gabanta yana faduwa

"Da kin bari bibi,tunda sun riga sun saba da wannan ai..... Bakiga kuma yadda ya karbesu ba?" Ama fada
tana tana fuskar bintou

"Kinga hamdiyya ki daina bata bakinki,darajar nonon uwa daban da madarar bature,kinsan Allah?,
billahillazi daga yau su da madara saidai a matsayin ciko" kuka sultana ta saki tsoro yana kamata,yanzun
ace nononta zasu tsotsa?, fisabilillahi har mutum biyu?,ta ina?.
"Don Allah bibi kiyi haquri"

"Yo ai bansan baki da imani ba,haba sultana,kece za'a ce kiyi haquri dai,don nono kaman sun shashi sun
gama" idanu sultanan ta wuwwulga a falon,ba wani sauran me cetonta,aba ne ya rage dama,shi kuma
tunda aka fara batun shayarwar ya fice.

Duk irin kukan da sultana keyi saboda tsananin tsoron shayarwar bai damu bibi ba,nan ta
gwaggwafe hada wannan tsuma wancan,zuwa safiya sai ga nono yazo.

Bibi da kanta ta taka ta amso benazeer da batoul daga wajen ama,wadda tuni tayi musu wanka
ta shiryasu tsaf sunata tashin qamshi sai tsotsar baki suke,da alama dama a yunwace suke. Qin bin bibi
ama tayi kada tausayin sultana ya mata tasiri ta hana abinda ita kanta tasan shine dai dai,abinda ya
sanya bata taba tilastata ta basu din ba alqawarin hakan ta yiwa kanta,kuma bata fatan hakan ya haifar
mata da wani raunin cikin zuciya,ko taga kaman aman tana biyewa soye soyen zuciyarta ne tunda ita din
bataso,biyayya kawai takeyi.

[17/05, 11:58 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 30

"Yaran ummin aneesan fa?,suma ba kano din suke tafiya ba?,don Allah aba kada ka hana,kada kuma ka
bari ta gane zucoyarka tayi rawa akan al'amarin,muna da buqatar mu.maida sultana ainihin mutum,aikin
da maina ya gagara yi inaso na aiwatar masa,koda baya raye na tabbatar hakan zai bashi sukuni cikin
kushewarsa" ta qarasa fada zuciyarta na yin wani irin nauyi. Shuru yayi tun daga lokacin bai sake cewa
komai ko ya nuna baiso din ba,hasalima da dukka kudinsa ya bayar akayi komai daya dace,itakam
sultanan ma batasan meke faruwa ba,don rayuwar kebe kai tafi komai yi mata dadi a yanzun,sai ayi abu
cikin gidan sau babu adadi amma bata sani ba.
K'arfe tara na dare ta tura qofar dakin sultana din ta shigo. A lokacin benazeer na rungume a
kafadarta tana taba rigima,batoul na cinyar aba tana bacci,don ita din ba kasafai ta fiya rigima ba.

Da shanyayyun fararen idanunta ta waiwayo tana duban ama,kafin ta janye idanun nata ta
dorasu akan benazeer da aman ta kwantar mata saman gadon,sai kuma ta dauke duban nata daga kan
benazeer din ta sake maidawa fuskar ama

"Hala shirin kwanciya kikeyi?" Ama ta tambaya tana sake qarema sultanan kallo. Ta sauya sosai,har
yanzun dai batayi qiba ba,amma jikinta yayi kyau kai sai ka rantse bata taba sanin d'a namiji ba bare ayi
zancan haihuwar 'yan biyu,wannan kyawun nata ya sake fita da wani irin sirri na cikar cikakkiyar
mace,idanunta sun sake girma da haske,hatta da idonta dayan da ya samu dan matsalar da sai ta sanya
masa glass babu lallai kai ka fahimci hakan saboda yadda suma suka bude fes dasu kaman dayan.
Gashinta ya wani sake cika kamar kowacce gaba ta jikinta ke fara nuna girma na asali bawai girman da
samuwar ciki ya tilasta zuwansa ba.

"Eh ama" ta amsa mata tana bude man shafawarta sannan ta koma ta zauna saboda ta fahimci da
magana ama din ta shigo.

"Ya kamata,sultana"

"Na'am ama" ta amsa mata a sanyaye tana fatan ba wani sabon abu bane kuma ya taso

"Kinsan rayuwa babu abinda yakai ilimi dadi da daraja,babu kuma abinda yakai ilimi maidaka cikakken
mutum haka ne?" Kai ta gyada a sanyaye karo na biyu

"Mun yanke shawara,in sha Allah nan da sati biyu masu zuwa tare zaku wuce kano tare da yaran ummin
aneesa,zaki fara makarantarsu,saidai mun roqi alfarmar koda daga j.s3 ne idan hakan ta samu" ama ta
qarashe fadi tana zubawa sultana idanu. Kai ta jinjina,ita a yanzun batajin akwai wani abun da zai taba
mata zuciya,ko ya sosa mata rai,batajin akwai wata tsana ta wani abu cikin zuciyarta da zatayi girman
tasirin wutar tsana da qiyayyar dake ruruwa yanzu haka a zuciyarta
"Allah ya kaimu" sultanan ta fadi a sauqaqe kai tsaye kuma ba tare da taji komai cikin zuciyarta game da
batun ba. Sake kiran sunanta ama tayi a karo na biyu,sai ta kuma amsawa tana duban ama

"Ki daure kiyi karatu sultana,banason wadanda suka sanki a shekarun baya su sake ganinki dai still yadda
kike,ba wani ci gaba,babu kuma abinda ya canza daga gareki" murmushin qasan zuciya ne ya subuce
mata,tadan murmusa ta yadda ita kanta ama din ba zata gani ba,ita wai meye ya ragewa
rayuwarta?,bata da MANUFA burika da fata na rayuwarta dukka sun jima da bizne kansu cikin qarqashin
duk wani buqatu na rayuwarta gaba daya.

*********K'arfe takwas na safiya suna qofar gidan ama,yaran ummin aneesa da suka kasance 'yammata
kamarta a shekaru ne. Anata zuba kayansu cikin mota,sunata kuma kai da kawowa cikin 'yar hargowa da
rigingimu nasu irin na sako da sako.

Daga gefe daya sultana na tsaye kawai,jingine jikin motar. Sanye take da uniform da yayi matuqar
karbarta ainun,idanunta saye cikin farar kwalbar glass wanda ya zame mata tamkar ado,ba zaka taba
tunanin lalurar idanu bane suka sanyata sakasu,sun amsheta ainun,sun kuma qarawa zagayayyun
idanunta wani irin kyau da kuma kwarjini matuqa.

Sai da aka gama komai tas sannan ta buda motar ta shiga,ama ta shiga gaba dauke da BATOUL,
goumar ya buda gidan baya dauke da BENAZEER yanata cakularta da wasa tana qyaqyacewa da dariya.
Shigowarsa gefanta ya sanyata daga shanyyun kewayayyun idanunta ta kalleshi dasu. Kusan tare suka
kalli juna,wannan yayi sanadiyyar haduwar idanunsu guri guda.

Hasken fararen idanunta ya dakeshi sosai,yayi saurin zare idanunsa shima yana ci gaba da
tsokanar benazeer suna sake cikawa sultana kunne. Basu kuma bar kunnuwannata sun huta ba har suka
isa airport. Wannan karon su aneesa nata murna,sun huta dogon zaman mota daga abuja zuwa
kano,tafiyar jirgi ce cikin mintuna qalilan zasu isa.

Basu kuwa dauki lokaci ba,duka duka mintuna qalilan suka sauka a filin sauka da tashin jiragen
sama na malam aminu kano,daga can din kuma suka samu daya daga cikin motocin dake zirga zirga cikin
airport din ta daukesu zuwa HASSAN IBRAHIM GWARZO.
****Motoci da dalibai fal qofan makarantar. A irin wannan lokacin akan samu cikowar mutane irin haka
da ababen hawa.

Cikin lokaci qalilan suka isa office na shugaban makarantar,ama tayi dukkan abinda ya dace
goumar yana tsaye yana rungume da twins. Daga goumar din sai ama,su biyun kacal sukafi sakewa dasu
fiye da kowa,sun gane goumar sosai kamar yadda suka gane ama din.

Tattaki suka yima sultana har zuwa hanyar da zata sadata da bangaren mata. Iya ama da su
benazeer,don goumar tun daga can mararrabar section din maza da na mata suka dakatar dashi. Haka
tsarinsu yake,kome alaqarka da mutum ba zasu tabi bare ya tsallake wannan shingen ba muddin ba
section din jinsinka bane.

"Allah ya bada sa'ar karatu sultana,shikenan sai munzo visiting?" Ama ta fadi tana duban fuskarta. A
sanyaye ta daga kai ba tare data dubi ama ba,hankalinta yana rarrabuwa akan yadda rayuwa zatazo
mata cikin makarantar. Ta gani komai da ama ta shigar ta shigar dashi ne dai dai da na kowacce yarinya
matashiya budurwa.

"Shikenan,Allah ya bamu alkhairi" ama ta sake fadi,sai sultana din ta kuma jinjina kai kana ta fara taku
daya biyu zata wuce ciki,saidai kuma batasan dalili ba,can qasan zuciyarta takejin wani irin nauyi yana
mamayarta,kamar akwai abinda takeson aiwatarwa,kamar akwai abinda zuciyartata keso wanda ta gaza
yi mata shi

[20/05, 6:43 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 33

"muje kiyi wankan kafin lokaci ya qure" Metron asabe ta fadi tana amsar mata bucket. Ba musu ta miqa
mata,Metrom tayi gaba sultana na biye da ita. Duk sai su fatima suka bita da kallo,can qasan ranta itama
sultanan tana mamakin yadda metrom din ta kebeta ita daya.
Toilet dinsu da iya su yasu ta sanya muqulli ta bude ma sultanan ta shiga. Duk da a tsaftace yake
amma sai ta dinga jin wani bawai. Sam baiyi koda rabin toilet din da ma'aikatan gidansu ma ke shiga ba.
Hakanan tayi wankan a gaggauce saboda jaddada mata iya sauran lokacin da ya rage da Metron tayi.

Koda ta isa hostel an fara counting an kusa kaiwa qarshe,hakanan tabi lafiyar gadonta ta
kwanta. Bata wani matsawa kanta can bama baccin ya dauketa kasancewar tana da buqatar yinsa,don
tsahon rayuwarta bata taba daukan lokaci haka yini guda tana a tsaye ba,bata jurewa wahala aam,shi
yasa take gudun islamiyya kamar me?. Babban abinda ya sanya ta tsani boko kuwa baccin safe da take
hana mata,ta tsani tana bacci a yanke mata shi,yanzun zakaga bacin ranta.

Ilai kuwa tana tsaka da baccin sautin muryar fatima ta ratsa kunnenta. Bata gama wartsakewa
daga bayanin fatiman ba taji wannan kakkaifar muryar wadda tamkar an halicceta ne don qididdige
musu mintuna ta fara musu lissafi. A kasalance ta jawo hijab dinta na house wear ta zura,ta sauke
qafafunta qasa tana saukowa daga saman gadon tana jan wani mugun malalacin tsaki. Kanta gaba daya
sara mata yakeyi,wannan wanne irin stress ne haka?.

Sallah suka sake wucewa sukayi cikin jam'i kamar dai ta azahar,sukayi dukkan azkar sannan suka
wuce babban filin da suke zama don maimaicen karatun da akayi a ranar. Yana daya daga cikin dokoki da
qa'idan makarantar. A bisa radin kansu kowanne zaiyi muraja'ar karatunsa,cikin rukuni,idan kuma anso
awarwartsasu kowa shi kadai. Ajinsun ta lura suna da himmar karatu,team guda sukeyi suna yiwa juna
tuni da qarin haske,a yanzun ma hannunta saman habarta,littafinta a bude amma kuma idanu ne nata.
Ta baza dukkan hankali da nutsuwarta amma har yanzun bata fahimci komai ba,sai ta sauke ajiyar
zuciya,wani abu yana darsuwa cikin zuciyarta,wani abu da bata taba jin irinsa ba sai a wannan karon.

Sha'awar taga ta iya karatunta kaman kowaacce daliba,tana karantashi sosai kamar yadda taga
Fatima ahmad da ameena aleeyu nayi,bisa dukkan alamu ma sune jagororin zaman,ta fahimci suna
ganewa matuqa,sai suka dinga bata sha'awa ta dinga binsu da kallo.

Karfe biyar suka koma hostel,masu wanka gyaran gado,saka net duka suna aikinsu,tana zaune
tana sake nazarin kowa tare da bin kowa da kallo. Ameena aleeyu ta taba kafadarta tana kallonta
"Ki gyara gadonki sultana,kinsan komai namu yana da qayyadadden lokaci,qarfe shida zamu fita a
nan,idan ka wuce haka kuma sai kayi zaman istigfari,ga punishment" ta qarasa fada tana dariya saboda
tuna makarar da Fatima ahmad tayi wata rana da lokaci ya qwace mata

"Wai dama istigfari din da ake tsareka kayi shima wani azabar ne ban sani ba?,saika bude duk muryarka
ka qwala da qarfi kamar wanda kake saka ran mutanen sama su tayaka lissafawa?" Maganar ke sanya
ameena aleeyu dariya har yau,duk sanda kuman tayi dariyar fatiman tasan da ita take,to in sha Allah sai
takai mata duka. Kamar yanzun ma dundu ta bita dashi tana sauke net dinta,ameenan ta qwace tana
gocewa,sai Fatiman ta zarto gadon sultana tana cewa

"Tashi na kama miki mu gyara muyi mu fita da wuri" ta fuskanci duk irin gatan da suke taqama dashi
sultanan ta damesu,ta sake tabbatar da hakan sanda sultana ta kasa tabuka komai. Batasan ta yadda
zata kama zanin gadon ta zaunar dashi sosai saman katifar ba ballantana net din da bata taba bacci
qasan net irinsa ba,na saman gadonta ba irin wannan bane sam sam sam,aba ne ya siyo mata shi
musamman daga turkey,daga gadon har net din,shi kansa duk da kyau da tsadarsa bata fiya shiga ciki
ba,don gidan kwata kwata basusan wai wani abu da ake kira sauro ba bare sauran qwari,gida ne dake
bisa tsari yake samun cikakkiyar kulawa daga ma'aikata kowanne lungu da saqo na gidan

"Kaman haka a irin wannan lokacin muke gyara makwancinmu,duk lokaci irin wannan sai na tuna da
talatu" fateema ta fadi tana dariya dariya

"Suna qoqari sosai,a lokacin bakasan zafin abun ba,sai yanzu da rayuwar makaranta ta gaya maka"
ameena itama ta fadi tana tata dariyar. Lokaci lokaci sukan zauna suyi hirar masu aikin gidajen
nasu,zuwansu makarantar ya sanya suka qara ganin kima da matsayinsu da kuma girman hidimar da
suke musu.

Hannu kawai sultana ta sanya ta dafe goshinta,itama tanja ce ta fara fado mata,sau daya kuma
koda wasa bata taba daga tsintsiya da sunan share dakinta ba,hatta suturarta idan ta cire tanja ke killace
mata,me taci?,me zataci,dukka suna wuyan tanja,hatta panties nata washing machine ke hidimat wanke
mata su,yau gata cikin rayuwar yiwa kai komai,ba kuma cikakken 'yancin lokaci,sai iya abinda aka
qayyade maka.
"Ya Allah" karon farko ta furta sunan ubangiji da a lokacin zuciyarta ke ayyana mata shine zai dafa
mata,ta waiwaya ta sake kallon gadon tana mamakin yadda fateeman ta gyarashi tsaf,ita dinma kamarta
kenan take ada?,dole ta sanyata koya?,ta yaya ta kuma ina ita zata fara nata koyon?.

A masallacin sukayi magariba,suka sake komawa kitchen sukaci abincin dare,sukayi isha'i sukayi
tilawar litattafan addini sannan suka wuce makwanci.

Kamar jiya din,yauma da farko juyi ta dinga yi,gaba daya yininta na yau take nanatawa cikin
ranta. Wata irin rayuwa data banbanta da rayuwarta,ta banbanta da rayuwar data saba yi,yau gata
tsundum cikin makaranta, makarantar da babu abinda ta tsana sama da ita,yau sai gashi ba jeka ka dawo
bama makarantar kwana ce. A Hankali tunaninta ya gangaro kan yadda rayuwar karatunsu take. Kowa
kusan gwanine za'a ce cikin daliban,tana hangen yadda kowa ke zagewa ya kuma dage don ganin ya kai
maqurar iya karatunsa,ta tuna yadda a kowanne darasi ta dinga baza idanu,nan da wani lokaci idan
batayi da gaske ba zata zama cikin sahun dalibai na kashin baya,wadanda kowa zai fahimci qarancin
ganewarsu. Wannan tunanin ya sanyata hantsilowa daga gadonta,wani abu yana dasa mata qaimi cikin
zuciyarta,tana jin ba zata lamunci faduwa ko rashin iyawa ba. Ta saka hannu gefan gadonta inda
qaramar locker dinta take ta fidda jakar makarantarta,ta zazzage dukka litattafan da a yau sukayisu,ta
soma budesu daya bayan daya tana dubawa.

Da qur'ani ta fara,ta dinga hada baqin yana guduwa,ta dinga qoqarin maimaita shafukan
daidai,a haka ta kashe awa daya kusan da rabi kafin taji ta fara kama hanyar karatunta bisa qa'ida. Bata
sare ba bata kuma gaji ba,tayita nacin maimaitawa har sai da taji ya zauna mata a harshenta,ta tabbatar
zuwa gobe koda za'a ci gyaranta kadanne. Kowanne subject sai da tayi maimaicinsa,tun bata fahimtar
abinda take ta faman karantawar har sai da taji kamar qwaqwalwarta tana budewa ne a hankali. Sanda
ta duba agogo awa uku kacal ya rage lokacin tashinsu dsga bacci yayi. Sai ta zauna tsakiyar gadon tana
son tuna addu'a daya daga cikin tarin addu'o'in da taji suna yi,yayin tashi a bacci,kwanciya bacci,cin
abinci,shiga bandaki,shiga aji da komai ma na rayuwar daliban makarantar. Ba wani abu guda da taga
wani dalibi yayi bs tare da yayi addu'a ba,tamkar ma ta shiga jinin jikinsu ne sun kuma saba. Duk sallolin
da akayi yau din cikin jam'i abinda bata taba yi ba tsahon rayuwarta......duk sanda aka idar suka hada
baki duk yawansu suna addu'o'in da akeyi bayan idar da sallah,sai taji wani sanyi dadi da nutsuwa suna
shigarta,sai taji wani sukuni yana ratsata,har sai taji kamar ma kada lokaci ya cika, kamar kada su daina
addu'ar.

Waiwayawa tayi ta dubi su fatima dake bacci abinsu. Cikin ranta ta ajema kanta zasu zame mata
mudubi in sha Allah cikin rayuwar makarantar,zata kuma yi qoqari tayi catching up na dukkan abinda
suka tsere mata.
Abunda ya bawa su fatima mamaki a yau ita ta tashesu maimakon jiya da sune suka
tasheta,kafin kace meye ta kammala komai da sukeyi kafin fita masallaci sallar asuba. A bakin hostel din
suka cimmata tsaye da metron asabe tana gaidata

"Ina fatan baki da wata matsala ko?,idan kun kammala karatu kina da sha'awar wanka kafin ki wuce aji
kiyimin magana saiki shiga kiyi"

"Ba komai,zan jira har lokacin da kowa yakeyi,idan ban samu toilet ba zan miki magana sai nayi s
gurarenku din" ta amsa mata tana rungume da qur'aninta cikin wata murya me sanyi. Da kallo metron
asabe ta bita,bata taba zaton zata sameta da sauqin kai har haka ba,bata taba kawowa cewa zatayi
saurin daukan shawararta ba,sai gashi daga jiya zuwa yau kacal tana qoqarin kiyaye dokar makarantar.

Yadda ta dinga nacin bibiyar kowanne harafi da ake qara musu ya sauqaqa mata qwarai. Kafin
akai ga tashi sai gashi ta iya karatun fes kamar kowa. Dadi sosai ta dinga ji cikin ranta,har kuma hakan ya
nuna a fuskarta,duk da ba murmushi takeyi ba amma fuskarta a washe take sarai.

Gurin sharar compound na hostel dinsu kuwa kamar kowa ta karbi tsintsiya. Metron asabe na
cewa ta bari amma tace zata iya. Tana sharar tana mamakin meye dalilin metron asabe nason dauke
mata wasu wahalhalu na makarantar ne?,me yasa take kawo mata hanyoyi sauqi da
sauqaqawa?,ahalinta ne fa da hannunsu suka danqata a makarantar,komai na ama bisa manufa da tsari
yake,ta tabbatar ba a banza ama ta aikata hakan ba,ba shakka akwai dalili,kuma akwai hujja.

Koma meye ita dai ta barma ranta zata rayu kamar kowa,tayi alwashin zatayi irin rayuwar data
samu cikin makarantar,zata rungumi kalar sabuwar K'ADDARAR da ta risketa. Can kuma qasan ranta
takejin kamar dai ama ta kawota ne don tasan rayuwa?,kamar dai ama ta kawota ne don ta fahimci
bayan duniyar da take rayuwa a ciki akwai wata duniyar ta daban?,kamar dai ta kawota ne saboda wasu
abubuwa masu yawan da ita kanta bata gama fahimtarsu ba.

Tana ankare da yadda labour prefect huda keta wani fusge fusge da sanya mutane aiki cikin izza
da gadara. Duk wanda ta kira ita da team dinta da sassarfa yake isowa ya kuma zube yana kiran
"Aunty gani" ladabi ne wannan na makarantar da dole kowanne dalibi ya koya ya kuma ginu akai,amma
batajin zata iya zube musu har haka,hasalima batajin tana da LOKACIN shiga sharafinsu.

[20/05, 6:43 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 34

Lokacin data sake kame kanta tare da takatsantsan da lamarin huda da sauran maqarrabanta
ita kanta sai tayi mamakin kanta,har batasan sanda qaramin murmushi ya subuce mata ba abinda ta jima
bata yishi ba,wai yau ita sultana ita ke kaucewa rigima da wasu,ita sultana da batajin tsoron rigima da ko
waye,mace ko namiji,yaro ko babba,bata tsoron tunkararka ko qaddamar maka,lallai giwa tayi lafiya ta
fadi qasan zuciyarta tana shafar gefan fuskarta,to ko hankali ta soma yi?,ta yiwa kanta tambayar data
sanyata sakin wani murmushin.

*****A hankali A hankali cikin wani irin yanayi sauyi na bazata ke ruskar rayuwarta. Ingatacce kuma
gamsashen sauyin da yayi nasarar taba ainihin ruhi da zuciyarta. Cikin ba zatar da ita kanta bata sani ba
ta tashi daga SULTANAn bibi,sultanan aba sultana ta nijer zuwa sultanan Nijeria,sultanan hassan Ibrahim
gwarzo,sultanan fateema Ahmad da kuma ameena aleeyu. Ba wanda take bari ya huta tsakanin fateema
Ahmad da ameena,kowannensu ta samu ta riqeshi to tabbas sai yayi mata qarin dukkan wani kwantan
karatu da aka tsere mata,tashin cikin dare ya fara bin jikinta,a lokacin da kowa ya sanya haqarqarinsa
yake bacci.....a lokacin take tashi bita da tilawar katatuttukanta. Cikin kowanne mataki na karatunta
batajin akwai ya kamar ALQUR'ANI. Tana jinta wani fresh a sanda take karantasa,tana jin wani softness
cikin zuciyarta,tana jin kuma nutsuwa tana shigarta,shi ya sanya cikin lokaci qanqani ta kamosu ta kuma
hade da izifin baya da suka wurwuceta,abinda ya baiwa kowa mamaki,sauri da kaifin basirarta,duk da a
farko sun mata kallon hadarin kaji,kallon dalibar da bazata wani basu matsala ba. Tana da rivals da yawa
a ajin,matan da sukaci buri suke ganin sune na gaba gaba wajen samun yarda da amincin malamansu,sai
gashi cikin dare daya wata baquwar haure na shirin yi musu shalll. Wata irin murya Allah ya mallaka
mata me dadi,sai take sake qawatuwa da sautin karatun qur'ani da wani irin daddadan sauti.

Bata da lokacin kowa,ba wanda take bi ta kansa,bata kuma hulda da kowa idan ka debe fateema
da ameena. Muddin kaga hirarta sosai to da sune,idan kaga motsawa kumatu da labbanta to da ameena
dinne,sun dinke sun zama kaman wasu 'yan uwa, dabi'a da yanayin sultana din su ke burgesu,suna mata
kallon wadda gayu gata da shagwaba suka yiwa yawa shi yasa komai nata ya fita na dabanne.

Kowanne kwanan duniya sai metron asabe ta tambayeta ko tana da wani buqatar?,amsarta
daya ce A'ah,a nata tunanin tanason gwadawa ama zata iya rayuwar data zabar mata,zata kuma
wanzuwa a kowanne bigire ko muhalli da rayuwa ta gangarata cikinsa.

*_VISITING DAY_*

Tun daren jiya daukacin daliban makarantar ke cikin farinciki da walwalar ganin ahalinsu a
goben,kamar yadda fateema da ameena aleeyu suka bi sahun sauran dalibai.

Safiyar yau din kowa shiryawa yakeyi don 'yan gidansu su ganshi fes..... sultana na zaune kusan
sai da kowa yayi nisa wajen nashi shirin,wasuma suka soma fita sannan ta shiga tayi nata wankan da yau
ta zabi tayi cikin tsaftatattun toilets dinsu ba nasu metron asabe yadda ta saba yi ba.

Komai nata cikin wani sanyi da nutsuwa ya koma,babu sultanan nan ta anihi,haka ta tsaya gaban
gadonta ta shirya kanta cikin house wear kaman kowa,bayan ta daure jelar manyan kitson da fateema
da ameena sukayi taron dangi sukayi mata,saboda sulbinsa da tsahonsa ya sanya ba kasafai take kitso
ba,koda anyim ma baya dogon zango yake warwarewa.

Tayi kyau sosai,don sabbin house wear ta sanka,dinkin kuma ya zauna sosai ya qara fidda tsaho
data qara,saidai kuma tadan fada kadan wanda hakan baya rasa nasaba da sabuwar rayuwar da take
qoqarin daidaita kanta taga ta hauta bisa tsari.

"Sultana mohmoud mayak'i" aka maimaita kiran sunanta har sau uku. Waiwayawa tayi tana duban me
kiran nata,senior dinta ce cikin wadanda zasu fita makarantar a shekarar da ake ciki
"Kina da baqo" ta fadima sultana din tana juyawa. Turarenta ta miqa hannu da sauri ta dauka ta fesa ta
maidashi,sannan ta zura house shoe dinta ta soma tattakawa cikin wani irin zumudi tana ratsa hostel din
nasu

"Tacan zaki zagaya" dalibar ta fadi tana mata nuni da hannu sannan ta wuce gararin gabanta.

Sosai take takawa da zumudinta shiyyar da ta nuna matan,qasan ranta cike fal da dokin ganin
ama da aba,tasan kuma zaiyi wuya ace bibi batazo mata ba,BATOUL da BENAZEER......taji an kira mata
sunan yaran daga can qasan zuciyarta,ta lumshe idanunta murmushi na subuce mata,wata irin
mahaukaciyar kewar yaran ta taso ta lullubeta,karon farko daga can qasan ranta taji wani irin tausayinsu
ya saukar mata.

Tsaiwa tayi cak ganin tana ta cusa kai area din da babu motsin kowa babu kai kawon kowa. Ta
tayi ta tsaya cak,wai mema dalibar tace mata ne

"Kinyi baqo" ta tuna da abinda tace

"Baqo......baqi...." Sai taji kwanyarta ta rikice. To ko aba ne shi daya ya samu zuwa?,idan hakane ai ba
za'a barshi ya qaraso har gate na biyu na sashen mata ba,akwai askar da basa bari maza su wuce
gurin,kuma bata nan ya kamata ya tsaya ganin nata ba.

Wani mummunar bugawa zuciyarta tayi. Cikin jini tsoka da jikinta taji kamar ana fusgar hankali
da kuma numfashinta sakamakon shaqar wannan qamshin.......wannan qamshin dai da hanci zuw
qwaqwalwa ba zasu iya gaza fayyaceshi ba,wannan qamshin dai da yake da taushi dadi da
laushi......amma a nata hancin kama yakeyi mata da qamshin MUTUWA.....Tabbas inda mutuwa tana da
wani qamshi na daban......wannan qamshin shi ya dace a baiwa wannan sunan.

Waige waige ta fara yi jikinta yanason fara rawa, hankalinta kuma nason yin qaura daga gangar
jikinta
"Ki nutsu,ba kowa a wajen nan,ba shi daya aka qerowa turaren ba,bashi daya kaf duniya yake siyan
turaren ba......ki nutsu kada ki ruda kanki sultana" zuciyarta ta fara rada mata cikin kunnuwanta yayin da
qirjinta ke wani irin bugawa da tsananin qarfi har numfashinta yana rarrabewa.

"Sultana mohmoud mayak'i" ta sake ji an kirata,kiran sunan da ya hautsinata gaba daya ta waiwayo da
wani irin sauri. Wata dalibar ce cikin daliban da suke ajin farko wato J.s one ke nufota. Hannunta riqe da
wani babban abu da ya yima sultana zubi da kwali. Har ta iso gabanta sultana na dubanta qirjinta kuma
bai fasa dagawa ba,sai ta miqa mata kwalin tana kallonta bayan ta rusunawa sultana din kamar yadda
yake doka ne na makarantar dole na qasa ya rusunawa babba

"Wai gashi" bin kwalin dake hannun yarinyar tayi da kallo sannan ta maida dubanta ga fuskarta tana
tattaro ragowar miyau din bakinta,da qyar ta tambayeta

"Wai inji wa?" Kai ta karkada yarinyar

"Ban sani ba,nima wata daliba ce ta bani tace itama wata ce ta bata tace a baki" fuska tadan motsa
kadan,abun yadan daure mata kai,tayi kaman ba zata karba ba,to amma yadda yarinyar ke rusune sai
taga bai kamata ta barta a haka ba

"Ya sunan wadda ko wanda ya bada?"

"Nima na tambaya tace bata sani ba,wancan din tace me bada saqon sunanki kawai ya kama yace a
baki"

"Kodai aba ne yake sauri bazai iya tsaiwa ba ya bayar a kawo?" Wannan tunanin ya sanyata miqa hannu
ta karba,yarinyar ta juya da sauri sauri tana barin gurin don kada azo mata ba'a sameta ba,sai itama
sultana din ta soma takawa tana riqe da kwalin tana barin wajen zuwa nana aisha hostel,har a sannan
hancinta yana jin qamshin nan data yiwa maqurar tsana

[22/05, 10:00 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 35

Tana tafe a hanya tana juya kwalin,ba qato bane hakanan ba qarami ba,yana da matsakaicin
girma,amma kuma yana da dan nauyi. Kai tsaye ta koma hostel dinsu,sanda ta isa dakin da yawa an
yoye,kowa ya fita waje,wasu gurin family dinsu,wasu kuma suna jiran tsammanin isowar 'yan uwan
nasu.

Gefan gadonta ta zauna a nutse,ta aza kwalin saman cinyarta ta fara budeshi.

Sannu a hankali ta kammala yage takardar jiki tsaf,wani irin kwali ne na musamman tamkar
qaramin akwati,sai daukan idanu yakeyi da wani irin santsi da tambarin dolce and Gabbana ko ina a
manne a jiki.

Doki ya kamata,muddin wannan kyautar daga hannun aba take to ko shakka batayi tafiya yayi ya
kuma tuna da ita

"Allah sarki ubana,maganin kukana" ta furta hawayen qaunar aba na cika mata idanu.

Cak ta tsaya tana duban kyaututtukan da aka shirya cikin box din. Tarin tsagwaron
chocolates,dukka kalolin wasu chocolate da takesha babu wadda ba'a zuba ba a cikinta. Wani siririn
agogo da take da tabbacin zaiyi wuya chain dinsa idan ba gold bane a jiki. Turaren da take amfani dashi
sanda tana sultana dinta wanda a yanzun ma tuni ta sauya zuwa wani kalar daban. Biro da wasu
qananun notebook masu masifar kyau da tsari,sai wata memo itama daban da zata baka damar tsara
komai na rayuwarka da date da komai,sai wani greeting card da duka rubutun jiki layi qwaya daya ne tal

"Best wishes" kadai ke rubuce daga tsakiyansa.


Bin budadden box din kawai takeyi da kallo,cikin jikinta ta dinga jin wannan kyautar ba daga
hannun aba ta fito ba,batama dace da ace daga aba din take ba,to anya ba batan suna sukayi ba?,tunda
dai daliban makarantar ba suna da yawa qwarai,kuma bazaiyiwu kaf makarantar ace ita daya ce qwallin
qwal me suna sultana mahmoud ba. Juya bayan katin tayi,a nan ta samu amsar tambayarta,cikakken
sunanta harda na qasarta ne rattabe a bayan,hakan yana nufin me aiken yanason bata tabbacin saqonshi
ne.

Wani abu me kama da bacin rai ya biyo bayan mamakinta,ta sake juya katin ko zataga alama
koda ta sunan me saqonne amma babu,tsoro da shakka suka kamata,daidai sanda ameena aleeyu ta
shigo da sassarfa

"To kizo ga duka 'yan gidanku nan gaba daya,har mun gaisa da aba ma,ama nada maqurar kirki,atta da
almu suna yanayi dake" ameena din tace da sultana cikin nuna zallar zumudi.

Da sauri ta tashi hae box din dake saman cinyarta ya watse a wajen,sam batabi ta kansa ba tayi
hanyar waje duk da tana jiyo ameena na fadin

"Kinyi barna,wannan agogon me tsada .......Allah yasa baki fasa glass dinshi ba".

Tana tafiya zuciyarta na nanata tambayarta daga ina wannan gift din ya fito?,indai har ga aba
yazo to waye ko wace ta aiko da gift din?.

"May be dai still aba dinne" zuciyar dake neman nutsuwarta ta fada tana bata tabbaci.

Tun daga nesa data hangosu murmushi ya subucewa fuskarta,kasa jurewa tayi ta isa garesu a
hankali sai ta dan saka da sassarfa,ta qarasa ga ama ya fada jikinta tana riqeta da kyau,bakinta har rawa
yakeyi wajen fadin sunanta

"Ama.....sannu da zuwa ama"


"Wato ama dinki kawai kika gani ko?,ni baki ganni ba?" Muryar bibi ta doki kunnenta. Waiwayawa tayi
da sauri tana duban bibin,sai ta saki ama ta nufeta itama ta fada jikinta tana qanqameta

"Ban lura da bibi na ba,bibi tun daga nijer kikazo ganina?" Ta fadi tana murmushi. Harara ta balla mata

"Kuma gashi an yanqwanani ko ganina ma ba'a yi ba?" Ta fadi tana yatsina baki,saidai kuma qasan
zuciyarta na mata wani irin sanyi saboda sauyi muraran da take gani tattare da sultanarta. Baya taja tana
duban bibin

"Ni ya kamata nayi fushi bibi,kina can kina qiba abunki aba yana baki kayan dadi,ina nan kin barni da
abinci da horon boarding" ta dan taba tsokanarta wanda abune da kusan dukkaninsu kunnuwansu sun
manta rabon da su jishi daga bakinta,sai suka sanya dariya,wanda muryar aba ta fito a ciki,sai a sannan
ta ankara dashi shima,abinda ya sanya tadan yi qas da kanta ta kuma nufeshi da hanzari.

Zamewa tayi ta tsugunna a qasa tana gaidashi

"Barka da warhaka aba,ina kwana?" Ba wanda bai dubeta ba yadda take komai cikin nutsuwa da tsantsar
girmamawa. Yana dan saki murmushi ya amsa mata

"Lafiya qalau sultana,tashi a qasa kada ki bata uniform dinki,ga abun zama can an shimfida mu qarasa"
tanja ce ta riqe hannunta,saita waiwaya tana duban tanja din

"Kina Nigeria ko kina nijer tanja?" Ta tambayeta bayan ta gaida tanjan itama cikin rusunawa,abinda
sultana din bata taba mata shi ba koda wasa,kai kwata kwata ma ba zatace ga sanda sultanar ta taba
gaidata ba,ba zata iya tunawa ba.

"Inaaa......ina nan gurin iyayen dakina,in tafi nabar 'yan biyu?,ai bazan iya ba" ta amsa mata tana
murmushi. Sai a sannan hankalinta yakai kai,bataga benazeer da batoul ba,idanu ta shiga warewa can
qasan zuciyarta tana jin shauqin ganin yaran,amma ko me kama dasu bata gani ba. Duka sai taji
zuciyarta ba dadi,ta dinga nacin kallon inda goumar yake amma bataga alamun suna tare ba,har goumar
din ya lura da yawan kallon da takeyi,sai ya saki murmushi ya watsa mata hannuwansa,qasa qasa kuma
yadda babu wanda zaiji yace da ita

"Me na satar miki ne kuma yau?,mutumin da ko kallon fuskarsa ba'a sonyi yau shi aketa kalla?,ki bude
baki kawai ki cewa ama ina 'ya'yanki ko?" Harara ta watsa masa gabanta yana faduwa,salon maganarsa
sak yaa maina,kusan wasu abubuwan nasu suna bala'in kamanceceniya da juna,kamannin fuska ne sam
Allah bai sanya sunyo daya ba. Qaramin tsaki taja tana dauke kanta ta maida ga sashen su ama daketa
bata labarin abubuwan da suke wakana bayan batanan,sai muryar goumar ta motsa cikin dariya

"Allah bibi wannan 'yar jikanyar taki ladabin qarya tayi muku,qanzo ne ya sanyata yin laushi,bata canza
hali ba ashe rashin kunyar nan tana nan,yanzun nan ta gama min tsaki harda harara" ya qarasa fadi yana
dariya sosai. Harara bibi ta watsa masa

"Qaniyarka sarkin sharri,ta ina ta hararekan dukkanmu muna nan idanunmu suna gani?"

"Wannan idon naki ai ya kusa rubewa,don inda kina gani sosai da a yanxun kinga wani abu da ni kadai
nake hangowa" ya furta maganar yana kallon wani guri daban. Ba tare da Bibi din ta waiwayo ba tace

"Kaji dashi ja'iri" saita jawo wani mazubi ta miqawa sultana,wanda ba komai ciki sai kayan ciye ciye da
tasan tafiso.

Cikin wata irin sassanyan nutsuwa ya maida wayar tashi me bango biyu ya manneta guri guda
ya rufeta. Qirjinsa da zuciyarsa tana masa wani irin nauyi,da gaske goumar yakeyi bazai taba ganin yaran
ba?,da gaske yake,yau din rana ce da zata iya sake nesantashi da damar sake ganin kowa da komai da ya
shefeshi ko ahalinsa.

Yayi kwadayi qwarai wajen sakasu a idanunsa,yaso ya samu wannan damar koda zata kasance
dama ta qarshe a garesa,tunda bai san yaushe ba?,baisan sai wanne lokaci ba.

Wannan babbar dama ce a gareshi da muddin ta gushe masa baisan sai yaushe zai sake samun
wata damar makamanciyarta ba,zaiyi komai zaije zai kuma aiwatar dukka domin sa,domin ahalinsa.
A hankali ya isa dab da motar da mutumin da idan baka matso kusa dashi qwarai ba zaka
tsammaci mutum mutumi ne. Yana isowar ya sanya hannu ya bude masa bayan motar,ya zura gangar
jikinsa cikin wata irin kasala da galabaita tamkar wanda yayi watanni yana aikin kauda duwatsu ba tare
da ya huta ba. Wata wawiyar ajiyar zuciya ta subuce masa,ya lumshe kyawawan idanunsa yana jin kamar
ajiyar zuciyar zata fita ne tare da zuciyar dake qirjinsa,ya maida bayansa jikin kujerar yayi relax yana jin
yadda zuciyarsa ke tsananta bugawa sanda motar ke gangarawa tana barin wajen.

Har ta rako su aba bakin mota,suka kuma fidda komai da komai da suka kawo mata cikin
zuciyarta bata kasa juya batun box dinnan ba,daga ina yake?, itace tambayar da taketa nacin nanatawa.

Tana nan tsaye har suka kammala shiga motar. Ama ya sauke glass din bangarenta ta miqa ma
sultana wani box. Kallonsa tayi sannan ta sanya hannu ta amsa. Madararta ce,madara mafi soyuwa a
gareta,madarar da tana begenta amma kuma tana nisantata da rayuwarta saboda tuna mata da takeyi
dashi

"Gashi inji benazeer da batoul da baki tambayesu ba,sunce suna gaidaki" wata irin kunya ce ta saukar
mata,tanason tambayarsun amma batasan ta yaya zata fara tambayar tasu a gaban ama da aba din
ba,uwa uba ga bibi a gefe,ga kuma dan sanya ido goumar

"Ace ina gaidasu" ta fada da sassanyan muryarta

"Basa amsawa,sai da aka roqa musu" goumar ya fadi cikin salon tsokana. Harara kawai ta samu damar
binsa dashi saboda tashin da motar tayi bata samu daman maida masa raddi ba.

Duk wata kujiba kujiban zuwan masu visiting lokaci yana yi aka rufe gate din makaranta,doka
kuma taci gaba da aiki. Suna saman gadonsu kowa na kintsa wajensa da gyara kayayyakin da aka kawo
masa daga gida,dakin nasu fal kaya saboda dukkansu kusan daga gidan iko da wadata kowacce ta
fito,babu wadda ta fito daga qaramin family.

Da wuri sultana ta gama komai,tana daga saman gadonta ameena aleeyu ta qaraso da box
dinta ta miqa mata
"Ga box dinki nan" binsa tayi da kallo tana jin shakkar amsa,sai ta maida dubanta ga ameena

"Bansan waye ya aiko dashi ba,ki ajjiyemin kawai zan nema maishi saina karba"

"To ya wuce saurayinki?" Ta tsokaneta tana dariya. Dukanta maganar tayi har tsakiyar zuciyarta,sai ta
daga kai tana kallonta gami da jefa mata harara

"Ba saurayi ba dattijo" ta fadi cikin hushi. Yanayin yadda tayi maganar gauraye da harshen qasar nijer
cikin kuma fushi dukkansu ya basu dariya,bata sake ce musu komai ba ta janye qafafunta zuwa gadonta
ta juya musu baya.

Iyakar tunaninta kaf ta gaza canko wanda zai iya aiko mata da saqon

"To kodai goumar ke yimin wasa da hankali?" Tayi tunanin haka daga qarshe,sai ta cije lebanta tana jin
qamshin gaskiyar hasashenta. Tabbas da ta tuna hakan kafin su tafi saita yayyaba masa magana,ta
fuskanci kamar yana yawan son yiwa rayuwarta shishshigi.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[23/05, 8:59 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 36

**********Sannu a hankali rayuwa taci gaba da tafiyar mata,tana sake hankali tana kuma sake fahimtar
me ainihin rayuwa ke nufi kadan kadan.

Sosai kwanyarta take budewa,a hankali kuma ta fahimci gatan da ama tayi mata data kawota
makarantar. Kafin takai ga zuwa ss3 ta zama wata sultana ta daban. Azkar ya kama bakinta
ainun,karatun qur'ani da wata nutsuwa dake nuna sanin haqiqanin rayuwa. Tabbas! Ilimi wani irin haske
ne da babu irinsa,wani abu ne dake busawa zuciya da rayuwa wani ruhi na musamman. Hatta da
kamanninta sun sauya,sun cika da wata irin nutsuwa da wani sirtaccen kyau nata dake boye. Idan ka
kalleta a sannan babu abinda zakaji cikin zuciyarka dangane da ita sai tsananin burgewa,saboda wata
kamala annuri da kwarjini da ilimi ya zuba mata,komai nata sai ya zama cikin nutsuwa da kuma kamun
kai. Kalaman bakinta sun canza sosai,hakanan mu'amalarta,saidai kuma tun wancan sanyin da tayi.....tun
wancan sauyawar......tun a wancan lokacin har zuwa yanzu sai ta zama me matuqar sanyi,miskila mara
yawan surutu hayaniya ko kuma kwarafniya kwata kwata.

Tana S.S3 ama ta saka su benazeer a free nursery,surutu da wayonsu ya isa,wani irin wayo ne
dasu da yafi na shekarunsu,duk da batoul nada kalar nata miskilancin,amma tun kafin shekarunsu su fara
nisa kamanceceniyar halayya wajen yawan surutu rigima da rawar kai na sultanan can baya benazeer ta
kwafe tsaf!,wannan ya sanya ama tafi maida hankali akan benazeer din sosai,tanaso dukka wadannan
halaye da Tayo gadonsu su kasance kan tsari da kuma cikakkiyar kulawar tarbiyya. Saboda kwadayin
ingantar tarbiyyar yaran ya sanya gaba daya ama ta daina tunanin komawa nijer,tafison a nan din inda
suke suyi tasu quruciyar da wayon,saboda itace babbar shaidar banbancin tarbiyyar da qasashen biyu ke
dashi.
A shekararta ta qarshe a makaranta ta yiwa kanta gata me tarin yawa. Tayi joining classes da
akeyi na musamman bayan wadanda suka zama wajibi. Litattafai ake musu na addini masu
yawa,zazzafan karatu ne da ya sanya da yawa daliban basu fiya joining ba sai masu wayo da masifar
nacin so karatu irin sultana. Yadda zazzafar qiyayyar karatu ta juye mata zuwa zazzafar soyayyar karatu
tana bawa ama mamaki. A duk sanda sukayi hutu tazo gida yakan zamana kamar ba hutu ta samu ba.
Duk bayan kowacce daqiqa tana maqale da litattafai,wani lokaci hadda takeyi wasu lokuta kuma tilawa.
Ta samu hadisai sosai,wasu ta haddacesu ne,musamman wadanda keda alaqa da mu'amala da kuma
rayuwa,wasu kuma a yayin da aka karanta mata ta iyasu a rubuce kuma tana tsintar wasu tana amfana
dasu. Kosu benazeer bata basu lokacinta kamar yadda take bawa litattafanta. Sai ya zamana ba wata
shaquwa bace can can a tsakaninsu da ita. Da ama suka budi idanu,ama itace mommansu,ita sultana
AUNTY kawai suke kiranta,kuma suna mata kallon auty dinsu ce,saboda tsakaninsu hukuntawa ne da
tsawatarwa idan za'a yi ba dai dai ba tamkar na qaramin yaro da babbar yayarsa.

Watannin qarshe da suka rage musu a makarantar,dab da zasu fara jarabawa sukayi saukar
alqur'ani me girma. Kyawawan qira'o'i dukka guda bakwai din da muke dasu babu wanda bata iya ba.
Karatu take tartilan babu gargada,babu bata,zakayi tsammanin ta jima da saukeshin a yanzun maimaici
kawai takeyi. Tana cikin zaqaquran dalibai guda goma na farko da aka fidda cikin ajinsu.

Sanda suka fara jarrabawa dukka tunaninta sai ya sake fadada akan qara nisan zangon
karatunta,batajin zata zauna haka,yanzunne ta soma jin gardin ilimi,ashe ilimi dadi ne dashi har
haka?,ashe muddin kana da ilimi kuma kana aiki dashi basai an zauna ana fama wajen gyaraka da saitaka
ba?. Sau tari idan su ameena aleeyu sukaga tana zaune guri daya tana murmushi sukan cika da mamakin
meye yake sata nishadi yayin kadaicewa ita daya?. Murmushin ta kan fita ne a duk sanda ta tuna da
quruciyarta,ta tuna da rayuwarta a niamy,ta tuna irin tabara da rashin hankali da zallar wauta data
tafka,yadda ta qaunaci rawa,xuwa party zuwa birthday kamar hauka,a yanzun idan dukka ta tuna
wannan sai kunya ta kamata. Ta sake tabbatarwa da lallai komai lokaci gareshi,komai kuma yana zuwa
ya shude ne cikin rayuwa tamkar a allon majigi.

Abu guda daya ke zuwa ya tsinke kyakkyawan zaren wannan tuna baya nata,idan ta tuna da
MAINA. Komai yana shafewa a zuciya da ruhinta,komai yana shafewa daga tunaninta amma banda abu
daya,banda MAINA banda yadda ya yiwa rayuwarta da mutuncinta dirar mikiya,banda yadda ya wargaza
mata kyakkyawar rayuwa yabar mata wata rubutacciyar qaddara a rayuwarta,ya kuma shura qafafunsa
ya bace battt daga sararin duniya tamkar zuwan walqiya da daukewarta. Komai ya sauya cikin rayuwarta
amma wannan tabon yana nan a zane radam......wannan tsumammiyar qiyayyar tana nan a rubuce dara
dara bata kauce ba,daga qarshe takan buge da xubda hawaye me tarin yawa.
Takan jaye jikinta daga cikinsu fateema Ahmad duk lokuttan da suke hirar samarinsu,soyayya ko
hirar data shafi 'yammatanci,saboda a sannan kowacce ta soma cika mace,takai kuma ganiyar
'yammatancinta. Cikin jiki da ruhinta takejin kwata kwata bata cikin sahunsu,to meye zai zaunar da ita a
cikinsu ana hirar da ba layinta ba?.

Su kuma dukkan wannan sun azashi ne cikin zallar miskilanci irin na sultana,son zaman kadaici da
zaman shuru,kamewa da rashin son hayaniya. Takan saki siririn murmushi da jerarrun fararen haqoranta
a duk sanda suke mata tsiya

"Kin fiya shuru shuru wallahi,ke ba dama ki zauna ayi hirar arziqi dake."

"Baku riski sultana a sanda take sultanan ta ba,kun samu sultanar nijeria ne,sultanar hassan Ibrahim
gwarzo,sultanan ama,auntyn benazeer da batoul.......ba sultanan nijer ba,sultanan bibi da aba,da hirar
tsiya ma duka sai anyi,saikun nema wajen fakewa daga gareta" takan raya haka ne cikin zuciyarta.

Ta riqi sallah sosai,ta kuma koyi azumin litinin da alhamis a gida ko a makaranta,tun daga sanda
suka karanta hadisin dake bayanin falalar azumin litinin ko alhamis basu taba ruskarta tana da cikakkiyar
lafiya ba tare da tayi azumin nan ba. Saidai har yanzu jikin nan yana nan ba wata qiba,amma kai tsaye ba
zakace a rame take ba,sai tsaho data qara,duk wata halitta tata ta qara cika,kyawun nan na cikakkiyar
buzuwar asali,jinin NADEEYA MUHAMMAD MAYAK'I ya hudata sosai,ya zamana har hirarta akeyi sashi
sashi cikin makarantar,domin kaf cikar makarantar da batsewarta babu wata diya mace data isa ta tsaya
a tudun mizanin kyau tare da ita,wannan ya sanya take sake kame kanta da kuma fita a dukkan shirgin
da ba nata ba. Sai kuma Allah ya zuba mata farinjini da kwarjini wajen juniors,bata da mugunta ko
kadan,hasalima cikin sabbin shigowar nan duk yarinyar da ta gani ne rawar kai iyayi da surutu sai taji
tana tausaya mata,wani lokaci kuma ta saki murmushi don suna tuna mata da shekarun baya da suka
shude mata.

*_GRADUATION DAY_*

Rana ce me matuqar tarihi cikin rayuwarta,ranar data sanyata xubda hawaye me yawa,ranar
data sakata dana sanin zaman da tayi ba karatu a wadancan shekarun,ranar kuma data sakata a godiyar
Allah me tarin yawa daya fiddata daga duhu zuwa haske.
Taro ne akayi gagarumi na saukar dalibai tare da yayesu,tana cikin dalibar farko da aka kira aka
karramata har hawa uku gaban dubban al'umma,gaban familynta,gaban mutanen da suke tamkar iyaye
a wajenta,gaban mutanen da suka debe tsammanin zamantowarta a yadda take a yanzun.

Duk inda ta motsa kyaututtuka ne na yabawa da karramawa. Da yawa mutanen dake wajen da
sukasan family din MAYAK'I sun mata kyaututtuka na alfarma,har sai da goumar ya taso ya dinga tayata
karba.

Data dawo mazauninta ta zauna kasa jurewa tayi,taja hijab dinta ciki ta boye fuskarta tana
kuka. Abun mamakin sai batoul ta kalli benazeer cikin kwabe fuska kaman zata saki kuka

"Benz(haka take kiranta don bata iya kiran full name din ya mata tsaho da nauyi),waye yasa aunty
kuka?" Waiwayowa benazeer din tayi ta zubawa sultana idanu,itama sai ta kebe baki kamar zata sanya
kukan tana duban goumar

"Oncle.......ko itama aunty ta tuna da daddynmu da kace yayi tafiya?" Sosai maganar ta doki qirjin
sultana,har batasan sanda ta fidda rabin fuskarta ba tana duban goumar. Kamar dama ya shiryawa
hakan,shima ita yake kalla,suka zubawa juna idanu na wasu lokutta suna kallon kallo. Tanata hadiye
bacin ranta da maganganun da takeson gaggaya masa saboda cikin bainar jama'a suke. Wato kebewar
da yake da yaranta har gaya musu yakeyi suna da wani daddy da yayi tafiya?,waye ya sashi?,shi
awa?,meye hadinsu da daddyn da yake musu maganarsa?, tabbas ba zata qyaleshi ba,sai tayi warning
nasa,kada ya sake bari wannan maganar ta shiga kwanyar yaranta,bata buqatar hakan.

Wannan maganar kawai ta dauke hawayen fuskarta,sai suya da zuciyarta keyi mata tana fakon
goumar tana jira su samu matsawa daga wajen ta amayar masa da abinda ke cikin ranta.

Bata samu wannan damar ba sai da suka tashi komawa gida,bayan taro ya watse,makaranta ta
sallamesu sai kuma zuwa karbar result na exam dinsu. Ta gama koke koken rabuwa ita dasu fateema
Ahmad da ameena aleeyu,aminan qwarai da ba zata taba mancewa dasu ba,sunyi exchanging phone
numbers da full address nasu,har Adress dinta na nijer dukka ta basu saboda batasan me rayuwa ta
tanadarwa gobenta ba, al'amuranta bata fiya basu amana ba,ta fahimci caccanjawa sukeyi a duk sanda
sukazo hakan,koda yake umarni ne daga rabbussamawati.
Ita da aminata,najma da yasmine su ya dauka a motarsa wadda bai jima da siyenta ba bayan
kama aikinsa baya bayan nan da kammala karatunsa. Kusan duk wani hali da dabi'a na maina yana dasu.
Har rabon motoci aba ya yiwa samarin cikin dangi yace bazai amsa ba,yafison ya fara hawa wadda ya
siya da guminsa. Kusan aqidar maina ne,neman nakai,ya tsani a masa alfarma,ya tsani ya rabu da wani
ya dinga cin albarkacinsa,wannan dalili ya sanya har yabar gida baida motan hawa na kanshi,duk da
cewa akai akai yana bisa hanya duk kusan sati ko sati bibbiyu tsakanin niamy da marad'i.

Ta fahimci akwai wata kyakkyawar alaqa tsakaninsa da najma,saidai a yanzun ba komai take
magana akai ba shi yasa batace komai ba,amma tunda su aminata sukazo ta karanci akwai gulma fal
bakinsu,bata dai tsaya ta basu lokaci bane,amma ta tabbatar sai sun fesa mata koda ba zata saurara ba.

Kyawawan 'yammatan buzayen da suketa daukan hankulan jama'a suka jera reras su hudu
bayan tashin motarsu aba suka wuce zuwa inda goumar ya ajjiye motar tasa. Hirar suke amma sultana
bata fiya sanya musu baki ba,don burinta kawai ta fesarwa goumar abinda yake cikinta.

Akwai takadda guda daya ta sultana da ya tafi karbowa don haka suka dan tsaya suna
tattaunawa daga bakin motar tasa kafin ya iso ya bude musu.

Yaro ne da duka duka bazai wuce shekara sha hudu ba ya iso gurin. Fari ne siriri,yana da dan
tsaho kadan,yanayin zubin fuskarsa kadai zai shaida maka bafulatanine usul. Sanye yake da wata
dakakkiyar shadda sai maiqo takeyi fara qal,kanshi sanye da jar dara sosai irin ta ainihin bare bari. Kana
dubansa kasan daga gidan gata ya fito,kuma alamun jikinsa da fatarsa na nuna ainihin jin dadi da yake
ciki.

A gabansu ya tsaya yana sallama fuskarsa a sake. Dukkansu suka daga kai suna dubansa,aminata
ta amsa masa,sai sultana ta maida kanta tana daidaita qananun litattafan azkar dinta data qarasa
debowa daga drawer dinta ta jikin gadonta don bawa 'yan ss2 da zasu maye gurbinsu damar cin gadonsu
da kyau. Gaishesu yayi sannan yace musu

"Wai anason yin magana da wannan" ya fadi yana dan murmushi hadi da nuna sultana da yatsa. Kusan
dukkaninsu sai da wuta ta dauke musu na wucin gadi,ba sultana kadai ba,su kansu saida tsoro da
fargaba ya cika zukatansu. Suka zuba mata idanu dukkansu,yayin da ita kuma ta zubawa yaron nata
idanun ba tare da sanin takamaimai amsar da zata bashi ba.

[24/05, 11:57 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 37

______________________________

https://chat.whatsapp.com/CKY0xZDtpby6MTkGrPkXLr

____________________________

"wai inji wa?" Najma tayi qarfin halin tambaya da alamun sanyi qwarai cikin muryarta

"My broz....gashican,yace idan ba damuwa zai qaraso.....don Allah aunty ya qaraso din,mun gaji so muke
mu aurar dashi mu huta" ya fada yana qyalqyala dariya,da alama akwai sakewa sosai tsakaninsa da
wanda ya aikoshi din.

Dukkansu suka maida dubansu inda yaron ya nuna musu. Baiyi qarya ba,matashin saurayine fari
tas da yayi zubin buzaye yarensu,saidai su da yake suna shaida duk wani da sukejin harshe daya dashi
take suka shaida bafulatanine shima tamkar qaninsa. Yana sanye da shadda da hula sak irin ta qanin
nasa,komai nasu irin daya kamar yadda suke kama da juna

"Kaje kace masa matar wani ce" muryar goumar ta ratsa kokwanto da walagigin da zukatansu suka shiga
na yadda zasu kaucema wannan kiran.

A birkice ta daga kai tana kallon goumar


"Matar wani?" Ta furta a fili amma a hankali. Juyowa goumar yayi wanda yaji fitar lafazin nata yana
duban qwayoyin idanunta kamar yadda ta kafeshi da nata

"Eh..... qarya nayi?" Ya fadi kanshi tsaye yana sake kafeta da kallonsa. Mummunan faduwa gabanta taji
yayi. Tsahon kwanakin watannin da kuma shekarun bata taba tuna cewa wai har yanzun itadin matar
aliyyu bace,bata sake tuna har yanzun a sunan matar aure take ba,bata sake tuna akwai igiyoyin aurensa
guda uku qwarara a kanta ba.....to wai zaman meye takeyi da igiyoyin auren maqiyinta kuma
makashinta?,me ta zauna tana yi dasu tsahon shekara hudu?. Kai ta jinjina tana zare kallonta daga kan
goumar,taji daci qwarai har saman harshenta,saidai kuma taji dadi da yayi mata tuni da wani muhimmin
al'amari da ya kamata ta tuna dashi ta kuma kawo qarshensa cikin rayuwarta gaba daya.

A yanzun ita din wata sultana ce ta daban data fara sanin dadin rayuwa,kyawun rayuwa da
kuma cikakken 'yanci da rayuwa ke dashi,tanaso tayi rayuwa kamar kowa,tana so tasan me duniya da
rayuwa suka qunsa?,tanason ta fita tayi gwagwarmayar da al'umma zasu amfaneta,dole ta kawo
qarshen wannan maqalallun igiyoyi da ko daya bataga amfanin barinsu a sarqafe ba.

Najman ce a gaba dukkansu suna baya su uku,tana iya hango yadda fuskar saurayin ta canza
sanda qaninsa ya iskeshi a sanyaye yana labarta masa,batasan ya suka qarke ba,tadai ga yabi bayan
motarsu da kallo har suka fice daga makekiyar harabar makarantar.

Cikin motar kanzil bata ce ba,aminata da yasmine sunta hirarsu,goumar da najma da batasan
me suke fadi ba suma tasu hirar suke,sai ita daya da suka fari da hannu dafe da gefan kanta tanata zane
saman bangon littafin dake cinyarta,wanda ita kanta batasan me take zanawa ba saboda tsabar tunani.

Iska ta shaqa sosai da suka shiga tangamemiyar harabar gidan aba dake garin abuja bayan jirgi
ya saukesu a airport. Tadan bi harabar gidan da kallo yadda ya qawatu matuqa da gaske. Sabon gida ne
da basu jima da tarewa ba,duka duka sati biyu. Cikin shekarun nan wani irin tumbatsa arziqin aba dama
na hamdiyya ABDU ME KANO wato ama keyi,kaman an sake yiwa dukiyarsu yayyafin
albarka,mahaukatan kudi kowannensu yake samu. Yanzu haka sun budewa benazeer da batoul manyan
manyan boutique cikin garin abuja har guda uku,wanda kowanne kudade ya lasa ba qananu ba,saboda
girman boutique din ya kusa wani mini supermarket din B&B BABY DREAM. Komai nasu na dabanne
saboda ana sarrafashi ne daga wani kebantaccen kamfani dake sanya tambarin B&B a kowanne kaya,shi
yasa kayansu ya fara zama na daban,ya kuma samu karbuwa qwarai da gaske,karbuwar kuma tana da
nasaba da yaran da Allah ya hore musu wani irin farinjinin mutane.
Randa sultana tazo wani hutu ta amshi wayar yaran da ama ke musu amfani da ita tana duba
account nasu na insta abun ya bata matuqar mamaki. Followers suke dasu masu yawan gaske. Account
ne na musamman da ama ta bude kawai saboda yaran,ba abinda take dorawa sai hotunansu. Tun
sultana tana kallon pics din har ta gaji saboda yawansu,ta aje wayar kawai tana murmushi

"Kakar zamani" tayi gulmar ama a ranta tana dan dariya qasa qasa.

Motar goumar ya tsayar a farfajiyar ajiyar motoci dake gidan wadda gari ne kusan guda,ya kalli
najma

"Samomin wani abu me dan sanyi,ki tahomin da BB(benazeer da batoul)zamu fita dasu wani guri"

"Okay sir" ta fadi tana murmushi sannan ta bude motar ta fice.

"Akwai abinda na riqe miki ne madam?" Goumar ya fadi yana gyara qaramin pillow din dake gefan
kujerarsa. Sai data sanya qafafunta waje sannan ta waiwayo

"Goumar" ta kirashi kai tsaye wani irin tsauri na fita daga cikin qwayar idanunta

"Na'am madamme" ya amsa fuskarsa a sake ba komai

"Karka bari ka barar da sauran mutuncin dake tsakaninmu"

"Tofa!,ikon Allah,me kuma nayi?"

"Da batoul da benazeer basu da wani abu a duniya yanzun,kayi qoqari ka daina yi musu tilawar abinda
babu wanzuwarsa a duniya......haka nima......ni ba matar kowa bace,ba matar wani bace ni" wata
siririyar dariya ya sake mata,ba abinda yake ganowa a idanu da fuskarta sai zallar quruciya da har yanzun
shi baiga ta fita kwata kwata a jikinta ba

"Basu da uba a duniya.....ke ba matar kowa bace to kece kika kashe musu uban?" A kaikaice ya waiwaya
tana dubansa,maganar tasa ta sake tsaya mata a wuya kamar mulmulallen dutse. Gaba daya abinda ta
fahimta goumar kallon shashasha kuma yarinya yakeyi mata,baima dauki maganarta da muhimmanci ba.

"ko ya mutu koma ya rayu wannan duka ba abinda ya shafi sultana bane,abu daya sultana ta
sani,bata da wani hadi ko alaqa ta kusa kota nesa dama ko waye" ta fadi da salon tsiwar nan tata data
jima bata taba ba

"Ashe dai da sauran bakin har yanzu" goumar ya fada qasa qasa yana dariya sanda take fita a motar. Ta
jishi sarai,bata kuma gama fahimtar abinda yake nufi ba,saidai duk da haka ta juyo ta zabga masa
harara,ta murguda qaramin bakinta tace

"Baqin ba'abzine,Allah ya qara gwara da Allah ya barka a baqinka" ta buga murfin motar ranta yana suya
da ambatar mata sunan maina tana qarawa gaba zuwa cikin gidan cikin sassarfa.

Dariya sosai ya kwashe da ita yana duban hanyar da tabi

"Baki gama laushi ba kenan,hali zanen dutse" ya fada a ransa yana gyada kai gami da ci gaba da
dariyarsa sannan ya sanya hannu yana daga glass din motar zuwa sama tare da duban hanyar dawowar
najma.

[26/05, 9:53 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 39
Dif wuta ta daukewa kowa dake dakin. Tun daga tsakiyar kan ama har tafukan qafafunta sai da
taji wani ya tsarga mata,ba wanda ya taba hasashe ko tunanin maganar da zata fada kenan. Kaf cikinsu
kowa ya kasa furta komai,kimanin wasu sakanni har sultana ta debe tsammanin wani a cikinsu zaiyi
magana sannan aba ya sauke ajiyar zuciya,kafin yace komai bibi ta furta

"Sultana?.....me kike fada haka?" Hannu aba ya dagawa bibi yana kallonta,sai tayi shuru,tsam ama ta
miqe ta zagayesu tana barin wajen,saboda batason jin duk wani hukunci da zai fito daga bakin aba,don
ta tabbatar zaiyi wahala hukuncin ya dace da abinda ita takeson ji ko son ya kasance

"Kinyi qoqari qwarai sultana da kika iya zama da igiyar auren mutumin da har yau ba wanda yasan inda
yake,a raye ko a mace duk ba wanda ya sani,kika raini cikinsa kika haife,kika shiga makaranta kika
gama,don yau kin buqaci hakan ba laifi bane,tashi kije zan nemeki in sha Allah,Allah ya yiwa rayuwarki
albarka,idan kuma goumar ya shigo ya duba miki sakamakonki"

"To aba,na gode qwarai" ta fadi tana miqewa daga zaman durquson da tayi. Tana shirin juyawa sashen
dakunansu suka hada idanu da goumar dake tsaye daga can bakin qofar falon jingine da
qofar,hannayensa goye a qirjinsa,da alama kuma yaji komai,don abinda ta gani cikin idanunsa ya karanta
mata haka. Harara taso watsa masa amma saita shareshi kaman itama bata ganshi ba ta juya ta wuce
lobby.

"Amma dai hamid,kada kacemin ka amshi zancanta da gaske kana nufin yi mata abinda takeso din?" Bibi
ta tambayeshi murya qasa qasa tana duban qwayar idanunsa. Ajiyar zuciya ya sauke yana gyara zamansa

"Komai a musulunci bibi yana da iyaka,yana da doka,a shekarun da maina yayi baya nan ba wanda ke da
tabbacij yana raye fa,kuma ko a musulunci miji yayi irin wannan bacewar ba tare da ya sake waiwayar
matarsa ba ya halatta alqali ya raba auren ayi ma matar GAIBA ta auri wani.....bibi sultana yanzun ba
qanqanuwar yarinya bace,ta iya yiwuwa tana da buqatar tayi aure shi yasa ta bijiro da wannan batun da
ya kamata ace mu muka fara dubashi" zama tayi sosai tana jifan aba din da wani irin kallo hadi da
gatsine fuska
"Hamidou......ka fara kasheni tukunna saika tsinka auren maina kaji"

"Subhanallahi bibi,abun baikai har can ba"

"Ah to,yo Allah na tuba,don qaniyarta nawa take duka duka da har za'a ce waiko tana da buqatar aure?,
ina cewa kwata kwata sha tara shekarun nata suke?,to ko labarin mutuwar maina aka samu ai bata isa
tayi wani auren ba sai tayi masa idda"

"Ya maina ma yana raye......" Goumar ya fada

".........in sha Allah,jikina yana bani haka" ya qarasa fadi ganin dukka sun waiwayo sun zuba masa
idanu,sai ya sauke hannayensa yana ci gaba da takowa cikin falon

"Bazamuyi masa fatan mutuwa ba aba baiga jininsa ba diyoyinsa,kai din ubane,a duk inda yake kaci gaba
da yi masa addu'a Allah ya bayyanashi,ko kuma ubangiji ya karkato da hankalinsa gida" shuru sukayi su
dukka jikinsu a a mace,saidai maganganun goumar dake cike da nutsuwa da kuma hankali sun ratsasu.

Tunda ta shiga daki take nanata kowacce kalma data fita a bakinta,saida zuciyarta ta gamsar da
ita bata aikata wani abu me muni ba,hakanan batayi amfani da tsauraran kalamai ba wajen bayyana
musu yankewar igiyar aurensu takeso,hannu ta daga tana addu'a Allah yasa aba ya yanke hukunci da
wurwuri,ta yadda zata samu cikakken 'yanci kamar kowacce mace,tayi karatunta iya yadda takeso ta
kuma gamsu.

Agogo ta dinga dubawa har sai data tabbatar da lokacin da goumar yake zama babban falon
ama shi dasu benazeer su cikawa mutane kunne da karadi,sai ta dauki hijabinta ta sanya saman kayan
baccinta donta gama shirin kwanciya,kasancewar bata fiya kaiwa dare can can batayi bacci ba.

Takardunta ta diba ta sanya loppy tana fita a dakin. Yau din sabanin kullum ne,zaka samesu ko
yaushe sun cika falon da hayaniya da wasanninsu,amma a yau din sai ta samu yaran duka sunyi bacci
zube a tsakiyar ama da goumar din. Daga goumar din kuma har ama idanunsu na bisa tv.
Motsinta ya sanya ama da goumar din juyowa duk suna kallonta. Idanun goumar bai sanyata jin
komai ba,amma sai idanun ama taji sunyi mata mugun nauyi. Ta dinga jin kamar ana dabaibayeta,cikin
gangar jikinta ta dinga jinta kamar me laifin da aka tsare.

Miqewar ama din kafin ta iso tana daukar benazeer ya sanya ta dan sake ji wani iri tana cewa

"Tanja zata zo ta dauki batoul,sai da safe"

"Allah ya bamu Alkhairi ama" ta fada a kunyace

"Ameen sultana" yadda ta amsa matan a sake sai ya rage mata tsarguwar da tayi,ta samu waje ta zauna
tana duban fuskar batoul dake bacci. Bakinta gaje gaje da chocolate,tasan kuma ba aikin kowa bane sai
na goumar,shi yasa yaran kullum qara habaka suke suna qiba mul mul abinsu,duk wanda ya gansu saiya
tanka,wannan ya sanya duk sati ama ke sanyawa ana sauke musu qur'ani.

Hannu ta sanya ta shafi cute face din batoul tana dauke mata gashin daya warware daga band
din kanta don suma sunyo gadon gashi me tsaho da santsi irin na iyaye da kakanni

"Ah waima,unuhunn......wai a haka fa sonta kikeyi ko?,bayan kin gama kashe musu uba da baki,kina
kuma neman a sakeki" goumar da bakinsa baya shuru muddin shi da sultana ne ya fadi. Miskilin gaske ne
a zahiri da fuska,amma indai shi da sultana ne dama tun tale tale sun saba. Idanuwa ta dago ta zabga
masa hararar da bata samu daman sakar masa ba dazu

"Wai kai meye yayi maka zafi da shiga sha'anina ne baqin buzu?"

"Fadi ki sake fadi,baqin buzu nake me farar aniya da zuciya"

"A hakan?,kaga ma ni ba wannan bane ya kawoni,don bani da lokacin wannan maganar,aba ne yace idan
ka shigo ka dubamin exam dina"
"Zan duba miki yanzun kuwa,don ni din me jin maganar magabatansa ne......exam kuma dai saidai a
cirota a ajjiye don ba inda zaki sake tafiya,sanda akeson kiyi karatun bakiyi ba sai yanzun da kike matar
wani?" Ya fadi kansa tsaye ba tare da damuwa da abinda zataji ba yana sanya hannu ya dauko laptop
dinsa dake ajiye a gefansa wadda bai jima da gama aiki da ita ba.

Tsam ta miqe,ba goumar ba,har wajen da take zaune a kansa sai da taji ta tsanesa. Hawaye fal
idanunta tana dubansa dishi dishi,tana shirya kalaman da zata gaya masa da zata fanshe wannan
maganganun da ya yaba mata,abu biyu ta iya gaya masa taji muryarta ta soma rawa,saita juya bata ida
gaya masan ba,tana jinsa yana cewa ta kawo takardun ya cika aikin aba,ko waiwayoshi batayi ba bare ta
saurareshi. Ko a jikinsa yaci gaba da aikinsa yana dariya qasa qasa cikin ransa hadi da cije lips dinsa na
qasa.

Tun daga lokacin bata sake bi ta kansa ba,bata kuma sake bari sun hada koda hanya cikin gidan
ba bare mazauni,rainon maina ne,tasan kuma zai aikata abinda yafi hakan,duk zuciyar tasu iri daya ce ta
gayawa kanta,shi yasa ta yanke hukuncin nesanta qwarai dashi.

Aba ne da kansa ya kirata ya miqa mata hard copy na result dinta. Sanda ta karba hawaye ne ya
kwance mata,ta samu fiye da marks din da ta tsammaci zata samu,ta cinye kowanne subject,abinda tayi
hasashen zata samu ta samu fiye da hakan,ta kifa takardun saman fuskarta tana kiran sunan Allah,yau
sultana ita keda wannan result din da abaya kaf gidansu koda cikin mafarki ba wanda ya taba kawo mata
kwatankwacinsa saboda zallar qiyayyarta da karatu.

Ba ama ba hatta aba abun ya faranta masa rai matuqa da gaske,bai kuma yi sanya ba ya bata
option ta zabi duk kalar kyautar da takeso yayi mata,ya bata dogon takarda yace ta rubuta list. Hannunta
rawa ya dinga yi,ta kasa rubuta komai,sai daga bisani cikin rawar bakin bayan ama ta matsa mata ta
rubuta din tace

"Umra nakeso aba"

"Sau nawa?" Hawaye ya biyo kuncinta tana tuna adadin zuwanta,sau uku ne,amma saidai duk sanda taje
din tana cikin rudu,tana asalin sultanarta,batasan muhimmancin wajen ba,batasan kuma dimbin falala
da wajen yake dashi ba,taje ne kawai taji dadin jirgi,ta kuma shaqata a kantunan dake daura da
harami,tasha chocolate laban da ice cream har sau babu adadi. Amma a yanzun da tasan muhimmanci
da girman wajen sai shauqinsa yaketa kamata,yanzun da ilimi ya ratsata burinta kawai shine zuwa wajen
sau babu adadi cikin rayuwarta

"Sau nawa kikeson xuwa?" Aba ya tambayeta

"Sau babu adadi" ta qarasa fadi tana rushewa da kuka

"Kin samu in sha Allah" ya fadi yana nufin hakan har cikin zuciyarsa kuwa. Diyar mohmoud ce tafi qarfin
komai,uwa uba ya samu sanyin idaniyarsa halittu mafi soyuwa a gareshi da silarta BENAZEER DA
BATOUL. A arziqin da Allah yayi masa inda ana zuwa kullum kuma tana da buqatar zuwa din zai iya kaita.

Ya mata alqawarin muddin yana raye din zata yita zuwa har sai sanda tace ta gaji. Ita kuwa
tasan zata yita zuwa kenan muddin ranta,muddin akwai wadata wa aba,akwai lafiya cikin jikinta,saboda
bata tunanin akwai ranar da zatazo tace ta gaji da zuwa wannan gurin.

**. **. **. Randa bibi zata juya nijer sai taji haka kawai tana sha'awar zuwa. Tare suka tafin,da harda
goumar ta kafe indai tare zasuyi tafiyar ita ta fasa,dole yayi gaba daga baya aba ya basu driver da escort
uku.

Sosai taji dadin xuwa nijer,ta ji har cikin ranta lallai a gida take,abu daya ke yawan takurata,duk
sanda ta gilma wani guri da tasha dabdala a baya,ko guraren da maina yafi yawan zama sai taji duk
walwalar da take ciki ta gushe,wannan ya sanya ta dinga kame kanta daga shiga wasu guraren,ciki harda
nahiyar dakunan dake sassan bibi wanda anan me akkuwa ta auku.

Wata guda ta shafe a nijer,daidai lokacin kuma muqamin aba ya tabbata,tafiya ta tabbata daga
nijer to nijeria har zuwa qasar FRANCE!.

*_TOFA MASU KARATU,DAB MUKE DA ISA GURIN😄,muna dab da mu qarasa gurin da na tabbatar kowa
ya qagauta a isa_*
*_FRANCE......NEW CHAPTER UNLOCKED_*🥰

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank
_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[26/05, 9:53 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 40

*FRANCE _(PARIS)_*
*Charles de Gaulle Airport*

*Avenue champs elysees*

_8th arrondissements_

Cikin awa daya da saukesu da jirgin qatar airways yayi a airport din Charles de Gaulle suka iso
champ elysees avenue. Unguwar dake da matuqar kyau tsari da kuma dadin zama,wadda take dauke da
dukkan nau'ikan shop shop,malls restaurant da coffee shops harda makarantu. Unguwa ce me kyau
qwarai da dadin rayuwa,wannan ta sanya aba ya zaba musu zama a cikinta. Cikin daya daga cikin
apartment dake unguwar wanda gwamnatin nijer ta bashi.

Babban apartment ne dake qunshe da dakunan bacci guda hudu,biyu ta gaban gidan inda zaka
bulla har balcony zuwa harabar gidan, biyu kuma ta cikin gidan wanda suke hade da backyard na gidan.
Kowa yasan ginin bature gini ne me matuqar kyau da daukan hankali,komai na gidan a tsare yake a kuma
killace,sun iso cikin gidan bisa jagorancin wakilan qasar nijer a nan din da suka tarbesu a
hukumance,suka yiwa aba duk wata tarba data kamata.

Karfe hudu agogon paris suna cikin gidan,sun gama zagaya ko ina da duba ko ina. Sultana kam da
ido take bin komai tana sake tabbatar da maganar hausawa da suke cewa tafiya mabudin ilimi,tun daga
abuja zuwa gidan da suke ciki a yanzun take ganin mabanbantan al'amura. Benazeer da batoul kam sai
tsalle tsallensu sukeyi,suna biye da ama duk inda ta sanya qafarta. Walwalar yaran data qaru kawai ta
sanyawa ama farinciki,tana ji a ranta zaiyi wuya tabar qasar nan nan kusa,har sai yaran sun samu kalar
ilimin da take musu kwadayin samu. Tanason su fita daban,su zama na musamman,kamar yadda gatan
da suke samu ya banbanta da gatan duk wani d'iya dake familyn MAYAK'I,kamar kuma yadda suka zamo
jikokin farko a wajensu aba din.

A nutse ta taka izuwa babban curtains daya suturta babbar qofar glass na dakin da zai iya baka
daman ganin cikin unguwar da kuma duk wanda ke zirga zirga ta street din nasu. Qofar ta murda ta fita
zuwa balcony din,sassanyan yanayi na la'asar sakaliya dake gauraye da qamshin tsirrai da suka wadaci
unguwar ya daki fuskarta,iskar ta shiga sosai cikin hancinta ta isa hunhunta ta sauketa a nutse tana kuma
fidda wata me zafi. Ajiyar zuciya ta sauke,tana fatan taji ruhi da zuciyarta ta nutsu amma. Ta lumshe
fararen kewayayyun idanunta da suke da wani irin qwalli kamar an diga mai a cikinsu,haka kawai taji
bugun zuciyarta yana dan sauyawa a hankali yana qara gudu. Da hanzari ta ware idanun nata cikin
mamakin abinda ya haifar mata da hakan,sai ta aza hannun nata saman qirjin nata tana qoqarin
controlling sabon yanayin data tsinci kanta a ciki.

Tsahon wasu mintuna babu sauyi,sake maida idanunta tayi zata lumshe karadin benazeer ya
cika mata kunnuwa

"Aunty......aunty kinga" hannayenta ta sauke tana waiwayowa zuwa ga yarinyar. Da gudunta take
nufarta tana nuna nata wata qatotuwar teddy. Murmushi ta saki dan siriri tana tuna rayuwarta,yadda
tayi yayin tara teddy kaman hauka,batajin cikinsu ma akwai wanda zai qaunaci teddy din yadda ta sota

"Kizo inji ama" benazeer ta sake fadi tanata qoqarin ganin ta goya Teddy din,sai kuma ta juya da gudu
gudu tana sauka hadi da kiran

"B.....B" Juyawa tayi tana komawa cikin dakinta ta dauki mayafin gown din jikinta ta yafa tana bin
bayansu.

Daga qofar dakin da ama ke ciki din ta tsaya saboda rashin ganin dacewar shigarta dakin,don
daki ne da ama ta zabawa aba,duk da cewa aba dinma baya nan ya fita tare da mutanen da suka yo
masa rakiya zuwa nan din.

Knocking tayi ama dake ciki tace ta shigo. Hakanan cikin jin nauyi ta murda qofar dakin tana shiga.
Babban dakine da yafi kowanne girma da kyan furniture,aman tana tsaye da wani folder a hannunta
tana dubawa,ta amsa sallamar tana kallon sultana sannan ta miqa mata takardun tana cewa

"Ba hutu,ba zama,sun kusa gama daukar dalibai,aba yace ki duba,cikin universities din wacce ce tsarinsu
yayi miki?"
"Allah sarki ubana na kaina" ta fada hawaye yana cika idanunta. Hannu biyu tasa ta karba tana kallon
folder din. Itakam dai kawai tayi rashin mahaifinta hamani ne,amma zata iya cewa iyayenta sun maye
mata gurbinsa har fiye da haka,batasan wani abu waishi maraici ba,bata taba ji ko ganin zumunci irin
nasu ba,tasan indai ana batun dacewa da family itakam ta dace

"Amma ki kula ki duba location na kowacce university ki zabi wadda ba zaki dinga shan doguwar tafiya
ba"

"In sha Allah ama". Ta fadi farinciki yana cika zuciyarta fal,burinta ya kusa cika na zama 'yar jarida,ta
rungume folder din tana fita daga dakin.

Tsabar zumudi ya hanata tsaiwa ta kintsa dakin ta zauna duba jami'o'in,tanayi tana browsing a
wayarta da babu layi a ciki duk kuwa da tsadar wayar,akwai wifi da suka samu a gidan don haka bata
buqatar komai don research din.

Har tanja ta gama abinda ya dace tayi ta biyo ta dakin tana nade tsakiyar gado tana aikin canki
canki. Cikin zolaya tanja tace

"Wai sultee kamar yanzu zaki fara zuwa makaranta a rayuwarki,wannan zumudi haka?,xuwa makarantar
ma kamar yafi komai yi miki dadi" tashi tayi ta zauna tana yatsina fuska saboda yadda bayanta ya riqe
sakamakon rub da cikin da tayi na kusan awa daya tana cewa

"Ji nakeyi kamar yanzu aka haifeni tanja,kaman yanzu ne na soma rayuwa,ai da can ba rayuwa nakeyi ba
tanja,rayuwar da babu ilimi a ciki?,meye marabarka da gawa?"

"Irin wannan lokacin maina yakeson gani,shi yayita burin gani tattare da ke,ya Allahu ko ina wannan
bawa naka ya shiga?" Qwaqwwaran motsi sultana batayi ba,sai tayi kaman bataji abinda tanja tace
ba,inda sunsan adadin dimuwa da qyamatar da ruhinta ke yiwa sunansa kawai bama shi din kansa
ba.......da babu wanda zaiyi kuskuren sake kiran sunansa a gabanta

"Bari na kintsa miki wajen kafin ki gama" a hankali ta motsa labbanta tace
"To" tana maida hankalinta ga wayarta cikin tsananin nutsuwa,yayin da zuciyarta taci gaba da motsa da
wani irin sautin tsana da qiyayya duk sanda kunnuwanta suka tuna mata sautin kiran sunansa da tanja
tayi.

Satinsu daya suka gama huce gajiya,sai ama ta fara diban jikokinta suna fita shan iska. Kullum da
inda zasu,sai idan sun dawo kaji labari cakwai a bakin benazeer,don ba kasafai batoul ke da surutu haka
ba. Hasalima ita saita nema debo dabi'un abbanta sak da sak,tana da wani irin miskilanci da kuma
basarwa. Haka kawai idan taso saita tashi da 'yan shirun, benazeer tayi hirar duniya taqi kulata,idan taga
haka tasan tana nufin yau ba zasuyi wasa ba ko ifce ifcensu da suka saba ba sai tahau tsokanarta,ba
kuwa zata qyaleta ba har sai ta sakata kuka,sau tari sai ama ta shiga tsakani,ko kuma idan suka cikawa
sultana kunne ta leqo shikenan sai benazeer din tayi laqwas ta shiga taitayinta.

A irin wannan lokacin ama kan zauna kawai tana binsu da kallo, zuciyarta tana mata haske tana
kuma mata fari,wani lokaci kuma damuwa ta cika zuciyarta,dukkansu su biyun sun dauko attitude na
mutum biyu ne, benazeer sak SULTANA tana yarinya,batoul kuwa MAINA ce har yabar gabansu.

Duk da garine dake da ababen kallo sosai,gari ne dake da ababen sha'awa amma ita bata
sha'awar fita ko ina. Zaman kadaicin da taketa yi ya sanyata karance karance a matsayinta na wadda
keson fadawa harkar karatun jarida,a hankali har abun ya zame mata jiki. A nan taga wata makarantar
koyar da girke girke na qasashe daban daban,koda ta duba kudin registration din sai taga yayi yawa,don
haka ta maida site din ta rufe bata sake budeshi ba. Ranar ama ta karba aron ipad dinta taga ta soma
register,ta fahimci yawan kudin ya hanata qarasawa. Murmushi ama tayi,sultana..... sultana,akwai barin
kashi a ciki,ba zata taba bude baki tace ga matsala ko damuwarta ba,sai ta shiga site din ta qarasa komai
ta biya kuma kudaden,sai gayawa sultana tayi ranar da zata fara zuwa.

Nauyi da kunyar ama suka sake kamata,tana kunyar yadda ta azama kanta dukkan
nauyinta,komai nata itace,bata qyashin kashe mata ko nawa ne, ba'a maganar su benazeer da suke
fuskantar wani irin gata,idan akace gata ana nufin gata na qarshe,irin gatan da ake kwatance dashi.
Komai nasu me tsada ne,komai nasu kuma na musamman ne,hatta kuwa da brush da zasu wanke
haqoransu. Amma kuma duk da gatan da ake gwada musu hakan bai sanya sunyi lako lako da
tarbiyyarsu ba. Sosai suke samun kulawa da tarbiyya,don ama da kanta take koya musu qur'ani. Da yake
sunyi gadon kwanya,sai gashi da qananun shekarunsu sunyi nisa a alqur'ani,hadda kuma tartilan cikin
qwaqwalensu. Ta siya musu kayan karatu kala kala da zasu taimaka musu, harshensu kuma ya fara
juyewa da qira'ar sheik imam khusari.
Makaranta me kyau aba ya duba ya sakasu,inda suke karatu da dukka harasa biyun, French da
English harda qarin larabci.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_


09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[27/05, 9:28 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 41

Cikin watanni biyu aba yayi settling komai ta fara zuwa makaranta. Qaramar mota ya siya mata
daidai d'iya mace,ta kaita makarantar koyon tuqin mota ya zube kudi ta koyi tuqi da kyau suka bata
license. Hakan ya mata dadi qwarai,don ta huta da tafiya railway ko kiran taxi.
Shigarta makarantar ya sake sanya idanunta suka bude da rayuwa,ta qara sanin mece
duniya?,tarin al'umma mabanbanta masu mabanbantan halaye da dabi'u. Ta sake sanin tabbas duniya
tana da girma da fadi,taga kalolin tarbiyya iri iri al'adau dabi'u da kuma halaye,wanda kusan kullum idan
ta dawo sai ta bawa ama labari. Murmushi kawai ama keyi,itama sai yanzu take sake tabbatar da
quruciyarta,lallai a baya in banda quruciya da tabara babu abinda sultanan ta sani. Duk da haka suna
biye kuma suna kula da ita,ko don girman igiyoyin dake saman kanta,wanda tun wancan lokacin da bibi
tayi magana ba'a sake tada zancan ba.

Suna exam semester farko aba ya ajjiye musu visa dinsu na zuwa umra. Ranar kasa bacci
sultana tayi. Hakanan Allah ya jarabceta da son zuwa madina da makka,tun daga sanda ilimin addininta
ya fara zurfi ta fahimci muhimmancin gurin gaba daya zuciyarta ta tafi can.

Washegari goumar ya dira a Paris,sai a sannan tasan dashi za'a yi tafiyar. A sannan tana parlor
tana duba wasu litattafai nata door bell tayi qara,tanja ta bude masa ya shigo riqe da jakarsa. Daga
benazeer har batoul yarda abun wasan hannunsu sukayi sukayi kansa kamar zasu shide saboda
murna,shi kuwa ya tattarasu duk da girmansu ya dagasu yana zagaye dasu.

Har suka gama abinsu tana zaune bata daga kai ba,sai da suka nutsu suka zauna tanja ta ajjiye
masa drinks da snacks tana gaya masa ama tana bandaki,sai ta fara tattare litattafanta da zummar barin
wajen idanunta na kallon litattafan nata tace dashi

"Ina yini,kana lafiya?"

Gwanin tsokana baya fasa halinsa,tabe baki yayi yana cewa

"Nidai ban roqi gaisuwa ba bare a wulaqantani ehe,meye wani ina yini kana lafiya?" Tsaiwa tayi da
abinda takeyi ta xuba mishi fararen idanunta, kwanyarta na mata tariyar tarin kamanceceniyar halayya
dai da uban dakinsa sarkin zalunci da mugunta wato maina kaman yadda ta rada masa

"Kaidai ba'a iya maka wallahi,Allah ya sawwaqe" saita dauki kayayyakinta a hannu tana yin gaba
"Ya kyauta mana gaba daya,mutum se shegen qunci da dacin rai kamar wanda aka kashewa diyan fari"
ya qarasa fada yana galla mata harara. Tasan halin goumar,baiqi su kwana sunayi ba,don haka ko
waiwayoshi batayi ba ta shige dakinta,amma ranta cike fal dashi,tana kuma tunanin hanyar da zata bi ta
taka masa burki,yadda yake shige mata sharafi ya soma isarta hakanan.

Bata qara bari sun gamu ba sai ranar da zasu wuce. Tafiyar tasu dukkansu ce,harda tanja,amma
sai ya zamana duk cikinsu sultana din tafi zumudi saboda a wajenta tamkar zuwan farko ne.

Tafiyar awanni tara bayan yada zango a wani qasar Wizz Air Malta ya saukesu a filin tashi da
saukar jiragen sama dake garin madina don can suka fara sauka. Wata ajiyar zuciya me qarfi ta sauke
kamar wadda aka finciki zuciyarta. Ta furzar da iska daga bakinta tana jin daukin ganinta cikin masallacin
ma'aiki. Daga wankansu cin abincinsu a masaukinsu zuwa fitowarsu masallacin duk sai taji kaman basa
sauri,ji take kamar duk duniya ita daya keda buqata,kamar duk duniya ita keda damuwa a qirjinta,kamar
kowa baya da matsala sai ita kadai. Tana ganinta a raudha kuwa kuka ta saki sosai,saidai qasan ranta taji
nutsuwa tana saukar mata,wannan ya taimaka ta samu nutsuwa tayi addu'a sosai.

Dukka kwanakin da sukayi a madina babu wanda bata amfaneshi ba da tarin addu'o'in da ita
kanta batasan adadinsa ba. Sai gata a yau wai itace da yiwa ummanta NAFESSA da mahaifinta HAMANI
addu'ar samun rahamar ubangiji,lallai hankali da nutsuwa ya samu,madalla da wannan rayuwa data
samu sauyinta.

Randa suka sauka a garin makka kuwa kayanta kawai ta ajjiye tayi wanka ta fice,ko ama su
benazeer ta barwa sallahu su gaya mata ita ta wuce harami. Ta kasa nutsuwa don masaukin nasu daga
nan idan ta bude window din dakinsu tana gano harami sosai,saita dinga ji kamar ana fusgarta.

Sanda suka fito ma ita ta bace cikin masallacin,don haka ama ta fara tata ibadar, benazeer da
batoul ma sukayi nasu waje,wanda ama batasan ma ina sukaje ba sai da suka dawo hannu dumu dumu
da siyayyan kayan zaqi,tunda kafin su fita dama already aba ya basu kudi a hannunsu.

Da rigima suka dawo,mutuniyar batoul tayi kicin kicin da fuska tana harara benazeer,tambayar
duniya taqi bayani sai ice cream da ta saka a gaba,ita kuwa benazeer ba abinda ya shafeta ta zauna ta
bude abinta ta fara sha tana dariya. Da kallo ama ta bita,sak yadda sultana ke cakar da yara zamanin
quruciyarta da shegen tsokana da yiwa yara dariya. Daqyar ama ta lallasota ta gaya mata
"Mutane take kulawa ama,sai kuma tayita basu labari mu 'yan nijer nigeria da paris ne" waiwayawa
aman tayi tana duban benazeer,suna hada idanu jikin benazeer din yayi sanyi saboda tasan kalar
wannan kallon na ama

"Bana hanaki dogon surutu irin haka ba benazeer?,kina so na saka wuqa na rage miki tsahon bakinki?"
Da sauri ta girgiza kai idanunta na hada hawaye

"To daga yau na hana,idan zakuje siyan abu kuje ku dawo,ba ruwanku da kowa kina jina?" Kai ta gyada
mata tana lanqwashe qafafunta taci gaba da shan sanyinta. Dariya taso qwacewa ama,wato tsoratar da
itan da tayin bazai hanata qarasa shan kayanta ba

"Gado ba karambani ba" ta furta can qasa tana sake tuna mata da sultana da qananun shekarunta cikin
qasar nijer mansion house na MAYAK'I family.

Da wata irin kasala mutuwar jiki data zuciya rungume da dardumarta take fitowa daga
masallacin. Idanunta sun tasa sun kuma yi jaa saboda yawan kukan da tayi a gaban ka'aba. Rabin kanta
sarawa yakeyi saboda abincin da bataci ba wunin yau din gaba daya sai zam zam data dinga sha sosai
kaman ba gobe.

Sanye da baqar jallabiyya yake takawa a farfajiyar wajen. Tsahonsa bayananne ne,hakanan
nannadaddiyar sumarsa.

Bata lura dashi ba kamar yadda shima din da alama bai lura da ita ba yana cikin gaggawa
ne,wannan yayi sanadin da saura kadan kafadunsu su hade waje guda,abinda ya sanya sultana janyewa
gefe zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu saboda qamshin turarennan da hancinta ya shaqa qwarai
da gaske fiye da yadda take jiyo qamshin daga nesa a mabanbantan gurare..........qamshin yaja
hankalinta ta waiga a hargitse tana duban wanda ya giftata din........

[28/05, 8:26 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 42

Rufewar da idanunta sukayi,da kuma irin bugun da zuciyarta keyi ya sanya idanunta suka nuna
mata shi a matsayin maina,daga bisani kuma a hankali ganinta ya washe,ainihin kamanninsa suka fito
mata

"Sannu ko?,yi haquri don Allah" ya fada yana daga Mata hannu da sassauqar muryarsa dake bayyana
zallar sauqin kansa,ya bata haqurinne da hausa kawai don baya tsammanin ko kadan zataji me zaya
fada,don kuwa koda alama batayi masa kama da launin jinsin hausawa ba. Kanta ne yayi wani
mummunar sarawa,sai data sake matsawa nesa kadan dashi sannan ta gyada kai tana furta

"Ba komai" a wahale sannan ta juya da sasarfa tana barin gurin,don ko kusa bata qaunar sheqar qamshin
wannan bala'e'en turaren

"Uhmm......nace ba,don Allah ko zan iya sanin masaukinku?" Taji ya fadi a bayanta bayan ta baro wajen
sosai,don tayi tsammanin ma inda suka tsaya din daga nan ba lallai ka hangoshi ba. Muryar tasa ta
sanyata waiwayowa sai suka hada ido. Kai ta girgiza masa alamun a'ah,sai ya marairaice yana ci gaba da
binta

"Don Allah,kada kice a'ah" hannuwanta dukka ta sanya tana dage doguwar rigarta tana kuma qarawa
qafafunta karsashin yin sauri,don burinta ta tsere masa daga wajen. Ba abinda yake sake hadsasawa
zuciyarta sai wani irin bugawa

"Please" ya sake fadi ba tare daya dakata da binta ba

"Ka daina bina,nan din waje ne me alfarma"


"Na sani,ni dinma alkhairi nake nufinki dashi,bata yadda zan miki magana a nan kuma zuciyata sharri ne
a cikinta game dake"

"Na gamaka da girman gurin da wanda ake bautawa a wajen ma dakata" ta sake fada daidai sanda ta
hangi goumar yana nufo wajen,yana riqe da hannun BATOUL tana bashi labari,shima kuma da alama
dukka hankalinsa yana kan batoul,saidai hango sultana da wani na biye da ita ya sanyashi dauke dukka
hankalinsa a kan yarinyar ya maido kansu batoul.

Bata fasa sassarfar tsere masa idanunta nakan fuskar Goumar data tabbatar sai yayi mata
shishshigi,kaman yadda bai fasa binta yana mata magiya ba,hakanan goumar bai fasa nufosu ba fuskarsa
da idanunsa na nuna wani irin emotion.

Ta karanci abinda ke fuskar Goumar,kaman ma a fusace yake ainun,yau kam sai tayi maganinsa
taga idan akwai abinda zai iya,don haka suna zuwa dab dashi ta dakata,ta kuma karantawa matashin
Address na hotel harda number dakinta

"Na gode sosai,sunana suhail kefa?"

"Sultana" ta fadi a taqaice tana juyawa ta rabe goumar ta wuce.

Sai data fara nisa da gurin suhail ya maida dubansa ga goumar da yayi tsam ya zuba masa
wannan idanun nasu me matuqar kwarjini da haiba irin na maina,idanun buzaye dake da wani irin sirri
da kuma launi na daban.

A idanu suhail yaga suna kamanceceniya da sultana,saidai shi din baqi ne sosai kuwa akan kalar
fatar sultana dake jazur kamar ta fito daha yankin larabawa,wannan kama da ya gani yasa ya miqa masa
hannu yana fadin

"Assalamualaikum" girman kalmar da sanin ma'anarta kadai ya hana goumar qin miqa masa hannu. Ya
bashi hannun,saidai kuma ya bar masa saqo yana fadin
"Ita din matar wani ne,kada kayi gangancin shiga gonar da ba taka bace,kada kuma kayi yunqurin keta
dokar Allah" sosai sai jikin suhail yayi sanyi,amma a yadda karo daya yake jinta cikin kowanne sassa na
zuciyarta daga kallon farko,sai yaji kalaman goumar basu shigeshi ba

"Ni jikina sam bai bani haka ba,idan ma kai din rival ne saidai nace maka kayi haquri na riga na
kamu,ma'assalama" ya fada yana yin gaba.

Tun daga ranar sai goumar ya dauke mata wuta tsaf,ta daina ganin koda haqoransa,itakam
hakan yafi mata dadi,don dama so take ya fita a sabgarta kuma ya fita din,takance a ranta

"Aikin banza aikin wofi,koshi wanda kakeyin abun saboda shi bai isheni kallo ba,bai kuma isa yace zai
damu rayuwata ba bare kai"

Suhail kuwa tasha ganinshi a hanya ko cikin masaukin nasu da alama ita yake nema,saita bace
masa kota koma har sai yabar wajen. A daidai lokacin lokacin ubangijinta kawai take dashi,ita kanta cikin
zuciyarta taji nutsuwa da gamsuwar lallai tayi ibada iya yadda ubangiji ya bata iko,fatanta kawai ta zama
karbabba,muddin kuwa ta karbun tayi imanin zata cimma dukkan nasara da kyautatuwar rayuwa.

Sati uku sukayi suka koma Paris ta rungumi karatunta,wanda babu abinda take gani sai budi da
nasara,duk wani nasibi da budi data roqo akan karatunta tana ganinsa,karatun tamkar ana buda
kwanyarta ana zuba mata shi,nan da nan kafin ma su kammala ajin farko sunanta ya fara yin fice cikin
makarantar tsakanin dubban dalibai dake department dinsu.

Duk yadda takai ga janye jikinta da rashin son jama'a sai Allah ya bata farinjini sosai cikin
makarantar,kowa ta zauna dashi dai ya qaunaceta,duk da miskilancinta bata iya wulaqanci ba sam,sannu
sannu sai gashi ta fara dan sakewa da jama'a. Koda ba zatayi mu'amala dakai ba amma zata maka
murmushi saman fuskarta,wannan sai ya sake zama abun burgewar jama'a a wajenta.

Tun wannan zuwan da sukayi sai zuwa umrar ya zame musu tamkar jiki kamar yadda aba yayi
mata alqawari. Abun sai ya zama kaman ya tsara musu kanshi da kanshi,duk sanda suka samu hutun
makaranta ita dasu benazeer to a saudiyya suke yin abinsu,suyi wata guda suna ibada sannan su dawo
kuma a soma shirye shiryen komawa bakin karatu.
Ta riqi karatunta gam da matuqar muhimmanci,tana bashi dukkan lokacinta,saidai kuma hakan
bai hanata ibada ko koyon wasu abubuwa da suka shafi rayuwa ba wandada tasan tana da naqasu ta
bangaren,kaman koyon girke girke,hanyoyin kula da kai da kuma gyara kai da wata balarabiyar oman ke
koya musu. Macace me baiwar sanin ilimin halittar diya mace,shiga ajin matar ya faranta mata
ainun,don ya sake maidata wata irin 'yar gayu..... mace me aji,irin macen kuma da tasan kanta ciki da
waje. Sai a sannan ta karanci ama cikin hikima. Wato ita ama ba'a banza ba ta fita daban a zuciyar
aba,duk da cewa aure qaddarar wasu mazajen ce,to amma bata tunanin tana cikin qaddarar aba,wasu
abubuwan ma da yadda take kula da rayuwarta da kuma kanta dukka sai yanzu hankali da ya game
sultanan take karantarta,wasu abubuwan tayi qoqarin daukesu,wasu kuma su bata kunya.

Abinda bata sani ba ama din ta fita zurfin nazari sanya idanu da qwaqwqwafi,tuni ta fahimci
sultana,sai bata nuna mata ba,amma itama saita sakata a nata ajin na yadda mace zata amsa sunanta
mace a idanun mata 'yan uwanta dama maza abokan cudayyarta. Ta sake salute na ama,ba banza ba ta
sake fita daban da faccalolinta,tun tale tale komai na ama dabanne,she's so classy,har kuma a yanzun
dabi'arnan tana nan,shekaru da fara zuwan girma bai sanya ta canza ba.

Ta zame mata mentor sosai ta fanni da dama,ita kadai data kalla ya sake sanya mata sha'awar
koyon girke girke iri daban daban. Ama din kamar half cast za'a kirata,uwa uba kuma ita din tayi zaman
qasashe tun zamanin quruciya har zuwa yau,wannan ya sanya ta iya nau'ikan abinciccika kala daban
daban,kuma da kadan da kadan sai da sultana da iya da yawa daga cikinsu.

*_KOMAI NISAN DARE gari zai waye_*

Cikin babban dakin taron dake mallakin makarantar,cike yake da dalibai irinsu sultana dake
murnar amsar sakamakonsu na kammala karatun aikin jarida fanni daban daban,sai kuma manyan baqi
iyaye da 'yan uwan daliban dake qasashe da kuma garuruwa daban daban cikin paris da wajenta.

Tana sanye da academic regalia data dora saman wani tattausan lace da ya lashe kudade masu
ciwo da ama ta siya mata,ta kuma bayar akayi masa dinki me aji. Lite make-up ne a fuskarta wanda zaka
iya rantsuwa da Allah ba komai saman fuskarta saboda nutsuwa da kwanciyar da kwalliyar tayi a saman
fuskartata.
Tun daga takalmin qafarta har zuwa mini handbag da medium mayafinta idan akayi lissafi a qalla
zasu tada jari me qarfi ga wani. Komai nata me sanyi da tsari,kaman yadda halittar ta take da daukan
hankali da saukar da wani irin nutsuwa.

Siririn kwallin da aka sanya ma fararen qwayoyin idanunta da kuma red lipstick da ta shafa ya
fidda mata wata haiba da kwarjini na musamman.

Tana zaune a inda aka tanada saboda dalibai,amma gaba daya hankalinta yana kan batoul da
benazeer da aka yiwa kwalliya sosai cikin wata red gown da tayi masiiiifar kwanciya a lafiyayyar fatarsu
da hutu da gata ya jiqa sosai. Sai kai kawo sukeyi suna 'yan guje gujensu tsakanin mutane,duk kuma inda
zasu gifta din sai sunja hankulan mutane. Wasu su jasu suyi hotuna,wasu su basu qananun gift da ba'a
raba baturen mutum dasu.

Kiransun da aka fara yi daya bayan daya ya sanya dole ta haqura da lura da kai kawonsu,duk da
tasan idanun aba ama goumar harma da bibi da tayi tattaki tun daga nijer domin ganin yadda gudaliyar
tata a yau zata karbi sakamakon da zai bayyanata a cikakkiyar 'yar jarida.

Sanda sunanta ya fita a cikin mic haka ta miqe tana ratsa mutane,kunya gami da nauyin
idanuwan da sukayo kanta dukka suka cikata,haka ta dinga takawa cike da nutsuwa har takai saman step
din da kowanne dalibi ke tsaiwa tana qasqantar da ganinta.

Idanu sosai takeji cikin jikinta tamkar yawansu ya wuce yawan adadin jama'ar dake wajen kadai.
Bayan gajeriyar gabatarwar dake nuna da qwazo da nagartarta,kwanya da kaifin ganewa da take
dashi,da kuma kasancewarta daya daga cikin dalibai guda biyar da sukafi kowanne dalibi samun high
mark. Ji ta dinga ji kamar zata fadi a wajen,gaba daya qafafunta sunyi laushi hawaye ya cika idanunta. A
kowanne bigire na rayuwa data tsaya ba abinda take gani sai haske,wani irin budi take gani a duk
matakin karatun data taka,batasan abinda ke nufi da hakan a gareta ba,me yiwuwa akwai hukimar
ubangiji da ya sanya qiyayyar karatu me yawa a ranta a baya.

Kuyi haquri dai,ku qara haquri,naso yau na kaiku inda ya kamata aje din,amma yau da gobe ta riqeni,duk
da haka ku bini bashi gobe in sha Allah,na gode sosai

[29/05, 9:56 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*


*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 43

Hannu ta sanya ta amshi certificate dinta,wanda tayi tsammanin bayan ta karba din zata koma
ta zauna ne kamar kowanne dalibi......amma kuma a'ah. Kyaututtuka na karramawa ne suka yita fitowa
saboda qoqarin data nuna da hazaqa a guraren da suka danyi ayyuka dasu na neman qwarewa watannin
da suka wuce da kuma cikin makarantar kanta,kasancewar su mutanene masu girmama mutum
irinta,sunason suga mutum me talent qwarai da gaske. Sai ta dinga ji kamar tarihi yana maimaita kansa a
hassan Ibrahim gwarzo makarantar da har yau take kewarta,take kuma jin tamkar ta koma can.
Makarantar ta zame mata wani mabudi,ta kuma zamewa rayuwarta haske kuma fitila dan jagorarta daga
duhu izuwa haske.

Kafin a kammala taron duka ta bata fuskarta da koke koke,sai tissue da ama keta bata tana
goge fuskar saboda hotuna da aketason dauka da ita,musamman su benazeer da suka ja hankulan
mutane qwarai.

Tana duqe tana qoqarin controlling hawayenta muryar benazeer ta karade hall din ta cikin
mic. Da zazzaqar muryarta tayi sallama,sallamar data sanya kowa dake wajen murmusawa,ta kuma saka
sultana dagowa da sauri. Tayi dare dare saman step din tana murmushi,cikin yaren france da ya kama
harshenta matuqa da gaske tamkar yaren hausa da suke magana dashi yau da gobe a gida ta soma
magana

"Ina gaida aunty na.....ina gaida mommy na ama.... oncle goumar....kaka na aba.....sai daddy
na.......daddy na ina gaisheka......muna kewarka daddy,yaushe zamu ganka?" Ta qarashe fada muryarta
tana raunana.

Tafi wajen ya dauka,yayin da maganar ta doki qirjin duk wani ahalin mayak'i dake a wajen.
Sultana kam maida bayanta tayi makarin kujera ta jinginar tana rufe idanunta, qirjinta yana bugawa kusa
da kusa. Goumar ya riga ya gama yiwa tunaninsu lahani,ya gama cusa musu wannan tunanin na
mahaifinsu wanda batasan yaushe zaibar zukatansu ba.

Kusan jikinta a sanyaye aka kammala taron,saidai dab da za'a kammala din saiga sanarwa daga
wani gidan tv kai tsaye suke neman sultana zuwa channel dinsu zatayi interview,suka bata date wanda
ya dauki makonni kusan hudu,dai dai da sanda suka kammala wasu gyare gyare na shirye shiryen da
suke gabatarwa a channel din nasu. Wannan shine abinda ya wanke mata zuciyarta,farinciki ya kamata
sosai,abinda bata taba tunani ba,yau ita sultana wani tashan talbijin dake a qasar turawa ke nemanta da
kansu?

"Alhamdulillah" kawai ta dinga maimaitawa tana jin farinciki yana ratsata,ko ta ina addu'arta ke
karbuwa,cikin qaramin lokaci buri da muradinta ke dab da cika.

Koda suka koma gida bacci tayi sosai na gajiya,bata tashi ba sai azahar,tana yin sallah ta sake
komawa,don duka kwanakin zirga zirga sukeyi don tabbatuwar taron. Bayan sallar la'asar benazeer ta
shigo,ta bita da kallon harara sannan ta zaunar da ita. Data fara yi mata fada akan abinda tayi dazun
saita sakar mata kuka,abinda ya sanyata sakin baki kawai tana kallonta,sannan kuma cikin bacin rai tace

"Oho.....tun bankai ga dukanki ba?,hala duka kike buqata ko?" Kai ta girgiza tana share hawayen fuskarta

"We missed him mommy,uncle goumar yace yana nan amma bamu taba ganinsa ba,sai a hoto ya taba
nuna mana shi sau daya" gabanta yayi mummunar faduwa,da gaske goumar yakeyi bazai bar shiga
shirginta ba?,wato har wani nuni yake musu dashi a hoto

"Tashi ki bani waje" ta fada tana watsa mata harara. Har ta miqe sai ta dawo a sanyaye,ta tsugunna
gabanta murya a sanyaye

"Kiyi haquri aunty" ta fadi tana mutsuka idanunta da qwalla ke fita. Ido tadan xuba mata na
sakanni,tausayinsu su dukka yana ratsata,ita da yaran gaba dayansu ababen tausayi ne,sai itama taji
nata idanun sun ciko,ta sanya hannu ta jawota ta rungumeta a jikinta.
Ajiyar zuciya yarinyar ta saki tana yin luf a jikin nata,kasancewar basu fiya samun wannan
damar ba,saida tayo controlling nata hawayen don kada ta gani sannan ta sake tana cewa

"Kije wajen bibi naji kaman tanja na kiranki"

"To" ta amsa tana miqewa da dan tsallenta tamkar komai bai faru ba,gashinta dake daure yanaya lilo a
bayanta ta fice a dakin.

Binta tayi da kallo har zuwa bakin qofar,sai a sannan taga ama dake tsaye hannayenta goye a
qirjinta. Sauke hannuwan tayi ta tako cikin dakin,yau dai sau daya tak taji zata yima.sultana din
magana,zafin qiyayyar aliyyu da take gani a idanunta sun fara bata tsoro,tayi tsammanin ilimi shekaru da
kuma wayewa sata samu zasu goge komai,koda komai din bai gogu ba tayi zaton xai ragu ainun har ya
zamana bai iya bayyanuwa a idanun mutane

"Sai yaushe sultana?,sai yaushe zaki sassautama ranki wannan abun dake qulle cikun zuciyarki?" Karon
farko tayi mata tambayar ido cikin ido.

Qasa tayi da kanta,ba zata iya jurar kallon qwayar idanun ama ba,nauyin da dukka ruhi keji
akan uwa game da d'anta ya saukar mata. Da alama abun ya zafafi ama a yau tunda har ta
magantu,shine abinda sultana ta raya a ranta,kamar ta karanci abinda take rayawar sai ta bata amsa
tana gyara zamanta

"Kada ki dauka naji haushi ne ko nayi fushi ko kuma zanyi fushin,ko kadan,shekarun da muka dauka
abinda nake gani cikin idanunki na saba ganin irinsun......amma yanzun rayuwa tana sauyawa ne,yaranki
yaran aliyyu ne,bai kamata kina bari suna karantar wannan harshness din dake cikin idanuwa da
kalamanki ba,wani abun bau cancanci 'ya'ya suna sani akan iyayensu ba,wata kakkaifa kuma qaqqarfar
dangantaka ne da tafi qarfin kowa yayi shishshigi a cikinta.........zamu je umra cikin satinnan in sha
Allah,daga can zamu wuce nijer sai bayan bikin aminata da yasmine zamu dawo,amma immediately
saboda maganar gidan tv dincan" kai ta gyada hawaye suna son sauko mata,amma batason tayi
kukan,kada ama ta zaci don ta mata fada ne

"Kiyi haquri" tace da ama bayan aman ta miqe,a sanyaye ta waiwayo tana dubanta
"Ke ya cancanci ayita bawa haquri sultana,ba za'a daki mutum a hanashi kuka ba,kawai dai kukan saffa
saffa ya dace kayi,tunda kayi imanin ko meye ya sameka ko zai sameka daga Allah ne" kai ta sake kadawa
a sanyaye.

Hannuwanta dukka biyun ta sanya ta lullube fuskarta dasu tana sakin wani asirtaccen kuka. Ita
kanta ciwon da qirjinta ke mata a kullum ta tuna da ita din wacece ya soma isarta,bataso,tanaso ta rayu
da zuciya sakakkiya kamar kowa,ta rasa me yasa ta kasa watsar da komai,ta manta da komai?,ta manta
da wanzuwarsa a duniya kamar yadda yayi nesa da rayuwarsu itama ta nesanta kanta da komai da
yashafeshi

"In sha Allah wannan zai zama jigon addu'a ta a wannan tafiyar......in sha Allah zan gayawa ubangiji
na......zan roqeshi da dukkan sunan da yake amsa addu'a idan an kirashi da su,zan masa magiya ya sake
nesantaka daga cikin tunani......daga cikin rayuwata ni da 'ya'yana......zan roqi ubangiji ya kawo silar
tsinkewar igiyarka data daureni" ta yiwa kanta wadannan alqawuran.

Tana takawa zuwa dakinta amma tunani ne fal zuciyarta. Duk da rakinta da ake gani.....duk da
qin yarda da daukan qaddarar da wasu ke gani kaman ta gaza JARUMA ce sultanar,zama da igiyar wani
da bakaso tsahon shekaru babban nauyi ne,ya kamata susan abunyi akai......amma wai ina maina?,INA
MAINA YA SHIGA?,YANA RAYE KUWA ANYA?. Da wannan tunanin kadai saida zuciyarta ta buga,idan har
ya mutu a ina?,a hannun wa?,waye ya sururta d'anta?.

*_M A I N A_*

Wani irin matsakaicin falo ne dake da wani irin atmosphere mai matuqar daukan hankali da
tafiya da tunani. Komai dake wajen tun daga color da yanayin da aka tsarashi da kuma unguwar da
ainihin ginin ma yake zakasan ya banbanta ya kuma yi nisa qwarai da kalar tamu rayuwar.

Cikin daya daga cikin luxury sofas dake zagaye da falon yake zaune sosai,irin zaman da zakasan
lallai yayi relaxing yadda ya kamata,bashi kuma da nufin tashi yanxu,hakanan da alama ba wani schedule
dake a gabansa.
Zabgegen farin ba'abzine,jazur tamkar ka sanya yatsa jini ya fito,dogo me murjajjen
jiki,ma'abocin baqar sassalkar suma,tun daga saman kanshi,girarshi,gashin idanunsa har zuwa
kumatunsa da aka yiwa sumar wani irin gyara dake zamewa fuskar mazaje ado na musamman me kama
da gold a inda akasan daraja da kimarsa.

Yanayin kayan dake jikinsa pajamas ne masu gajeran wando da kuma gajeran hannu,farare
tassss tasu masu tsananin taushi da aka saqasu daga audiga mafi tsada da daraja. Dogoyan fararen
qafafuwansa da hannayensa dukka lullube suke da gargasa baqa sidik saidai duk yawan gargasar bata
hana bayyanuwar murdewa damtse da qafafunsa ba da kuma tsananin da fatarsa ke dashi wanda ke
cakude da sirkin ja......duk da a zaune yake structure na jikinsa ya fita sosai a matsayin mutum ma'abicin
shiga gym da daga qarafuna.

Babu gilmawar annuri ko kadan saman fuskarsa,hannunsa na dauke da tab dinsa,a nutse kuma
yana bin hotunan daya bayan daya yana kalla.

A duniya bai taba jarabtuwa da soyayyar wani abu da baisan asalinsa ko tushensa ba irin yadda
ya jarabtu da soyayyar wadannan twins din ba,a duk sanda yake kallon hotunan yaran yakanji tamkar ya
cirosu daga jikin hotunan ya gansu a zahiri,yakanji har a ransa soyayyar d'ansa da goumar ya gaya masa
sultana ta haifa tana hauhawa a ransa,yaron da ya tabbatar da gangan goumar yaqi bari ya gansa tsahon
shekarun,duk wata jafa ko hanya da zaiga yaron goumar din ya tosheta,ya gaya masa.muddin yanasin
ganinsa ya dawo gida,ya dawo cikin ahalinsa ya fuskanci ko ma meye. Abinda ya tabbatar goumar bazai
fahimta ba a sannan,duk bayanin da zaiwa goumar bazai fahimceshi ba,shi daya yasan meke faruwa
dashi,shi daya zai iya fahimtar damuwar da matsalar. Ya zuwa yanzun yana jin haqurinsa ya gaza......
tafiyarsan nan ta qarshe da ta zama cikamakin burikansa tazo masa da abubuwan ban mamaki masu
tarin yawa,mafarkinsa yakai ga gaci,ya cimma nasarar rayuwar da a mafarki bai taba tunanin zata isar
masa ba......yanajin yakai qarshe,ya kuma tuqe......yana da buqatar yayi gaba da gaba da ahalinsa......ya
shirya karbar kowanne hukunci,ya kuma shirya fuskantar su dukka gaba daya. Yanason ganin
d'ansa.....yana da buqatar ya bayyanawa d'ansa shi waye a wajensa,amma kuma dukka wadannan
abubuwan me ya tanada?.

"Ina da rabb" ya bawa kansa amsa,saboda yayi imani shi daya yasan me yake cikin zuciyarsa,shi daya
yasan gwagwarmayar da ya fada shi daya yasan yadd ya rayu ya kawo wadannan shekarun har ya qarasa
zama CIKAKKEN MUTUM ya fita a cikakken DR MAINA.
Shawara guda daya tak zuciyarsa ta bashi yaji farinciki da gamsuwa. Yaji a ransa tabbas
mafitarsa kenan,ya dangane da dakin Allah yakai masa kukansa kamar yadda ya saba,a wannan karon ya
nemi qwarin gwiwar tunkarar ahalinsa,ya nemi jarumtar iya karbar kowanne hukunci da mahaifansa
zasu yanke masa

"Harda hukuncin rabuwa da sultana?" Mummunan tunanin da yaso birkitashi ya darsu a zuciyarsa lokaci
guda.

Kai ya dinga girgiza da sauri da sauri yana jin kowanne sashe na jikinsa na qaryata yiwuwar
karbar hakan. Ya aza dukka qarfinsa ya tankwabe tunanin gefe,ya tattara hankalinsa akan sabon hotunan
yaran.

Murmushi ya dinga saki yana binsu da kallo gami da saukesu daya bayan daya akan tab din
kamar yadda ya saba. Yana da hotunansu bila adadin dashi kansa baisan yawansu ba,abinda ya sani dai
ba'a taba dora wani hoto nasu a personal Instagram account din yaran bai saukeshi ba. Yayi bincike yayi
bincike amma ya kasa fahimtar 'yan wanne qasa ne?,ina ne asalinsu?, ba'a taba dora hoton wani abu ko
hoton wani ba sai nasu,ba wani abu da aka tana dorawa da zai sanyaka fahimtar su din su waye.

Sai daya gama saukesu tsaf sannan ya sauya wallpaper na iPhone da tab dinsa da sabon hoton
nasu kaman yadda ya saba. Tsaiwa yayi yana kallon yadda hoton yayi kyau saman screen din wayar
tasa,wani miskilin murmushi ya kubce masa.

Mutanen da suke mu'amala dashi wansunsu da yawa suna tsammanin yaran 'yan uwansa
ne,banda sunsan single yake da yawa zasu zaci nasa ne yaran saboda yawan hotunansu da yake dasu,da
kuma yawan dorasun da yakeyi zaman dukka screen nasa da yake using dashi. Wasu lokutan shi kansa
yakan gayawa kansa ya zaqe da yawa,to amma shi kansa baisan me yasa yake jinsu har cikin jininsa ba.

Knocking da akayi a qofar falon dake waje hade da kada bell ya sanyashi daga kansa,ko ba'a yi
magana ko ya duba camera ba yasan waye,ba wanda ke hada masa irin wannan rubdugun knocking da
bell din idan ba suhail ba,sai ya aje tab din ya miqe zuwa bakin qofar.
*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261
*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[29/05, 9:56 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 44

Yana bude masa qofar ya dawo ciki abinsa ya koma inda ya tashi ya zauna. Suhail din ya shigo
kunnensa manne da waya yana amsawa. Hannun kujera ya samu ya zauna yana ci gaba da amsa
wayar,yayin da maina ke sake ci gaba da kallon fuskokin yaran.

"Haka Allah yake jarabtar bayinsa da qaunar wasu bayin nasa na daban da basusan da zamanka ba"
suhail ya fada yana danna wayarsa. A nutse maina ya daga kai yana duban fuskar suhail cike da mamakin
furucinsa. Yaune karon farko da yayi magana akan yaran cikin kwantar da harshe da kuma murya. Kusan
ko yaushe yafi zabar tsokanarsa da yi masa iya shegen
"Mutumina gwara kayi aure ka haife mana twins dinnan ko fuskokin yaran nan zasu huta" sau tari saidai
yayi murmushi kawai ya shafi sumarsa. Har yanzu cikin suhail da ahmad bello da sukewa laqabi da
sardauna.....mutanen da suka zame masa shaqiqai kuma makusanta bayan barinsa gida basu taba sanin
ya taba aure harda yaro ba.

Wani irin mutum ne shi tun asali me tsananin zurfin ciki,zaiyi wahala kaji qorafi ko wani zance
daban a bakinsa. Tun a halittarshi yana da qaranta magana da surutu......a yanzun kuma sai abun ya
zame masa ninki.

Akwai yawa yawan mutane da sukayi tsammanin kurma ne shi din,rana ta farko kuma da yayi
magana a gabansu a mamakance suke waiwayowa suna dubanshi saboda ranar ne suka fara jin lafazin
bakinshi.

Kallon da maina din yakewa suhail ya tabbatar tambaya ce cikin idanun nasa,amma yasan zaiyi
wahala ya tambayeshin kai tsaye,don haka ya aza wayar saman qawataccen glass table din gabansa ya
goye hannayensa a qirji yana duban idanun mainan

"Na fada soyayya da kallo daya tak aliyyu......I don't know how to explain it....abun kamar shirin
film,ganina daya tak da ita ta ban kuma ganinta ba,har yanzu ban mance fuskarta da kuma kamanninta
ba.....ina jinta kusa da zuciyata qwarai,bazan kuma fasa nemanta ba a duk inda nake tunanin zan ganta".

Kamar maina ya samu statue haka ya zuba masa idanunshi har ya kammala,suhail din ya
fuskanci hakan,yasan halin mutumin qwarai da gaske,ba lallai ya fahimci dukka dogon bayanin nan nasa
ba,don haka yaja dan qaramin tsaki yana daukar wayarsa

"Bansan me yasa na zauna naketa maka bayani ba bayan zuciyarka ba'a halicceta don taso diya mace har
tayi sha'awar aure ba.......abu daya naga kana yiwa mahaukacin so wadannan yaran da bakasan nahiyar
ma da suke ba" ya qarashe maganar yana zuba idanunsa kan wayarsa. Maganar tasa ta sanya maina
maida dubansa saman fuskar tab dinsa,sannan ya zame tab din ya ajjiye yana hade hannayensa guri
guda
"Me yasa ka yiwa zuciyata wannan fassarar?" Ya jefawa suhail tambayar da wani irin sound me taushi
saidai kuma cikin tsakiyar taushin muryar tasa akwai wani irin deep amo me saurin isar da saqo kunnen
me saurarensa koda baka shirya hakan ba.

Sai da suhail ya waiwayo ya kalleshi sannan yace

"Ah..... Mr man,nayi qarya ne?,ko iya yadda LAILAH keyi maka tsahon shekaru inajin ya kamata zuciyarka
ta narke ka saurareta......amma fa banga alama ba,ba alamun zakayi giving up,ko kunyar sardauna baka
ji?" Kai kawai ya kada yana kallon gefansa

"Akwai abubuwa da yawa da baki bazai iya bayaninsu ba suhail......."

"I see" ya maida masa cikin gatse,sai kuma ya tsaya cak yana sake duban maina

"Kai.......if i can remember kamar naga face din yaran nan zuwa na umra last fa?" A nutse maina ya sake
kallonsa ba tare da ya motsa ko yace komai ba,saidai cikin qasa da second biyu ya fahimci ba wasa bane
irin na suhail,da gaske yake

"Really?" Ya tambayeshi yana dage dukka girarshi biyun

"Yes.....da gaske nake.....kaman a hannun rival dinnan da kaji ina bawa sardauna labari.....a harami ne
tabbas" haka kawai ajiyar zuciyar da maina baisan dalilinta ba ta kufce masa,muryarsa so cool yace

"Zuciyata gaba daya ta karkata zuwa umra,ka dubamin yadda zan samu ticket da wuri mana please"

"Kai da ka fini xuwa akai akai ai kaman ka fini sanin masu siyan ticket da wuri ko?"

"Baya nan man din.....baya kusa" ya amsa mishi da alamun zaquwa sosai cikin muryarsa,sannan
shigowar Moses wanda ya fito daga kitchen dauke da breakfast tray na ogan nashi yaja hanakalinsu.
Rusunawa yayi ya gaida suhail,suhail din ya amsa masa yana dan janshi da tsokana kadan
sannan moses din ya wuce yana shirya dining

"Amma zuwa nayi muji yaushe sardauna zai dawo,mu kammala lissafi saboda nasan kowa yana da nashi
plan din ko?"

"Bazan zauna jiran sardauna ba.......kuyi komai koda bananan ba matsala bane,tunda idan na dawo
dinma duka duka bazan haura sati daya ba zan wuce paris......next month asibitin zai fara aiki in sha
Allah"

"Alright......ba matsala" suhail ya fadi yana lalubar wata number

"Kwana nawa zakayi?" Idanunsa na a rufe,yatsansa guda daya ya dagawa suhail sannan labbansa suka
motsa da

"Month". Sai ya maida kansa ga dannar wayar,ya sani duk sanda maina ya shiga irin wannan mode din
bai fiyason takura ko yawan magana ba,wannan ya sanya suke dauke masa qafa da kuma yi masa
uzuri,duk da basusan taqamaimen damuwarsa ba har kwanan yau.

********Benazeer da batoul ke akan gaba janye da wasu kyawawan qananun qawatattun luggage dai
dai su wanda ama ta bada order yinsu musamman saboda benazeer da batoul din tun daga dubai.
Kowanne luggage na dauke da sunayensu a jiki da wani ruwan gold din rubutu. Abayar jikinsu ma haka ta
kasance,gray color ce da tayi masifar dacewa da yanayin yaran. Kubul kubul dasu babu rama babu
mummunar qiba,hutu jin dadi da zallar nutsuwa ta bayyana tattare dasu. Komai dake a jikin dayar akwai
jikin dayar,abinda zai matuqar rudar dame kallonsu yayi tsammanin mutum daya ne aka tsagashi gida
biyu,don hatta da rufaffen takalmin dake qafarsu na kamfanin D&G ba abinda ya banbantasu dana
juna,haka siririn agogon gold dake hannuwansu.

Suna gaba ama da sultana na biye dasu,su dinma abayar ce a jikinsu me matuqar tsada da
daukan hankula.
Batasan me ya sanya ba wannan karon tunda suka diro madeena gabbanta suke a
sanyaye,tayita neman tsari daga sharrin shaidan koda shike da niyyar hanata ibada wannan karon
tuquru kaman yadda ta saba,tunda shi din maqiyin duk wani dan adam ne,ta sanya hannunta ta gyara
zaman glass dinta dake taimakawa ganinta,wanda akayi mata tun a wancan lokacin da idanunta suka
samu raunin gani. Tun zuwansu Austria ama ta sanya aka sabunta mata shi,aka maidashi na ado sosai,a
wancan lokacin qin yin amfani tayi dashi,sai a sannu data fara fahimtar inda rayuwarta ta sanya gaba ta
nemeshi,ya zuwa yanzun kuwa tana nan dasu kala kala,dukkansu zaka dauka tana sakasu ne saboda ado.

Ba yadda aba baiyi da ita ya fiddata a duba idanun ayi mata aiki me kyau ba amma ta qiya,tsoro
takeji qwarai,tana ganin idan aka tabata ana iya rasa idanun duka ma.

Kamar ko yaushe suna isa masauki tayi wanka taci abinci ta wuce masallaci,tayita zuba idanun
ganinsu benazeer da batoul amma bata gansu ba,har ta kammala ta dawo bata gansu ba.

Samunsu tayi cikin dakin sun baje kayan ciye ciye sunata fama,benazeer tafi batoul bawa abun
muhimmanci,ita batoul da alama ta gama ta koma kan waya.

Harara ta watsa musu dukkansu sai suka nutsu,bata ce musu komai ba har tashiga ta sake
wanka ta fito,sai ta samu dakin wayam da alama sun gudu wajen ama,ta gyada kai tana jan qwafa ta
koma saman gado ta nade ta fidda wayarta tana dan duba wasu abubuwa da suka shafi channel din da
take sanya ran farawa aiki tare da dakon jiran shigowarsu. A qalla yanzun sun fara girma,shekara hudu
cikin ta biyar ai sun san gabas sunsan yamma,ba zata barsu haka siddan su dinga zuwa waje me alfarma
irin wannan ba tare da sunsan muhimmancinsa ba. Har ta gama jiran bacci ya saceta basu dawo ba,basu
hadu ba sai data tashi sallar asuba,sai data kammala tata sallar sannan ta tashesu sukayi tasu,ta ritsasu
tana tambayarsu me ya zaunar dasu jiya?.

Inda inda suka fara mata,daga qarshe batoul ta sanya kuka, benazeer ce me bada haquri,ta
musu kashedi sosai,wanda tana tsaka da yin ama ta shigo.

Dariya ta dinga yi ciki ciki,ita tunda take bata taba ganin alaqar uwa da d'a irin ta sultana
ba,gaba daya ta zame musu wata senior master bawai mummy ba. Da ama tabi ba'asi sultana ta gaya
mata,sai ama taqi bin bayansu
"Eh da gaskiyar auntynmu,daga yau a dinga qoqarin zuwa masjid kunji ko?,amma kuma auty ayi mana
afuwa,a dinga tafiya daga baya zamu taho tunda munsan wajen kuma bamu da nisa,munyi alqawarin ba
zamu sake zama daki ba,idan kuma mukace mun gaji a barmu mu dawo daki mu huta" ama ta fada tana
hada hannayenta waje guda. Murmushi ne ya subucewa sultana hadi da nauyin ama,saita kada kai
kawai,ama dai ta samu ta kwashe 'yan jikokinta suka fice hawaye shabe shabe.

Tun daga ranar kuwa basu saba alqawari ba,kamar wasu manyan 'yammata,koda ta tafi zasu
biyo bayanta,saidai kuma sai sun gama qailularsu,siye siyen chocolate da fadace fadacensu na tsakanin
sako da sako.

Satinsu guda kacal bibi itama ta iso,sukayi jiranta ta gama nata ibadar suka wuce makka.

*_makka_*

*_Al_ajyad street_*

*_SWISSOTEL HOTEL MAKKA_*

Kai tsaye motar kamfanin dake da alhakin tarbarsa ta wuce dashi swissotel,wanda kusan duk
sanda ya shigo garin makka din bashi da hotel din da ya wuce wannan,hotel ne da yake jin dadin zama
cikinsa sosai,saboda daga nan yana iya hangen haram tarwai,har wasu lokuta idan yayi tsaye daga bakin
window din dakinsa yakan yi addu'o'i sosai kafin ya sake labule ya wuce.

VIp suite suka bashi saboda cancantarsa da cab din,aka tabbatar da shigar da jakarsa ciki,da
kuma tambayar abinda yake da buqata suka gabatar masa sannan suka danqa masa dakin a hannunsa.
A nutse yake cire lallausar rigar saman kayan jikinsa,daya daga cikin shigar 'yan qasar hindu,riga
ce me wando da top dinta qarama me budadden gaba,wadda an saqata ne da yadin zaren vicuna mai
matuqar daraja da tsada. Da baya ya zauna saman sofa din dake dakin yana lumshe idanunsa,kanshi
yana kallon sama yana furzar da numfashi da kadan da kadan ta cikin bakinsa da wata iska me zafi.

Wata nutsuwa ke zagayashi,a duk sanda ya tsinci kansa cikin qasar sai ya dinga jin zuciya da
qirjinsa wasai,saidai kuma hakan baya hanashi jin wani abu a jikinsa,irin jin da me nauyin laifi saman
kansa yakanji a duk sanda ya gujewa laifinsa da ya aikata. Tsahon shekaru yana jin wannan abun a dukka
wani motsi ko tattaki na rayuwarsa,ko sau daya koda na minti daya zuciya ruhi da kuma gangar jikinsa
basu taba samun hutu ba game da hakan,a haka ya rayu.......darare da yawa bacci yana qauracewa
idanunsa......lokutta da yawa yana sarayar da baccinsa ya zauna dangwargwar,sautukanta......furucinta
da lafazzanta suna dawo masa sabbi fil cikin kansa..... zuciyarsa na tuhumarsa,tana sake maimaita
tuhumrsa,me yasa?......don me ya gaza kai zuciyarsa nesa?,don me yasa ya kasa haquri ya dauke kai?,me
yasa ta gaza cin albarkacin nafessa?,ya cika alqawari?,yayi abinda ya dace?,a yau inda nafessa zata dawo
duniya zaya iya fuskantarta?. Bai sani ba shima.....baisan me yahau kansa ba,baisan me ya fusgeshi
ba......kawai yaji har cikin ransa ya aikata,hakan kima shine dai dai.....shi zai sanyata nutsuwa,shi zai
zama mafarin lanqwasuwarta da shigarta taitayinta. To ashe dukka yayi bahaguwar fahimta,ashe muqulli
ya sanya zai kuma bude musu sabbin shafuka da qofofin qaddara masau tsauri da nisan zango irin
wannan.

Sai daya samu nutsuwa gabbansa suka huta sannan ya bude idanun nasa yana duban agogon
dake manne a bango, mintuna qalilan suka rage a tayar da sallar isha'i,kuma yana da matuqar muradin
samun sallar cikin jam'i,kamar yadda duk tsanani ko wuya ko a ina yake baya barin jam'in kowacce sallah
ya WUCESHI,musamman asuba da isha'i saboda falala dake cikinsu.

Kayan jikinsa ya fara ragewa,yana cirewar yana jin yadda wayarsa ke qugi. Baiyi koda attempting
din tabata ba,saboda yaga wacece me kiran,yasan kuma ba Wanda ya shaida mata ya tabo nan din sai
suhail,yanzun kuma ba lokacin wasa ko lokacin bata lokaci bane,duk da dama can ya bawa wajen
muhimmanci me tarin yawa cikin rayuwarsa,da har baya iya daukan lokaci baizo ba,to amma yanzun
buqatu gareshi masu nauyi,wani babban aiki ne a gabansa da yake da buqatar jajircewa yayi addu'a da
kyau.

Cikin kayansa ya fidda bathrobe ya rataya sannan ya wuce toilet abinsa.


A gaggauce suka iso swissotel suka kuma gama komai suka karba maqullan dakuna guda biyu
kamar yadda suka saba,daya na ama da aba,daya kuma nata da su benazeer da bibi,don haka classic
room suka dauka me gadaje uku.

Suna shiga ta duba lokaci,sannan ta sake duba babban agogon nan dake garin makka. Lokacin
isha'i ya kusa yi,don haka a gaggauce ta cire kayanta don watsa ruwa,tanason a qalla takai tsakiyar dare
gaban ka'aba,akwai tarin buqatu da take dasu,ta kuma tabbatar tayi imani tare da yaqinin amsasu a
wajen kamar yankan wuqa yake,ba wata addu'a da tayi bataga karbuwarta ba,a yanxun ma tazo da
kukan yankewar igiyar aure da tayi saura tsakaninta da maina,don bata da qwarin gwiwar sake fuskantar
su aba da zan can. Tun tana kasa kunnuwa taji aba din ya nemeta harta fidda rai,kullum zancan yana a
ranta,saboda xuwa yanzun tasan girma da nauyin igiyar dake kanta tsahon shekarun........

"Ku gama abinda kukeyi da wuri,da minti goma yau zan rigaku fita" ta fada tana daga musu yatsunta
gami da shigewa toilet din,sai bibi ta bita da kallo tana kama baki,abun mamaki wai yau sultana ce da
tsantseni da tsananta tarbiyya

"Yar nema,kina kamarsu ma sanda kike zuwa daki kike kwance abinki har muje mu dawo kina bacci shine
yanzun da wanan sirisirin hannuwan naki kike irga musu lokaci" qaramar dariya ta saki tana tsaka da
brush,don fes taji abinda bibin ta fada. Itakam ta karanceta irin mutanen dake son jikoki da yayan jikoki
ne fiye ma da yadda sukewa yaransu da suka haifa soyayya

"Allah yabar mana ke bibi" ta fada qasa qasa tana tuna wasu lokuta na quruciyarta can shekarun baya
murmushi ya sake subuce mata

"Ba abinda bashi da iyaka sai ikon Allah" ta fadi a ranta

*_KACIBUS..........😂INJI HAUSAWA DON BANA QARASA BA,SAI NACE KUZO MUJE*_

*_KWANKWASON JIMINA_*
*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261
*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[30/05, 9:30 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 45

Sun dudduba benazeer sun kuma tabbatar masa ba komai,don dama faduwar ba wata babbar
faduwa bace. Dariya ta dinga yima maina

"Uncle......wai tsoro kaji?,banji ciwon komai bafa,faduwar ma kuma babu zafi" ta fadi tana dariya gami
da tafa hannuwa. Idanunsa shidai carrr a kanta,sai ya saki qaramin murmushi sannan cikin tsokana yace

"Na ganki 'yar lukuta ne,kuma lukutaye basu da qarfi,sannan ma ance mutum idan ya cika fari shima
bashi da qwari wai" ya qarashe fadi yana dan tabe baki kaman zai saki kuka yadda yara qanana sukeyi.
Wannan karon har batoul sai data qyalqyale da dariya,sai shima ya biye musu yana tayasu,suka amsa
receipt suka fito daga pharmacy din.
Shagunan ice cream ya nufa dasu,yaja kujera kawai yayi zamanshi abunsa kamar wanda bashi da
sauran aikin yi yace su duba duk wanda sukeso. Aifa benazeer an samu abunyi,duk bayan daqiqa sai ya
waiwayo ta dubeshi

"Uncle a sakamin banana flavor?"

"Eh a saka miki" sai ya amsata yana murmushi,bayan wata daqiqar saita waiwayo tace

"Uncle vanilla fa?" Sai ya sake murmushi yace

" A baki" at last ya fahimci sun saba da shansa ne,kuma suna sonsa sosai don haka yace da ma'aikacin
wajen

"A musu takeaway na dukka flavours din da suke dasu". Murna ya kama benazeer harda qaramar
rawa,shikam yana zaune tamkar wanda ya samu tv dake bashi nishadi.

Duk yadda suka sake dinnan dashi abinda ya bashi mamaki,qememe wani sukaqi bin wani
balare da yace musu shagon gabansu zai siya musu gift na Pizza. Suka hau kallon kallo gami da maqale
kafada suna kuma satan kallon maina din. Dariya suka bashi suka kuma burgeshi qwarai,dole sai nan ya
siya ya kawo musu,a nan dinma maina ne yace su ansa,saboda yasan wajen wajene mai aminci,ba wani
abu na cutarwa ko me cutarwa da zaiyi tasiri a wajen.

Shi ya riqo musu ledan suka qarasa haram sukayi sallah tare dasu bayan kowacce ta gyara
mayafin abayarta,ya dinga dariya sanda suke gardama tsakanin benazeer da batoul,ita batoul tace lallai
sai benazeer ta sauya alwala saboda ta fadi,kuma ma tayi surutu da yawa,itama kuma ta dage kai da fata
alwalarta ba abinda tayi,da qyar ya raba gardamar.

Kiran wayarsa da akayi ya sanyashi miqewa don ya matsa gaba kadan ya amsa wayar saboda
wajen da sukayi sallar yana ganin bai kyautu ya daga wajen ba. Yana Allah Allah yacemusu su tsaya ya
maidasu masaukinsu amma number dake kiransa din tana da matuqar kima da martaba a wajensa,don
haka ya taka a hankali yana qoqarin dagawa.

Kallon benazeer batoul tayi tana miqewa

"Mun dade B,nidai tafiya zanyi,kya taho"

"Bamu yiwa uncle sallama ba" ta fada cikin yanayin damuwa tana kallon hanyar da yabi

"Gobe sai muyi masa" ta bata amsa tana sanya takalmanta. Miqewa benazeer din tayi tana yarda da
maganarta,suka gama sakawa suka dauki ledarsu sukayi hanyar da zata sadasu da swissotel hotel.

Sassanyan turarenta ta feshe jikinta dashi bayan ta kammala sanya rigar baccin me taushi da
rashin nauyi,ta maida turaren ta ajjiye tana satar kallon bibi dake kwance tana kallon tv. Daga kai tayi sai
suka hada ido da sultana

"Wai ina yarannan ne suka tsaya haka?" Bibi ta fadi tambayar kuma data yiwa sultana din dadi kenan.
Abinda taketa lissafawa kenan cikin zuciyarta,sun dade fin yadda suka saba,duk da dama shiriritarsu
yawa ne da ita amma basa kaiwa haka basu dawo ba.

"Ban sani ba bibi,hala shiriritarsu suka tsaya" ta amsa mata cikin basarwa tana ninke abayar data cire

"Ke kinga banson kidifirin banza....sanya jilbab dinki ki bisu,don kunga waje amintacce ne kunsan ba
abinda zai faru dasu amma ai yana da kyau a dinga bibiyarsu ko?" Bata musa ba ta miqe ta saka hijab din
nata,don dama abinda takeso tason yi kenan,kunya da kawaici ya hanata. Bata taba tsammanin akwai
yaran cikun zuciyarta da rayuwarta gaba daya ba sai yanzu.

"B fuskar uncle fa kamar ba santa Allah" benazeer ta fadi tana yamutse fuska irin na yara masu surutu da
shegen wayo. Harara batoul ta balla mata tana tura baki gaba
"A'ina kika sanshi,yau muka fara ganinsa fa,kuma Allah duk sai na gayawa auty da ama abinda kika dinga
yi" ido ta zaro tana kallon batoul din

"Me kuma nayi?"

"Ba an hanaki surutu da kula wanda baki sani ba,shine kiketa bashi labarin school enmu ko da fada masa
sunayenmu"

"Kuma daga wannan shine zakice zaki gayawa aunty?,don Allah B kinji kada ki fada,kinga uncle ai yana
da mutunci,kuma ai don ya bugeni ne na kulashi,bazamu sake ma ganinsa ba inajin tunda bamusan ina
yake ba"

"Sai an fada din" ta fada tana murguda baki tare da fitowa daga elevator din bayan ya tsaya a floor dinsu
benazeer ta biyo bayanta tana magiya.

"Meye ake cewa kada a fada?" Suka tsinci muryar sultana dake qoqarin shiga elevator ta fasa saboda
ganinsu.

Tsuru tsuru dukkansu sukayi,sai kuma suka hau kallon kallo. Idanunta ta zuba musu sosai yadda
ta saba musu duk sanda takeson gano laifi ko gaskiyarsu,a hankali kuma ta maida dubanta ga ledar
hannunsu

"Daga ina kuke?,waye ya baku wannan kuma?" Tayi furucin tana nuna ledar

"Uncle haidar ne" benazeer ta furta da shagwababbiyar muryar nan tasu data cakuda da sauti na tsoro.

"Uncle haidar?,waye haidar kuma.?" Ta tambayesu gabanta na wani irin faduwa,sunaye ukun nan a
duniya,duk lokacin da zata jisu sai sun barwa zuciyarta razani ALIYYU HAIDAR MAINA.
"Mun taho masallaci na siya ice cream dina ya bugeni ya zube,shine ya kaini pharmacy aka dubani ya
kuma siyo mana wannan" yadda suka tsorata ya sanya ta sassauto

"Da nace kada a siyoshi sai anyi sallah shine bakuji ba?,ku wuce ku bani waje" ta fadi a dan fadace. Da
sauri sauri har suna rige rigen wuceta a tsakaninsu suka bar wajen,tana nan tsaye sai data tabbatar sun
shiga dakin sannan murmushi ya qwace mata. Tabbas idan bakayi da gaske ba yaran saisu maidaka wani
abun wasansu.

Kudin hannunta ta duba,akwai abinda takeson sauka qasa ta siya itama,don haka ta matsa
gaban elevator din tana yunqurin kiranshi, saidai ta nuna mata akwai mutum ciki dake haurowa
saman,wannan ya sanya ta tsaya daga gefe tana danna wayarta tana jiran isowarshi.

Kansa yana qasa,shima kuma wayar yake dannawa,a haka ya fito itama idanun nata nakan waya
ta sanya kai ciki. Lokacin da suke gifta juna......iskar data debo kowa ta bugi dan uwansa har cikin jini da
jijiyoyinsu sai da sukaji wani irin yanayi. Turarensa shi ya fara bugar da ita ya kuma haifar mata da
qaqqarfar faduwar gaban data fusgi hankalinta,ta kuma kawar da hankalin nata daga kan waya,ta daga
kanta tana duban bayansa......yana takawa ne a hankali kamar bayasin taka qasar,tsayyayen namiji me
cikakkiyar siffa da zati,kwantacciyar sumarsa dinnan na kwance luf daga qeyarsa da take iya hangowa,
dogayen hannayensa dake dauke da wasu veins kawai take iya hangowa,ta zubama bayan nashi idanu
tana jin mahaukacin bugun da zuciyarta keyi irin wanda bata taba ji tayi irinsa ba,tilas ta yiwa kanta da
kanta tambayar a fili yadda iya labbanta ne kawai suka motsa

"Waye wannan?" Ta furta idanunta bisa bayan nasa. Tayi imani ba'a banza zuciyarta ke wannan bugun
ba,tayi yaqinin koma waye akwai wani abu me qarfi tsakaninsu,tabbas!!!!..... zuciyarta ba zatayi wannan
bugun da ya sabawa qa'ida ba muddin ba wani abu mummuna ke shirin faruwa da ita ba,wanda wannan
tunanin ya sake haukata bugun zuciyarta.

Shi kansa yasan ya danyi nisan tazarar taku tsakaninsa da elevator din yana replying saqon da
ya zame masa kaman dole ne ya amsa din bawai don yana so ba.......amma cikin kowanne jini dake
harbawa jikinsa wani abu yaji yana bibiye da harbawar tasa zuwa qwaqwalwa da zuciyarsa. Cikin jikinsa
yaji kamar akwai wasu idanuwa masu kaifin gaske dake kallonsa,akwai wani dake bibiye dashi daga
bayansa,wannan ya sanya ya juyo a hankali zuwa saitin elevator din,daidai sanda ta gaji da barin kanta
da kanta a hangame ta soma rufe kanta.
Cikin idanuwanta idanunsa suka fada,haduwar idanuwa hudun da suka bada wani gigitaccen
yanayi cikin zukata da qwaqwalensu. Dukkaninsu jinsu sukayi kamar daga wata duniya suka fado
kwatsam ba tare da kowannensu ya shirya ba,babu wani dake iya cikakken motsi bare yunqurin janye
idanunsa tsakanin shi da ita,har sai da qofar ta fara motsawa zata rufe din. Kamar wani magnet ya jashi
haka yaji,ya fara takawa da wani irin sassarfa da hanzari yana nufar elevator din.

Ruf ta rufe kanta kafin yakai ga isa,yana miqa hannu kuma ta fara sauka qasa dauke da sultana
wadda ta kama qarfen jikin elevator din kam ta riqe gudun kada takai ga faduwa,saidai kuma duk da
hakan zuciyarta da ruhinta dukka sun gaza samar mata da qarfin da zaya iya riqeta a tsayen,dole ta
sulale a hankali cikin elevator din ta zauna dirshan tana jin kamar tana shirin fita a hayyacinta ne.

[01/06, 11:04 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 46

Da sauri ya lalubi wani elevator din,ya kuwa samu a kurkusa dashi,ya iso ya shige,saidai ya kasa
tsaiwa waje daya,yana jin kamar dakin ba tafiya yakeyi dasu ba,kamar a tsaye yake cak waje daya,cikin
qwaqwalarsa wani abu ke masa yawo kaman ana yamutsata.

Cancan nesa da hotel din nasu ta kai kanta,wani mayalwacin guri da babu kowa sai haske da
tsirrai da aka qawata wajen dashi. Sulalewa tayi agun,ba ruwanta da wai a qasa take,ta zuba dukka
hannuwanta saman fuskarta tana qoqarin maido da numfashinta daidai.

Kokawa tsakaninta da zuciyarta ruhi da kuma numfashinta,tsahon wasu mintuna masu yawa
kafin ta samu numfashin ya dai daita a qirjinta

"Maina na gani?,haidar?,Aliyyu?,da gaske yana rayen kenan kamar yadda goumar yasha gaya
mata?.......kenan hakan yana nufin watan watarana zai dawo zuwa cikin rayuwarsu?,ama tasan yana
raye?,yana kuma kusa dasu?,aba fa?" Tambayoyin da sukayi mata tsaiwar mashi aka kenan,saidai daga
bisani zuciyar ta bata tabbacin

"Basu sani ba!,duka tambayarki amsarsu basu sani ba" kanta ta sanya tsakanin cinyoyinta,sai taji kawai
babu abinda take sha'awar yi irin kuka,kuka data jima da ajeshi cikin rayuwarta,ta tattara duk wani koke
koke tun daga sanda ta soma hankali cikin hassan Ibrahim gwarzo ta ajjiye ayau shi ya dawo mata sabo
fil,ta sakeshi a hankali ya soma fita da wani zazzafan tsohon miki.

Daga cikin swissotel tun daga first floor zuwa floor na qarshe baisan adadin sau nawa ya duba
ba,daga nan ya sake maida qafafunsa zuwa cikin haram bayan zuciyarsa ta gaya masa ta tafi tayi
addu'a,ya zagaye haram har qafafunsa suka soma gaya masa tafiyar ta soma yawa akan wadda ya saba
yi.

Duk wani tunaninsa ya kulle,abinda kawai yake iya tunawa sultana ya gani,kuma ita yakeson ya
lalubo,baiji gajiyar zaryar da yakeyi ba har sai da zuciyarsa ta ladabtar da dukka gabansa,ya sulale ya
samu waje cikin reception din gaba ya zauna bayan ya shafe awanni yana abu daya.

Wayarsa kawai ya sake zarowa,ya lalubi number yayi kira. Cikin nauyin bacci suhail ya daga kiran
ya saka a kunnensa

"I thought kayi bacci tun tuni,ko murnar ganin dream twins dinka ya hanaka?" Idonsa ya lumshe yana jin
bugawar da zuciyarsa takeyi,shi kam ya manta ma da batun yaga yaran,abinda ya gani yanzun duka ya
shafe wannan

"Inason kayima mutanen nan magana,nijer da Nigeria duka nakeson shiga,banzan ainihin inda zan
sameta ba,a rage lokacin da aka dibamin,bazan iya kaiwa har sannan ba.......next week zan bar nan".

Duka zantukan sai suhail ya kasa ganesu,don baisan komai akan abinda maina ke magana ba

"Wacece zaka samo?,me zakayi a nijer kuma?"


"Kayi yadda nace please,ayi arranging komai saboda idan na shiga bansan ranar fitowa ta ba sai Allah"
yayi furucin duk wani qarfin gwiwa da yake tunanin zai samu yana narkewa daga zuciyarsa

"Are u okay maina?"

"Yes iam" ya bashi amsar dashi kansa yasan ba ita bace haqiqanin gaskiyar yana zare wayar daga
kunnensa,sai kawai ya maida bayansa jikin kujera yayi relaxing,idanunsa naci gaba da bibiyar kai kawon
mutane cikin wajen,yana jin kamar ya tabbata a wajen har sai ya gano ainihin location nata.

Maida dubansa yayi ga ma'aikatan dake wajen,yayi imanin da zai bincika akwai komai nasu cikin
hotel din muddin a nan din ta sauka,to amma bashi da yaqinin daga ina take?,ina ta tafi?,wajen wasu
tazo?,duka bai samu wannan information din ba. Number goumar da ya rasa shine mafi girman rashi da
yayi a wancan shekarar,ya daina jin komai,komai ya yanke,baisan kuma ta yaya zai sake samo wani abu
da zai sadashi da goumar din ba. Abune me wahala su bada information na wani room,ba zasu bada
ba,hasalima zai sanya sunyi zarginsa da wani abu. Wannan tunanin ya sakashi qarasa debe duk wani
tsammani nasa,ya maida idanunsa ya lumshe,sai ya dinga jin sunayen Allah na zuwa kanshi. Fara
maimaitasu yayi daya bayan daya,yana yi a hankali yana samun nutsuwar zuciya da kuma ta ruhi.

Sosai taji yadda idanunta sukayi nauyi suke mata kuma mahaukacin radadi,ko da bata duba ba
tasan sunyi kumburin da duk wanda ya kalleta zai fahimci kuka tayi ba na wasa ba.

"Ya hayyu......ya qayyumu..... birahmtika astageesu....hasbiyallahu lailah illa huwa alaihi tawakkaltu wa
huwa rabbul arshil azeem" ta dinga furtawa a fili,saidai can qasa ta yadda idan ba mugun kusanci bane a
tsakaninka da ita kunnuwanka ba zasu iya jin abinda bakinta ke furtawa ba.

Sanda ta duba agogon wayarta sai tayi mamakin yadda lokaci yaja dare kuma ya fara
nisa,tasan zasuyi tsammanin ta koma haram ne saboda sun santa da nacin addu'a idan akazo wajen. Ta
saba raba dare a wajen,baccinta kuma qalilanne,wannan dalilin tasan shine kadai ya sanya basu nemeta
ba.

Dukka wani kuzari da za'a samu jikin dan adam babu shi a jikinta,a haka ta dinga takawa har ta
maida kanta swissotel.
Ta samesu dukkansu sunyi bacci,yaran na jikin bibi duk su biyun,da alama tatsuniya ko labaran
data saba basu take basu bacci ya daukesun. Taji dadin hakan qwarai,saita lallaba ta daura alwala,daga
zaune tayi sallah raka'a biyu amma ta kasa roqar komai,ta maida kanta ta kwantar saman qafafunta
wasu hawayen na zirarar mata.

Wani irin wahalallen dare yayi cikin wani yanayi dashi kansa baisan taqaimemen inda ya dosa
ba......baisan me gobensa ke tanadar masa ba,kuma har yanzu baisan da fuskar da zai kalli ama ba,ta bibi
me sauqi ciki cikin sauqi ma......amma aba fa?. Yafi kowa sanin waye din aba,ya sanshi tamkar yunwar
cikinsa,shekara biyar ba wasa bace.....ya sani aba bazai taba aminta da cewa ba GUDUN K'ADDARA yayi
ba.....bazai taba yarda cewa SHIKE BIBIYAR QADDARAR BA.....cikin kowacce dama daya samu.....daidai da
second daya bai taba daga qafa ba saidai idan DAMAR ta kubce masa.

Yadda ta tashi da zazzabi me zafi haka ya tashi da mugun ciwon kai,saidai ko sau daya bai
matsa daga bakin tafekeken window din dake dakin ba me kamanceceniya da qofa,idanunsa dukka cikin
sashen harami,shine abu guda daya dake sanya masa nutsuwa da kuma juriya.

Kiran sallar azahar daga masallacin haram shine abinda ya tasheta. Ta bude idanunta a hankali
tana qarewa dakin kallo. Ta tabbatar cikin dakinsu take na hotel din,abinda ya bayyana mata inda ta
ganta a yanzun mafarki tayi.

Shareren fili ne dake dauke da wani irin farin yashi iya ganinka,ba kowa cikin filin daga ita sai
maina din. Wasu fararen kaya ne a jikinsa farare qal matuqa da sukayi kusanci da yashin dake shimfide
qasan qafafunsu. Sutura ce irin ta asalin buzaye,ya kuma qawata shigar tasa da nadi irin na asalin
ba'abzine,nadin farin rawani shima tas dashi wanda ya sake qarawa fuskarsa wani madaukakin kyau da
kwarjini. Tsakaninsu duka duka taku ne baifi biyar ba,ita dinma kuma cikin shigen shigarsa take na
fararen kaya,kanta babu dankwali sai iska dake wasa da gashinta daga hagu zuwa dama. Suna tsaye
carko carko,kallon kallo sukema juna su duka,a duk sanda maina yadan motsa sai ta matsa baya,sunyi
hakan ya kusa sau goma,daga qarshe ta jita caraf a hannunsa,kafin kuma tayi kowanne yunquri ya
lullubeta da faffadan qirjinsa. Mutsu mutsun qwatar kanta ta dinga yi amma hakan ya gagara,yanason
rada mata wani abu a kunne ne amma taqi bashi dama,daga qarshe ta soma cizonsa tana yakushinsa
amma tamkar ba jikinsa takema haka ba........sai muryar benazeer ta bayyana tana qwala mata kira,kiran
nata da tayi shi ya sanyata farkawa daga baccin ya kuma yanke mata mafarkin.
Sai data tattara nutsuwarta sannan ta miqe a hankali,ta zauna sosai tana duban jikinta da kyau.
Haka kawai ta dinga jin kamar qamshinsa ne cikin jikinta,wannan ya sanya kanta yaso sarawa,ta saka
dukka hannuwan nata ta dafe kan nata bacin rai yana ratsa zuciyarta.

Ta tabbatar kuma jikinta yana bata masaukinsa yana a wahen,ko cikin hotel din ko kuma wajen
hotel din,muddin kuwa haka ne ya zame mata dole tayi takatsantsan ta kuma kula da kyau harsu
kammala kwanaki hudun da suka rage musu subar qasar. Ba zata taba bari wani yaji labarin wai ta ganshi
ba,hakanan zatayi duk me yiwuwa ta tabbatar baiga yaranta ba. Wannan tunanin ma ya sanya ta janyo
wayarta ta kira number ama.

Bugu daya ta daga, muryarta adan dakushe tayi sallama

"Kin tashi kenan?,mun dan fita siyayya kina bacci,zazzabin ya sauka?" Boyayyar ajiyar zuciya ta ya sauke

"Ya sauka ama,batoul suna tare dake?" Tayi mata tambayar dake qasan ranta

"Eh muna tare....." Ta bata amsa matuqar mamakin tambayar sultanar tana kama ama,saboda abune da
bata taba yinsa ba

"Akwai wani abu ne?" Ama ta kasa shuru ta tambayeta,da sauri ta girgiza kai kaman tana wajen

"Ba komai,kawai jiya sai da na fita nemosu ne ama,suna nisan kiwo sosai" mamaki ya sake kama
ama,yau sultana ke magana haka akansu batoul kai tsaye?.

"Kinfi kowa sani muddin cikin haram ne ba abinda zai faru,just relax....." Aman ta fada murmushi yana
subuce mata. Sautin murmushin ama din ya sanya kunya tadan kamata,saita wayance dayi musu adawo
lafiya,ta maida wayar ta ajjiye gefanta tana sauke ajiyar zuciya.

Har yanzun kallon kallon da suka yima junansu a daren jiya ya kasa barin idanu da
kwanyarta,hakanan kallonsa na cikin mafarkin me kama dana jiya. Qatuwar tsaki taja,wani irin tsanarsa
yana ratsata,ba abinda fuskarsa ke tuna mata sai zallar azaba qunci da jarrabawar daya afka rayuwarta a
ciki.

*_Masu karatu......marabanmu da isowa gaba😂😂😂.......wasan zaya fara,sai nace Allah ya hadamu


ranar litinin muji_*

*Waye zaiyi nasara?"

*Waye zaiyi giving up?*

*Ta yaya maina zai fuskanci mutum hudu zuwa biyar?*

*Ama*

*Aba*

*Bibi*

*Benazeer batoul*

*Me gayya me aiki SULTANA?*

_ASHA HUTUN QARSHEN MAKO LAFIYA_

*HUGUMANKU CE*🥰

[03/06, 4:43 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 47

A nutse ya rufe mas hafin qur'anin dake hannunsa,yayi addu'o'i na wasu sakanni sannan ya
maidashi ya ajiye. Wayarsa ya jawo ya bude,makeken hoton benazeer da batoul dake saman screen din
wayarsa ya bayyana. Sunyi matuqar kyau cikin wasu pink gown,komai dake jikinsu pink ne,hatta ribbon
da aka musu adon ka dashi da qananun dan kunnayen azurfa masu pink din duwatsu ne.

Ajiyar zuciya ya sauke karo na babu adadi,fuskoki ukun wunin yau duka su suka hanashi kuzari
ko wani karsashi. Fuskokin yaran da baisan meye hadinsa dasu ba yakejinsu da wani irin qauna me zurfi
a zuciyarsa,da kuma fuskar sultana.

Yes,sultana ce,ba wani abu ba kuma wasu shekaru yanayi ko zamani da zai iya hanashi
ganeta,halittar daya raina da hannunsa ya bata dukkan kulawa. Ko ina yaronsa?,da waye yake kama?,ya
girmansa yanzu?,duk bai sani ba,yana kuma daya daga cikin burikansa a yanzun. Yayi zirga zirga yau din
tsakanin haram zuwa cikin hotel tsakanin kowacce sallah amma baiga wani abu da yayi kamanceceniya
da ita ba. Ciwon kan da yake fama dashi duka yau bai barshi zama a masallacin ba,dole idan ya idar da
sallah yake dawowa daki ya kwanta,amma yanzun da ake shirye shiryen kiran sallar isha'i sai yaji yana da
muradin sake fitan. Yanason sake ganin yaran,ko suma sun nemeshi oho?,ko a wanne hotel suka
sauka?,duka bai sani ba.

Alwala ya sake duk da wancan bai baci ba,ya feshe jikinsa da turarensa ya sanya qaramar hular
da bahaushe ke kira tashi ka fiya naci saman kansa sai gashi ya fita a balarabe sak,ya sanya takalmansa
ya fito a dakin.

Yana takawa har zuwa cikin haramin zuciyarsa na masa saqe saqe iri iri,bakinsa da kuma zuciyar
tasa duka ambaton Allah sukeyi. Zuwa yanzu yanajin kamar ya rufe ido ya bude ya ganshi a nijer,yana jin
ya shirya facing duk wani challenge.....duk wani tuhuma da kuma kowanne hawa da sauka bore da kuma
bijirewa daga gurin koma waye.
Cikin tsantsan sawa kai nutsuwa da kushu'i akayi sallan isha'i da shi,ya kammala dukka
addu'o'insa,sai ya samu kansa da zama a hanyar da sukayi clashing da yaran jiya,saman wata concrete
chair.

Yana lazumi a hankali iskar wajen kuma tana ratsashi, cikin ruhinsa kuma yana jin kewar
yaran,sai ya dinga hango fuskokinsu a jiya,daga shi har cikin yaran a cikin nishadi suke,dukka moment da
sukayi spending tare ya zame masa memorable.

"Uncle haidar....... uncle haidar" ya jiyo muryar dab da shi. Kaf qasar a yanzun yasan su daya ne zasu
kirashi da wannan sunan,don su kadai ya gayamawa wannan suna,a ko ina da aliyyu maina yake
amfani,idan yaso ya qara da MAYAK'I.

Idanuwansa ya bude yana waiwayawa,dukkansu suna sanye da jilbab daidai jikinsu da yayi
matuqar haskasu ya kuma qara musu kwarjini. Daga benazeer me giggiwa har batoul miskila murmushi
sukeyi masa,alamun dake nuna sunji dadin ganinsa qwarai da gaske.

"U are highly welcome my BB" kafin ya gama kaiwa qarshen zancan ma benazeer ta zagayo tana neman
gurin zama kusa dashi

"Dama na cewa batoul zamu iya ganinka fa,tunda aunty bata kiramu ba mu duba ko zamu ganka kafin
lokacin komawa gida yayi" murmushi ya saki yana juyawa wajen batoul,yayi mata alama da hannu kan ta
taho. Bata musa din ba ta zauna a daya gefan nasa,ya basu hannu sukayi musabaha dukkansu yana
gaidasu da larabci. Ga mamakinsa sai yaji sun responding masa,yadan zaro idanu

"Wanne yare da wanne kukeji?" Dariya benazeer ta bushe dashi tana kallonsa,saita nuna masa yatsa
hudu

"Ehnn......wanne da wanne?" Ya tambayeta irin amazingly dinnan yana fidda murmushi

"Hausa,english,arabic....... France small small" dariya sosai ta bashi da yadda ta fadi small small din tana
daga qaramin yatsanta.
Kai ya jinjina sosai suna sake burgeshi,da alama sun samu background me kyau ta kowanne
fanni na rayuwa

"Za'a yimin magana da kowanne?" Kai suka gyada kusan lokaci guda,sai ya saki murmushi yana gyara
zamansa sosai a gaskiyarsu,yana jin zuciyarshi da ruhinsa yana masa wani irin dadi,yana jinsa tamkar a
tsakiyar ahalinsa

"Bari na gayawa kowa abinda zaice" yana rufe baki benazeer ta maida masa da arabic,sannan ta sakeyi
da sauri ta maida da France,sannan ta sake maida masa da english

"Daman da hausan ka fada" ta qarashe zancan da fadin hakan. Dariya ne ya kamashi,fararen haqoransa
dake a jere ras suna sheqi suka bayyana.

"Na yarda....yanzun muje na bada gift na wannan abun" ya furta yana miqewa. Duk sai yaga basu motsa
ba,ya waiwaya yana dubansu

"Oya...... muje"

"Aunty zatayi fada uncle" batoul ta fada tana maqale kafada. Dawowa yayi ya zauna ya dafa kansu

"Idan zatayi fada kuce uncle ne ya baku sabeel.....kun gane?"

"Idan mukace haka ba zatayi fada ba?" Kai ya gyada yana murmushi,duk sai suka sauka da karsashinsu
suka bisa.

Kaman jiya ya musu siyayya,saidai yau din ya siya musu dai dai daidai yadda zasu iya cinyewa ma
a gurin,gudun kada ya sanyawa iyayensu rashin nutsuwa a zuciyarsu da kuma ayar tambaya. Tsakiyarsun
ya zauna sunata ciye ciyensu suna qananun fadansu da ba'a raba sako da sako,wani lokaci kuma su
sakashi a ciki ya raba ko su jefashi a hirar su har suka gama.

Sanda ya niyyaci rakasu suka fidda idanu,suna tsoron ya hadu da sultana,don ko jiyan susan
banda sun iso da wuri data fito nemansun nan saita gansu,sun tabbatar kuma zasusha fada qila harda
punishment

"Uncle zamu iya zuwa da kanmu" idanunsa ya lumshe yana gyada kansa

"Goodnight"

"Goodnight uncle" suka maida masa,zukatansu dukkansu cike da shauqi,kowanne a cikinsu yana jin
kamar kada ya rabu da dan uwansa.

Sai daya qara wasu awanni a wajen,ya sake addu'a sosai yana neman ubangiji ya shiga
lamarinsa. Sai kusan sanda dare ya raba sannan ya wuce masaukinsa.

A dakin kusan abun jiya ya hanashi bacci. Fuskar sultana da a yau yayi mararin su sake ganin
juna,da kuma yaran. Baisan wacce jarrabawa ce take bibiyarsa akan yaran ba,amma yana jin wata irin
tsaftatacciya kuma tatacciyar qaunarsu cikin zuciya da ruhinsa.

*******Dukka kwanakin da suka rage musu cikin makka din a darare take,kowanne motsi sai take ganin
kamar zata ganshi a masaukinsu kowanne fita da yaran zasuyi sai taji kaman zasu hadu,kaman zai
kwashe yaran a nemesu a rasa,kowanne fita tata cikin kaffa kaffa takeyi da lura da duk inda zata gifta
din. Tun daga rabar bata sake bin elevator ba ta gwammace tayita bin stairs har takai qasa,wanda idan
ta fita din sai tayi zamanta cikin masallaci,idan ta dawo ciki kuma ta dawo din kenan sai kuma washegari.
Duk sanda tayi hanyar elevator sai taga kamar zasu sake haduwa,kaman zata sake ganinsa irin yadda ta
ganshi rannan.

Kwana hudu kacal da suka rage subar makka su wuce nijer sukayi wani irin sabo dashi,hakanan
shima yayi wani sabo dasu ta yadda har bai tuna haduwa sukayi kuma kowanne lokaci shi ko kuma su
wani zai iya tafiya yabar wani. A jikinsa yake jin kamar gurin zamansu daya,kamar wani family ne shi
dasu dake rayuwa cikin gida daya,kamar a nan zasu dawwama da yaran. A kullum bayan sallar isha'i sai
ya zauna ya jirayesu. Duk irin yadda yake girmama lokaci......duk irin yadda ya tsani jira cikin
rayuwarsa,duk kamewa irin tasa da rashin shiga sharafin kowa.......duk uban miskilanci da tsananin
ginshira irin nashi amma bayan sallar isha'i saiya bata wananna awa daya zuwa biyun. Ko yana zama su
iso,ko yazo ya samesu zaune a wajen suma suna jiransa. Ice cream da chocolate sun sha har babu
iyaka,masu tsada ya koma siya musu irin wanda canjin da ama ke sanya musu cikin jaka bazai isa su siya
ba,babu kuma me biyewa ciye ciyensu a cikinsu bare ya bisu ya siya musu da nasa kudin,don dukkansu
sunsan girman wajen,zaman masallacin yafi komai cinye lokacinsu a wuni guda.

Tunda benazeer ta fahimci a ranar zuwa azahar jirginsu zai bar makka hankalinta ya soma
dagawa,tasan dai ba zasu kai lokacin da suka saba haduwa da uncle ba bare suyi sallama,ta kuma gaya
masa zasu tafin. Gaba daya sai ta kasa sukuni,tana cikin kujera a kwance tana ta kallon batoul dake cin
chips da fork,tana ta son ta kalleta suyi shawarar yadda zasu ga uncle su gaya masa zasu tafi,shima
yaushe zai tafi?,yaushe kuma zasu sake ganinsa?.

Yawan surutu kuzari da karsashin batoul ya sanya kusan kowa ma ya fahimci tana da damuwa.
Tuni sultana ta fahimta,amma saboda kawaici da batason fiya zaqewa cikin lamuran yaran bayan ga
qashin bayansu nan jigonsu a gurin saita kauda kai,saidai kuma tanata monitoring komai nata,ta kuma
karanci tsaf akwai abinda yake damunta ya kuma hana mata sukuni.

Qaramar akwatinsu da ama ta shirya musu tsaraba a ciki tazo ta ajjiye,saita juya kadan tana
kallon benazeer

"B....me yake damunki yau?" Tayi tambayar cikin salon nuna muhimmancin tambayar saman fuskarta.
Zamewa tayi ya sakeyin lamo cikin kujera,sannan ta motsa qaramin bakinta

"Ba komai"

" Da gaske?" Kai ta gyada a hankali


"Ko kuma kayan shaye shayen sanyin nasu takeso ba,tunda na fahimci duk sun zama shazumamu,sunma
fi uwarsu son shan jarabbaben zaqin nan ai" Dariya ama ta danyi,ta jawo purse dinta data shigo da ita ta
fidda riyals tana cewa

"Su kenan suka ragemin dama......aje a siyo na bankwana" ta furta tana murmushi. Idanu sultana ta
dauke gefe zuciyarta na motsawa,zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba ganin soyayya tsakanin kaka da
jikokinta ba irin ta ama da su batoul. Haqiqa bibi ta sota,ta qaunaceta,ta kuma nuna mata soyayya me
yawan gaske.....amma akwai wasu kusakurai da ramuka masu yawa a hanyar,wadanda tasan ta
tsallakesu ne kawai saboda qilan taci albarkaci ko darajar wani ne.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[03/06, 4:43 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 48
Da sauri benazeer ta miqawa ama qaramin hijabinta ama din ta sanya mata, batoul ma ta ajjiye
abincin tana sanya lausasan wasu rufaffun takalma masu kyau suka sanya kai suna ficewa riqe da
hannun juna,ama ta bisu da

"Ayi addu'a"

"In sha Allah" suka hada baki wajen fada.

Sai da benazeer ta tabbatar sun sauka sannan ta kalli batoul

"Nifa uncle zan nemo na gaya masa mun tafi fa" ido batoul ta zaro tana kallonta

"A ina zaki ganshi?"

"A inda muke zama,muje mu siya ice cream sai mu dawo mu wuce ta wajen ko zamu ganshi" dan jim tayi
kaman me nazari,sai kuma tayi murmushi

"Muje to".

Shop din da ya saba kaisu suka shiga,suka zabi kowa flavor din da yakeso,har ma'aikatan wajen
suna tsokanarsu

"Yau babu fada?,ina uncle din nasu?" Dariya sukayi, benazeer tace

"Baizo ba?,nemansa muke" daya balaraben yace


" Tare kuke zuwa, sai dare yake zuwa tare daku" basu wani fahimta ba,sundai gane kawai baizo ba don
haka suka sanya kansu suka fice benazeer na cewa

"Ma'assalama". Suna riqe da ice cream din suna sha suna kuma bin duk hanyar da suke ganin zasu iya
ganin uncle haidar amma babu shi babu dalilinshi,har batoul ta gaji,taja tunga sanda aka soma kiran
sallar azahar

"Kizo mu tafi gida tunda bamu ganshi ba,kada aunty tayi mana fada,ama ma kuma tace fa mu dawo da
wuri" juya idanuwa benazeer tayi kaman me shirin sakin kuka,ta sake waiwayawa bayanta kamar me
fatan ta bude idanunta ta ganshi a wajen,saita dawo da kallonta ga batoul wadda itama dinma duk ranta
ba dadi

"Muje" ta fadi a sanyaye. Haka suka jera suna komawa hotel din ba um ba um um. Sanda suka isa dakin
duk sun fice zuwa sallar azahar,amma kuma kayansun sun gama hadasu tsaf,kowacce saita samu waje
tayi lamo ba wani me magana ko kuzari a cikinsu.

Koda suna shirin fita a dakunan saida ama tayi qorafi

"Anya lafiya kuke kuwa.yau dinnan?" Ta fadi tana taba wuyansu,sanyi taji ba alamun zazzabi ba
komai,batoul ce tace mata ba komai

"To Allah yasa alkhairi" aman ta furta,saboda tsahon tarenta da yaran bata taba ganin jikinsu ya mutu
haka ba.

Nannauyan numfashi ta sauke tana furzar da iska daga bakinta. Cikin ruhinta takejin wani
salama da nutsuwa suna saukar mata,zuciyarta kuma tana gaya mata tayi masa nesa ta tsere masa. Ta
window din take kallon fadin sararin airport din,tana jin kewar barin qasar kamar yadda ta saba,amma
tana jin farinciki idan ta tuna ta tserema idanun maina,sannan nan gaba kadan zata dawo ta sake
ziyartar dakin Allah.
Tafiya miqaqqiya daga birnin makka har zuwa qasar nijer. Tafiyan awanni goma sha daya suka
sauka a niamy,daga nan wani jirgin suka sake hawa suka wuce marad'i.

Iska ta shaqa sosai ta qasar nijer sanda tayi relax cikin daya daga cikin lafiyayyun motocin
mallakin aba da ama. Wasu emotions suna cakuduwa cikin zuciyarta,qamshin qasartata yana motsata
tare da tuna mata abubuwa masu yawa,wanda kusan fiye da rabinsu quruciyarta ne......yarinta da zallar
wauta da ta tafka a rayuwarta,wani abun ya sanyata murmushi wani ya bata takaicin da shima din dai
murmushi ne na dole ke qwace mata.

Tun barinta nijer zuwanta daya kacal......wannan shine zuwa na biyu da tayi,zuwan daya
banbanta da zuwanta na farko. A yanzun ta sake dawowa qasarta a matsayin cikakkiyar sultana,me yara
har guda biyu,wadda ta mallakin hankalin kanta......sannan masaniya cikakken sani a harkar ilimin jarida.
Sultanar da a yanzun kai tsaye zaka iya kiranta da madam. Dukkan wata sura da halitta nata na kyawu ya
gama cika,ya kuma cakuda da zallar kwarjini da hasken ilimi. Ta zama classy qwarai,ta banbanta da
girman tazara da wancan sultanar me rawan kai yawan surutu fitsara da rashin kunya. Yanzun ta zama
wata sultana me yawan shuru shuru,wadda ba shirgin kowa take shiga ba,abinda ya shafeta ma ba
kowanne take daga idanu ta kalla ba har ta bashi lokutanta.

Isowarsu qofar makeken gate din mansion house din mallakin MAYAK'I ya sanyata daga tsintsiyar
hannunta tana gyara zaman siririn agogon gold din dake hannunta,lokaci ta duba murmushi ya subuce
mata sanda hancin motarsu ke shiga harabar gidan. Ba wani abu ta tuna ba illa lokaci irin wannan da
take hada dabar hira,sam qawaye mata a sannan ba damuwarta bane,maza ma sunfi mata dadin
qawance qwarai,saboda su din zata musu tsiwa tayi musu fitsara kuma su daga mata qafa don suna
kallon ita macace kamar sauran mata. Idanunta cikin farfajiyar gidan da ta sake qawatuwa qwarai,anyi
mata gyara sosai,da alama kuma dukkan gyaran yana da nasaba da bikinsu aminata ne. Ko ina yayi
fes,tamkar sabon gini,tamkar ba wannan tsohon ginin da qarfi d kuma qoqarin NADEEYA ya samar dashi
shekarun baya ba. Ko kusa ko alama mamallakan gidan basu taba barin tsufa ko shekaru su
cimmasa,saboda kusan koda yaushe cikin aikin gyaransa suke,duk wanda ya samu dama a cikin
kawunnan nata saidai kawai mutanen gidan suji ana shelar a kwashe ko za'a yi aiki.

Idanunta ta janye sanda suka sauka a wannan bigiren....muhalli ne da kusan yafi zama a cikinsa
akan ko ina cikin gidan,waje ne da yake zama yana kula da shige ficensu yana kuma monitoring motsinsu
da tarbiyyarsu. A duk sanda zata kalli wajen koda sau dubu ne sai taji ranta ya baci sau dubun,shi ya
sanya zabinta daya kauda kai a irin wannan lokacin.
Motarsu na tsaiwa kusan duk wanda ke wajen ya ankara da isowarsu. Kafin kace meye wannan
mutanen dake cikin gida ma sun fara fitowa tarbarsu. Kusan kowa ya fito ta batoul da benazeer yake.
Batoul sarkin rashin yarda da shegen miskilanci da taga ama ta kutsa kai cikin jama'a sai ta koma jikin
sultana ta lafe. Abun sai ya soma baiwa sultana kunya,saboda idanuwa data ja mata,kowa sai ya matso
ya tsokaneta ya kuma tsokani sultanar,wadda a sannan idan kaga batoul dake jikinta zatayi rantsuwa
yayarsu ce bawai uwa mahaifiya ba. Ko kusa ko alama duk qwaqwafinka baka isa kaga alamun sultana ta
isa ta mallaki tiqa tiqan yara har guda biyu kamar benazeer da batoul ba.

Wata motar ce ta shigo,najma aminata da yasmine ne a ciki amare. Najma ke driving aminata da
yasmine da houda cousin dinsu suna baya,a kujerar gaba kuma djamilla ce itama dukka kakanni daya
suke dasu sultana.

A gaggauce najma ta tsaida motar,dukkansu cike da farinciki suke qoqarin fitowa,saidai ta


rigasu ma qarasowa,fuskarta dauke da nutsatsen murmushin nan nata,da muryartannan me sanyi tace

"An fara yawon amarcinne?,amma ko a jirani?" Junansu suka kalla da dan mamaki,ba wanda ya kawo
zata nema sakewa a cikinsu shi yasa wasu abubuwan ma basu tsara da sunanta ba

"Zaki iya yawo a cikinmu?" Houda ta fadi tana 'yar qaramar dariya. Waiwayowa tayi tana dunan houda
da murmushin da ya tsaya saman kumatunta tace

"pourquoi pas?(me zai hana?)" Ta fadi tana kallon houda

"Yar jarida ce ke yanzun a qasar France...... kinga dole muyi takatsantsan karmu shiga ajin da ba namu
ba" dole ta sanya sultana sakin siririyar dariya,siraran jerarrun haqoranta suna bayyana

"Banason sharri houda.....har yanzun baki sauya hali ba?"

"Inaaaa......wannan canjin saiku......na rantse bada wasa ba ko.......ban ganeki ba sai da kika matso sosai"
kada kai tayi tana murmushi,tasan halin houda da kyau,tun suna qanana,tasu tafi zuwa daya saboda
halin tsokana irin nata na da da take dashi
"Amma sœurs(yan uwana)su ba zasu kasa ganeni ba ai"

"Nima canzawarki ta jawo"

"Ku bani hanya naje naga babies dina,don idan aka biye taku naga alama zamu jima tsaye a nan"
aminata ta fada tana maida headphone dinta qaramar handbag din dake hannunta. Rufe qofofin motar
sukayi suka fara takawa gaba dayansu zuwa cikin gidan,suna tafe suna tattaunawa akan dame dame aka
tsara yi a bikin.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/06, 9:16 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 49
Sake duba agogon wayarsa yayi don bai fito da agogo ba. Wannan dubawar yana irge ita ta
zame masa cimakin dubawa na goma sha biyar kenan. Zubawa fuskar wayar idanu yayi wadda ke dauke
da hotunan yaran,yaja godon numfashi daya sauka har cikin huhunsa. Kanshi ya sake dagawa yana
duban jama'ar dake shige da fice cikin haram din wai ko zai ga gilmawarsu,saidai ko twins guda daya bai
gani ba bare ya sanya ran dasu a ciki.

Ya fara sarewa da ganinsu yau,saboda tun wancan ranar da suka hadu din basu taba kaiwa
warhaka basu iso wajen ba,basu taba latti kaman haka ba,kamar yadda basu bata fashin zuwa ba.

Dauke kansa yayi ya maida idanun nasa qasa,sai ya samu kanshi ya tsawaita a addu'a cikin
zuciyarsa na zuwan yaran a nan kurkusa. Bayajin zai samu nutsuwa ko qanqani idan bai gansu din
ba,zuciyarsa da rayuwarsa a kwanakin jinsu yakeyi a rikice gaba daya,hatta da suhail da sardauna da
basu kusa dashi suna iya fahimtar haka cikin mu'amalarsu dashi.

Duk wata tattaunawa da ya shirya zasuyita through video call ya kasa halarta,wani lokacin ma sai
sunyi sun gama zaiga miscal nasu. Idan sun matsa da yabi sai yace musu duk yadda suka yanke yayi. Duk
kawaici na sardauna sai daya magantu

"Kafi kowa sani daddy bazai amince da dukka abinda zamuje masa dashi ba saiya tabbatar bisa yarda da
sahalewarka ne tunda dai kaine jagora......kuma ma,ta yaya zaka jagoranci harkar lafiya a qasar dake da
tsari da doka kana cikin dimuwa haka? what's wrong with you ne maina?" Sumarshi kawai yakan shafa
duk sanda suka masa tambaya irin wannan,don baisan amsar da zaya basu wadda zasu fahimceshi su
kuma gamsu ba,abu daya ya sani,Allah yana sonshi da ya kawo masa irin wannan yanayin a wajen da
dukkan dimautacciyar zuciya ke samun nutsuwa,a muhallin da amsa addu'a bashi da shamaki da
ubangijin dake amsa roqon bayi,banda hakan shi kansa baisan a wanne yanayi zaya kasance ba.

Miqewa yayi bayan ya fahimci ya sake qara wasu mintuna ashirin din masu kyau,ya zube
hannayensa a aljihun kaftan abaya dinsa ruwan bula(navy blue)wadda ta sake fidda ainihin kyawunsa na
cikakken ba'abzine kuma bafulatanin buzu,sai ya tsinci kansa da gangarawa bangaren shops din dake
hada hadar saida ice cream da sauran kayan zaqi,wajen da yasan duk dare shi dasu suna zuwa.
Kai kawo ya dinga yi yana duba ice cream din zuwa chocolates din,saidai kawai yana zaba ne shi
kansa baisan me zaiyi dasu ba. Nan dinma ya kashe kusan awa guda amma baiga alamarsu ba,har yakai
lokacin da.ya tabbatar a irinsa ne suke ce masa sun tafi,daha qarshe ya fidda riyals ya biya uban
chocolate da ice cream din da ya zaba yace su kyautar wa duk yaran da suka shigo.

Cikin wani irin nauyin jiki da na zuciya yake komawa swissotel, zuciyarsa a mugun quntace da
wani irin rashin dadi,duka ya rasa target dinsa,ba sultana ba kuma yaran,sai ya dinga jin kamar lokaci
yayi shima da zai bar wajen,lokaci yayi da zai cimma sultana,cikin nijer......cikin gidansu.

Yana fitowa daga elevator wayarsa ta dauki tsuwwa,sanda ya fiddata yaga me kiran sai da yaji
kamar ya kyautar da wayar,don baya cikin mode na amsa kowanne kira. To amma hausawa sukace wata
fuskar tafi gaban mari,ko don sardauna kawai kafin akai kan daddy,dole ta sanya ya daga kiran ya kara a
kunne.

A yangance tayi masa sallama,da qyar ya hada kalmomin amsa sallamar tata,yana jin kamar
numfashinsa baya sauka cikin hunhunsa da kyau

"Am sorry,zan kiraki wani lokaci" dan jim tayi,kamar bataji dadin furucin nasa ba,amma kuma sai tace
masa

"Okay" a taqaice sannan suka ajjiye wayar kusan a tare.

Kasa haquri yayi,kafin ya isa daki ya lalubi suhail. Komawa yayi ya jingina da qofar dakin bayan ya
maida ya kulle,idanunsa a kulle,kunnuwansa na sauraron yadda kiran ks gangarawa wayar suhail,gefe
daya kuma yana sauraron bugun zuciyarsa.

Sama sama suka gaisa,kai tsaye ba kwana kwana ya gabatar masa da uzurinsa

"Banason na wuce kwanaki biyar suhail ban isa nijer ba"


"Why?,me yasa kake caccanzawa kamar wani wahainiya ne maina?"

"je ne sais pas non plus(nima ban sani ba)"ya fadi da harshen faransanci

"Me kace?" Suhail din da yaren turanci yafi yawa cikin nasa harshen ya tambayi maina abinda yace din

"I don't know suhail...... I don't know why"

"But amma kasan a yadda muka tsara zakayi koda one week ne a Paris a gama komai koda a tsaitsaye ne
sai ka wuce"

"Noooo suhail,no.....bazan iya ba,koma meye ya jiraci dawowata......na gaya maka.....kwana biyar kadai
zan qara a nan din.....bazan canza ba" daga haka ya katse wayar don kada ma suhail din ya sake kawo
masa wani hanzarin,don bayajin akwai wani abu a yanzun da zai iya dakatar dashi kai kanshi nijer din.

*********Tunda suka sauka a nijer shirye shiryen biki kawai ake cikin gidan babu kama hannaun yaro.
Da fari ta soma halinnata na dararewa da kebe kanta akan komai,daga bisani su aminata suka mata bore
kan basu yarsa ba

"Abinda yayiki shi ya yimu,kuma meye hujja ki dalilinki na tsame kanki daga cikinmu sultana?,bayan idan
kin koma paris sai mun ganki fa" wannan dalilin ya sanya tayi qoqarin sakewa sosai a cikinsu. Duk wata
hidima sai sun tsomata a ciki. A hankali saita fara warewa,wannan yanayin......wannnan
yanayin......wannan lokacin da wancan zamanin dukka da ya dade da shudewa cikin rayuwa da
mafarkanta sai ya dinga farfadowa. A hankali ta dinga samun nishadi cikin zuciyarta,wani nauyi dake
qirjinta ya dinga raguwa kadan kadan. Son kadaicewa......jin kanta kamar ta banbanta dasu ya dinga
raguwa sosai.

Mutum daya ke neman matsanta mata,babu daman ya gansu sun fito sai ya matso gaban
motarsu,idan anci sa'a ita keda driving ranar kafin ya iso take maka baqin glasses wa idonta ta finciki
motar su fice,najma tayita mitan ta bari mana ko wajenta zayazo amma bata bi kanta,idan kuwa najma
cw driver dinsu na ranar to ya samu yadda yakeso. A fakaice yake gasa mata maganar
"Karki manta,tu es la femme de quelqu'un d'autre(ke matar wani ce)" Baisan iya adadin yadda kalmar ke
motsa zuciyarta ba,sai ranar da abun ya qureta kawai taji hawaye ya tsinke mata. Cikin arashi kuwa a
gaban idanun uncle bashar abbanshi,shi yayi masa tas yace su shige mota su tafi abinsu,Allah ya tsare.
Daga ranar ta samu sauqinsa,saidai fa hausawa sunce me hali baya fasa halinsa,duk ko yaya ya samu
dama sai ya sake fesa mata,duk hade ranta da dauke kanta bai dameshi ba.

Siyayya sosai ama tayi musu na biki a dan tsakanin,kayan gargajiya na hausa sosai,ready made
na atamfa da laces,don su benazeer din basu da wani kayan gargajiya sosai saboda yanayin inda suka
taso. Kafin wani lokaci ama ta kammala musu komai,don wasu abubuwan amma matar uncle bashar ta
kammale musu dama.

**********Tun yammaci ta sanya driver ya dawo da ita gida ta baro su aminata suka wuce wajen
booking musu lallen biki. Ba yadda batayi su cire sunanta ba amma najma tace

"Sai kiyita yi" najma ta fadi tana jan motar, driver modu ya jata ya dawo gida da ita.

Duka saurin da takeyi don ta amsarwa ama girkin aba. Tana sallar la'asar ta kammala
komai,qarfe biyar aba ya aiko atta a fito musu da girkin wani kebataccen waje daga bayan gidan,da
alama suna sa tattaunawa ne shi da uncle omar da oncle bashar.

Tun daga nesa ta fahimci zaman na musamman ne,akwai invitation na daurin aure da yawa a
wajen da sauran takardu.

A nutse ta durqusa ta ajjiye musu komai akan tsari,sannu dukka suke mata. Iya 'yan kwanakin
kawai kowanne mamakin sultanan yake,kamar ba sultanar data fita a gidan bace wata ce daban aka
sauyota.

"Allah yayi albarka,ya shirya miki zuri'arki" aba ya fadi cikin qauna da kuma tausayi
"Ameen aba" ta amsa ranta yana mata fari sosai

"Bashar......ka rubuta cikin calendrier (schedule) na abinda zamu tattauna.....mu duba yadda zamu
warewa marainiyar Allahn nan igiyar wannan yaron daga kanta don mu bata damar rayuwa cikin 'yanci
kamar kowacce yarinya...".

Wani numfashi ta zuqa me zurfi da nauyi tana jin kowanne gaba ta jikinta na rawa, zuciyarta ta
motsa sosai da wani irin matsanancin bugu,qafafunta na hardewa ta qara sauri tana barin wajen ba tare
da ta jiyo amsar dasu oncle bashar suka bawa aba ba......

[05/06, 9:16 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 50

Da dan sassarfa ta qarasa sassan bibi don shi yafi qarancin mutane. Dakin bibin ta wuce don
rabonta da dakinta har ta manta,tun wancan ranar sam bata iya shiga dakin ta zauna,saidai idan wani
abu zata dauka kota ajiye,tana shiga kuma take fitowa.

Sai datakai can quryar gadon sannan ta kwanta,rigingine tayi tana qoqarin ganin fitar
numfashinta ya dai daita. Tsahon wasu mintuna sannan ta motsa bakinta a Hankali idanunta na runtse

"Ya Allah.....ya rabbussamawati ka bawa wannan bawan naka ikon rabani da wannan alaqaqai din igiyar"
tayi addu'a tana fita daga tsakiyar zuciyarta.

Har cikin ranta taji addu'ar ta karbu da gaske,sai taji tadan samu nutsuwa,ta juya barin hannun
damanta tana fadada tunaninta na yadda zata tafi da rayuwarta cikin 'yanci,tana sake fadada mafarkinta
na zama fitacciyar 'yar jarida a duniya. Da wannan tunanin a hankali a hankali bacci yazo yayi awon gaba
da ita.
Washegari me qunshi ta musamman dakewa ama qunshi tazo yi mata. Su benazeer tace a fara
yiwa. Da farko batoul taqi yarda wai tsoron lallen takeji,tunda ba'a taba yi musu ba tunda sukazo duniya.
Bibi kaman ta ari baki,ta dinga fada

"Haihuwar faransa rainon faransa.....ai dole,ba abinda kuka sani daya shafi al'adar africa.....don lalacewa
atamfa nan murna wai yarannan suke zasu daura zani,laifin hamdiyya ne.......banga ta barinku ku
tabbata a turai ba,gwara ku dawo nan kusan rayuwa" Dariya surukai da sauran 'yan uwa dai daiku da
suke wajen suka dinga yi. Benazeer babu tsoro ita ta fara miqa hannunta akayi mata,sai da batoul taga
benazeer din ta cire,lallen yayi matuqar kyau a fara tas din fatarta, benazeer din nata murna tana
shafawa,abun yana bata sha'awa ita karan kanta sannan batoul ta yarda ayi mata.

Matsawa batoul din tayi kusa da sultana dake shirya duka kayan da zasu sanya cikin bikin a
wasu madaidaitan akwatuna guda biyu,ta zura mata hannun saitin fuskarta

"Auty bakiga hannuna ba?,kaman ba nawa ba auty,kema ayi miki,zaiyi miki kyau aunty" tayi nisa a
tunanin da ita kanta batasan na meye ba,haka kawai tun jiya gabanta ke yawaita faduwa,ta laluba kafff
batasan dalili ba,saidai zuciyarta tafi raja'a akan kodai tana tunani akan wanne hukunci su aba suka
yanke game da makomar igiyar auren dake kanta?,tayi winning ko batayi ba?.

Fararen idanunta masu yalwataccen gashi ta daga ta kalli fuskar yarinyar,sannan ta maida ga
hannun da taketa zura mata. Ita kanta hannun yarinyar ya burgeta,jan lallen ya kwanta saman jar fatarta
kamar jan lalle saman hannun balarabiya

"Ma sha Allah,tabarakar rahman......kinyi kyau sosai" farinciki sosai ya kamata,ta buga tsalle saman katifa
tana kiran yaran da suke gurin sa'anni kamarta tana gaya musu

"Kunji ko?,ko aunty ma tace nayi kyau".

Washegari wuni sur basu zauna ba suna wajen lalle,qin yarda tayi ayi mata daga farko don
batason me yawa,tafiso sai an yiwa kowa me lallen ta gaji sannan ayi mata. Dan kadan din akayi
mata,janne itama har bayan hannu sai na cikin tafin hannu,na qafa ma duka kadan akayi mata,ikon Allah
sai ta zamana kamae zabarta me lallen tayi,gashi dai yafi na kowa qaranci amma kuma yafi na kowa yin
kyau,ai kuwa suka yiwa me lalle caaa,itadai dariya ta dinga yi matar tana cewa

"Ba daga ni bane,daga me hannun ne......ina cewa kuna gani dai,fatarta tafi ta kowa kyau da haske"
maganar matar dole ya sanya sultana murmusawa duk da jikinta da takeji wani iri babu dadi.

Ranar laraba aka fara biki sosai,komai nasu bisa tsari da kuma tarbiyya suka shiryashi,ba wani
abu da ya wucewa tsari.

Duk wata shiga idan sultana din tayi sai ta fita daban,kallo kam ta shasu,ta tabbatar banda tana
da yawan azkar tsaf baki zai kamata,komai nata me aji sanyi ds kuma nutsuwa. Wadanda suka jima basu
ganta ba kuwa mamaki kowa yakeyi

"Wai wannan sultana ce da gaske?,wadannan diyoyinta ne?" Abinda kusan dukka suke tambaya
kenan,wasu riqe da baki wasu kima fuskokinsu cike fal da mamaki. Itakam saidai tayi dariya ta wuce.
Benazeer abun nema ya samu,ba zama wai an saci dan barawo,idan ta fice cikin jama'a sau tari sai ama
tasa an nemota,bata nan bata can,kusan ita din akafi sani akan batoul,saboda kwata kwata ita din bame
hayaniya da surutu bane. Duk da kamannin da suke dashi yana rikita mutane,amma kuma dabi'unsu ya
sanya ake saurin banbancesu. Yawan qawayen da benazeer din tayi cikin dangi sai abun ya baka dariya
ds mamaki,duk wani team na yara idan kaga sun hadu sai kaga itace shugaba. Sak SULTANA saidai wasi
banbance banbance a tsakaninsu. Benazeer ta samu kulawar ama qwarai,data fuskanci yanayin dabi'u
da halayenta sai take tarbiyyantar da ita daidai da halin nata,wannan ya sanya duk surutu da rawan
kanta take da matuqar ladabi,tana da kirki tana da kyauta tana kuma da tausayi,bata iya rashin kunya ba
sam, kusan duk wanda zata gaisar sai takai har qasa,saidai fa za'a cikaka da surutu da kuma labari. Randa
aka soma bikin goumar baya nan,sai dare ya dawo washegari kuwa me daure musu qarqashi ya dawo?,ai
har batoul itama saita bazama,basa zama sam,wani lokaci ma sai sunyi bacci da dare za'a shigowa ama
dasu,sai kuma wata safiyar idan rai ya kaimu. Duk inda za'a suna gaban motar goumar din,kowa yasan
nan ne mazauninsu ma bame zama wajen,haka aka dinga gudanar da event din daya bayan daya,komai
ya qawatar ya kuma bada sha'awa.

Ranar juma'a itace ranar dinner. Qawatacciyar dinner da aka shiryata ga dukkan amaren da
danginsu dana angwayen aminata da yasmine,ga dangin uwayensu mata,wannan ya sanya aka kama
babban waje da zai dauki kowa da kowa a sake kuma akan tsari.
Tun asubar juma'a din ta tashi da wani dan qaramin zazzabi,har cikin qashinta take
jinsa,hakanan kanta bangare daya yana sara mata lokaci lokaci. Idanunta ta lumshe tana mamakin
abinda ya saukar mata da wannan zazzabin hade da bacin rai. Tasan dai lafiya lau ta kwanta bayan sun
dawo daga kamun amare da akayi alhamis,sannan ba wani zirga zirga tayi ba,don ama ta bata daya daga
cikin motocinta tace tayi hidimarta da ita,ko a canma tana zaune waje daya,saboda yadda idanu ke mata
yawa suna binta da kallo duk inda ta motsa ne bata so,abinda kuma ya sake bata mata rai ta samu waje
ta zauna,daya daga cikin abokan ango da tazo wucewa ta gefansu zata bude motarta ta daukowa wasu
friends din su aminata sevenniours. Ya jima yana binta da kallo duk inda ta gifta,shine mutumin da ya
sanyata ta dinga zabga tsaki har babu adadi,a yanzun kuma da zata wuce ta shiyyarsu sai yace da ita
murya can qasa

"quelle douce odeur(qamshi me dadi)" har cikin ranta maganar da ya fada din taji ta soketa. Eh
tabbas,ita kanta ta sani,tana amfani da wani irin mayen turare ne me masifar kama jiki da sanyin
qamshi,qamshin da hatta su aminata sai da suka magantu akai,tana maitar son turaren wannan ya sanya
ya gama kama jikinta,amma aiba huruminsa bane yayi magana akai ko?. Bata kulashi ba ko waiwayo
batayi ba ta wuce abinta,saboda kulawa ma ai yabawa ne. Sanda ta sake dawowa bai haqura ba sai daya
sake magana

"Banyi mamaki ba don baki tanka ba.....ko makaho kukayi gaba da gaba dashi zaisan ke ta musamman
ce......tu es une femme chic(macace ke me aji)" juyawa tayi tana dubansa,kamar zata tanka saita tuna
hala dama tankawar nata yake da buqata,don haka saita sake masa wani siririn tsaki ta wuce
abinta,abun haushin sai ta jishi cikin murmushi yana cewa

"Merci bébé(na gode baby)" maganar data qular da ita kenan ta samu guri tayi zamanta.

K'ofar aka taba alamun knocking,daga jin knocking din tasan bazai wuce benazeer ko batoul
ba,sassanyan muryar nan tata can qasa tace

"Entrez(shigo)" batoul ce sanye da wasu cotton sleeping dress. Tabi yarinyar da kallo,kullum da kalan
kayan baccin da zata gani jikin yaran,itadai batasan adadin guda nawa suke dashi ba,ita kanta wasu
abunuwan nasu batasan adadinsu ba,saboda ko yaushe ama cikin kashe musu kudi take,cikin musu
siyaya take,bata kuma iya musu siyayyan abu me araha ba,komai sai ta zuba me daraja da tsada. Kullum
sake girma sukeyi suna wani wayau,halittar da Allah ya musu kyautarta na sake bayyana,yadda taji ana
zancan har kamar ma sunason juyewa kamanninta.
"tante......ki fito inji ama kiyi breakfast,taji kaman su Yasmin suna cewa zaku fita" idanu tadan fidda tana
dubanta

"Yau kuma na koma tante,aunty din in English bai isa ba?" Dariya ta saki sosai irin me cike da quruciyar
nan

"Tante yafi dadi aunty......duka su aminata haka ake kiransu,kema a nan sunanki tante,saimun koma
nigeria ko Paris zaki koma autyn" kai kawai sultana din ta gyada,ta fuskanci yau da surutu itama BATOUL
ta tashi,don tanajin tanja tanata fama dasu daga cikin kitchen

"Ganinan zuwa"

"d'accord" ta amsa mata da farshen faransanci tana ficewa a dakin da dan tsallenta. Janye idanunta
sultana tayi daga qofar tana jin wani yanayi yana shigarta,haka kawai takejin tausayin yaran yana shiga
zuciyarta,dukka tayi qoqarin danne wannan,ta jawo qafafunta ta sauka ta wuce bandaki.

Wanka ta sakeyi hade da brush don ta hada gumi saboda maganin saukar da zazzabin da
tasha,kuma alhamdulillah sai taji ya sauka din,saidai kuma rashin qwarin jiki. Simple gown ta saka na
wata cotton atamfa maras nauyi,don ita ta tsammaci ma material ne da farko da ama tasa aka dinka
musu,ta lullube kanta da dankwali sannan ta dauki wayarta ta fito.

Fuskarta tayi fayau,ba komai saman fuskar sai dan alamun rashin jin dadin jiki. Akwai baqi a
falon,ta bisu ta gaidasu har qasa cikin girmamawa. Wannan dabi'ar tabi jikinta durqusawa yayin gaida
manya,tana daya daga cikin dabi'un da aka horesu dashi a hassan gwarzo. A nutse har ta qarasa
dining,ta taras da houda salamatu dukka cousins dinta ne,suka gaisa ta samu kujera ta zauna tana duba
abinda zata iya ci.

Tana ci suna hira a haka aminata ta fara shigowa

"Kun gama shiryawa?" Houda ta fara amsawa


"Mayafi na kawai zan dauko,Je pense salamatu est prêt(ins tunanin salamatu ma ta shirya)" ta fadi tana
duban salma din,kai ta gyada alamun hakanne,aminata ta dubi sultana cikin kokwanto

"Kefa?" Dan motsawa kadan tayi sannan tace

"Ina ji fa sai dare zamu hadu gurin dinner din kawai"

"Baki isa ba" aminta ta fada tafa hannuwa cikin bala'i. Cikin sa'a yasmine ta shigo dai dai lokacin,suka
hadu duka dinga mata. Ba wanda ta tankawa,don maganarsu ma so take ta daga mata ciwon kanta,ta
barsu sukayi iya yinsu,amma yadda suka tarar mata tasan bata da mafita,salin alin ta koma daki ta dauko
mayafinta kayan da zatayi amfani dasu da key din motar ta fito suka wuce. Mutun bibbiyu sukayi,
yasmine da salma a motar salma din,sultana da aminata a motar sultana.

Katafaren beauty lounge ne da yayi suna cikin marad'i da kewayenta. Wajene da idan kinsan baki
isa bama baki kai kanki wajen,service sukeyi na manyan mata tamkar a cikin gidanki. Tarba za'a miki da
drinks lemo harda kalan abincin da kike buqata,itakam sultana dukka batabi takan wannan ba,sai ta
wuce qurya salle de repos(resting room) nasu dake dauke da manyan sofas masu taushi tayi
kwanciyarta. Tana jiyo duk wani karakainar su tana kuma hango motsinsu ta cikin babban glass da ya
rabasu.

Idonta ta lumshe haka kawai yau takejin ta rasa gane kanta da kanta,hannunta ta zura cikin
jaka cikin sa'a taci karo da tasbaharta,saita maqalata a yatsa ta soma hailala don mugun faduwar da
gabanta keyi yana bata tsoro.

Awa biyu tsakani taji ta kasa nutsuwa,saita dauki wayarta ta soma kiran tanja. Har ta katse bata
daga ba,da alama bata kusa,kasa jurewa tayi ta sake kiranta,bugu biyu ta dauka. Hayaniya ya fara cika
kunnenta kafin muryar tanja

"Benazeer da batoul fa?" Ts tambayi tanja kai tsaye,tambayar data bata dan mamaki,shigen tambayar
data taba ma ama a makka,amma saita share mamakin tace
"Suna lafiya.....suna tare da goumar"

"Yayi......shikenan" ta fadi tana katse wayar,ajeta tayi saman kanta tana furzar da numfashi,duk sanda
akace mata suna tare da goumar nutsuwar zuciya da ruhi take samu,duk da irin yadda shi goumar din
baya gajiya da cakar da ita da kuma tsokanarta,tasan wannan a jininsa yake,kuma akanta kawai cikin
yaran gidan yake haka,duk da ita ta fara sanadin sanya masa sunan BAQIN BUZU da tayi.

[05/06, 9:16 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 51

Kaman kowanne event sai sun tsokaneta bayan kowa ya gama shiryawa,yanzunma sun
buwayeta da ya akayi komai lite tayi amma yafi na kowa kintsuwa da yin kyau. Ta gaji da wannan zolayar
tasi,ciwon kai kawai sukeson qara mata,don haka ta fita daga wajen ta koma mota ta zauna tana jiran
isowar angwayen da zasu dauki amarensu su wuce gurin dinner gaba daya. Har a lokacin jinta kawai
takeyi sama sama,basu jima ba kaman sunsan a qage take suka iso,dukka motocin suka tashi a tare suka
wuce.

*_MAINA_*

A nutse nutsuwar dake bayyana a iya fuska takunsa da ayyukansa na zahiri kadai.....yake
saukowa daga matakalar jirgin da yayi jigilarsu daga niamy zuwa nan marad'i bayan dogon zaman da yayi
daga makka a jirgin Ethiopian airlines.
Dogon ba'abzinen,Giant me wani irin qawataccen tsaho da murjajjen jiki......fari tas ma'aboci
sassalkar cikakkiyar sumar da kai tsaye za'a kirata da sumar gado,sanye cikin wata farar shadda qal.....da
aka zamanantar da dinkinta ya zauna a jikinsa tamkar don saboda shi shi kadai aka qirqiri dinkin. Dogon
wando ne da gajeriyar riga ta ciki me gajeran hannu,saidai kuma an qawata shigar tasa da babbar riga da
kuma dakakkiyar hular da bata rufa dukkan asirin sassalkar sumarsa ba. Daga nesa idan ka hangi
tsahonsa da yanayin jikin gami da shigar tasa zaka dauka jinin hambararren shugaban qasar nijer ne
wato mohamed bazoum,saidai kana kallon fuskar zata tabbatar wannan jinin MAYAK'I da jajirtacciyar
tsohuwar yar kasuwa NADEEYA ne.

Gujajjen D'a daga ainihin qasarsa ta haihuwa,daga ainihin gidansu abun alfaharinsu,daga ainihin
garinsa ahalinsa da kowa nasa......yau gashi cikin qasar da ya barta ba tare da sanin zuwa wanne lokaci
zai dawo ba?,yau gashi kan hanyar komawarsa gidan daya fita cikin fitar hayyaci da rashin sanin abinda
zai biyo baya,yau gashi zai fuskanci ABA AMA BIBI DA D'ANSA DAMA MAHAIFIYAR YARON SULTANA.

"Bienvenue Monsieur" yaji an fadi daga gefanshi da harshen faransanci ana yunqurin karbar luggage
dinsa da suhail ne ya samu nutsuwar hada masa kayan nasa. Kai kawai ya gyada ya sakar masan,don
already yasan waye,uniform din jikinsa ya sake gaya masa waye din,kuma aikin sardauna ne duka ya
sani.

Yana biye dashi har suka isa gaban wata Mercedes Benz baqa wul dake daukan idanu qirar
wannan shekarar ce da suka siyeta su ukun,shi sardauna da kuma suhail. Kai tsaye yace a turo tasa nan,a
ajjiye a kamfaninsu dake shirin fara aiki a qasar tasu.

Yau ya fara ganin motar ido da ido,amma a yanzun bashi da cikakkiyar nutsuwar qare mata
kallo,don haka shigewa kawai yayi back seat din da ya bude masa,ya maida motar ya rufe,ya shiga
mazaunin driver ya tayar da motar suka dauki hanyar fita daga airport din.

Baisan wanne yanayi zuciyarsa take ciki ba,baisan kuma meye yakeji a dukka jikinsa ba,abu daya
tak ya sani,zai fuskanci babban QALUBALE......zai gamu da komai,zai ga komai zai kuma ji komai,amma
koma meye ya dawo da dukka qarfinsa,ya kuma dawo da shirin fuskantar KOMAI DA KOWA.

Unguwar tasu ya dinga bi da kallo,a tsahon shekarun akwai ci gaba sosai,komai ya sauya,ba
wani abu da yaga yaci baya,har zuwa LOKACIN da ya driver din ya iso dab da gidansu.
Lumsassun idanunsa ya ware,ya miqa hannu ya taba kafadar driver din,da muryarsa dake can
qasa yace

"arrêt(tsaya)" bai musa ba ya gangara gefe saboda ya bawa motoci biyun da suka biyo bayansa damar
wucewa,ya tsaida motar daga gefe daya.

"Bani maqullin,tu peux y aller(zaka iya tafiya)"

"d'accord Monsieur(to yallabai)" ya fadi cikin girmamawa yana bude murfin ya fita kaman yadda ya
buqata.

A hankali ya fito daga bayan yana komawa seat din driver idanunsa bisa babban gate din mansion
house din nasu,jikinsa yana bashi wani hidima akeyi cikin gidan don yaga alamun haka,zuciyarsa ta raya
masa wani abu da tilas ya rufe idanunsa yana kiran sunan Allah sannan ya tayar da motar

"Bana fatan na mutu ban gurfana gaban aba da ama ba......bana fatan na mutu da hakkinsu" ya furta a
fili saidai can qasa bayan zuciyarsa ta raya masa kodai wani daga cikinsu ne ya rasu.

Motoci biyun da suka wuce su yabi,dukkansu security suka budawa hanya suka wuce ciki,saidai
kuma ana zuwa kanshi suka jaa qofan saboda kasancewar motar baquwa a idanunsu,sannan kuma basu
tabbatar da motar waye ba,don haka ba zasu bata daman shiga ba har sai sunyi checking nata.

Cikin dakewa da sanin makamar aiki daya daga cikin security din ke matsowa,idanu maina ya
zuba masa,houdu ne,daya daga cikin security na gidan tun kafin barinsa gidan. Ya tabbatar shine mutum
na farko da zaya fara shaidashi,saboda yasan fuskar tasa tun babu saje babu gemu,ya sanshi tun a sanda
saje ne kawai dashi,a yanzun da gashi ke kwance luf bisa tsari na samuwar shekaru a tattare dashi bazai
gaza shaidashi ba.

Abu daya tak yayi,houdu na matsowa yana sake glass din motar,dai dai sanda ya iso dai dai
sanda shima ya kammala saukewar,sai sukayi ido hudu da MAINA din.
Duk wani connection na jikinsa ya katse cak na wasu mintuna,sannan second kadai ya dawo
bisa saitinsa,idanunsa fes cikin nashi,sai yasa hannu yana cire hulan kanshi,sai maina ya dora hannunsa
saman lips nashi dole houdu ya maida maganarsa cikin cikinsa,ya kuma juya ciki da sassarfa yana bawa
saura umarnin su bude,ba musu tunda shine shugaba suka bude din ba tare da sanin waye cikin motar
ba,ya dage glass dinsa ya danna hancin motar zuwa farfajiyar gidan bangaren ajiyar motoci bayan
shekaru biyar da barinsa gidan...........

*_WELCOME BACK MAINA_*😂😂😂

Sanda take wucewa falon aba dauke da saqon aba a hannunta kunnuwanta sukaji qarar
shigowar wata motar. A ranta take dariyar mugunta,tana kyautata zaton goumar ne ya nemo najma data
boye ya maidota gida,don ta barshi a can ranshi bace yana nemanta,yayi rantsuwa bazai barta a wajen
ba. Ta rasa wanne irin kishi gareshi haka?,abun goumar yana daure mata kai,duk da migraine da take
fama dashi amma itama sai data rama yau dubu cikin abinda yake mata

"Ta can baya na ganta da wani farin buzu me irin tamu fatar" tayi furucin ko a jikinta tana bude motar ta
cilla kayanta ta shiga tabar wajen tana hangensa ta madubi. Gun data fada din yakeson zuwa,amma ya
dake yaqi nufar wajen yana tsoron ko tsiyarta ne yasa ta gaya masa hakan saboda yasan hali sarai,barin
hali kuma sai mutuwa,ta kuma karanceshin itama haka ta dinga dariya cikin mota ita kadai har ta fice a
wajen.

Daga qafarta zata sanya a falon aba din yayi daidai da qarasa shigowar motar gidan,ba kasafai
hankalinta ke kaiwa ga shigowar motoci gidan ba,amma wannan sai taji gabanta ya yanke ya fadi. Dan
dafa saitin qirjinta kadan tayi tana cewa

"Hasbiyallahu lailah illa huwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azeem"

"Waye a nan?" Muryar aba daga cikin falon ya isketa daga nan inda take
"Aba nice,saqon oncle sidi ne" ta amsashi tana qarasa shigowa ciki. Sai data shigo din taga bashi daya
bane,kamar kusan kowacce rana,tunda aka fara hidimar bikin basa rabo da irin wannan zaman waje
daya. Oncle bashar oncle umar da oncle issoufou,sai qani ga mahaifinsu da bai jima da dawowa nijer ba.

Bakinsa dauke da sunayen Allah ya ajjiye motar kan tsari kaman sauran motocin gidan,ya
kasheta ya kuma zura qafafunsa yana furta

"Bismillah" ya taka dandagaryar qasan gidan. Sai daya kulleta sannan ya juyo,juyawar daya samu
security na gidan tsaitsaye daga bayanshi suna kallonsa cikin tsantsar mamaki. Murmushi ya jefesu
dashi,sannan ya juya yana fuskantar ainihin ginin gidan,zuciyarsa na shawarta masa INA YA DACE YA
FARA NUFA?. sassa guda biyar din dukka sai sukayi masa kwarjini,daga qarshe zuciyarsa tayi masa
ragama izuwa sassan AMA saboda tuna masa da tayi UWA CE,zata iya zame masa tsanin zuwan kowanne
qalubale da sauqi.

Kasancewar kusan kowa bai dawo daga wajen dinner din ba sai daidaiku,sai ya dinga tafiyarsa
ba tare da yaci karo da kowa ba. Daf da qofar sassan ama din yaja burki kaman yadda wanda ya fito da
hanzari dauke da gorar babban lemo a hannunsa shima ya tsaya cak kamar an tsaida mashi.

Almu ne,wani irin kallon gigita da bazata yake bin maina dashi,sai gorar lemon hannun nasa ta
sulale ta fadi qasa. A nutse maina din ya duqa ya dauko masa,ya bude tafukan hannayensa ya zura masa
a ciki ya kuma damqe hannun cikin nasa,sannan cikin karyayyar muryarsa yace masa

"Kaini wajen ama" maganar tasa saita zamewa almu kamar wahayi,bai musa ba don dama tun dacan ba
musu tsakaninsu,bai kuma iya tambayarsa komai ba saboda tsananin mamaki ya wuce gaba maina yana
biye dashi.

Yasan inda ya baro ama din yanzun daya fito daga wajenta,tana falon farko wanda take da
bedroom a wajen,ya barta suna hada shimfidun da za'a fitarma dakin baqi na gidan ita da tanja,don haka
suna zuwa dai dai qofar dakin yaja ya tsaya yana bawa maina hanya,tamkar yana nufin

"Ya maina na gama nawa" idanun almu din ya kalla,sai ya sake kama hannunsa ya riqe sosai
"Ka jirani koda a nan ne,kada kaje ko ina" kamar mataccen qadangare almu dai ya gyada kai,yayin da
maina ya sanya hannu ya murza handle din dakin ya sanya kai bakinsa dauke da cikakkiyar sallama........

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_


09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[05/06, 9:16 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 52

Sallamar tasa ta iske kunnuwansu dai dai sanda ama ta miqawa tanja blanket din tana cewa

"Kowanne gado a canza don Allah kafin mutane sukai ga dawowa daga wajen dinne........." Cak sauran
maganar ta tsaye mata a qasan maqoshinta,kowanne gaba na jikinta yayi wani irin mutuwa gami da yin
sanyi kamar anabi ana zare mata laka.
Sake maimaita sallamar tasa yayi cikin karyewar murya da zuciya gaba daya,wata irin
qaqqarfan qaunar mahaifiya tarin madama da jin cewa shi cikakken me laifi ne yana taso masa. Gabanta
na faduwa ta kalli tanja,tun bata yiwa tanjar tambayar ba tasan amsar tambayar tata,amma saboda
tabbatarwa sai tace mata

"Tanja?,muryar waye kunnuwa na sukeji?" Ta furta da wani irin sauti muryarta da mugun sanyi

"Shine...." Tanja ta fadi itama kamar me tsoron gayawa ama din. Wata qatuwar ajiyar zuciya ce ta
kufcewa ama din,ta runtse idanunta sannan ta budesu,taja numfashi sosai cikin hunhunta sannna ta
fesar,sai ta durqusa tadauki wani madaidaicin blanket din ta sake miqawa tanja tana ci gaba da yi mata
bayani tamkar ba wata halitta baquwa data wanzu a wajen

"Ki ajjiyewa su bilkisu saiki dawo,akwai ragowar aiki a nan din" taci gaba da bayaninta.

Iya yadda tayi wannan motsin ya tabbatarwa maina akwai qototuwar matsala,ya taka zuwa
bayanta jiki a mutuqar sanyaye,ya sulale a hankali ya zube bisa gwiwoyinsa kanshi a qasa ya kasa furta
komai.

Cikin jikin nata taji alamun yana bayan nata,sannan satar kallon bayan nata da tanja takeyi yasa
ta sake fahimtar a bayannata yake tsaye har yanzun. Wani nannauyan abu yana fusgar zuciyarta,dukka
zuciyarta da kwanyarta na shirin shiga rudani,bataso ta waiwaya ta kalleshi......bataso ya saukar mata da
rauni a a matsayinta na uwa,idan tayi rantsuwa ko kaffara ba zatayi ba tasan cewa kaf gidan gurinta ya
fara dosowa kanshi tsaye.......ta tabbata ba wanda yasan da shigowarsa cikin gidan sai ita,akanme zata
sassauta masa?,akan me zata bari zuciyarta tayi rauni cikin lokaci qalilan har haka?,tsugunnonsa da
zamansa ba zata tana bari suyi mata tasiri ta kasa aiwatar da abinda ya kamata ace ta aiwatar din ba.

Dukka kayan tanja ta dauka sannan ta soma takawa tana barin dakin,duk taku daya sai ta
waiwaya ta kalli maina har ta fice,yayin da ama kuma ta soma hada wasu kayan,duk da batasan ainihin
me zatayi da kayan ba ita kanta. Cikin jikinta takejin wani irin yanayi,karyewar zuciya da mutuwar
kowanne sashe na jikinta,yadda yanayin bugun zuciyarta ya sauya ta tabbatar akwai fushi me tsanani
kwance a qasanta
"Assalamu alaikum.......don Allah ama koda ba zaki kulani ba ki amsa koda sallamata,ki amsa min da
neman aminci da albarkar ubangiji da na rasa tsahon shekaru" maganar tasa sai ta zame mata kamar
famin wani tsohon miki dake danqare qasan zuciyarta. Watsar da kayan hannun nata tayi sannan ta
gewayeshi da hanzari zata fita a dakin.

Cikin wani irin zafi irin na namiji yasha gabanta,sai ya sake zubewa a gabanta yana riqe da
dukka qafafunta da hannayensa

"Don Allah ama......na roqeki......ko sallamata kawai ama ki amsa min" janye qafafunta baya tayi da
sauri,karon farko ta watsawa fuskarsa wani irin kallo .......wani rauni ya sake mamayarta. Mainan ta
ne......ya zama cikakken mutum......mainanta ne.....ya zama babban mutum.....aliyyu ne da ya bar
gabansu tsahon shekaru,yanzu gashi duqe gabanta cikin qoshin lafiya da dukkan alamu na nutsuwa da
kwanciyar hankali tattare dashi

"Waye kai?,nace kai din waye?,don kaga na qyaleka a matsayinka na bare ka shigo har cikin dakina shine
zaka zaqe da yawa haka?" Ta jefa masa tambayar da murya me cike da fushi. Sosai kalaman nata suka
daki zuciyarta,suka kuma so tarwatsata zuwa piece's. Yau din shi ama ke barrantawa daga gareta?,shi ta
maida bare?,wanda bata masan fuskarsa ba?. Ya hadiye wani qatoton abu daya tsaya masa a
wuya,muddin ama tace zata qalubalanceshi ta haka bayajin zai iya dauka,ya shirya fuskantar kowanne
irin fada da ladabtarwa,koda kuwa suka ne,amma bazai iya jurar shariyarsu da wofantar dashi haka ba.

"Danki ne ama,ba wani bane daban,aliyyu ne ama......maina ne......danki bijirarre gujajje.....me tarin
laifuka a gareku.......don martabar manzon Allah S A W ama kada kice ta wannan hanyar zaki horani"
girman roqon da yayi mata yayi matuqar tasirin wajen rauna mata zuciya,amma hakan bai sanya ta kasa
sake janyewa baya ba ta kuma nufi qofa da sauri tana jin kamar hawayen da take riqewa zasu balle
kansu da kansu saboda girma da nauyin dake danqare cikin qirjinta.......ta jima da sarewa.....ta dade da
fidda rai daga samun rayuwarsa,tana raye ne kawai tabarwa kanta abinda zuciya ke yawan raya mata a
kanshi.....amma sam bata taba hasashen rayuwar aliyyu na nan tabbace saman doron qasa ba.

"Indai kazo ne na goya maka baya......na tayaka binne laifinka ba zaka samu haka ba aliyyu......nice
mutum ta qarshe da zaka fuskanta,hukunci na shine hukuncinna qarshe da zaka karbanan din ba shine
mihallin da zaka fara fuskanta ba" abinda ta gaya masa kenan a gaggauce ta fice a dakin,wani irin abu
yana zagayawa cikin jini da zuciyarta,tunaninta yana rarrabuwa. Tasan tabbas!,Allah ne ya amsa
addu'arta......amma me dawowarsa ke nufi?,meye kuma zai faru a nan gaba?,wannan dukka bata da
masaniya. Taja numfashi da kyau ta kuma fiddoshi waje,ga mamakinta sai taji dunqulallen abunnan daya
tsaye mata a maqoshi tsahon shekaru......wanda ta gaza gane meye shi tsahon wancan lokacin yana
narkewa a hankali yana sauka.

A lokacin yana jin dukka jikinsa ya masa nauyi,yana jin kamar bazai iya motsawa daga wajen
ba......yana jin kamar kwanyarsa ta daina tunani dai dai,saidai kuma a hankali ya kama sunan Allah,ya
fusgeshi da matuqar qarfi

"Alhayyu alqayyumu" ya fara maimaitawa,a hankali sai dukka qwarin gwiwarsa yaji yana dawowa,ya
kuma sake kiran

"Allah!" Da qarfin zuciya yana miqewa,ya nufi qofar dakin ya bude ya fice.

Inda ya tsayar da almu a nan ya sameshi,suna hada ido almu din ya sunkuyar da kai

"Ina zan samu su aba?" Da hannu almu ya masa nuni da hanya tamkar wani kurma,maina din ya karanci
me yake nufi,sai shima ya masa nuni da hannu akan suje din,almu yayi gaba,shi kuma yaci gaba da
bibiyar sahun almu din dake masa jagora zuwa falon.

Gaban aba ta qarasa ta durqusa kamar kullum tana musu barka da warhaka. Dukkansu suka
amsa cikin kulawa,ta sanya hannu ta dauki ledar tana miqawa aba fuskarta fadade da murmushi

"yauwa ma sha Allah,ya cika alqawari,ungo wannan" aba ya fadi sanda yake warware kilishin da sultana
ta kawo masa. Murmushi tayi ta sanya hannu biyu ta karba tana cewa

"To na gode aba sosai"

"Madalla" ya amsa mata,sannan ta yunqura tana miqewa


"Kinga sultana.......ki shiga ki gayawa mariya su duba abinda yayi ragowa a kayan amfanin gobe" oncle
umar ya fada

"To uncle" ta amsashi tana nufar qofar tana ji aba yana tsokanarsu kan cewa boye kilishinsa zaiyi,diyarsa
kadai zai iya bawa. Murmushi ta saki qasan zuciyarta,ba abinda zata ce ma Allah sai godiya,itakam
batasan maraicin uwa da uba ba.

Tsam almu ya tsaya daga bakin qofa ba tare da maina ya buqaci hakan ba, cikin jikinsa yaji bazai
iya jerawa da maina ba,yana jin bazai iya jure hukuncin kallo kadai da maina zai iya fara maraba dashi
daga dukka iyayen nasu ba. Bai waiwaya ya kalli almu ba,kaman ma baisan almun ya tsaya ba ya doshi
babbar qofar falon. Ya tube tsadajjen sau cikin qafarsa,ya sanya qafafunsa dake saye da safa cikin falon
yana janye labulen gefe bakinsa kuma dauke da cikakkiyar sallamar

"Assalamualaikum warahmatullah". Wani dogon numfashi almu ya saki yana qamewa jikin bango gami
da runtse idanunsa. Ya rantse da Allah.....tabbas inda shine ya maina bazai iya sanya kansa ga falon nan
ba,ya rantse da Allah bazai iya fuskantarsu ba saidai idan tara tara za'a yi masa,wanne irin qarfin zuciya
dakiya da jarumta ke gareshi?,ko kuwa dai baisan girman laifinsa bane a garesu?.

"Wa'alaikumussalam warahmatullah" sukayi hadin bakin amsawa,saidai kuma ba dukkansu bane suka
samu cikakkiyar lada da daman amsa sallamar.......kamar yankewa zubar ruwan sama sauran amsa
sallama ta tsaya saman harshen aba......yayin da oncle umar shima sauran furucin suka tsaye masa cak.
Wani irin rawa zuciyar aba tayi bayan daukewar sallamar daga bakinsa,a nutse kuma sai ya dauke kansa
daga kallon qofar falon ya maida ga takardar kilishinsa ya soma qoqarin nannadeshi.

Cikin qasa da second biyu da shigowarsa dakin da fitar sallamar daga bakinsa idanunsu suka
gauraya waje daya. Haduwar idanun data zame musu wani abu na bazata dukkaninsu. Batayi zaton
ganinsa ba.....baiyi tsammanin samunta a wajen ba......hasashe ko tunaninta bai kawo.mata ganinsa a
nan kurkusa ba. Wani wawan birki taja a matuqar Hautsine,a hankali taji hankalinta yana neman
firgita,nutsuwarta na shirin yin qaura daga ganganr jikinta. Wannan haduwar dai dai take da MUGUN
GANI a wajenta...... mummunar rana da kuma mummunan lokaci......maina cikin gidan?,a wannan
daren?,a kuma irin wannan lokacin?. Tambayoyin da suka kusan tsayar mata da gudun numfashi
tsakanin qirjinta da zuciyarta zuwa hunhunta kenan.
*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261
*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[06/06, 9:43 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 53

Dukkan zagayayyun lion eyes dinnan nasa ya kafeta dashi. Karon farko......lokaci na farko da
sukayi gaba da gaba dashi. Karon farko yau gashi tsaye a gabanta,a gaban wata sultanar da ko kusa ko
alama baiga tayi masa kama da wancan sultanar da ya bari shekaru biyar baya ba. Wani irin qaton abu
yake ji yana gangarowa daga zuciyarsa me matuqar nauyi yana kwaranyewa zuwa sassan jikinsa.

Da wani zazzafan karsashi ta janye idanuwanta,wata irin wuta na ruruwa cikin qahon zuciyarta.
Har tsakiyar qirjinta takejin wani irin zafi yana sauka,ta soma takawa cikin bawa kai qwarin gwiwa ta
kewayeshi tana nufin fita daga dakin, zuciyarta na jaddada mata bata da hadi dashi,ruhinta na gaya mata
cewa bata sanshi ba......bata ma taba saninsa a rayuwarta ba,tana kuma sake bawa kanta yaqinin bata
da wata alaqa dashi.
Dukkan kowanne sashe na zuciyarsa muradin binta da kallo yakeyi,abinda ya gani qasa da
second goma cikin qwayar idanunsa ya matuqar razanashi,to amma sanin da yayi cewa abinda ke
gabansa da kuma mutanen dake zaune cikin falon din dai dai yake da tunkarowar yaqi cikin rayuwarsa
sai ya tattara dukka wani abu daya taso ya tsaye masa a wuya yayi musu muguwar hadiya,hadiyewar
daya haifar da ciwo a qirjinsa da kuma jirkicewar ainihin launin qwayar idanunsa.

Tamkar gagarumin me laifin dake takawa zuwa gaban alqalin da zai yanke masa hukuncin
mutuwa ko rayuwa haka yaci gaba da daga qafafunsa da kuma saukesu yana tunkarar mutanen da ya
tabbatar suke da matsayar ci gaba da fuskantar rayuwarsa a yanayin daya kamata ko akasin haka.
Dukkaninsu idan ka dauke mutum daya tal wato ABA idanunsu yana kanshi,kowa yana dubansa ne da
zallar tarin mamaki da kuma bazatar bayyanarsa a irin wannan lokacin.

Dai dai sanda ya zube a tsakaninsu aba ya miqe,ko sau daya ko alama bai nuna yasan da
shigowarsa ko wanzuwarsa cikin dakin ba

"Issoufou idan kun gama ka sanya yara su shiga dakincan su fidda komai,zan din shiga ciki na kwanta
goben ina tunanin zan riga kowa fita don ina da baqi a gidan baqi na". Ba maina kawai ba,dukkansu
sunsan wannan miqewar da yayi bawai ya yita bane saboda yana nufin abinda ya fada din,ya yita ne
kawai saboda baya buqatar hada numfashi da maina,ya yita ne saboda isowar maina gurin,don a zaman
tattaunawar da sukayi duka duka basuci koda rabin abinda suka zauna su tattauna saboda shi din ba.

Kaman yadda ya yiwa ama haka ya miqe cikin zafin nama ya tari gaban aba sannan ya sulale a
gaban nasa.

"Waye wannan?,ku gaya masa ya matsa daga gabana!" Aba ya furta da wata irin kakkausar murya da
duk sanda ta fita da irin wannan sautin......duk wanda ya sanshi to yasan cewa yakai maqurar fushinsa
kenan

"Don Allah aba.....don girman Allah......!" Bai barshi ya qarasa magiyarsa ba sai saukar zazzafan mari da
sautinsa ya karade falon. Kaf dinsu jini ya dauke a jikinsu,don ba wanda ya tsammaci irin wannan
zazzafan hukuncin haka tashin farko daga wajen aba,kasancewarsa mutum ne bame yawan kaiwa koda
yara hannu ba bare maina da a yanzun ya zama cikakken mutum
"Kaci gaba da tsayamin bisa hanya kaga yadda zamu kwashe dakai mahaukacin banza!......zaka matsamin
ko sai na tattakaka a wajen?" Aba din ya kuma fadi cikin fushi. Cikin hanzari oncle umar ya miqe ya janye
maina wanda ko gezau baiyi ba,hasalima baiso oncle umar din ya janyeshi ba,zaifi masa dadi ya barshi a
wajen aba yaci gaba da dukansa wataqila ita daya ce sassauqar hanyar da aba din zaiyi saurin
sassautowa ya saurareshi.

"Zauna nan,kada ka sake tsaiwa masa a hanya aliyyu" oncle umar da zuciyarsa shima ta fara motsawa ya
fada cikin nasa fushin.

Kafeshi oncle umar din yayi da idanu,kaman yadda oncle bashar da oncle issoufou suka kasa
motsawa,idanunsu dukka akan maina din,saboda wani abu ne da yazo musu a bazata gaba dayansu.

A hankali idanuwansa suke sauya launi saboda abinda ke motsa masa cikin zuciya,wani irin
yanayi maras dadi qunci da zafin zuciyar da shi daya yasan me yake fuskanta.

"Yaushe ka dawo?, yaushe ka shigo gidan?" Oncle bashar yayi qarfin halin tambayar maina. Sanda ya
dago fuskanshi da zummar amsa masa dukkansu saida kowa yasha jinin jikinsa. Wani irin yanayi fuskar
tasa ta sauya,gaba daya kamanninsa sun canza.

"Yanxu oncle......yanxu na shigo,ama taqi saurarona tace saidai na sameku...... shima aba haka"

"Ba zasu saurareka din ba,don bakayi abinda zasu saurareka haka ta sauqi ba aliyyu" oncle umar ya fadi
da wannan yanayin nasa dake nuna zafinsa. Idanu maina ya maida kan oncle umar din yana da zafi shima
qwarai,har wani lokaci bibi ke ganin ta wajenshi ya gado zafi da kafiya,saidai nashi zafin da ya tashi ya
ninka na dukka uwayen nasa. Duk da zafinsa idan ya gama spark ya sauka yana da budaddiyar
zuciya,yana da zuciyar sauraro dake iya fahimtar mutum ta kuma bashi uzuri,yana da kafiya da qoqarin
fahimtar da aba harma da bibi a duk sanda suka hau dokin naqi,ya hangi nasara ya idanuwa da
bangarensa,don haka ya zamo a hankali ya gurfanar da kansa a gabansu

"Bansan da wanne baki zan fara baku haquri ba......bansan wadanne kalmomi ne zasuyi tasiri a kanku
wajen wanke fushina dake zuciyarku ba...... abinda zan iya fada kawai shine......ina me neman afuwa da
yafiyarku akan yanayin dana sanya zukatanku.....zullumi da fargaba dukka.......sannan gani a gabanku
kuyimin dukka hukuncin da kuke ganin ya dace kan cutarwar da na yiwa jikarku" kalamansa sun dakesu
sosai sun kuma sanyayar da jikkunansu. Dakin ya dauki shuru,kaman yadda basuce komai ba hakanan
shima bai motsa daga tsugunnon da yayi ba,har sai da oncle umar ya magantu

"Koma ka zauna maina" kasa motsawar yayi yana jin nauyi da kunyarsu,yanajin nauyin abinda ya aikata
din da yayi sanadin barinsa gida,yanajin kamar a yanzune komai ya faru,har sai da oncle issoufou ya
kama hannunsa sannan ya matsa gefe ya sake zama sosai.

Fada sosai oncle umar ya balle masa dashi,don dama shidin baya barin ko ta kwana,sha yanzu
magani yanzune ko akan waye,sai da yayi mai isarsa bashar da issoufou suna tayashi sannan ya rufe da
fadin

"Abinda ya faru tsakaninka da matarka za'a iya cewa me sauqi ne inda ka zauna baka nuna ragwantaka
ba...... za'a iya cewa rabo ne ya kawo haka,shi kuwa rabo baya tsallake rana da loakcinsa......ba kuma
wanda ya isa ya hana wannan rabon fita sai ya fita a sanda ubangiji ya tsara......abu mafi muni shine
tafiyarka,tafiya bata sati daya ko biyu ba,bata wata daya ko biyu ba,bata shekara daya ko biyu
ba.....shekaru aliyyu,shekaru a qalla biyar?,wanne irin rago ne aliyyu?me yasa ba zaka tsaya ka fuskanci
koma meye ba?,duk tsiya ba haramun dinka ka afkawa ba,me yasa ka tafi?" Ya jefa masa tambayar da
alama tafiyar tasa tana daya daga cikin abinda ya sosai zuciyarsa.

Tabbas yasan cikin bacin ran dake danqare aran oncle umar ne kadai ya sanyashi ya jefeshi da
kalmar RAGWANTAKA......saboda duk gidan yafi kowa sanin TSORO yana daya daga cikin abubuwan da
bai baiwa muhimmanci a rayuwarsa ba JA DA BAYA basa daga cikin kafatanin dabi'unsa,duk yadda zai
musu bayanin yadda yaji a sanda abun ya faru.....duk yadda zai kwatanta musu yadda qaddara ta dinga
janshi tana tilasta masa ficewa daga gidan ba zasu gane ba.......daga bayan barinsa gidan kome daya faru
dashi ya sakashi a mizanin wannan QADDARAR da tayi sanadin fitarsa a gida..... wanda yayi imanin
banda hakan ta faru......da tuni a yanzun ba shine ALIYYU MAYAK'I da ake magana a kai ba,da tuni ba
shine MAINA da yaketa qoqarin binne daukaka da matsayin da ya samu ba,bayan tarin qalubalen da ya
gamu dashi sanadin fitarsa a gida

"Dukka ka yiwa kowa laifi,amma tamu me sauqi ce,kuma mun yafe maka,a yanzun babban qalubalenka,
zamuyi iya abinda zamu iya wajen nema maka sasaauci,amma saukowarsu wannan tana
hannunka,tunda bamu isa mu tilasta musu su yafe maka ko mu goge abinda ke ransu ba......" Ko iya
wadannan kalaman na oncle umar kadai sun samar da wani sasaauci cikin gurbin zuciyarsa,sun kuma
haifar da wani dan qaramin hope

Baisan ta yadda zai gode musu ba, matsayin nagartattun kawunnai a wajensa,ya miqe da zummar
barin falon,yana kuma wassafa ta inda zai fara tunkarar wannan gundumemiyar matsalar........ babban
yaqi da zai zama madubin rayuwarsa muddin ya cimma nasara.

"Kaje zuwa da safe koma meye zamu qarasa magana akai......gobe daurin auren qannenka biyu"

"Waye da waye?" Ya samu kansa da jefawa oncle umar tambayar saboda wani fargaba daya kamashi.
Dukka sai suka dan tsaya suna dubansa kafin oncle umar din ya bashi amsa

"Aminata da yasmine" qas yayi da kansa kuma yana jin nauyinsu,yana jin kamar yayi tambaya akan
makomar aurensa da sultana......to amma kuma hakan kamar zai zama da gaggawa,karbarsa da sukayi
bawai yana nufin yanzun shi bame laifi bane a wajen kowa ba...... a'ah......yasan sun karbeshi ne saboda
tsananin zumunci irin nasu da yadda suka tashi da soyayyar junansu data yaran da suka fita daga
tsatsonsu.

"Aliyyu" oncle issoufou ya kirayeshi da sassaucin nan nasa,don shi din mutum ne da bashi da zafi
sam,duk cikinsu yafi kowa sanyin hali

"Ka kama bibi,ka tabbatar ta zame maka tsani" kai ya girgiza wani busashen murmushi na fita daga
saman labbansa,tamkar oncle issoufou din ya shiga zuciyarsa,bibi ce kawai last hope dinsa da yayi
imanin tana da power din da zata maida komai bisa saiti,ko meye zatayi duk wani borenta bazai bari ya
dameshi ba,zai runtse idanunsa,zai kuma gwada mata shi dan yau ne,domin yasan halin bibi sarai,zuma
ce sai da wuta,amma kuma yana da babban yaqini a kanta.

Daidai inda sukayi kacibus ya kalla sanda yake fita a falon,yaja dogon numfashi daya sauka har
tsakiyar hunhu da zuciyarsa
"SULTANA" ya maimaita sunan kamar yaune ya fara jinsa. Akwai babban game tsakaninsa da ita,yana
tunanin itace abu na qarshe da zai cimma,a yadda ya tsara itace zata kasance matakalar qarshe,yaya
zaije mata?,ta yaya zai risketa?,dukka bai san wannan ba......abu daya ya sani,ya kuma haqiqancewa
kansa shine........duk RINTSI......duk yadda za'a je a dawo ba zaya taba yarda da abinda zai shafi igiyoyinsa
ba

"Idan suna nan har yanzu?" Wani sashe na zuciyarsa ya jefa masa tambayar data tilasta masa riqe
hannun almu dake zaune zuwa yanzu a gefan qofar falon saman wasu qananun kujeru dake wajen don
ya gaji da tsaiwar jiransa

"Idan har yanzu sashe na yana nan......ina buqatarsa,ka gyaramin koda iya wajen da zan ajjiye kayana" ya
fada adan birkice,don har yanzun bayajin cikakkiyar nutsuwa a jikinsa. Kai almu ya gyada yana
miqewa,har yayi taku biyu mainan ya kirashi,sai ya dawo ya tsaya cak gaban maina yana kallonsa

"Bayan tafiyata ciwon kurumta ko bebantaka ya sameka ne?" Ya masa tambayar yana duban idanunsa.
Kai ya girgiza sannan ya matso taku hudu da sauri ya fada jikin mainan yana cewa

"Barka da dawowa ya maina,Tu nous manques(munyi kewarka)"

"merci(na gode)" ya ambata da raunanniyar muryar nan yana daga almu daga jikinsa yana kallonsa.
Shima almu din kallon fuskar maina yakeyi,yana mamakin yadda ya mainan nasu ya sake komawa.
Babban mutum da wani irin shinfidadden kwarjini da nutsuwa saman fuskarsa. Abinda shima maina ke
wassafawa a ransa kenan,almu din da ya tafi ya bari da sauran quruciya ya zama saurayi

"Ka girma almu,ina fata zaka taimaka wajen kawo wani haske komai qanqantarsa tsakanina da ama"

"je promets in sha Allah(nayi alqawari in sha Allah)" kai maina ya jinjina,yana a tsaye har almu ya tunkari
tsohon sashensa da baiga wani abu daya sauya ba ta wajen,saima gyara da wajen ya samu da kuma
kulawa.
A yadda idanunta suke a rufe sam bataga bibi dake zaune cikin falon ba tana kallo saboda
raguwar jama'a daga sassan nata. Sanda ta shigo din daga kai kawai bibi tayi ta bita da kallo,yanayin taku
da tafiyar sultanar dukka ba sune tattare da ita ba

"Ikon Allah" bibi ta fadi har zuwa sanda ta tura qofar dakin dake kusa da ainihin dakinta ta shige

"Allah ya kyauta.......itama wannan ja'irar na fuskanci ta zama baudaddiya" ta fadi a bayyane tana maida
toothpick din data zaro bakinta taci gaba da sakacenta.

Kamar daga sama taji sallamarsa,saita maida dubanta da hanzari bakin qofar qawataccen falon
nata. Yadda ya zuba mata idanu haka itama ta zuba masa tana jin kamar cikin mafarki take ko kuma
majigi take kalla

"Wannan kamar maina" ta fadi cikin tantama duk da yaqininta yafi yawa akan tabbas shi dinne.
Qafafunta dake saman kujera ta sauke,har yanzu bata dauke dubanta daga kanshi ba kamar wadda taga
fatalwa. Ta waiwaya kadan tana qwala kiran sunan

"Tanja!,ke tanja!!" Tanja tana kusa,don tana kitchen din bibi din zata zuba abinci taci,saita saki abinda
takeyi din,don yanayin kiran da bibi ke qwala matan baiyi kama da kiran lafiya ba,uwa uba kuma tanata
juya dawowar maina a daidai wannan lokaci.

Dashi idanunta suka fara cin karo,yana tsaye abinsa qyam daga bakin qofar,a dan rude ta kalli
tanja

"Wancan dake bakin qofar a tsaye ba aliyyu maina bane?" Tayi tambayar bihaqqi tana neman sani.

Tanja bata ma dubi wajen ba ta bawa bibi amsa

"Shine" kammala fitar haruffan guda biyar yayi daidai da miqewar bibi tamkar bame fama da ciwon qafa
lokaci lokaci ba,sai kawai ta soma jan zaninta tana daurin qirji dashi idanunta fes bisa fuskar maina da sai
data miqe din take sake qare masa kallo abinda daga maina din har tanja suka gaza gane abinda take
nufi da hakan

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_


09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[06/06, 9:43 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 54

Idanunsa fes bisa kanta,yasan dukkan wani kalar rigimarta,yasan meye zata iya aikatawa da
wanda ba zata iya aikatawa ba,yasan kuma lagonta qwarai da gaske.

"Billhuwallazi lailah illa huwa idan ma fatalwa ce ba aliyyu ba ni bibi nafi qarfinta.......idan kuma har da
gaske kaine.......da idanuwanka guda biyu a bude na rashin kunya ka iya dawo mana cikin gida to dai dai
nake dakai,shege ka fasa ni da kai" ta fadi cikin daukaka murya tana sake gyara daurin zaninta da kyau
tamkar me shirin yin dambe dashi. Dolen dole badon yaso ba murmushi ya subuce masa yana
kallonta,da gaske take tattara dukkan qarfinta kamar wadda ke shirin yin dambe da qaddararta.

A yanzun ba bibi kadai ba, kusan duk wanda keda ruwa da tsaki da rayuwarsa yasan a tunzure
yake dashi,bazaiyi wani abu kuma da zai sake tunzurata din ba don yanzun tamkar itace sitiyarin gidan
gaba daya,samun kanta shine samun kan kowanne mutum dake cikin gidan,don haka yaci gana da
takawa yana nufarta

"Au......ba zaka dakatamin a nan ba?,la'ilaha illallahu......da gaske dai aliyyu ne!, jama'a kuzo ku ganemin
ikon ubangiji na" ta sake fada cikin daga murya tamkar tanasom tara masa jama'ar gidan gaba daya

"Bibi kibi a hankali,ba fatalwa bane na gaya miki maina ne" tanja ta furta adan daburce ganin yadda bibi
ta dage lallai saita hada masa jama'ar gidan. Shikam ko gezau be fasa takawa zuwa wajenta ba,yayin da
taci gaba da kwakwazo da jan salati iri daban daban.

Yana isa dab da ita baiyi wata wata ba ya sanya hannu ya riqeta da kyau

"Sakeni,sakeni nace" ta fadi yana qoqarin qwace hannunta daga nasa cikin fada da hargagi

"Kiyi a hankali,tunda dai baki samu damar hadamin jama'ar da kikayi niyya ba aisai ki haqura ki zubawa
sarautar Allah ido ko?" Ya fadi yana qoqarin zaunar da ita. Dukka sauran qarfinta ta sanya ta tureshi cikin
fusata tana cewa

"Gafara can ka bani waje,wato nice marainiyar wayonka,ka tsallake katanga.ka shigowa mutane cikin
gida a sirrance zaka zo.ka cuceni,banga alamar akwai wanda yasan da shigowarka cikin gidan nan ba"
qaramin murmushi ya saki yana sake yunqurin riqota

"Allah ya kiyaye.......da lalacewa ta sameni,na gudu daga gida......na tashi dawowa na biyo ta
katanga?.....ai kuwa da nayi asarar suna,kuma da daga yau na ajjiye sunan Aliyyu na koma aliya"
"Ahaf.......lalacewa kuma ta nawa?,duk dan da zai tsallake albarkar iyayensa yabar gida shekara da
shekaru ai lalacewa ta gama samunsa" ta fada tana sake qoqarin tureshi . Har cikin zuciyarsa maganar
tata ta bashi dariya,saidai boren nata yayi imanin mataki ne na nasara,nasarar da ya tabbata tana da
alaqa da addu'ar da ya tsananta yi tun kafin ya sanya qafafunsa cikin gidan.

"Kina batan lokaci ki zauna ki marabceni kawai" ya fadi yana sanya qarfinsa cikin tausasawa ya maidata
ya zaunar saman kujera,sai ya waiwaya yana duban tanja

"Jeki abunki kija mana qofa miji zai gana da matarsa" dan qaramin murmushi me hade da hawaye ya
qwacewa tanja,tayi missing maina qwarai,bama ita ba,kowa dake gidan idan zaiyi magana ta tsakani da
Allah zai fadi haka. Duk da zamantowarsa me zafi fushi da kuma zuciya......amma kuma shi din mutum ne
me dadin mu'amala qwarai da gaske.

Gadon bayansa ta kaiwa dundu da dukka qarfinta tana fadin

"Allah ya kiyaye Allah ya sawwaqe nayi miji da kai,mijina jarumi ne,bai tana ja da baya ba" ta fadi tana
yarfa hannunta,don dukan data kai masan ba shine yaji zafin ba itace taji,ita dimma bata ankara da
wautar da tayi ba na kai masa dukan sai daya zauna ya babbake a gabanta sannan ta qare masa kallo
tsaf. Ya zama ingarma dake da wani irin ginanne kuma tsayyen jiki da nuna zallar qoshin lafiya da
cikakken qarfi,ko ina a murde alamun daga qarfe sosai sun bayyana ga jikinsa,duk da cewa cikin sutura
yake cikakkiya.

"Bafa mainan da kika sani a baya bane kike dukana haka bibi?"

"Na sani mana.....wannan wani shashashan maina ne,gudajje daga gidan iyayensa bayan yaso ya kashe
'yarsa kuma 'yaruwarsa sannan matarsa" ta fadi masa cikin fushin zuciya,tana jin takaicin yadda bata da
cikakken qarfin tureshi ta tashi a wajen ta daina kallonsa. Wani qasaitaccen murmushi ya saki yana
sadda kanshi qasa kafin ya dagoshi

"Kowa na gudu.....kowa guduwa nayi.......bien(da kyau),duk kuci gaba da fada,ba laifi tunda abinda idanu
suka gani kenan,amma nan gaba kadan zan tabbatar muku da sabanin fahimtarku" ya qarashe maganar
yana jan siririn hancinta me tudu kadan wanda kusan dukansu irinsa suka gado,wani irin hanci me kyau
dake qarawa fuska kyawu.
Hannunta ta saka ta buge hannunsa tana cewa

"Ka fita ka bani waje tun banci mutuncinka ba,ko kuma na kira ubanka ya fiddamin da kai,tunda naga
alama shi kake tsoro" idanu ya fiddo waje,sai ya sulale qasa yana riqe dukka qafafunta hadi da dora
kansa saman qafafunta,yayi laushi qwarai da muryarsa cikin sigar tausayi

"Indai ba bindigeni kikeso aba yayi ba kiyi haquri kada ki kiramin shi,dazun nan ya gama kwakwadamin
mari,bibi kaman zai tsinemin,ama taqi koda kallo na,kema nazo kin juyamin baya bayan ko meye ya faru
ke kika dauremin qarqashin aikatawa......." Bakinsa ta kaiwa bugu da sauri,saidai kuma bata sameshi ba
don ya kauce yana boye dariyar dake subucewa tun daga zuciyarsa,fiye da rabin tsoro razani da quncin
da yake ciki a yanzun baya jinsa tunda gangar jikinsa ta gamsu da cewa yana cikin gida...... yana cikin
family dinsa,yana cikin ahalinsa iyalinsa

"Ni nace kaje ka yiwa diyar mutane fyade?,ka kusa kasheta?,ka illata mata idanu maina?" Ta fadi adan
rude. Maganarta ta qarshe ita ta dakeshi,har ta sanyashi daga idonsa yana kallonta,dan siririn
murmushin da ya soma samu saboda tubura bibi da yakeyi ya bace bat daga saman fuskarsa

"Illata idanu bibi?, yaushe?,garin yaya?" Tambayar tasa ta sanyata daga hannuwanta dukka biyun ta
zuba masa ranqwashi da qasusuwan yatsunta da dukka qarfinta,ta yadda tazan zafin zai ratsa tarin
sumarsa ya kuma isa ga ainihin tsakiyar kansa. Idanunsa ya runtse gam,saboda da gaske zafin ya isa har
fiye da inda taso yaje din

"Ni zaka yiwa tambayar yaushe ka illatata din?,sanda ka aikata aika aikarka wa kayi shawara
dashi?,oh.....ni 'yar nan naga ta kaina......ban sake yarda lallai baka da kunya ba sai yau aliyyu......tashi ka
bani waje,kada ka sake shigomin guri,ban gayyaceka ba,daka dawo bani ka dawowa ba,tashi nace" ta
fada tana tureshi da gasken gaske. Yaga fushi da motsuwar bacin rai saman fuskarta,amma kuma ta wani
sashen da batayi zato ba akwai farincikin ganinsa danqare qasan zuciyarta wanda batasan wannan
hasken yana bayyana akan fuskarta ba.

Tsam ya miqe din yana dubanta na wasu sakanni ya qare mata kallo,sai ya zuba hannayensa a
aljihun wandonsa yana magana a nutse,duk da qasan ransa akwai razanin jin cewa ya yiwa idanun
sultana illa,saidai yana mamakin ta ina?,don baiga wani nakasu cikin fararen zagayayyun idanun nata
data jefa masa kallo dasu a makka da kuma dazu dazu ba cikin falon aba

"Zan tafi bibi,amma bawai na tafi kenan ba,zan dawo koda zaki yayyanka ni ki sakani a tukunya.......kafin
na karbi kowanne hukunci ya kamata a bani damar magana koda ta minti daya ne,zan bayyanar da kaina
a gobe gaban kowa,zan kuma karba kowanne hukunci da kuke tunanin na cancanci ns karbeshi" daga
wannan ya soma takawa don barin falon,amma kuma idanunsa manne da bakin qofar dakin,dakin da
bazai taba mancewa dashi ba......dakin da yasha mafarkin gashi a cikinsa.....wancan din daya faru yana
maimaita kansa har sau babu adadi.....cikin kowanne dare da zaizo ya shude. Cikin jikinsa ya dinga ji tana
cikin dakin,amma koda wasa bibi na wajen bazaiyi gangancin shiga ba,a yadda take a fusace ya tabbatar
tana iya tayar da boren da a yau aba da bibi ma basu isa sunyi bacci cikin gidan ba.

Dai dai lokacin daya fita din ta sulale qasa tana jingina bayanta da qofar dakin bayan ta gama
kallon komai dake faruwa tsakaninsa da bibita qaramar hudar da akayi don hangen wanda ke waje. Tana
ganinsun,amma kuma bata iya jin abinda duke fadi a tsakaninsu. Tun dazun hawaye ya gama wanke
mata fuskarta gaba daya,saita qarasa zama dirshan qasan dakin tana rufe fuskarta da dukka tafukan
hannayenta.

Duk da batajin me bibi ke gaya masa amma kuma sai tayi mamakin yadda bibin ta tsaya
saurarensa koda kuwa kanainayetan yayi. Ta dauka zata sanya qafa tayi fatali dashi,ta zaci zata sanya
madoki tayita dukansa har sai ya fice musu a daki da qafafunsa,duk wani action na bibi bai burgeta ba
duk data fuskanci bore tayi masa,so tayi bibin ta masa irin tarbar da zaiji baya da sauran sha'awar sake
zaman gidan.

"Ke sultana!.....,kukan meye kikeyi?,kin manta yanzun ke ba sultanar baya bace?,kin manta a yanzun ke
wata sultana ce ta daban?,a baya min xubda masa hawaye,a yanzun bai cancanci kici gaba da xubda
masa wannan hawayen ba,ki qarafafawa kanki gwiwa,ki gayawa kanki da kanki a yanzun damuwa bata
cancanceki ba.......kiyi moving forward,kada ki bari ya sake maidoki inda kika riga kika wuce" kaifafan
maganganun da suka dinga kai komo kenan a tsakiyar qwaqwalwarta.

Sosai taji ta gamsu,ta yadda yanzun shi din ba kowan kowa bane cikin rayuwarta,bashi da kaso
ko misqala zarratin a rayuwarta,me yasa zata bari ya dameta?. Da wannan tunanin ta isa gaban madubi
tana kallon kanta da kanta. Da gaske ta canza,da gaske ba sultana yarinya qanqanuwa bace wadda zai
yiwa qarfa qarfa......wadda zai yiwa.kama.karya......wadda zai yiwa dukkan abinda yaga dama yakeso,a
yanzun ta girma......ta kuma mallaki hanakalin kanta,koda jama'ar dake kewaye da ita wadanda zata rayu
dasu sai wadanda taga damar zama dasu ta kuma zabesu.

"Dole ya sani ya kuma shaidawa kansa da kansa da da yanzu ba daya bane" ta furta a fili qasa qasa tana
motsa jajayen labbanta. Bandaki ta shiga,ta raba kanta da kayan jikinta ta watsa ruwa hade da alwala.
Sakakkun kayan bacci ta saka don tafi sakewa,duk wani motsi nata tana furta

"La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin" saboda zuciyarta tayi sanyi. Hijab ta sanya har
qasa,ta isa qofar dakin nata ta murza key don kada ma su dawo su dameta,tun dacan dama bata kwana
da kowa dakinta don batason takura ko hayaniya,yanzun ma bata son kowa ya dameta shi yasa ta rufe
dakin,ta shimfida abun sallah tahau ta kabbara salla shafai ds wuturi sannan ta dora da nafiloli.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[08/06, 9:52 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 55
Idanunsa suna kan kowanne sashe na sassan nasa,yana nan kaman yadda yake,ba abinda aka
sauya ba kuma wani abu daya lalace kamar bai dauki wadannan shekarun baya nan ba.

Duk inda ya gifta ba abinda ke dawo masa sai shekarun samartakarsa, abubuwa da yawa ya dinga
tunawa har ya ratsa falonsa yakai ainihin bedroom dinsa.

Yana shiga almu yana ajjiye mop stick din daya gama goge masa tiles din wajen,suka hada idanu
da maina din,sai yadan sadda kansa kadan. Abun almu din yana dan bawa maina mamaki,duk ya
maidashi wani baqo qarfi da yaji,duk da ko a baya ba sakewa tsakaninsu sai desipline,amma kuma yana
tunanin kaman a baqon almu yake kallonsa.

"Ina goumar?" Ya tambayeshi, tambayar data sanyashi daga kai ya kalleshi,don a nasa lissafin maina din
bai wani san goumar can can ba

"Sunje niamy.....amma gobe da sassafe jirginsu zai iso da angon yaaya aminata" kai ya jinjina,shuru na
wasu 'yan mintuna ya biyo baya,sai ya gyada kai

"Shikenan jeka,sai da safe"

"Akwai wani abu da kake buqata?" Almu din ya tambayi maina,har qasan zuciyarsa yana jin
tausayinsa,duk da baikai wayon haka ba sanda yabar gida amma kuma yana iya tuna kulawa da yake
basu,sa'annan a yanzun ya san cewa gagarumin qalubalen dake gaban yaa aliyyun,duk wata kulawa
bazai sameta daga iyayensu ba

"Babu" ya amsa masa a taqaice


"Merci" ya sake fadi yana jin dadin yadda almu din ya nuna masa kulawa. A yadda yakeji din baya jin zai
buqaci wani abu,nutsuwa kawai yake da buqata da kuma kebe kansa har zuwa safiya. Don haka almun
yana fita ya soma zagayawa cikin dakin,yayi 'yan dube dubensa. Komai yana nan hatta da suturunsa ba
abinda aka taba,ya maidasu waje daya ya killace,don a yanzun bazai iya amfani da ko daya daga cikinsu
ba.

Kayan jikinsa ya cire ya daura towel ya wuce bandaki. Ya jima yana dumama jikinsa sosai, tunani
cunkushe a kwanyarsa. Baisan yaya safiyar gobe zata waye masa ba,baisan da wanne ido da kuma
wanne hannu zasuci gaba da tarbarsa,saidai koma meye yana bawa kansa tabbacin juriya da dagewa
hadi da jajircewa.

Kayansa da yazo da su ya bude,ya fidda pajamas marasa nauyi ya saka,kwanciya yakesonyi


amma bayajin zai iya kwanciyar,don haka ya shimfida abun sallah shima ya kabbara sallah da tarin
buqatu dake cikin ransa.

*********Tun asuba hayaniyar cikin gidan ta qaru saboda yawan jama'a da kuma hada hadar daurin
aure da aka fara yi,wanda duka daurin auren su biyun zai gudana ne a babban masallacin alhj
Mohammed mayak'i dake farkon street din nasu.

Tana idar da sallah ko hijabin jikinta bata fidda ba ta koma saman gado,idanunta fal da bacci
don a jiya bata samu cikakken bacci ba.

Batasan adadin awannin data shafe tana bacci ba,ta daiji anata knocking sama sama amma bata
ko motsa ba,don tasan mutane ne kawai zasu dameta,saidai a yanzun bugun da ake mata yasha banban
da wadancan,don yanzun kamar za'a tsinke qofar a shigo,dole ta miqe tana lalubar dankwalinta da ya
zame ta sanyawa kanta,sannan ta sauko daga saman gadon ta nufi qofar.

Yasime ne a tsaye,tayi kyau cikin shigar wani arnen farin lace da ya wadatu da ado da duwatsu
masu qyalli,kana kallonta basai an gaya maka ba amarya ce, fuskarta ta dauki makeup sosai wadda ta
sake bayyana ainihin kyan nan nasu da sukayi gado. Houda na tsaye a gefanta cikin army green shadda
da sukayi anko dukkansu 'yammatan amare suka tsara zasu sanya a yau din. Wata harara ta jefa mata
"Wai bacci ma kikey?" Hannu ta sanya tadan dafe kanta

"Da ciwon kai na kwana Yasmin,don Allah karkiyi qorafi" ta fadi tana karya murya. Dariya ta bawa
Yasmin din

"Kiyi ki shirya don Allah,kada azo daukan hoto bake a ciki"

"In sha Allah" ta amsa mata,wanda ita kanta tasan ta amsa mata ne kawai,amma sam yau bata sha'awar
fita ko nan da can. Harabar gidan gaba daya bata burgeta,ta tabbatar a yau din kusan labarin da zaiyi
trending cikin gidan shine labarin dawowar maina. Suna juyawa tana shirin maida qofar ta rufe tanja ta
qaraso

"Ama tace na dubaki kin tashi?"

"Na tashi tanja......don Allah tea nakeso me dumi sosai,madara da sugar kadan"

"Tea kawai?" Kanta ta gyada mata tana lumshe fararen idanunta,bakinta babu test kwata kwata,shima
tea din zata sha ne kawai maganin yunwa.

Tanja tana fita ta juya ciki ta soma zare kayanta ta fada wanka. Koda ta fito tanja ta aje mata tea
din,sai ta zauna ta fara kurba a hankali tana dumama cikinta. A hankali sai tunaninta ya koma daren
jiya,wata siririyar faduwar gaba ta ratsa qirjinta,ta maida idanunta ta lumshe tana son kauda surar
fuskarsa dake gilma idanunta. Benazeer da batoul ta tuna,wannan ya sanyata ajiye cup din a hankali,ta
jawo hijab ta zura ta nufi qofa. Tana gab da fita a dakin wata murya daga can qasan zuciyarta ta jefa
mata tambaya

"Idan kinje gurinsun me zakiyi?,zaki hanasu yawo ne bayan gidan cike yake da yara?,kada kiyi abinda
mutane ko shi kansa zaiyi tsammanin kin damu da sha'aninsa ne,bake daya ba,akwai dakaru a gabanki
da bai isa yace zaya dauki yaran ko ya aiwatar da wani abu ba" ajiyar zuciya me nauyi ta sauke sannan ta
dawo da baya jiki a salube,daga tsaye ta dauki tea din ta kurbe,saita koma wajen drawer dinta ta soma
duba kayan da zata saka, zuciyarta da tunaninta haka kawai ya raja'a akan yaran.
Tun asuba yayi alwala ya kuma fita sallar asuba kamar yadda kowanne namiji dake gidan yakeyi
tun gabanin barinsa gida,har kuma yanzun babu abinda ya sauya. Yana qoqarin fita daga makeken gate
din gidan sukayi kacibus da aba adan hanzarce,da alama shima yaso ya makara ne. Idanu suka hada da
aba din,sai ya janye idonsa tamkar ma baisan mainan ba,ya kuma qara taku ya wuceshi a sanda maina ke
yunqurin yi masa magana. Ajiyar zuciya me sanyi ya sauke yana lumshe ido hadi da budeshi,wannan
abun idan aba yana masa shi yana sanyashi jin tamkar zai mutu. Ba haka ya saba masa ba,a shekarun
baya kafin komai ya faru idan sukayi kacibus irin hakan da hannu yake masa nuni da ya matso,idan ya
matso din kuma sukan wuce masallaci tare da aba din kafada da kafada,a yanzu da yake ganin akasin
hakan sai yakejin kamar zuciyarsa zata tsinke daga qirjinsa,bazai iya jurar wannan halin ko in kula na aba
ba. A baya yaci gaba da bibiyarsa har suka isa masallacin,sanda aba ke qoqarin kafa sahu cikin zafin
nama ya tsaya daga gefansa,ya kuma daidaita sahunsa dana aba din. Yayi zaton zaiyi wani motsi amma
sai yaga ko daga kai ya dubeshi baiyi ba,tamkar ma baisan dashi suka hada sahu tare ba.

Suna idar da sallar aba din yadan ja gaba ya fita a sahun,sannan ya zauna sosai ya fara azkar din
daya zame masa.jiki duk safiya muddin yana da lafiya,idan kuma baya dan jin dadi yana komawa gida
yayi cikin falonsa balcony ko bedroom dinsa.

Daidaikun mutane da sukasan maina sai suka dinga matsowa suna gaisawa dashi tare da
tambayarsa yaushe ya dawo qasar,saidai ya danyi murmushi yace musu

"Jiya" yadda suka dinga masa barka ya alamta masa lallai sunyi zaton karatu ya tafi. A hankali a hankali
yana gaisawa dasu har zuwa sanda suka kammala,ya dan juya idonsa kadan ya saci kallon aba. Yadda
yake tun dazun har yanzu a haka yake a zaune,yaja numfashi sosai,sannan ya miqe cikin mazantaka ya
taka izuwa garesa.

A gabansa ya zube gwiwoyinsa,muryarsa cike da girmamawa da kuma rusunawa ya furta

"Barka da asuba aba" idan carbin dake hannunsa ya amsa shi shima haka,sai yaci gaba da jan tasbaharsa
baiko motsa ba bare maina ya sanya ran ya jishi. Sake maimaita gaisuwar yayi,wanda yana direta aba din
ya yunqura ya miqe yana durfafar qofa,baiyi qasa a gwiwa ba ya take masa baya,saidai kafin ya cimmasa
har ya sanya slippers dinsa masu tsananin taushi ya soma barin farfajiyar masallacin.
Dab da zai fita ya cimmasa,ya sake taresa karyar da wuya dama murya gaba daya

"Aba.......na roqeka don......"

"Bakaji abinda na gaya maka ba jiya?,kai wanne irin mahaukacin yaro ne?, meye alaqata da kai da zaka
dinga bibiyata haka?,ni bani da wani d'a me kamanceceniya dakai,ka fita daga harkata tun kafin na saka
hukuma su kamamin kai" yayi maganar a fusace yana nunashi da yatsa,sannan ya kewayeshi yana
wuceshi bayan yaja dogon tsaki. Sosai jikin maina yayi sanyi,abinda yake gani a idanun aba din me girma
ne,anya zaici gaba da tunkarar aba?,anya ba bibi bace kadai tsaninsa kaman yadda oncle issoufou ya
gaya masa?.

Cikin qarfin hali yaci gaba da takawa cikin gidan. Koda yakai bai koma sassansa ba sai ya zarce
sashen ama. Can dinma mutanen daya samu a sassanta wadanda suka tattashi sallah dukka basu koma
ba binsa suka dinga yi da kallon yaushe gamo?,ya gaisa da wadanda zai iya gaisawa dasu,ya tambayi bilki
me aikinta ta gaya masa yanzun ta shiga daki.

Sau uku yana knocking sannan ya murda qofar,bakinsa dauke da sallama,qasan zuciyarsa cike fal
da addu'a. Da ita ya fara tozali,tana zaune saman tattausan abun sallarta dinnan,jikinta sanye da ustazah
hijab da skirt dukkansu kala me haske. Tsananin tsafta da gayunta ya santa kusan komai nata me hasken
kala ne,sai dai daiku masu duhun kala. A nutse ya qaraso cikin dakin,ya kuma yiwa kansa mazauni a
qasan dandagaryar turkey carfet din dake malale a dakin wanda ya qarawa dakin kyau da kuma tsari.

Hannayenta a sama tana addu'a,sai shima ya buda nasa tafukan hannayen,sanda ta kammala
suka shafa a tare,sannan ta waiwayo suka hada idanu.

Kwarjinin nan nata yana nan,gaba daya fuskarta ta cika da hasken ibada sanin kima da martabar
kai. Wani lokaci su uncle abdulhakeem kan bata lokaci kan cecekucen kwarjinin da yayo gadonsa
yayi,amma basusan tsakanin hamid da hamdiyya waye yafi wani kwarjini ba?.

Sai data gama zuba masa dukka dafin kwarjinin idanunta sannan ta janye daga kallonsa.
Zuciyarta na hira a kansa ita kadai. Mainan nata ya girma,ya zama cikakken mutum wanda ta tabbatar
akwai maganganu masu yawa da labarai cikin tafiyarsa da kuma dawowarsa,saman kowacce fuska akwai
labari......cikin kuma kowanne littafi nan ma tasan akwai labari,amma a yanzu bata jin zata bashi wannan
qofar ko damar haka a kurkusa. Kaman yasan niyyan tashi ta bashi waje takeyi sai yayi caraf da dukka
hannayenta ya kuma hanata miqewar,koda ta daga kai ta kalleshi sai ta tsinci hawaye fal idanunsa. Kuka
a idanun aliyyu?,abinda zata iya cewa kaf rayuwarta bata taba gani ba,tun yana qaraminsa kuka abune
me wuya a wajensa bare kuma sanda ya mallaki hankalin kansa,yana da tsananin fushi kafiya da
zuciya,wannan ya sanya ko yara sa'anninsa basu fiya takalar fada dashi ba,idan kuwa kayi gangancin yin
hakan kaine zakasha qasa

"Don martabar fiyayyen halitta ama kada kiyimin haka,aba haka yakemin tun jiya,kema haka zakiyimin
ama?,idan duk duniya sun gaza fahimtata ama na dauka ke zaki riga kowa fahimtata,ke zaki fara sauke
fukafukan jin qanki a kaina ama?,ban tafi don wata manufa ba,banyi nesa daku saboda na rainaku
ba.....hasalima nayi nesa daku ne saboda kunyar keta maganarku......saboda kunyar na aikata abinda ya
kamata ace ya zama sirri ne tsakanina da ita saidai nayi ta yadda ya zai fita,na tafi ne saboda bansan da
idanun da zan kalleku ba,bansan da bakin da zanyi muku bayani ba......ama....... wallahi wallahi wallahi
ban tafi da nufin na tafi daga gareku kenan gaba daya ba.......na tafi ne da niyyar idan kun huce zan
dawo......a raina ban taba sakawa zan tafi nayi koda wata guda ba.......sai kuma gashi komai ya
sauya......ina biye daku ama......ina biye da duk wani motsinku ama.......ban yanke daga shiga rayuwar
sultana tare da sanin hakinda take ciki ba ama......amma kuma saidai a cikin tarko nake......ina cikin wani
dauri da muddin na bayyana a gareku rayuwata na cikin hadarin da bani da gatan da zai fiddani....
Lokacin kuma da nake tunanin na zama free......ina da 'yanci sai yayi dai dai da lokacin da zan cika BURIN
ABA.....MAFARKIN ABA.....burin dana tabbata a duk sanda na bayyana a gabanki babu shi kema zaki
qalubalanceni BABBAN LIKITAN ZUCIYA kuma DAN KASUWA CIKAKKE.....Na hadu da jarrabawar da na
tabbatar barinku ne sila......na kuma hadu da lalurar da afuwarku da kuma yafiyarku ne kawai zai bani
maganinta......" Hannu ta daga masa tana yin qasa da kanta,batason yaga zallar rauni da karaya daya
zubawa zuciyarta,batason yaga tausayin daya lullube qirjinta,irin tausayin da dukka uwa keji akan d'anta
komai girman laifi ko kuskurensa,saboda kasantuwar zuciyar mahaifiya ta banbanta da zukatan mutane
gaba daya,koda kuwa ita wannan uwar wata halitta ce daban bata dan adam ba......

"Banason naji komai daya faru dakai,koda zanjin zanji ne a tare a kuma lokaci guda da mahaifinka,kaje ka
nema yarda mutum ukunnan.......sannan ka dawo gareni" sai ta zame hannunta tana miqewa.

Shima bai zauna din ba sai ya miqe yayi tsaye yana kallonta tana barin dakin

"Kiyimin alfarmar amsa gaisuwata ama.....koda iya ita kadai na roqeki" har ya fidda rai don takawa take
tana barin dakin,kamar kuma ba zata amsa ba,dab da zata fita din tace masa
"Nayi maka" cikin dubunnan nauyikan dake qirjinsa yaji kaman an cire daya,ya fesar da iska me nauyin
gaske da ya fusgota daga cikin cikinsa yana aza tafin hannunsa saman fuskarsa wani farinciki yana dan
ratsashi,sa'annan yana jin qwarin gwiwarsa ya sake qaruwa. Sai daya ji ya nutsu sannan ya soma fita a
dakin,cikin takunsa me cike da qasaita,saidai kuma a yau din a sanyaye yake takawar.

Bangaren bibi ya nufata kai tsaye,shikam a yau yakeson gamawa da bibi din,don dama bai
azata a ma'aunin matsala ba,ya duba agogo dab da zai shiga sashen,ya kwasarwa drama dinta awa daya
kacal,don yanason ya koma bangarensa ya sake runtsawa koda na awa daya ne sannan ya shirya ya
fito,don yanason ayi daurin auren 'yan uwansa dashi.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[11/06, 8:34 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

Book 02 page 56
A falo ya sameta riqe da tasbaharta da masu aikin sassanta. Cikin girmamawa suka gaidashi
sauran da jiya basu ganshi ba sai yanzu sunata satar kallonsa hadi da mamakin ganinsa da sauyawarsa
lokaci guda. Da daya da daya suka zame a falon kamar yadda suka saba a baya,sai ya zamana daga shi sai
ita a falon. Zamowa yayi ya zauna a gabanta yana dan matsa mata qafafunta daya tabbatar suna dan
mata ciwo kadan kadan,ya kuma fahimci haka ne a rigimarsu ta jiya. Saurin janye qafafun nata tayi tana
jifansa da harara,yayi amfani da wannan damar ya sakar mata murmushi sannan yace

"Barka da safiya da fatan kin tashi lafiya uwar gida ran gida" harara ta sake jefa masa tana hade rai da
gaske

"Kaga ka fita a ido na,ni ba sa'ar wasanka bace,uwarka da ubanka ma duka basu isheni kallo ba bare kai
mara kunya fitsararre" tana kaiwa qarshe ta fara yunqurin tashi,bai hanata ba,ta miqe tsam ta wuce
bedroom dinta tana mita kaman zata ari baki. Biye yake da ita bata sani ba,sai data shiga dakin tana
shirin maida qofa ya shigo

"Me ka shigo yimin daki?"

"Ba komai,nazo mu fahimci juna ni dake"

"Lallai aliyu raini ya shigo tsakaninmu,waishin me yasa baka tunkari uwarka da ubanka ba?,sai khadeeja
marainiyar wayonka ko?,to na fika tijara" daga haka ta samu waje tayi zamanta. Qarasowa yayi gabanta
ya zauna,duk wani yanayi da yasan zai bata ta tausaya masa amma taqi ma kulashi bare ya sanya ran
samun wani ci gaba. Zuwa lokacin har maqoshinsa ya bushe kasancewarsa mutum bame yawan son
dogon magana ba,yaja numfashi yana lumshe idonsa,qirjinsa wani zafi zafi yakeyi yi masa,ya kallo agogo
yaga yana shirin cinye awa dayan da ya bawa bibi amma babu canji.

Tsam ya miqe yana tattare hannun rigarsa idonsa a kanta


"Allah ya gani nayi duk yadda zanyi na fahimtar dake kinqi fahimtata,shikenan zan tafi......kuma idan na
tafin bawai zaki sake ganina bane,ba zaki sake ganina na ba har abada" yana fadin haka ya soma takawa.
Da idanu ta bishi zuciyarta na rawa,tasan halinsa,aliyyu ne ba wani ba,komai ya fada yana aiwatar
dashi,tsanani ko wahala basa sanyashi sauyawa,yana gab da fita taji bakinta ya fusgi kalmar

"Ina zaka?" Cak ya tsaya yana jin ranshi yana masa dadi,bai waiwayo ba yace da ita

"Zan koma inda na fito mana,tunda dukkanku kunqi bani dama na fadi abinda nakeson fada din"

"Yo kaje mana,me jiya tayi ballantana yau......" Bai bari ta qarasa ba ya sanya qafarsa daya waje,sai
kalaman nata suka sauya da

"Amma dai kasan hukuncin me bijirewa iyayensa ko?,kasan hukuncin gudajjen bawa ma bare gudajjen
d'a ga iyayensa" idonsa ya lumshe hawaye na taruwar masa,ya godewa Allah.......tabbas ya samu baiwar
soyayya daga iyaye da 'yan uwansa,wannan reaction din kawai na bibi ya bashi qwarin gwiwa matuqa
fiye da kowacce sa'a da daqiqa,yasan a yanzun ya cimma kaso hamsin cikin dari,hamsin kadai ya rage
masa,shima kuma yasan ta yadda zaya biyo masa. Dawowa yayi da baya cikin wani irin sanyi da ita kanta
bibi ta lura dashi,tsugunnawa yayi a gabanta ya sanya fuskarsa tsakiyar hannayenta daya kama

"Ku yafemin bibi,ku yafemin.....na tafi na barku tsahon shekaru bayan nidin me laifi ne a wajenku" sanyi
jikinta yayi sosai da taji damshin hawayen aliyyu,ganin fitar hawaye a idonsa ba qanqanin lamarj
bane,sai dai ita dinma tanaji a zuciyarta bai kamata tanuna masa goyon baya ko.karaya tun yanzu yanzu
ba,don haka ta janye hannayenta tana cewa

"Ka tashi kaje kaci gaba da neman afuwar wadanda sukafi cancanta,zamu qarasa magana ko zuwa
anjima" bayan hannunta kawai ya juya ya sumbanta ya miqe a nutse yana ficewa batare da sake cewa
komai ba,don zuciyarsa tayi nauyi,bata yadda zai iya sake cewa wani abu.

Tunda sukaga dinkin dogayen rigunan atamfar da akayi musu da zasu sanya ranar daurin auren
suketa tsalle da murna,hakanan suka dami ama da cewa ranar yaushe za'a saka wannan kayan?. Tana
sane take tambayarsu sunan kayan don bakinsu bai iya fadin ATAMFA da kyau ba,saboda bawai saninta
sukayi sosai ba,saidai suyita qoqarin pronouncing dinta da suna kala kala,ama kuma tayita dariya. Suna
daya daga cikin ababen dake sanyata nishadi da debe mata kewa da damuwa qwarai,a yanzun cikun
rayuwarta bata jin akwai wani abu na biyunsu me daraja a gurinta,ko almu atta da saddi dai kawai ta
haifesu ne,amma soyayyar benazeer da batoul daban take a ranta,bama ita daya ba,duk wanda ya kalli
yaran haka kawai sai Allah ya jarabceshi da sonsu,suna da matuqar maqurar shiga rai.

Tun takwas na safe suke zaune a dakinta suna jiran ta shiryasu cikin kayansu da qananun
mayafai masu tsada data musu order tun daga dubai,hakanan qananun hand bags nasu hade sukazo da
takalmansu na musamman data zabi wanda za'a yi musun,kuma dukka samples ne na kayan da take
zubawa a qatoton boutique dinta dake dauke da kaya designers a garuruwa daban daban.

Dole ta ajjiye kudin da take sanyawa yaran da zasu yi mata clearance din kayanta ta dauki waya
ta kira tanja tace ta shiryasu. Nan ma wajen wanda za'a fara yiwa wanka suka gama fadace fadace,anayi
ana rigima a haka tanja ta gama shiryasu. Ita kanta tanja baya taja tana kallan yaran tare da tsarkake
girma da buwayar ubangiji daya samar da yaran cikin taqaitaccen lokaci cikin mahaifar mahaifiyarsu,ya
kuma basu tsaro da kariya,sannan aka haifesu da wani irin kwarjini farinjini da kyau. Dariyar yadda
suketa kallon kansu kayan na burgesu ta dinga yi,kana ganin yadda sukeyi kasan sanya atamfar ba
sabonsu bane.

Ana tsaka da fadan sanya turare wanda ama ta riga ta saba musu da sanyashi goumar yayi
sallama yana murda qofar,yazo kuwa a dai dai,duk sai suka watsar da turarukan suka ruga wajensa suna
masa oyoyo

"Maaa shaaaa Allahhhhhh BB na.......wai,wai wai" ya fadi saboda yadda kwalliyar tayima yaran kyau
qwarai yana bude musu hannayensa. A tare suka isa suka fada,ya hadasu ya rungume. Benazeer ce ta
fara mitan ya tafi ya barsu yau kwana wajen biyu,yadan saki dariya kadan yana lakuce bakinta data
turo,shima sultana yake gani a yawancin lokuta,amma kuma lokaci bayan lokaci idan tayi wani abun dan
uwansa MAINA take tuna masa

"Yanzun ai gashi na dawo ko?,am back"

"Ayi mana hoto,dama ama tace sai ka dawo"

"Tom an gama,kwana biyu nayi checking account dinku banga ama ta saka mana update na african twins
BB ba" .
A gaba ya sanyasu,yau kowacce taqi yarda ya dauketa wai kada ya bata mata kwalliya,su a dole
ga 'yammata. Ta baya can ya fita dasu,don ya tabbatar idan yabi dasu ta gaban gidan yadda sukayi kyau
haka za'a bata musu loakcine,kuma ba za'a barshi ya musu hoton da kyau ba.

Cikin rumfar da aba ya sanya aka yiwa bibi saboda zama lokacin zafi suka tsaya. Guri ne da aka
qawatashi sosai da zubin ginin gargajiyar qasar nijer,ya tabbata wajen zai bada background me kyau.

A nutse suka fara hotunan,kowanne idan ya dauka sai yaga yafi dayan kyau,suka gama tsaf,sai
ya samu kujera daya a wajen ya zauna yana duba duka hotunan zai turama ama ta watsapp.

Hannayensa dukka zube cikin aljihun rigarshi yake takawa a nutse,sassalkan gashinsa dinnan
me santsi da duhu yadan cakude kadan saboda baiyi combing nasa ba bayan yayi alwala. Yanayin da
zuciyarsa ke ciki ya sanya fuskarsa ta danyi ja kadan,hakanan idanunsa daketa qoqarin saye abinda ke
yawo a qirjinsa. Duk yana jin ba dadi cikin jikinsa,saboda ya saba kowanne lokaci kusan warhaka ya dawo
daga gym ne yana shaqar daddadar iskar balcony din dake gaban dakinsa,a yanzu duk sai kasala da
yanayin da zuciyarsa ke ciki suke son kashe masa jiki.

Kamar a iska yake jiyo muryoyinsu,yana ci gaba da takawa yana kasa kunnensa don yanason
tabbatarwa muryar yaranne ko ba nasu ba?,yana tsoron kada tsananin damuwa da yaran da ba nashi
ba,baisan me yaran waye ba ya sanya su fara shiga rayuwarsa har haka?,kada ya soma halin da ba nashi
ba wato damuwa da abinda bai shafeshi ba.

Yana sake kusanto wajen yana sake jin tashin muryarsu,a hankali a hankali kamar almara sai ya
fara hangensu yana kuma dab da isa inda suke.

Suna tsaye su biyun suna gwada yin selfie, benazeer ta matse batoul da yawa, batoul din na
mita tana qoqarin banbare hannun benazeer daga wuyanta. Ta samu sa'a kuwa ta cire din,sai taja da
baya tana tura baki gaba hadi da hararta
"Kina gani kina shaqemin wuyana?....bazanyi hoton ba ai uncle........." Bata iya qarasawa ba saboda dan
juyawar da tayin idanunta ya fada kan maina. Dukka idanunta ta fiddo waje kamar zasu fado,ba wani
jiran komai ta qwala kiran sunansa

"Uncle haidar!!!!....... benazeer kinga......zo kiga uncle haidar a gidanmu......" Da wani mugun sauri
benazeer din ta juyo kuwa tana jin daukin ganinsa, zuciyarta na raya mata qarya batoul keyi mata. Bata
iya jiran benazeer ba ta kwasa da gudu tana tattare doguwar rigarta ta nufeshi tana jin wani irin farinciki.

Da siririyar muryarta itama ta kwatsa wata irin ihu,abun tana jinsa kamar a carton da suke
kalla,sannan ta diba da gudu itama tayi kansa LOKACIN tuni batoul ta dade a jikinsa,harfa fara qwallar da
ita kanta batasan dalilinta ba.

Qarar batoul ita ta fara zuwa kunnenta,ta kuma ji qarar kamar daga baya wajen window din
dakinta,taja qaramin tsaki,yaran sun sake da yawa,tabaransu kawai sukeyi cikin gidan,kowa soyayya
qauna da kulawa yake basu,tana tsoron su sangarce da yawa da ganin yawan gatan da suke samu,saita
ware dankwalinta tana daurawa da zummar idan ta fita zata kirasu taja musu kunne da kokaye kokayen
banza,su nutsu cikin mutane suke. Saidai kuma bata sauke wannan tunanin ba muryar benazeer ta sake
iskota. Dogon tsaki ta saki tana soke daurin dankwalin gefen kanta ta juya ta nufi window din ranta adan
bace da ihun da suke sakima mutane.

Da zafin nama ta zuge labulen,saidai kuma abinda idonta ya gane matan ya kusa sanyata
sulalewa a qasa. Benazeer da batoul rungume da maina,wata irin runguma dake nuna zallar shauqi da
tsumammiyar qauna dake tasowa daga zukatan iyaye,ya dagasu daga jikinsa yana riqe da
hannayensu,fuskarsa na fidda wani irin murmushi kaman yadda idanunsa ke jifansu da wani irin kallo na
tausasawa.

Tambaya yakeson musu kamar yadda suma suka cikashi da tambayoyin,to amma sai yakejin
cikin jikinsa kamar akwai wani idon dake kallonsa,tashin farko kuma idon nasa ya canki daga inda ake
kallon nasa.

Sake haduwa idanunsu sukayi a karo na biyu,ko second biyu cikakke bata qara ba ta saki
labulen da hanzari tana komawa da baya,zuciyarta na wani irin mahaukacin bugu kamar zata fito daga
qirjinta,yayin da ranta ke mata wani suya
Meye hadinsa dasu?

Yaushe ya sansu?

Waye ya shaida masa su din yaransa ne?

Don me zai shiga rayuwarsu?

Shin ance masa suna sa buqatarsa?

Dukka tambayoyin da takewa kanta kenan a zafafe ba tare da samun wanda zai amsa mata ba.

*_muje zuwa_*

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[11/06, 8:34 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 57

https://chat.whatsapp.com/IQ6XVJntkTj5FFJ66euAIR

Hey everyone.. Assalamu Alaikum. let's build our business together. join our whatsapp group, ladies only

Zamu kawo kwararru a bangaren business da zasu yi mana bayanin yadda suka samu cigaba a
kasuwancin su,yaya zaka yi tallan kayan ki online ki saida online, ta ya zaki samu riba a kasuwancin ki?
Yaya ake marketing da branding da sauran su.

Wanda kuma suke son fara sana'ar amma basu san taya ba, in sha Allah you will find something to start
with

Lets grow together.

______________________________

Har ta zame tabar wajen bai daina kallon window din ba,shi kadai yasan me yakeji a zuciyarsa
game da ita,yadda tausayinta yayi shekara da shekaru yana masa didibniya cikin zuciyarsa shi kadai
yasan yadda ya luguiguta shi,ya kuma yi masa kyakkyawan kamun da zuciyarsa tayi wani mugun laushi.
Takun goumar shine ya ja hankalinsa yadan dauke idanunsa daga wajen ya maida ga goumar din,suka
hada idanu sai goumar din ya sakarwa maina murmushi,murmushin dake nuna tsananin farincikin dake
kwance qasan zuciyarsa da dawowar dan uwansa cikin ahalinsa
"Ya maina....bansan a irin wannan lokacin ka shirya dawowa ba ai,da banyi nesa ba,da na zama mutum
na farko da zan dauko ka na kawoka cikin gidan.

Harara ya jefeshi da ita da lion eyes dinnan nasa,dole goumar yadan dauke dubansa daga cikin
nasa saboda yadda idanun sukayi masa kwarjini

"Kayimin dukka qoqari goumar,amma kuma daga qarshe ka yanke alaqata dakai,ka barni ni kadai ins
fakan fakan.......ba uwa ba uba ba mata......ka hanani ganin fuskar yaro na fafur......ko sunansa ka hanani
sani bayan ina cikin asibitin ranar da za'a fiddoshi daga ciki" idanu goumar ya dora kansu benazeer,da
alama har yanzu bai samu masaniyar sune 'ya'yan nasa ba,sune wadanda cikinsu yazo cikin gagggawa
zazzafan rabo wanda ko cikin tarihi ba'a fiya samun irinsa ba,yaji dadin hakan,zai kuma ci gaba da wasa
ba hankalinsa har sai yaji ciwo cikinnzuciyarsa shima,yanason a ranar da zai san su benazeer yaransa ne
yasan hakan yana jin ciwon shekarun da ya dauka yana mutuwar sonsu ba tare da yasan mallakinsa bane
su

"Yanzun tunda ka dawo ai zaka san komai ba?"

"Ina d'ana goumar?,inason ganinsa,na tabbatar duk gidan nan babu me yimin maganarsa,kai kadaine
nake da fata a kanka" tsaiwarsa goumar ya gyara yana harde hannunsa a qirjinsa

"Yaronnan baya cikin gidan nan yanzu haka, infact ma banjin yana nijer gaba daya"

"Nigeria suka kaishi?" Ya jefawa goumar tambayar cikin damuwa,har hakan ya bayyana qarara saman
fuskarsa

"Ban sani ba,but amma zan tambayi ama naji" miqewa tsaye maina yayi,har yanzu suna riqe da hannun
juna shi dasu benazeer

"Alright......akwai maganganu da yawa da nakeso mu tattauna,inason nasan abubuwa da yawa bayan


wadanda na sani akan sultana"
"Saboda me?" Goumar ya jefa masa tambayar. Kallon da maina din ya jefa masa ya sanyashi shiga
taitayinsa,ya kuma tuna cewa har yanzun fa shine din dai ALIYYU MAINA HAIDAR ba abinda ya canza
daga wancan halin nasa,don haka ya gyara zancansa cikin basarwa

"Sanin komai akan sultana yana da tsada matuqa,nawa ne farashin?"

"Daga million daya har million goma kayi requesting......zaka sameta cikin account dinka" yayi maganar
yana fidda wayarsa saboda shigowar kira. Goumar yana dariya shi kuma dukka hankalinsa yana kan
wayar.

Yana jin nauyin yaqi daga wayarta amma kuma ya rasa me yasa ta gaza fahimtar take takensa
ta yiwa kanta fassara ba tare data wahalar da kanta har haka ba?. Daddy da sardauna mutanene da
bazai taba iya butulce musu ba......bazai kuma taba iya wulaqanta jininsu ba,don haka ya danne
zuciyarsa da duk wani emotion nashi ya daga kiran

"Hello.......Yaa maina kana jina?" Ta furta daga can bangaren murya can qasa

"Ina jinki laila.......ya akayi?" Zamewa tayi sosai ta kwanta daga can inda take tana narkewa,iya sautin
muryarsa kadai yana tafiyar da dukka damuwarta ya qara mata walwala da kuzari,yana da wani irin
husky voice dake ratsa zuciya qwarai da tunani,wani lokaci recording takeyi na taqaitacciyar hirarsu
tayita kunnata tana saurara duk sanda take tsananin kewarsa kaman haka. Ta fahimci yana cikin jerin
sahun mazan da su baki lokacinsu abune dake musu wuya,duk da ta bayyana kanta bata tsaya boye boye
ba,amma hakan bataga ya canza wata mu'amala a tsakaninsu ba,abinda har kullum yake sanyata
kokwanto

"Ya akayi kuma yaa maina?,bayan ka wuce nijer ka manta dani?,last wayarmu kace zaka kirani amma
shuruuu" boyayyar ajiyar zuciya ya sauke,bata qaunar saba alqawari ko kadan,amma shi sam ya manta
ma sunyi zaiyi kiran nata. Yanayin da yake ciki yanzu yana buqatar lokaci da kuma nutsuwa,don haka ya
gyara tsaiwarsa
"Afwan na saba alqawari,amma ina cikin wani muhimmin aiki dana tabbata sardauna zai iya dan gaya
miki muhimmancinsa a taqaice,ina tare da family na muna kashe wani issue......amma in sha Allah idan
na zama normal zamuyi waya" sosai maganar tasa tayi mata wani iri,amma da yake ita din me yawan
bada uzuri ce sai ta gyada kai

"Tou yayi...... Allah ya taimaka,i missed you"

"Thanks,but......kina iya kira duk sanda kk buqatar hakan" ya fadi don ya sassauta mata abinda ke yawo a
zuciyarta,don ya fahimci kaman maganar batayi mata dadi ba

"Na gode da wannan karramawar"

"U r welcome" ya sake fada yana katse wayar ya jefata a aljihu.

Idanu suka hada da goumar,sai yadan dauke kai kaman baiji wayarsa ba

"Yaran waye a family dinnan?" Ya jefawa goumar tambayar da baiyi zato ba. Idanu kadan ya zuba masa
yana tunanin amsar da zai bashi,sai kuma ya janye yana cewa

"Ba zakasan waye mama da babansu ba saina zauna na maka bayani,kuma qilan ka manta fuskarsu ma
yanzun.......zan wuce dasu na maidasu kada ayita nemansu ansan tare muka fito" ya fada yana riqe
hannun batoul da tafi kusa dashi. Idanu ya sakawa goumar din yana jin kamar maganar tasa bata hau
ma'auni ba,tunani ne iri iri cikin kansa,don haka ya ture wannan,ya durqusa a tausashe yayi kissing
goshinsu daya da daya sannan ya dubesu yana murmushi

"Zan shirya zan fito..... anjima akwai shan ice cream?" Ya tambaya yana kallon fuskar benazeer. Qaramin
ihun murna ta saki tana tsalle,sai batoul itama tabi sahu,don itama wannan karon sosai takejin dadin
ganin uncle haidar din,har bataso yabar inda suke. Tare suka wuce da goumar sunata bashi labarin
haduwarsu a makka,tausayinsu su dukka ya dinga ratsashi,ya dinga jin kamar ya koma ya bayyana musu
gaskiyar su din waye wa junansu?,amma kuma sai yaji bai kamata yasan yaran su waye a wajensa ta
cikin sauqi ba.
Ya samu kira daga wajen najjashi mutumin da sardauna ya hadashi dashi don ya masa hidima
yana tambayarsa ko yana buqatar breakfast ko wani abu me kama da haka?,yace masa a'ah,don ya samu
almu ya shirya masa breakfast din,komai da komai,yayi tsaye yana mamakin yadda almu zai iya shirya
abinci sosai kaman haka,amma kuma daya dinga qarewa salon jera kwanukan kallo da kuma yadda aka
shirya abincin sai yaji jikinsa yana bashi tabbas daga hannun ama aka aiko dasu.

Ya debi abincin yaci sama sama don bai fiya cin abu me nauyi da safe da kuma dare ba,ya wuce
bandaki yayi wankansa na kusan minti talatin yadda ya saba,sannan ya fito ya shirya.

Cikin wata shegiyan danyar gezna off-white ya shirya kansa,sai maiqo take da daukan
idanu,dinkin babbar riga wanda da 'yar ciki,hular daya sanya a kansa baqa ce wadda ta dace da rufaffen
baqin takalmin qafarsa me matuqar kyau da jan hankali qirar kamfanin WEITZMAN,fatarsa kawai idan ka
kalla zakasan ba qananun kudi ne suka mallaka masa shi ba. Sassanyan turarensan nan daya kasa
rabuwa dashi tsahon shekaru......sai kamfani kawai daya sauya amma da dsame qamshin shi ya
fesa,yana fesawar yana kallon fuskarsa cikin mudubi. Tabbas shekaru ba qarya bane,a yanzun fuskarsa
kadai ta zama cikakkiya wadda ke bayyana zuwan gejin girma da hankali a tare dashi,ya ajjiye turaren
yana qoqarin daura agogon fatar kamfanin blancpain sai yaji muryoyi a falonsa. Ko bai fita ba yasan
cousins nasa ne,daga bangaren aba da ama gaba daya. Baima gama tunanin ba yaji ana knocking qofan
bedroom din. Muryar attahir ne,ya lumshe ido yana murmushi kana ya budesu saman madubi,attahir
sunsan juna kaman yadda sukasan yunwar cikinsu,abokin fadanshi abokin adawarsa,shi fushi da zuciya
attahir kuma tsokana,haka zasuyita bugata saidai idan baije nigeria ba,d'a ne ga uncle abdulhakeem
babban d'ansa ATTAHIR ABDULHAKEEM ME KANO.

"Malam kada ka balla min qofa fa?" Ya fada yana gyara zaman agogon a hannunsa

"Idan kaqi fitowa tsaf zamu balla qofar......." Muryar bilal ya ratsa ta attahir. Dole murmushi ya subuce
masa,ya zari handkerchief ya fito.

Dukkansu cousin nasa ne kaman yadda yayi zato daga bangaren aba din da ama,kuma
dukkansu sa'anin haihuwarsa ne da kusan tare aka taso. Dukkansu kaman dai shi,sun zama cikakkun
samari,wasu a cikinsu ma basu jima da angwancewa ba. Rudu iya rudu suka hada a falon nasa,don ma
dai shi din ba gwanin magana bane amma duk da haka sai da sukayi yadda suka saba,sannan daga
qarshe suka fice can masallaci suna takawa da qafafunsu domin shaida daurin auren. Kafin sukai ga fita
din haka ya dinga bi yana gaida kowa,kowa kuma barka da dawowa yake masa,a haka suka isa
masallacin suka kuma hade da tawagar angwaye suka tsaya karbar daurin auren.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_


09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[13/06, 10:18 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 58

Kusan duk inda suka gilma sai sun debi kallon jama'a,kana ganinsu zakasan samari ne masu jini a
jika wadanda ilimi da hutu suka ratsasu,amma duk da hakan daban maina ya fita a cikinsu,saboda yadan
fisu tsaho da kauri hakanan sumarsa tafi tasu nannadewa,kaman yadda fatarsa ta dara tasu gogewa.
Cikin qasa da minti talatin aka kammala siga aka daura aure,sauran hidimomi ne suka biyo baya
kafin daga bisani a wuce babban hall na gidan da aka ginashi musamman saboda lokaci irin wannan.
Reception sukayi a ciki wanda family din MAYAK'I suka shirya,kusan duk biki suna yiwa dangin ango
wannan karramawar komai wadatarsu kuwa. Daga nan cikin gidan suka yi don gaida iyayen amarya.

Tana idar da sallar azahar houda na sanyo kai cikin dakin

"Ki fito za'a yi hoton family......ama tace nayi kiranki" kusan hoton hotone me muhimmanci ga dukkan
dan gidan,don ana maidashi enlargement ne a ajjiyesu,kuma kowanne biki kusan sai anyi hakan.

"Kice mata bana danjin dadi....."

"Kinsan Allah saikin fito, bazanje na gaya mata ba" houda ta fadi kanta tsaye tana jawo mata mayafinta.
Ko kadan bata qaunar fita farfajiyar gidan saboda dalilai biyu na farko bata son ta ganshi sam sam,duk da
tana ji a jikinta zai wuya ta sameshi a wajen saboda shi din bamai shiga ire iren wadannan abubuwan
bane,na biyu kuma bata qaunar kallo,ta rasa wanne irin kallo ne mutane ke binta dashi haka?,kamar ita
daya ce Diya cikin dangin?.

Gaban madubi ta tsaya ta shafa powder ta maida lipgloss din da houda ta matso mata,sannan ta
maida daurinta ta lulluba mayafinta a saman ka

"Kin saje da amaren ai wannan" houda ta fadi tana dariya,harara ta balla mata

"Zan fasa wallahi"

"Na tuba" ta maida mata amsar dai tana dariya. Plate shoe ta saka wanda ya dace qwarai da kayan
jikinta,ta fito suka jera da houda din.

Duk inda ta gifta sai an Mata magana,wasu sunata mamaki dama tana ciki?,tana amsa musu da
eh ta tashi ne yau bata jin dadi,da haka da haka sannu sannu har suka fara fita qatuwar harabar gidan.
Tanata raba idanu taga benazeer ko batoul amma babu wanda ta gani a wajen,harma ta haqura ta koma
hirar da houda ke mata tana biye mata.

Qoqarin saita tsarin hoton akeyi yana daga zaune saman kujerun dake wajen yana maidawa
suhail reply din saqon daya turo masa,yana gaya masa yana sanya ran shigowa NIJER nan da kwana uku.
Ya san suhail din nada family a nan amma ba masu yawa ba,to sai bai saki jiki sunyi wani hirarsu ba
saboda bayason Susan daga wanne yanki ya fito,yasan kuma zaiyi wahala ya ambaci family dinshi suhail
din bai sani ba duk da ba wai yana yawan shigowa bane. Har tsakiyar kansa yake jin hayaniyar tana
damunsa,banda son ya farantawa su bibi da aba dake wajen da tuni ya fice yabar wajen,don kwata
kwata kanshi baya iya daukar hayaniya haka.

Shigowarsu wajen sai ya zamana kamar sun taho da daukewar surutun dake tashi a wajen. Baya
ga shirun da baisan meye ya haifar da shi ba,cikin jikinsa ya dinga jin wani baqon yanayi,tilas yadan
dauke idanunsa daga fuskar wayar yana maidashi cikin farfajiyar wajen.

Gani daya biyu ana uku idanunsa suka fada kanta. Dan mitsitsin bakin nan dake dauke da wasu
irin pink lips......bakin daya saba da tsiwa a baya yana motsawa a hankali tamkar bataso,ta zube fararen
idanunta akan fuskar houda da alama wani magana suke me muhimmanci a wajensu.

Wani irin zuzzurfan kallo ya samu kansa da yi mata,yana karantar kowanne motsi nata. A nutse
ta jingina da wata qaramar bishiya dake a wajen ta kuma goye hannayenta a qirji, kyawawan fararen
idanun nata nata da abaya yasan ta qware wajen yin fari dasu idan tana jin rashin kunya a yanzun sun
rusuna qwarai,sun zama wasu irin lumsassun idanuwa dake qawace da eyelashes,sun kuma qara girma
kewayayyun idanun masu dauke da fararen qwayar idanuwa. Kwantaccen gashinnan da ya sani a gefe da
gefen kunnenta zuwa gaban goshinsa ya sake qawata fuskarta qwarai,ya sake cika da sake kwanciya luf
luf abinda ya zame mata kamar wani adon dawisu.

Yadda ta nutsu tana sauraron houda kadai ya isa ya gaya maka tarin nutsuwa da rayuwarta ta
samu,zallar aji da kamala dake tattare da ita. Gyara zamanshi yayi sosai cikin kujerar,sam yama manta da
waje ko muhallin da yake,don sai yanzunne yakema sultanar kallon tsanaki kuma kallon tsaf,yake kuma
ganin canji ga rayuwarta me mugun nisan tazara,irin sauyin da yayi mata kwadayin samu,irin canjin da ya
dinga fatan ta samu,amma kuma komai sai ya sauya,komai sai yazo ta bahaguwar hanyar da baiyi zato
ba.
Gilmawar wani ta gabansu da kuma dawowarsa gurin tsaiwarsa yaja hankalinsa. A nutse ya
maida dubansa sashen,har zaya dauke kai saboda baiga wani abun kallo a wajen ba sai idanunsa suka
hango masa mutum uku cikinsu. Mutum ukun da suka hade kai waje guda suna qus qus,dukkansu
idanunsu suna inda houda da sultana ke tsaye. Tashi yayi ya zauna sosai sanda zuciyarsa ta fara
bugawa,adadin gudunta yana son ya sauya daga yadda qa'idarsa yake. Kallo suke mata irin kallon nan da
ake kira na qurilla

"Hasbunallahu wani'imal wakil" ya fada yana jin yadda numfashinsa yake rawa. Ko shakka babu ita suke
kallo,maganarta kuma sukeyi,yana da saurin fahimta da kuma nacin gane me kake fadi koda daga nesa
ne ta hanyar karantar motsawar labbanka. Ya fuskanci shirin tunkararta suke ba shiri ya miqe don baya
jin zai iya tsaiwa ya kallesu koda a gefenta ne bare suyi mata magana,bayajin zai kasa taka musu burki
koda kowa zaiji bai cancani yayi hakan ba.

Murmushi ne ya kubce daga fuskar Goumar wanda ya gama karantar komai daga fuskar
maina,duk kuwa da cewa yana nesa kadan daga inda yake din,ba kuma lallai ya ganshi. Wani irin
zazzafan abu yake gani a fuskar maina din,mahaukacin baqin kishi,tun kafin yau,tun yana haidar dinsa
dan makaranta a niamy.....tun yana saurayinsa me qananun shekaru dama mutum ne shi me matuqar
kishi na gaske,wannan dalili ya sanya yayi ruwa yayuntsaki wajen kula da tarbiyyar qannensa mata
kamar me?......wannan dalili ya sanya tyj suna da qananunnshekaru ya haranta musu sanya qananun
kaya saidai atamfa da manyan riguna masu rufe jiki......wannan dalili kuma still shine ya zama silar
samun rashin jittuwa tsana da qiyayya me gurma tsakaninsa da SULTANA.....yana kishin dukka yan
uwansa mata qwarai,yayin da ita kuma sultana take kallon hakan a matsayin takurawa da kuma
tsangwama,don a sannan hankalinta baikai ta gamo girma da matsayin gatan da yakeyi musu ba.

Taku biyu kacal yayi sai ya hangi goumar har ya isa gabansu sultana din. Maganar da takewa
houda ta katse,ta daga kai tana duban goumar da kallo me kama da hararara harara

"Me kuma ya faru?" Ta jefa masa tambayar tana hade girar sama data qasa. Tun kafin ma ta ajjiye
harshenta maganar data tsani ya fada mata ita ya gaya matan

"Kefa matar wani ce,duk wajen nan kuma kusan mazan wajen ke suke kallo" sosai ranta ya baci,yakai
qololuwar baci ma

"Baqin buzu......wai oncle umar baiyi mana tsakani dakai ba?"


"Don yayi mana tsakani saina tsaya na kasa tunasar dake girman nauyi da haqqin dake kanki?"

"Nauyi?,haqqi?, dukka na waye?,ba haqqin kowa kaina, goumar ka dameni......ka shafamin lafiya,wai
idan nace aure zan daura yau ko gobe ka isa ka hanani?" Shi dinma dan uwan maina dinne wajen
kishi,maganar tata sai yaji ta zafafeshi tamkar shike da igiyar auren nata a hannunsa

"Baki isa ba.....kema kin sani,saidai kiyi aure akan aure,wanda kuma badai cikin family dinnan ba"

"Haka kace?,zaka gani kuwa yanzu,badai taqamarka igiyarsa ba?,to yau zata zo qarshe naga da meye
zakamin taqama" ta fadi a zafafe sannan ta zagaye houda tana nufar hanyar ficewa,tanata qoqarin riqe
fushi da hawayenta amma ta kasa,ita kanta batasan meye ya zafafi zuciyarta har haka ba.

Bayanta houda tabi tana kiranta, kiran nata da takeyi sai taji ya qarasa karya mata gwiwa,don
haka ta soma takawa da sasaarfa tanason kubucewa ganinta.

Tunda aba da oncle issoufou suka nufo wajen,wadanda barinsu gurin sunje suyi sallama da wasu
baqin aba dinne su dawo suka hangi tahowar sultana da houda. Sam sultana bata gansu ba saboda
yadda idanunta suke a qasa,har sai data ci tuntube da aba sannan ta dakata. Saurin riqo hannunta aba
din yayi yana fadin

"Subhanallahi.......lafiya kike?" Idanunta da suka cika taf da qwalla ta daga suka hada ido dashi,sai kuka
kawai ya taho mata gaba daya,ta sanya daya hannun nata ta riqe hannun aba da kyau tana sakin kuka
me sauti.

"Subhanallah......ya salam......ke houda.....me yake faruwa?" Aba yayi mata tambayar yana jin tuhumar
maina cikin ransa. Dan daburcewa tayi saida oncle issoufou ya maimaita mata sannan ta gaya masa
komai.

Sosai ran aba yaji ya baci matuqa.....ta kowanne fanni gani yakeyi kaman basa yiwa yarinyar
adalci,zuwa yanzu ko a musulunci tana da haqqin zabawa kanta abinda takeso,to don me yasa su zasu
tauyeta?,me yasa zasu bari a dameta akan abinda bai zame mata dole ba?,me yasa za'a dinga dukanta
kuma ana hanata kuka?,shi me laifin waye ya dameshi?,waye yake sanyashi kuka tunda ya shigo gidan
kusan awani arba'in da takwas?. Hannunta ya kama yana juyawa zuwa hanyar sassansa,oncle issoufou
yana biye dashi. A yadda aba din ya fusata ya sani zai iya kowanne hukunci shi yasa bai barshi ya wuce
shi kadai ba. Yana ganin aba din ya zaro wayarsa daga aljihun babban rigarsa shima ya zaro tashi,a
gaggauce ya turawa oncle bashar tex

_"mu hadu a falon yaaya yanzu yanzu don Allah karka wuce wadannan mintunan komai na iya faruwa"_
ya tura masa ya maida wayar nasa aljihun,dai dai lokacin yaji aba din yana magana

"Kazo inason ganinka yanzu yanzu,ka taho da kuma wanda ya sanyaka ka gaggaya mata maganar.... Eh
aliyyun nake nufi" ya fadi a hasale sai ya maida wayar aljihu yana jan wani dogon tsaki zuciyarsa na masa
zafi.....

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200
_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[13/06, 10:18 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 59

"koma ka dauko mata ruwa me sanyi" aba ya fadi sanda suke shiga falon,atta da ya gama sanya masa
turaren wutar da ama ta bashi ya saka din yana shirin fitowa sukayi kacibus. Da kallo yadan bisu sannan
ya koma ya ajjiye kwalbar turaren ya bude fridge ya ciro ruwan,ya hado da kufunan gilasan da suka
zamewa saman freezer din ado,ya qaraso gaban sultana da kanta ke duqe a qasa,hawaye yana layi
saman fuskarta. Fuskartata har ta dan hada ja,abinka da farin mutum

"Gashi aunty sultana" atta ya fadi yana miqa mata ruwan. Cikin ransa tausayinsu dukka yakeji,duk da
baisan har yanzu ainihin abinda ya sanya ya maina barin gida ba,bai kuma san abinda ya hadasun
ba,amma yadda suke ganin komai ya sauya a shekarun sun tabbatar ba na dadi bane.

Hannun tasa ta karba,muryarta na rawa tace dashi

"Na gode" bai iya amsawa ba ya miqe,ya dauki turarensa yana barin falon.

Ko zama aba baiyi ba sai kai kawo da yakeyi tsakanin oncle issoufou da sultana da suke
zaune,zuciyarsa na masa lissafin wahala fadi tashi dawainiya da mohmoud yayi dasu,jininsa bai cancanci
zubda hawaye ba.

Baiji ko d'ar ba sansa goumar ya gama gaya masa saqon aba yana kiransu

"Amma ya maina......me zai hana ka fice,zan gaya masa yanzu yanzu kuka fita dasu tahir" idanunsa ya
daga ya watsa saman fuskar Goumar

"Na fita goumar?,na sake fita a gidannan?,na gama fita goumar......kasan sunan da nafi tsana a
duniya?,kasan abinda nafi tsana a wajen d'a namiji?,RAGWANTAKA.....kalmar da ban yarda a kirani da ita
ba kenan......don meye zanta guje guje akan halas dina?,meye zai sanya na yita guduwa?,kasan meye
ma'anar sunan HAIDAR?,fassararshi na nufin jaririn ZAKI,ka taba ganin zaki ya gujewa wata masifa?,to
haka nake goumar.....wancan da ya faru na yarda yana cikin babin qaddarata.....ba kuma wai nayi
GUDUN K'ADDARA bane...... a'ah.....rubutacce ne dole sai na fita nabar gida na wannan shekarun kafin
na zama abinda na zama a yanzu....muje goumar,zan iya fuskantar aba" bai sake bawa goumar second
chance da zaiyi magana ba ya fusgi hannunsa,har cikin ransa yana jin wani karsashi yana cikashi. Shima
ya gaji,yafison ayita baro baro......yafison su fidda duk kalar hukuncin da suka yanke masa,yafison yaji
meye matsayinsa?,yasan daga inda zaya fara.

Mamakin tsananin jarumta da yadda yake takawa ta kama goumar,sai ya kasa tabuka komai
sai kallo da yake binsa dashi,ya kuma ci gaba da binsa tamkar raqumi da akala.

Sai da suka isa qofar falon sannan ya saki goumar din,ya durqusa ya sabule takalman qafarsa
ya sanya qafars a falon bakinsa dauke da cikakkiyar sallama,dukkan wata gaba ta jikinsa tana bayyana
nutsuwar zuciyarsa.

Oncle issoufou ne ya amsa masa yana binsa da kallo. Bai tsaya ko ina ba sai daya dangane da
gaban aba sannan ya durqusa, goumar ya biyo bayansa shima ya tsugunna gabansa. Cak aba ya tsaya a
gabansu su dukka biyun,saidai kuma goumar yake kalla

"Ina cewa kwanaki umar ya maka gargadin kiranta da matar wani?,wanin da ba'asan a wacce nahiya
yake ba?,......ko yanzun kuma da akasan nahiyar da yake bashi da nagartar rayuwa da d'iyata....... inason
naji shi ya aikeka ka sake maimaita mata?!"

"Nine aba" maina ya furta cikin qanqan da murya da kuma nuna tsananin girmamawa

"Goumar kai nake tambaya!" Aba ya kuma maimaitawa fushinsa yana motsuwa. Abun ya taba oncle
issoufou sosai,bai taba ganin zallar madarar fushi akan fuskar aba irin na wannan lokacin ba,don haka ya
sake fidda wayarsa. Wannan karon direct ya kirayi bashar,akayi sa'a ya daga,baice masa komai ba
yabarshi speaker bude,yadda yasan zaiyi sautin aba din. Yaji din kuwa take hanakalinsa ya dawo
jikinsa,ya katse kiran, oncle issoufou din yana ganin ya katse sai ya sake rubutawa oncle umar gajeran
saqo yasan shi din zaiyi wuya bai gani akan lokaci ba saboda yana yawan mu'amala da waya
_idan zai yiwu ka shigo da bibi da kawu_ ya rubuta masa daga qarshe. Ya nemi tallafinsu ne saboda yana
gudun kada ayi aika aika,yadda yau din fushin aba ke hauhawa bayajin shi daya a matsayinsa na autansu
zai iya controlling nasa.

"Abokin wasanku zaku maidani kai dashi din?......." Ya fada yana sake fusata saboda yadda kowa ke son
maida laifin kansa kusan minti biyu kenan. Basu amsa masa ba don haka yayi taku biyu baya ya dauki
qaramar jotting paper da pen dake maqale a jiki ya wurgawa maina,ba bata lokaci ya sauka a fuskarsa

"Maza maza rubutawa diyata saki......saki ukku kuma nake buqata bawai daya ko biyu ba".

A razane ya dago kansa,karon farko ya kalli fuskar aba da idanunsa da suka sauya launi

"Eh abinda na fada din nake nufi...... girman idanunka ba zasu razanani da komai ba,ka rubuta mata
sakinta guda uku......"

"A'ah yaaya ba za'a yi haka ba,wannan hukuncin ai yayi girma da yawa" oncle issoufou ya taso yana son
riqe hannun aba

"Kada ka dakatar Dani issoufou.....me za'a jira?,meye amfanin igiyarsa?,ya gama shekarunsa dai ya dawo
ba?,to ya sallamarmin diya zan zaba mata miji na kere sa'a,me tarbiyya wanda yasan mutuncin na gaba
dashi" kamar ya zanya tsinin qaho ya caki qirjinsa haka yaji,wannan radadi da ciwon da qirjinsa keyi
masa lokaci bayan lokaci.....ciwon da tunda ya fara zuwa gaban ka'aba yana shan zam zam shi da
azababben ciwon cikinsa suka shafa masa lafiya a yau din kalaman aba sai yaji suna shirin tayar masa
dasu

"Don Allah yaaya ka daina....."

"Sai ya saketa don bata dace dashi ba" ya sake maimaitawa,kalaman da suka sanyashi zamewa ya zauna
sosai saman carfet,sallamar oncle umar da oncle bashar ta baqunci wajen. Oncle umar ya duba bibi din
bai ganta ba,don haka sukayo gaba shi da oncle bashar,don saqon issoufou din ya nuna musu ba lafiya
ba
"Bazan iya sakinta ba aba.......bazan iya sakin diyar NAFESSA ba!" Ya furta cikin dakiya da jarumta. Sak
aba din yayi,don bai taba tunanin maina zaiyi masa musu ba.

"Sai yanzu kasan diyar nafessa dince?,sai yanzu kasan da haka?"

"Na yarda da dukkan wani laifi da kuke tuhumata dashi aba.....na yarda da duk wani kalar suna da zaku
laqabamin......na kuma yarda da kowanne hukunci amma na roqeka da girman mahaliccinmu banda
saki"

"Saboda?" Ya tambayeshi yana matsowa gabansa

"Bazan iya sakinta ba!,ina qaunarta.......ina qaunar jinin nafessa!" Ya fadi wasu siraran hawaye na biyo
gefan idanunsa

"Zan yita baku haquri ku da ita iya adadin numfashin da ya ragemin.......aba koda nayi ma sultana laifi
banajin yakai a yankemin hukuncin rabuwa da ita........naku laifin da nayi muku gani a qasa ina roqon
afuwa da yafiyarku!"

"Kasan yadda ta rayu tsakanin shekarun?,kasan da yadda aka samu rayuwarta?,ka tafi ka barta da
dawainiyar cikin yara har biyu?,don bakasan yadda mata sukeyi ba idan suna tare da juna biyu?,baka da
tausayi bakasan ya rayuwarsu take komawa ba?,yara biyu da qananun shekaru irin nata?,wannan shine
qaunar?,wannan shine tausayin?"

A hautsine ya daga jajayen idanunsa yana kallon goumar

"Yara biyu?,twins?" Ya yiwa goumar tambayar idanunsa a kanshi,da alamun ya zaqu matuqa yaji
cikakken bayani,kamar ma ya manta a gaban waye yake,kamar ma ya manta cikin kotun aba yake. Ganin
goumar bai dago ya dubeshi ba sai ya dafa kafadarsa da qarfi
"BENAZEER DA BATOUL?" Ya fadi muryarsa tana shacking

"Ka bani amsa goumar!...... benazeer da batoul?,nadeeya da BINTOU?" Ya kuma fadi cikin yanayin
matuqar rudewa,rudewar da sai data sanya kowa dake wajen zuba masa idanu.

Kiran sunayen nasu da yayi sai ya zamana kamar kiransu yayi,sai gasu da gudu daya tana bin
daya, benazeer ce ta qwace Sweet din nadeeya ita kuma ya biyota kan lallai sai ta bata. Sun cire duk
wani kayan adon da aka saka musu dazu,kama daga abun hannu sarqa harda takalmansu,sai wani sock's
me kyau da aman tace a saka musu don tasan ba lallai su iya wuni da high hill ba. Ko dankwalin kansu
dukka sun yar,gashinsu kawai da yasha gyara yake matse a band ne jelar keta yawo a bayansu.

"Benazeer,batoul" ya kirasu yana kallonsu da idanunsa da zuwa yanzu suka koma kamar an diga musu
jini. Suna hada ido dashi suka manta da rigimar da sukeyi sai kawo sukayo kansa kowacce nason ta riga
'yar uwarta isowa. Tafukan hannayensa ya bude musu,ba bata lokaci suka shige,ya maida hannuwan
nasa ya lullubesu tsakiyar qirjinsa,ya matsesu gam yana boye fuskarsa tsakanin kafadunsu,sun lullubeshi
da surutu,yayin da shi kuma wani zazzafan hawaye ya qwace masa,hawayen da bazaiso kowa ya gani ba.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂


[13/06, 9:59 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*[6/22, 8:57 PM] +234 810 626 2369: *_GUDUN
ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 60

"ka sake mata yara ka rubuta mata takardarta" aba ya fadi yana hadiye abinda yake taso masa

"Bazan iya ba aba..... I can't" ya fadi da rawar murya,yayin da benazeer da batoul sukayi tsuru tsuru a
jikinsa,don basusan abinda yake faruwa ba,basu shaida komai ba

"Baka isa ba kuwa......ba abinda zai hana ka sakarmin diya" aban ya furta cikin hargagi

"Kai hamidou,meye hake faruwa ne?" Muryar kawu ta halarcin gurin yana takowa zuwa falon bayan ya
cire takalmansa. Dubansu suka maida kansu,har cikin ran aba baiso shigowar kawu a wajen ba,don yasan
zaiyi wuya bai karya masa budget ba. Yanaso a barshi ne shida maina kadai,akwai lesson da yawa da
yakeson ya koya masa.

"Samu waje ku zauna.....kai aliyyu,ku zauna sosai" kawu ya fadi yana zama kujerar dake tsakiya.

Dole kowa din ya zauna,shuru ya ratsa wajen na wasu mintuna,sai batoul da benazeer dake
faman kallon fuskar maina,kaman yadda shima yake kallon nasu fuskokin,yana jin wata soyayya da
qauna da qaunarsu na ratsa kowane sassa na jikinsa.

Kiran sunan maina din kawu yayi,ya amsa masa kanshi a qasa.
"Abinda ka aikatama matarka baikai girman kuskuren barinka gida da kuma rashin waiwayosu ba" ya
fada shima yana nuna bacin ranshi sosai

"Akwai dalili kawu.....ba haka kawai bane ba" ya fadi muryarsa a karye.

"Wanne dalili indai har kana raye kuma cikin hankalinka?......" Fada sosai ya tsinke dayi masa,har sai
daya fidda dukkan abinda ke zuciyarsa dama wanda ya fahimci yana narke cikin zuciyar aba din.

Tsahon wasu mintuna ya dauka,har ya gama ba wanda yace komai a cikinsu,sai daya kammala
sannan ya maida dubansa ga aba

"Hamidou,abinda ya faru ya riga ya faru,tunda har Allah ya dawo dashi lafiya,fatan kawai da za'a yi shine,
ubangiji ya sanya hakan yaci gaba da zama silar alkhairi wa kowa....."

"Nifa dama kawu ba abinda yayimin,d'a dama idan ka haifeshi ai ka gama naka.......abu daya nakeso
yanzu ya sakarmin diyata" ajiyar zuciya kawu ya fidda,ya sani shima aba din ba baya bane wajen taurin
kai da kafiya,yasan kuma tunda ya kafe din saukeshi daga abinda ya niyyata din sai babban abu

"Ta yaya zaka ce haka?,bayan yace shi bazai iya sakinta ba?"

"Idan bazai iya sakinta ba ai kawu ita ba sonshi takeyi ba" ido maina ya lumshe yana ganin qiyayyarsa
quru quru cikin idanun aba,wanne irin abune haka?,duk yadda yakai ga son sultana baya jin zai sota
kamar shi din,gudan jininsa,kuma dansa na fari da ya fara mallaka a duniya

"Waye ya gaya maka?......ke sultana......karki duba girman laifin mijinki,kada kuma ki duba mu mu
dukkanmu da muke a nan wajen,aliyyu mijinki ne,kuma uban yaranki da a yanzun baku da kamarsa,kina
son mijinki ko kuwa a'ah?" Duk wanda yake wajen yasan cewa kawu yayi tambayar ganganci ne saboda
bashi da masaniyar yadda sultana ta dauki maina.......a wajen maina din kuwa,ji yayi kamar ya maida
tambayar data fita a bakin kawun......don ya sani abune me wuya yaji abinda yake da muradin ji din daga
wajenta
"Bana sonsa kawu......na rantse da Allah bana sonsa" ta furta muryarta tana rawa,fuskarsa na tsakanin
dankwalin data warwareshi tana tsane siraran hawayen dake sauko mata.

Saukar wani abu me tsini yaji tsakiyar zuciyarsa kamar saukar mashi,kalaman nata yaji sun
matuqar yi masa girma a zuci da gangar jiki gaba daya. Kalmar QIYAYYA ba qaramar kalma bace dake
raunatar da mutum gaba daya, qiyayyar ma kuma da aka sanar da ita cikin bainar jama'a,a gaban
idanuwan mutane,ba mutum daya ba biyu ba,iyayensa da yaran cikinsa,ya ilahi wannan wanne irin
qiyayya ne?,bazaici darajar koda mutum daya a wajen ba!? .

"Shikenan,duk da kince baki sonsa amma hakan bazai sanya ayi gaggawar cewa ya sakeki ba sultana,ki
sake nazari,kowace mace na iya fuskantar irin wannan bacin ran,amma bayan zukata sunyi sanyi ana iya
fahimtar juna"

"Sai yaushe zuciyata zatayi sanyi?,sai yaushe zan fahimci maina?,bana jin hakan zata kasance har
abada,kullum tsanarsa ninkuwa takeyi cikin raina,kullum burina na bude idanuna naga nayi nesa da
rayuwarsa shima yayi nesa da tawa,kullum neman hanyar da zata qara nisantani dashi nakeyi" abinda ta
fadi kenan cikin zuciyarta tana dunqulewa waje daya sabon kuka yana kubce mata

"Kawu,inda za'a dubi rayuwarta ayi mata adalci shine......ya bata takardarta tukunna,duk wani fahimtar
juna da ake buqata a sameshi daga baya"

"Yaaya..... inaga ayi haquri a gwada maganar kawu tukunna" oncle umar ya fadi yana duban aba cikin
girmamawa

"A'ah,ku rabu dashi,ai dan kanshi ne,sai yayi yadda yakeso kaman yadda zuciyarsa takeso" muryar bibi
data shigo afujajan ta fada,wadda almu ne ya isketa cikin gida ya shaida mata saqon oncle umar,kuma
tazo akan gaba.

Gurin zama suke qoqarin bata amma bata bi ta kansu ba,sai data dangane da kujerar dake gaban
aba ta zame ta zauna a qasa a gabansa tana kallonsa
"Kafin ka kashe wannan auren inason ka fara kasheni ne hamidou kaman yadda na taba gaya maka" ta
furta kanta tsaye da qarfin gwiwarsa.

"Subhanallahi" kawu dasu oncle umar suka fadi,yayin da aba ya zame qasa kusa da ita babu shiri ya
zauna yana dubanta a matuqar ladabce

"Bibi.....me yasa kk irin wannan maganar?" Kafin ta sake cewa komai oncle umar ya dubesu

"Goumar......ka dauki benazeer,maina dauki batoul ku wuce ciki" tuni goumar ya gaji da ganin wannan
tashin hankalin dama,don haka a gaggauce ya miqe ya dauki benazeer,ya miqawa batoul hannu,ga
mamakinsa saita maqale kafada tana sake dafe maina tana kallon fuskarshi. Wani siririn murmushi ne ya
subuce masa duk da yanayin da zuciyarsa take ciki,ya miqe a nutse ya dagata bisa kafadarsa,sai benazeer
itama ta zame daga hannun goumar tana jin kishin bai dauketa ba,ya duqa a tausashe ya azata saman
daya kafadar tasa ba tare da yaji nauyinsu ba sam sam suka fara takawa suna barin dakin oncle umar da
issoufou da kawu suka bisu da kallo kowa tausayin yadda qaddara ta samar dasu tana ratsashi

"To eh mana...... tunda muke da ubanku har yabar duniya ban taba yaji ba bare akai ga batun
saki,hakanan tunda na kafa zuri'ata ba'a taba sakin kowa ba a cikinta......sai yanzu za'a fara daga kan
maina da sultana?,su zasu kafa baqin tarihi cikin zuri'ata?" Maganar saita zafafi sultana dake zaune a
tsakanin kujeru,wato a nan bibi tana nufin tayita dakon aurensa?,ko tana nufin taci gaba da zama dashi?,
abinda har abada bata jin zata iya koda a mafarki kuwa,a taqaice dai kaman ma goyon bayan mainan
takeyi?,ta manta dukkan wasu azabu da wahalhalu da tasha?,ta manta da qyar ta samu rayuwarta ta
daidaita?,da qyar ta tsira da ranta?,ranta ya sake baci sai ta miqe tsam tana barin wajen tana raba
hanya.

A nutse yake takawa dauke da yaran,kunnuwansa sunata jiye masa surutun da suke zubawa
su da goumar,alamun sabo da shaquwa me qarfi na nunawa a tsakaninsu.

Abubuwan da suka wanzu a yanzun ne kawai ke kai kawo a zuciyarsa,tunda suka fito daga
dakin ya kasa furta koda kalma guda daya,sai kunnuwansa dake tsintar surutan yaran.

Haka kawai yaji gidan ya quntace masa,yana buqatar nutsuwa da kuma kadaicewa,yanason ya
kalli yaransa son ranshi,yanason ya sake sosai da yaransa wanda yasan muddin cikin gidanne bazai yiwu
ba,da wannan tunanin sai kawai ya wuce parking lot na gidan,kafin su qarasa kuwa sunsha kallo shi da
yaran,sunyi wani kyau a jikinsa,sai a sannan kamanni kadan kadan suke bayyana tsakaninshi dasu da
suka jera dashi.

BMW dinsa ya bude,ya kuma bude gidan baya ya saukesu suka shige suna murna,kamar wani
sakarai yayi tsaye yana kallonsu har suka gama shiga ya rufe musu qofar,ya koma mazaunin driver ya
shiga,daidai sanda goumar ya bude seat din kusa dashi ya shige shima.

"Me yasa kayimin qarya?,me yasa ka boyemin kyautar da Allah yayimin?" Ya jefawa goumar tambayar
ba tare daya kalleshi ba yana qoqarin tayar da motar. Kallonsa goumar yayi sannan ya maida dubansa
gaban motar

"Bai kamata zuciyarta ita kadai ta wahala ba,bai kamata ace ita daya tasha wannan azabar ba......taci
wahalar da babu wanda ya zatar mata rayuwa,duk wani information da nake baka kana jina ne
kawai,amma bahaushe yace gani ya kori ji......banda wasu dalilai.......banda kuma wasu hujjoji tabbas
bazan bari ka dawo ka sameta da aurenka ba...... tabbas da na......"

"Goumarrrr!!!" Ya kira sunansa da wani irin sauti me qarfi. Waiwayowa goumar yayi yana
dubansa,idanun nan da suka sauya launi tun dazun yanzun sunfi haka jirkicewa, murmushi can qasan
zuciyarsa ya qwace masa,yana sane ya gaya masa hakan, yanason ya motsa masa zuciyarsa da kyau a
kanta,yana kuma son shima ya dandani koda kadan cikin quncin da zuciyarta ta wanzu akai. Duk yadda
yake takurata yake tsokanarta......amma yana jin babu dadi da yanayin da haidar din ya sanyata ciki

"Karkayi tunanin don kana dan uwana..... kuma ka yimin wata rana hakan ya baka daman shiga gonar da
ba taka ba" yayi maganar fuskarsa nayin jaaa. Qaramin murmushi goumar ya sauke,sai ya sanya hannu
ya bude murfin motar ya zura qafafunsa waje sannan ya waiwayo yana kallonsa

""Ban fada da zummar cin zarafi ba,Allah ya baka haquri" daga haka ya fita a motar salin alin ya rufe
masa. Kaman jiran fitar nasa yakeyi ya bawa motar wuta,ya juya kanta da zafi zafi ya nufi gate yana
sakewa security horn,cikin iya aiki da cika umarni suka bude masa gate din ya fice da mugun gudu har
yana cin taya.
Sanda ya saitu a saman titin batoul ta saqalo hannunta ta wuyansa,abinda ya sanyashi sauke
wata ajiyar zuciya me sanyi

"Uncle haidar.....me ya sanyaka hawaye dazun kai da auty?" Tambayar tazo masa a bazata,sai ya dinga
juya amsar da zai bata din. Baisan yadda zai gaya mata yadda zaga fahimta ba,hakanan kuma bayason ya
mata qarya

"Ko aba ya dokeku ne?,kuma shi ai baya duka,bai taba dukanmu ba" batoul din ta sake fadi sanda
benazeer ta zuro hannu tana shafa gashin habarsa dake da santsi cika da kuma baqi sidik.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[6/22, 8:57 PM] +234 810 626 2369: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 61
Kai ya girgiza qaramin murmushi yana subuce masa,ko da basu fada ba,kallo daya zaka yi musu
kasan sun samu gata gami da tsantsar kulawa me tarin yawa

"Aba be dokeni ba,autynku nakeso......ita kuma tace bata sona" ido suka hada yaran suna hangame
baki,qwaqwalwarsu bata gama fahimtar ainihin ma'anar maganar ba,amma kuma sunsan meye so a
suna bawai a ma'ana ba

"Uncle babu kyau,Allah ya hana acewa mutum ba'a sonshi ko?" Benazeer ta furta har tana leqowa
fuskarsa. Hannu daya ya sanya ya shafa sumarta yana sake sakin wani murmushin,har cikin zuciyarsa
yana jin suna sake zama jinin dake harbawa a zuciyar tasa suna narkewa da kyau

"Ba kyau beenaz......zaki gaya mata ta daina fada?"

"Eh Uncle"

"Kefa batoul?"

"Eh nima haka uncle"

"Am not Uncle.....am dad" ya furta a hankali yana duban yanayin fuskokinsu ta madubin gaban motar.
Sak yaga sunyi suna sake kallon junansu,sai suka kasa fadin komai saboda kwanyarsu kamar tana
mamakin maganarsa

"Kun taba ganin daddynku?" Ya sake jefa musu tambayar. A tare suka hada baki wajen cewa

"Eh...." Batoul ta daga yatsanta daya tana cewa


"Amma fa sau daya"

"Nayi kama dashi?" Ya fadi yana nuna kanshi. Tsit suka sakeyi suna duban fuskar nashi ta cikin mudubi su
dukka biyun,kowanne kwanyarsa na dawo masa da surar abban nasu da goumar ya taba nuna musu shi
har sau biyu

"Kuna kama sosai uncle....." Benazeer ta fadi

"Kaman kai ma" batoul ta sake fada tana Dora hannun a qirjinsa tana qaramar dariya. Shuru yayi shima
yana murmushi,zuciyarsa na masa sanyi,komai daya sameshi a baya a yanzun sai yaji kaman bai sameshi
ba,komai sai yaji yana sauka masa a zuciya,wani farinciki na ratsashi da kadan da kadan. Kalaman bibi
suka dawo masa,ya tabbatar da izinin Allah komai ya kusa zuwa qarshe,kuma tunda bibi na goyon bayan
barin igiyar aurensa.......yana da yaqinin shike da nasara...... matsalar aba kuma zata zo masa da sauqi
tunda dai da bibi a gefansa,rigima da kuma daru ne yasan zaya shashi

"Sultana fa?" Zuciyarsa da tun dazun take motsawa ta jefa masa tambayar dai dai sanda yake karya kan
motar zuwa titin dake dauke da hotels da kuma guest in. Ya gama karantar lamarin sultana,yana da
kuma plan guda uku zuwa hudu dukka a kanta,yana kuma kyautata zaton bazai hau dukkan matakan ya
sauka babu nasara ba. A yanzu yanaso yayi calling attention dinta ne har ta tsaya dashi,bayan ta tsaya
din maganar fatar baki ta hadasu,wannan shine matakin farko da yake da buqata,saidai kuma ya
fuskanci shine abu mafi wahala a dukka tafiyar. Tunda yazo qasar ko kalmar A bata taba hadasu ba,ta
yaya zai samu ya tsaidata suyi magana shi da ita?.

Kai tsaye ya gama zagayen titin,ya kuma zaba musu hotel me kyau. Bayan sun bashi key bai isa
dakin ba,sai daya daukesu suka tafi yawon siyan kayan maqulashe. Ci wannan ci wancan,duk abunda
suka nuna sona so sai ya siya musu,haka suka dawo masaukinsu da tsaraba fal,suka yada zango a
dakinsu.

Da kansa ya musu wanka,ya kuma shiryasu cikin wasu baby pink din pyjamas masu ratsin
maroon sannan shima ya shiga yayi nasa wankan,daya fito cikin irin nasu pyjamas din ya shirya,ya feshe
jikinsa da tattausan turarensa ya kuma gyara lallausar sumarsa ya maidata baya,sai ya sanya slipper din
da ya siyo,ya kunna musu tv yace zaije yayi sallah,bazai jima ba kada suje ko ina. Su din ba baqin abun
bane already sun saba,don haka har yaje ya dawo suna zaune abinsu. Dukka kayan ciye ciyen ya sake
baje musu sukaci iya cinsu suka bar na bari,sai ya tattara komai ya dawo ya zauna a tsakiyarsu.

"Kuzo kuga daddynku" ya fadi yana buda wata folder daya adana dukkan tsaffin hotunansu,wasu da yan
gidansu wasu da aba ama,wani shi da sultana sanda suna dasawa qwarai.

Kallon hotunan sukeyi suna kuma duban fuskarsa,kaman yadda duk inda akazo wajen da take a
ciki sai ya tambayesu waye wannan?sai suce

"Kaine"

"Shine daddynmu" batoul take yawan nanatawa sai ya daga musu kai yana murmushi. Sai da suka gama
kalla tsaf sannan yace

"Bari daddynku ya baku labarin mommynku" kwance sukayi a jikinsa fuskokinsu cike da farinciki,sun
kanainayeshi gaba daya suna maimaita

"Uncle haidar......kaine daddynmu?" Da alama abun yana bugar da tunaninsu yana kuma basu mamaki

"Baru na kira muku uncle goumar a tambayeshi"

"Yes" benazeer ta fada tana miqewa ta zauna sosai a gabansa gami da tanqwashe qafa,ta kuma tsireshi
da idanun nan nata. Sak abun sai ya masa kama da yadda sultana ke masa,ya saki siririn murmushi ya
soma laluben number goumar.

Sau uku tana sanya hijab dinta tana zareshi kana sai ta koma ta zauna a wajen data tashi. Ta
sake duba agogo,still dai dare yana dada yi,ba motsin benazeer ba na batoul,ta kuma lura tunda ya fita
dasu daga falon aba ne. Taga goumar har kusan sau biyu,bata ganshi da yaran ba,sannan bataji kowa
yana maganar yaran ba. Idanunta ta lumshe zuciyarta tana bugawa,tun dazun abu daya zuciyarta ke raya
mata,kada fa ya gudar mata da yara?,kada fa a sake nemansa a rasa da yaran?,tunda dai shi din mugu ne
dama,mugunta bai dauketa a bakin komai ba.

Zumbur ta sake miqewa a karo na hudu zuciyarta na tsunkularta ta maida hijabinta,saidai kuma
tana takawa zuwa waje tana tunanin waye zata kaima qara ko ta tuhuma?.

Tana tsananin kunyar ama ba zata iya tunkararta ba,aba kuwa batason sake assasa qiyayyar da
yake nunawa diyan cikinsa qarara a kanta,bibi kuwa ta fara sallama lamarin bibi,duk da bata fito kai
tsaye ta nuna tana yi da maina ba,amma kuma ta fuskanci ta karkata gareshi

"Goumar" zuciyarta ta gaya mata, tabbas shi daya ne zaisan inda suke,tunda zuwa yanzu ta fahimci tun
asali munafukinsa ne,kamar akwai wata boyayyar alaqa tsakaninsu.

Gidan yayi shuru saboda raguwar 'yan biki,don tun magariba aka kai amare aka dawo,amaren
da bata samu daman zuwa kaisu ba. A nutse take taka farfajiyar gidan,zuciyarta na mata fargabar amsar
da zataji daga goumar. Har ta nufi hanyar dakunansu sai ta fasa,ta dawo da baya tana nufar bakin gate
din farko na gidan. A bakin motarsa ta sameshi a tsaye yana amsa waya da qaramar wayarshi,saita
nufeshi kai tsaye tana saita nutsuwarta.

Sanda yaji ana nufoshi waigawa yayi kadan,sai yayi qoqarin yin sallama da wanda ke kan layin
dab da sanda ta iso gareshi.

"Ina yara na?" Ta tambayeshi tana shan mur idanunta a kansa. Qaramar dariya ce ta qwace masa,ya
gyara tsaiwarsa yana kallonta,kamar ya tsokaneta yace daman kina sonsu har haka?,sai kuma ya fasa
kada qilu ta jawo bau,ya hada nutsuwarsa da kyau sannan yace

"Bansan ina suke ba,amma dai sunbi mahaifinsu" haushi kalmar mahaifin ta bata har ta gaza jurewa ta
jefa masa wata tambayar

"Dama suna da wani mahaifi ne?" Shigowar kiran wayar goumar sai ya zamana kamar amsar
tambayarta,sai ya hadiye amsar da yayi shirin bata ya zaro wayar yana dubawa.
Murmushi ne ya qwace masa,abun yazo masa a dai dai,don haka sai ya miqawa sultana wayar
kai tsaye yana duban qwayar idanunta

"Ga mahifin nasu,saiki gaya masa ya dawo miki dasu ko?"

"Kana tunanin bazan iya bane?,ko kana tunanin jiya yau ce?" Ta furta da zafi zafinta tana fusgar wayar
daga hannun goumar cikin fushi. Dagawa tayi ta kuma sanya wayar a kunnenta. A nutse yayi cikakkiyar
sallama

"Assalamualaikum" ya ajjiye sallamar a hankali,saidai kuma a maimakon yaji muryar goumar sai wannan
sautin......sautinnan da bai taba gushewa daga kunnuwa da memory dinsa ba,sautin nan dake tsaye
tsakanin zuciyarsa da jinin jikinsa,sautin nan da yayi matuqar kewa.......yake kuma son yaji koda sau daya
tak ne ya mamayi qirjinsa da kunnuwansa

"Ka dawomin da 'ya'yana,kada kuma ka yarda komai na cutarwa ya samesu,don baka da hurumin
tabamin yarana" idonsa ya lumshe wani abu yana kwarara tsakiyar zuciyarsa,ya tabbatar idan bai
tsokaneta ba,bai kuma tunzurata ba maganarta dashi ta qare,don haka yace

"Wadannan kam sun zama nawa,saidai ki haifi wasu" ji tayi kaman ya doka mata guduma saman
kai,idanunta suka rufe,tana son yayyaba masa maganganu amma kuma idanun goumar na bisa
kanta,batason kuma ta sauka da yawa daga control dinta

"Wannan duka cikin matsalarka ce,nidai na gaya maka ka dawomin da 'ya'yana.......mtsewwe" ta rufe da
jan tsaki kaman zata tsinke harshenta sannan ta zare wayar a kunnenta tana miqawa goumar.

Lips dinsa na qasa ya cije sosai yana rintse idanunsa saboda yadda sautin tsakin ya rasashi
matuqa. Tsaki?,ta manta yana cikin abubuwa biyun daya tsana?,tsaki da gunaguni?,har cikin ransa yaji
saukarsa matuqa,sai ya gaza bude idanunsa har zuwa sanda yaji muryar goumar ta maye gurbin tsakin
nata
"Yaa haidar" ya fadi zuciyarsa ba dadi na tsakin da tayi masa

"Goumar" ya kirashi kai tsaye

"Kay...."

"Shshshsh.......wannan ba huruminka bane,kayi kaman bakaji ba,zanyi handling abun...... BINTOU da


NADEEYA keson sanin waye daddynsu?" Ya masa tambayar yana maida wayar free. Murmushi mai sauti
ya fito daga bakin goumar har sautin nasa yana bayyana

"Kaine daddynsu....... wanda na taba nuna musu uncle haidar shine daddy maina daddy aliyyu,ya dawo
daga tafiyar da yayi,kuma dama ya musu alqawarin zai dawo din" kamar shiri kamar hadin bala'i
dukkansu suka saki qaramin ihu suna ruqunqumeshi. Kashe wayar yayi yana murmushi ya hadasu dukka
shima ya rungumesu.

A nan saman cinyarsa suka kwanta,ya shiga basu labarin quruciyarsa da na sultana saidai kuma
iya abubuwa masu kyau da zasu basu dariya ko suyi musu dadi yake gaya musu. Sannu sannu dukkansu
bacci ya daukesu,ya miqe ya kwashesu gaba daya ya maidasu saman gado ya kwantar,sai ya kasa
tashi,ya sanyasu a gaba yana kallonsu,hannunsa cikin tafukan hannayensu.

Tunda Allah ya jarabceshi da soyayyar yaran yake tambayar kansa why?,me yasa yake mutuwar
sonsu haka?, duk tarin twins din dake Instagram me yasa sai su?,jikinsa yasha bashi ba'a banza ba,
zuciyarsa kuma ta taba raya masa sau daya TABBAS YANA DA DANGANTA DASU TA KUSA KOTA
NESA,saidai kuma ya qaryata hakan, din yayi lalubensa kaf baiga ta inda zasu hada dangantaka ba.

Murmushi ya sake kufce masa,ashe ubangijinsa ya cika masa muradinsa ba tare daya sani
ba?,yara matan da yasha alwashi ya kuma jima yana yiwa ama alqawarin kyautar mata dasu ashe Allah
ya jima da cika masa burinsa?,ya sani koda ba'a gaya masa ba sunsha gata da kalar kulawar da ba
kowanne yaro ke samu ba.
Tsakinta na dazu ya sake dawo masa fes a kunnensa,sake cije lips din nasa yayi ya girgiza kansa
kadan,bata canza bane ko da saura?, Ya jefawa kansa tambayar. Lallai zai dauki komai amma banda
raini, wadannan tsakin akwai buqatar nuna mata bai kamaci tayi masa shi ba,tabbas.........

*_maina sarkin son girma😂,me karatu kada fa ya qara b'aro wani aikin muzo mu hadu da wasu twins
din?,ba ruwan HUGUMA dai_*

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 62
Cikin jikinsa yaja yaransa bayan ya gama shafa'i da wuturi,ya rungumesu tsam suna jin dumin
juna yana sauke ajiyar zuciya. Sai yanzu yake sake tabbatarwa lallai jininsa ne,lallai wani bangare ne na
jikinsa. Ni'imtaccen bacci yayi wanda ya jima baiyi irinsa ba cikin nutsuwa da kwanciyar hankali,haka
yaran suma,babu wadda ta motsa a cikinsu haka suka qarar da daren.

Juyi kawai ta dinga yi tana tuna yaran,sam bacci ua qauracewa idanunta,tana tsoron kada ya
aiwatar sa abinda ya fada din,don ta gama sallamawa shegen kaifin maganarsa guda daya kafiya da
taurin kansa. Batasan haka take qaunar yaran har cikin jininta, batasan haka zuciyarta ke mutuwar
qaunar yaran nata ba,bata taba kuma kawowa haka take jinsu a ranta ba sai a wannan daren,ta jima
tana juyi kafin daga bisani baccin yayi awon gaba da ita.

********Tunda sukayi sallar asuba washegari basu koma ba,shi dasu zaman hira sukayi,duk wata
tambaya idan sukayi masa haka zai amsa musu,hakanan shima ya sakasu gaba da tambayoyi. A nan din
ya samu information sosai akan sultana,wasu abubuwan da bai sansu ba sakamakon yankewar sadarwa
tsakaninsa da goumar dukka yaji a bakinsu benazeer. Shuru yayi yana sauke boyayyar ajiyar
zuciya,tausayinta yana sake illata masa zuciya. Yana da buri sosai a kanta,burin da yasha banban da
burinsa na baya,amma kuma dukka abinda zai gudanar dole saida hadin kanta.

Yana tsaka da wannan tunanin wayarsa ta dauki tsuwwa,batoul dake game a ciki ta miqo masa
a nutse yasa hannu ya karba yana mata murmushi. Daddy ne,alhj Bello Muhammad mahaifin
sardauna......mahaifin kuma laila..... Mutumin da ya zame masa bango jigo kuma makwafin mahaifi.
Tashi yayi ya zauna sosai yana jin wani iri,bai kyauta ba kwata kwata,duk kansa ya shiga kawuna,sam
baiyi kiran daddy din ba tsahon kwanaki,abinda kuma bai saba ba.

Yana qoqarin gaidashi shi kuma yana qoqarin tambayar lafiyarsa

"Lafiya alhamdulillah daddy"

"To ma sha Allah......'yar rigimarka ce ta sakani a gaba,wai na binciki lafiya kake?,ka zama wani mugun
busy kwana biyu" sumarsa ya yamutsa,laila tana daureshi da jijiyar jikinsa,duk sanda ta hada lamarinsu
da daddy din a ciki sai ya zamana kamar ta masa dabibayi ne. Ko dazun bayan asubah da ya tashi yaga
saqonta,yayi mata reply ne ya zame masa jidali har kawo yanzu.
"Lafiya alhamdulillah nazo wajen family nane.....ina da buqatar lokaci ne daddy,akwai matsaloli da
nakeson gyarawa" ajiyar zuciya ya saki yana jin farinciki yana ratsashi. Tunda suke da maina din tsahon
shekaru uku bai taba zancan gida ba,hakanan shima bai taba tilastashi game da komai nasa ba,amma a
matsayinsa na uba kuma mahaifi ko yaushe yana da wannan tunanin a ransa,dole kuwa a yanzu yayi
farinciki

"Ma sha Allah, alhamdulillah,to Allah ya yaye damuwa ya shiga lamarin"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu daddy na gode sosai " ya fadi har qasan ransa yana jin kimarsa tana sake
qaruwa. Mutum ne me tsananin dattako,kamili na gaske wanda yasan abinda ya kamata

"Gashi karbi" daddy ya fada yana miqawa laila wayar. A dan kunyace ta karba sannan ta miqe tana barin
wajen,ta tabbatar yau din zata samu kulawa data d'ara wadda ta saba samu.

"Yaa maina.......barka da warhaka" ta furta tana karyar da murya

"Barka kadai laila......kina lafiya?"

"Uhmmm......to, lafiya alhamdulillah,amma ba lafiya sosai ba"

"Me yake faruwa?" Ya tambayeta cikin son nuna kulawa

"I missed you so much yaa haidar,and it's killing me wallahi" tayi maganar tana fita daga tsakiyar
zuciyarta da gasken gaske. Ido ya lumshe sannan ya budesu,bayason yadda kullum kwanan duniya take
sake zurmawa cikin soyayyarsa,baisan ta yaya akayi ta fara sonshi ba,baisan kuma yaushe ba,tabbas ba
shakka da bazai barta ta fara ba. Har yanzu zuciyarsa jaririya ce akan soyayya,yana jin kamar rainonta
yake, zuciyarsa batayi fadi da girman amsar kalolin soyayya ba

"Ina gida as i said......ina wajen family na......ga 'ya'yana su gaisheki" ya furta da zummar cimma manufar
dake qasan ranshi
"Yayanka?,when...... yaushe ka haihu?" Murmushi me sauti ya fidda

"It's a long story........ batoul ga aunty laila" ya fadi yana hadasu da wayar yayin da ya koma yayi relaxing
jikin kujera yana kallonsu.

A qalla sun kusa mintuna biyu kafin su miqa masa Wayar,ya karba ya saka a kunnensa

"Yayanka ko yaran cousins naka ko yaran sisters dinka?"

"My biological daughters" d'if tayi na wasu sakanni kafin ta furzar d numfashi

"Okay...... okay,it's ok,see you later?,zaka kirani?,ko ni zan kira?" Ta tambayeshi tana karyar d
wuya,maganarsa ta yanzu kuma tana dukan zuciyarta

"Idan kinji shuru zaki iya kiran nawa na bada dama" qaramin murmushi ta saki

"Thanks,bye.....ka kula da kanka please"

"Na gode" ya amsa mata a taqaice,sai ya zame wayar yana kallonta.

Yayi tsammanin daya gaya mata wannan zata rude ne,ya dauka zata katse wayar,ya kira kuma
taqi dagawa,ya zaci zatayi fushi,sai yaga dukka babu wannan a tattare da ita.

Har rana yayi kawai yana zaune cikinsu suna sabgoginsu,yayi musu doki,ya dora wani a bayansa
wani a qafafunsa,suyi wasan buya dukka. Abinda ya sake haifar da wani irin shaquwa tsakaninsu qasa da
awa ashirin da hudu. Sukayi wani mugun sakewa da shi,qauna da soyayyar nan dake tsakanin mahaifi da
'ya'yansa ta sake bubbuga sosai,duk wata soyayya ta motsa qwarai. La'asar liqis suka baro hotel din,ba
kuma gida ya nufa dasu kai tsaye ba,yayi kiran hadiminsa ya bashi jan motar suka wuce wani qaton mall
dake garin marad'i.

Siyayya ya dinga yi musu harda ta hauka,sosai yake jin kansa a matsayin mahaifi,yake kuma son
ya soma taka wannan rawar,yake muradin ya amsa sunansa na mahaifi din. Sanda yake musu 'yan
tambayoyi don sanin abubuwan da ba lallai ya jisu daga bakin ama ko wani a gidan ba.....sai zuciyarsa
dukka ta raunata,ya fahimci tsantsar gatan da ama ta nuna musu,kulawa da sadaukarwar da aba ya
musu. Ya sani koshi ne a wajen ba lallai ya musu irin wannan gatan da suke samu, zuciyarsa sai ta sake
rauni,qauna da soyayyar mahaifiyarsa ta sake cika masa zuciya. Ita din ta daban ce......mahaifiya
soyayyart daban ce kamar yadda take ta daban. Yawan siyayyar motarsu tayi kadan ba zata iya cinyewa
badon haka suka zuba abinda zasu iya dauka,sauran kuma ya bada location dinsa sukace zai taras da
kayansa har qofar gida in sha Allah.

Daga nan ya sake biyewa dasu ya cikasu da kayan maqulashe,hakanan ya tsinci kansa da yiwa
driver umarni suka dauki hanyar wajen tsohon me namansu da bibi da ama ke so sosai,bama su kadai ba
harda aba din.

Suna dosar wajen komai yana dawo masa sabo,wajen da yayi silar wanzuwar komai cikin
rayuwarsu,muhalli da daga nan aka fara qulla zaren saqar K'ADDARARsu,daga nan komai ya fara.

Daga nesa kadan ya sanya yayi parking,yace su benazeer su zauna cikin motar,sai suka maqale
wuya

"Daddy ba zaka dade ba?" Kai ya jinjina yana murmushi

"In sha Allah" ya fadi yana shafa sumarsu,shi kansa yana jin inda zaiyiwu ko na second daya bazaiyi nesa
dasu ba,ya janye jikinsa driver ya maida murfin ya rufe.

Lokacin da yayi sallama yana kan hadar hadar killace naman da aka samu gasawa,bayan dadin
da namansu ke dashi suna da matuqar tsafta qwarai,wannan ya sanya maina din duk iyayinsa da zabe
zaben abinci da yake dashi bai taba challenging namansu ba.
Idanu ya zuba masa sanda yake amsa sallamar,kamannin maina din suna masa yawo a
ido,saidai wannan din ba yaro maina bane yake gani,cikakken saurayi da Hankali ya game jikinsa,me
cikar zati halitta da wani uban kwarjini dake yawo saman fuskarsa

"Ka ganeni?" Ya tambayeshi yana qaramin murmushi

"Eh to.....magana ta domin Allah naso na shaidaka,amma kuma ina tantama idan kaine din,kamar dai
maina ko?,dan gidan alhj hamidou mayak'i?" Kai ya jinjina yana murmushi. Murna ta cikashi ya ajjiye
kayan hannusa yana cewa

"Kai,Allahu akhbar....... ashe rai kanga rai,shuru babu kai ba dattijuwar arziqi?" Mamaki yadan
kamashi,kenan bibi ma tabar aikowa a siya mata kenan tun bayan da yabar gidan?. Gaya masa yadda
yakeso ayi masa yayi yace ya aiko masa dashi mota yanzu zai jirashi. Jikin yahuza na rawa ya soma
aiwatarwa,don ya tabbatar yau qila dukka kudin namansa ne zasu fito daga jikin maina din. Kamar yadda
ya zata din kuwa,don sai waiwayowa yayi kawai yaga ya ajjiye masa bandir daya da CFA,wanda yayi
imanin sun ninka kudin namansa ma,don haka ya zage shima ya cikashi da naman da yafi yawan wanda
ya buqata,yana sake jinjina kyauta irin ta jinin 'yan gidan da kirkinsu.

Yinin ranar duka cikin rashin sukuni ta yishi,ta kasa zaune ta kasa tsaye tsakanin sashen bibi
dana ama,damuwa ce sosai cikin rai da fuskarta,wanda sai kana da mugun nazari zaka kula da haka. Ta
dauka da sassafe aba ama ko bibi zasu tasashi gaba da sababi ya kawo mata yaranta,ko kuma shidin ya
kawosun amma sai taga ba wanda ma yayi batun yaran. Sanda taga har azahar ta shigo tana shirin
ficewa damuwarsa da fargabarta sai ya qaru,idan ma barin qasar ne tasan zuwa yanzu sun jima da
ficewa. Qaruwar damuwar ya ankarar da ama,tana sane,tasan ya kwashesu tun jiyan bai kuma dawo
dasu ba,ta fahimci kuma sultana din a dame take,tayi shuru ne saboda ko yaya dai a bashi chance shi da
su da zasusan shine mahaifinsu,susan suna da mahaifi,ya kuma yi duk hirar da yakeson yayi dasu din.
Idan shi me laifi ne su ai basuyi laifin komai ba,basusan kuma komai ba,bai kamata a lullube musu
ubansu ba, shi kadai yayi laifi,shi kadai zai amshi hukunci,abinda ke tsakaninsa da mommynsu kuma ba
hurumin yaran bane bare a tsundumasu a ciki basuji ba basu gani ba,bayan suma kawosu akayi cikin
rigimar da basusan da zamanta ba.

Yamma lis ta sameta a kitchen tana qoqarin diban abincin rana da bataci ba,don ko na safenma
dai tsakurarsa tayi. A iya safen zuwa yanzun aman ta fahimci itama me qulafucin yara ne,wani dalili ne
kawai dama yake sawa take nuna halin ko in kula dasu,amma tana qididdige da dukka motsinsu da
takunsu.
"Lafiya kike yau kuwa sultana?,ko bakya jin dadi?" Kai ta girgiza,sai taji zuciyarta tadan tsinke,aman bata
san abinda ke damunta ba kenan

"Lafiya lau nake ama,kawai kasala nakeji"

"To Allah ya qara lafiya,Alla ya rufa asiri" ta amsata tana ajjiye plate din data shigo dasu ta gama abinda
zatayi sultana din na satar kallonta qasa qasa har ta juya ta fice. Ajiyar zuciya ta sauke tana ajjiye abincin
data debo din,ta rungume hannayenta ranta na sake baci,magariba na dosowa ya kwashe mata yara tun
jiya har yanzu ba duriyarsu?, bacin ran ya sanyata jin qwalla ta cika mata ido,sai tayi qarfin halin son
maidasu amma duk da haka sai da suka zubo,ta daukesu tana yiwa kanta fadan

"Ashe har kwanan gobe shike cin nasara a kanki tunda baki daina masa kuka ba,bai daina saka
hawayenki zuba ba" wannan maganar ta sanya dole ta jawo jarumta ta azama zuciyarta,ta zuba abinci
me yawa kaman da gaske zata iya cinyewa sannan ta juya ta fice.

Ana kiran magariba suna isa qofar gidan,kaman ko yaushe ya sallami driver din ya karbi tuqin
motar ya nufo bakin gate din da ita. Horn daya hudu ya qaraso,yaja da baya cikin girmamawa ya bude
masa ya shige da motar.

Parking lot na gidan gaba daya cike da motocin 'yan gidan,alamu dake gwada kusan kowa yana
gida kenan. Ya tsaida tasa motar ya juyo yana kallonsu benazeer

"Zaku shiga ciki,kuje wajen ama da bibi kuce dukkansu ina gaidasu, benazeer ki bawa ama wannan,
batoul ke kuma bibi,zanyi sallar magariba zan shigo daga nan"

"Kada ka dade daddy" batoul ta fadi a raunane. Murmushi ya saki,tausayinta yaji ya ratsashi, yarinyar da
alama tana da tsananin qulafuci akan abinda takeso,kamar dai yadda yake,yana fata kada Allah ya bawa
mamansu galaba a kanshi,zayaso su rayu tare cikin aminci
"Kada ki damu B na,magarib da isha'i zanyi,zanzo muci abinci tare a wajen ama ko bibi" dan qaramin
ihun murna suka saki, murmushi ya kubce masa,sai ya sauka ya bude musu qofar motar suka fice sukayi
cikin gidan. Yana shirin kulle motar yaji maganarsa a bayansa, goumar ne da alama shima masallacin
zashi,ya qaraso yana dubansa cikin bashi girma kuma yace

"Barka da yamma" yayi gaisuwar yana karantarsa. Daga jiya zuwa yau daya dauki yaran kadai walwalarsa
ta qaru,kai idan ma idanunsa sun gani da kyau nutsuwarsa ma ta ninka ta jiyan

"Barka kadai malam oumar me qarya" ya qarasa fada yana dagowa daga rufe motar da yakeyi. Sunan da
ya bashin ya sanyashi bushewa da dariya harda dan ranqwafawa,wannan ya bawa maina daman buga
masa duka a tsakiyar bayansa, goumar ya gantsare yana jin zafi yana ratsashi. Tun ba yau ba sunsan
hannun yaa maina bashi da dadi,shi yasa ba kasafai suka fiya son yi masa laifi ba

"Bayana yaa maina"

"Eh,ai bansan me zanyi maka na huce ba,ashe kaima da nake ganinka me imani ba imanin gareka
ba,twins fa?,ashe nawa ne?,nayita kwana ina tashi da begensu?,kacemin yaro guda ta haifamin,ashe
jaruma ce ita din" ba shiri goumar ya qyalqyale da dariya. Wato har wani sunan jarumta ya bawa
sultanan,saboda baisan ainihin fadi tashin da akasha kafin yaran su rayu ba a cikin mahaifarta,tashin
hankalin data dinga yi,saidai duk da haka yanason bashi abinda zai karya lagon bibi sosai

"Eh to,zaka iya kiranta da hakan......amma kasan banda tsananin rabo da tuni bibi ta sanya an markade
maka yara tun suna 'yan tayi?" Dif wuta ta dauke masa,Girarsa ya tsuke saboda kasa fahimtar abinda
goumar ke shirin gaya masa

"Kaman yaaya?" Ya tambayi goumar din yana sakin wuyanshi da ya riqe,miqewa tsaye sosai goumar din
yayi yana gyara rigarsa

"Eh,so tayi a zubda cikin,wai sultana tayi qanqanta,wannan ai shine silar tafiyarsu Austria da nace maka
sunyi a sace" Ajiyar zuciya ya sauke tamkar zata fito hade da zuciyarsa,sai yaji qafafunsa sun kasa
daukarsa,ya koma ya jingina da motarsa. Ba komai goumar yake gayanmasa ba kenan,akwai abubuwa da
yawa da bai bashi information akai ba. Inda bibi ta aikata masa hakan ya tabbatar babu wani abu da
zatayi wanda zata wanke kanta,kuma yasan tabbas a lokacin da goumar ya gaya masa abinda bibi ke
shirin yi kenan......yayi imani duk yadda yake aboye to sai ya bayyana kansa

"Alhamdulillah lillahil lazi bi'ni'imatihi tatimmus salihat......lallai bibi Allah ya taimakeki" ya furta a fili
yana jinjina kai. Dariya sosai abun ya bawa goumar

"Cool down yaa maina,ya wuce ai" idanunsa ya zubawa goumar din yana jin ciwon abun a ransa kaman
yanzu ya faru,kafin ya sake cewa komai sai suka hangi fitowar aba da oncle issoufou,wannan ya sanya
suka saita kansu.

Dab da zasu gotasu ya russuna yana gaidasu, oncle issoufou ne ya amsa cikin kulawa,yayin da aba
ya kalleshi sai ya dauke kai yana yin gaba,sannan kuma ya amsa gaisuwar tasa da qyar. Murmushi yayi
yana miqewa,iya hakanma ya masa dadi,ya tabbatar kuma yabi maganar kawu ne kawai.

"Muje masallaci kada lokaci ya qwace,akwai maganganun da nace maka zamuyi" ya fadi yana duba
kwantaccen agogon Rolex dake daure a hannunsa

"Okay to" sai suka fara jerawa suna takawa a hankali

"Sultana fa?" Ya jefawa goumar tambayar duk da yanata qoqarin controlling harshensa kada ya
tambayeshin don bayason ya samu lagonsa ko ya soma rainashi. Dan satar kallon maina din yayi sannan
ya qunshe dariyarsa,abinda bai sani ba mainan ya ganshi amma yayi kaman bai gani ba

"Da yammar nan naga fitarta,ta shiga gidan alhj hamza duba matarshi" kai ya jinjina,komai zayazo masa
da sauqi kenan.

*_KWANKWASON JIMINA_*
*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*
09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[13/06, 9:59 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 63

Da gudu suka isa sassan ama suna qwala mata kira,idar da sallarta kenan,ta miqe tana duban
ta inda zata ga sun bullo. Tun jiyan suna ranta,tana kuma sane da fitarsu da rashin dawowar tasu,saidai
kuma bataso tace komai ko ta shiga hurumin d'a da ubansa. Ta sani tafiyar tasu ce kawai zata samawa
maina nutsuwa a ranshi,hakanan su kansu yaran fitar da zasuyi dashi ta tabbatar zuciyarsu zata ginu da
sanin waye mahaifinsu. Tun daga jiya zuwa yau din ba abinda take juyawa a ranta irin hikimar ubangiji da
ya hadasu tun kafin susan su din waye a wajen junansu?,suka kuma yi wani irin sabo cikin lokaci qanqani
haka,wannan kadai yana sanyawa gwiwarta tayi sanyi,ta kuma sake yin imani da al'amarin
ubangiji,yadda yake saqa faruwar abubuwa cikin hikimarsa da buwayarsa.

Sai da suka isketa a dakin sannan suka daina kwaroroton kiranta din,sukayi turus suna dariya,ta
jefa musu hararar wasa kaman yadda suka saba yi lokaci lokaci. Dariya dukansu suka saki,yayin da
mutuniyar benazeer ta taho da sauri tana haye mata kafada
"Amanmu"

"Ba wani nan,bayan kunga abbanku kun manta da ama din?"

"Ashe da gaske daddynmu ne din?" Batoul da har yanzu mamaki da murna basu barta ba ta tambayi ama
kai tsaye tana kallon idanunta. Murmushi aman tayi,sunan maina matsayin uba,ubanma na yara har biyu
yana faranta mata rai matuqa da gaske,yana sata jin wani iri,yana kuma sakata din farinciki. Wani kyauta
ne ta ba zata da Allah yayi musu,duk kuwa da cewa akwai madaci sosai da aka tauna kafin zuwan
wannan lokaci

"Daddynku.....shine abbanku" Alamun murna suna bayyana saman fuskar batoul sosai,yayi da benazeer
ta sake maqaleta da kyau,sai ta saki dariya itama tana saukota daga wuyanta

"Karki ballani tunda ubanki yazo" ta qarashe fadi suna yin dariya dukansu.

Bayan sunyi sallar magariba din cikin masallacin suka zauna shida goumar,yana tambayarsa
abubuwan da suka faru da bai sansu ba bayan ya tafi. Wasu abubuwan su sanyayar masa da jiki,wasu su
sakashi murmushin dole,a haka har lokacin isha'i yayi,suka sake tada jam'i suka yita suka idar,sai ya samu
kansa da sake tsaiwa gaban ubangiji yana neman afuwa da yafiya,yana neman sauqi sassauci da kuma
rangwame hadi da zuwan komai da sauqi tsakaninsa da sultana. Koda ya idar sai suka jero zuwa
gida,saidai gab da zasu isa gidan kira ya shigo wayar goumar,ya daga yana duban maina

"Zan koma titi,akwai abokina da ya iso yanason ganina" kai maina din ya daga,goumar ya juya yana
komawa da baya,shi kuma yaci gaba da takowa cikin gidan.

A nutse ya wuce gate din farko ya shigo na biyu sukayi kacibus da saddi,ya rusuna cikin
girmamawa da matsayinsa na babban wa a garesu ya gaidashi,ya amsa masa yana fadin

"Sultana ta shigo?"
"Bata shigo ba,taje dubiya maqota amma bata dade da fita din ba" kai ya jinjina yana lumshe idanunsa.
Yana ji sosai cikin jikinsa yana da shauqin ganinta,yana da shauqin magana da ita,koda kuwa bazata
tanka masa ba,koda ba zatace komai ba,koda tsiwa zata masa,don haka ya taka a hankali ya isa wani
gefe can daban da muddin zata wuce sai tabi ta wajen,dab da qofar falon daya daga cikin saukar baqinsu
na gida ya zauna saman qananun concrete chairs guda uku dake wajen tsakanin shukokin da suma taka
rawa wajen qawata harabar gidan.

Wayarsa ya fidda,sai yaci karo da saqonnin laila birjik, numfashi yaja,bayan fatan taci gaba da
jarabtuwa da sonshi,duk da ya fahimci kusan kullum kaman tana sake zurfi ne a ciki,duk da yadda yake
jan jiki da kuma yin baya baya da ita. Dole ya buda yana dubawa,saboda aqalla bai kamaci ace a duk
yawan saqonnin bata samu amsa guda daya daga gareshi ba.

A nutse take takowa zuwa harabar gidan. Sanye take da simple gown na atamfa da aka yiwa
yalwataccen dinki,dinkin daya tafi da sigarta da kuma murjajjen jikin nan nata,kanta ba dankwali tadai
yafi madaidaicin mayafi baqin sidik wanda ya qarawa fuskarta kyau ya kuma fidda ainihin kamanninta na
cikakkiyar ba'abzina. Idanunta a fede babu kwalli,hakanan fuskarta fes take babu digon komai,amma
kuma hakan bai hana sassanyan qamshin nan nata na har abada ba fita daga jikinta.

Wata siririyar waya ce a hannunta wadda aba ya bata ita gift na gama makaranta. Waya takeyi
da daya daga cikin ma'aikatan gidan tv din da zata fara aiki dasu,suna sake gaya mata ainihin date din da
zasu fara zuwa aiki,da kuma ainihin program din da sukeso ta fara gabatar musu,wanda ya shafi al'adun
a yankin africa.

Yadda hanakalinsa ya dauku akan wayarsa nata yafi haka daukuwa. Sosai take qaunar wannan
aikin har cikin jininta,hakanan kuma sosai take zumudin farashi. Tasan yana daya daga cikin abinda zai
samar mata ragowar farinciki da kuma walwalarta data rasa.

Takawa ta fara yi slow sama da yadda ta shigo gidan qirjinta yana bugawa. Wucewar qamshin
kawai ta kafofin hancinta suka sanya zuciyarta motsawa,a hankali sai harshenta yadan fara sarqewa da
bashi amsa da yaren faransanci da suke magana. Qoqarin baza idanunta takeyi don hango daga wanne
bangare yake ta kaucewa rabar wajen,saidai yadda hankalinta yadan tashi ya sanya ta gaza ganoshi dab
da flowers din dake gefanta. Rashin gano taqamaimen location din da yake ya sanyata ta jita bata da
tsaro,ta gwammace ta tsaya cak a wajen,don bata qaunar haduwarsu koda na wucewar second daya
ne,bata kuma da tabbacin idan taci gaba da takawar ba zata ci karo dashi ba,gwara ta tsaya daga nan ta
gano daga inda yake sai ta zabi sashen da zata wuce,sassan bibi ko na ama din.

Sautinta da suka isa kunnuwanshi su suka ankarar dashi isowarta wajen,a nutse ba tare daya
daga kanshi ba ya kashe wayar yana maidata aljihu sannan ya miqe cak yana zuba hannayen nasa a
aljihun nasa,ya kuma fara takowa inda take a tsayen. Tana qoqarin yin sallama da mutumin don ta
tattara hankalinta waje daya,gefe guda kuma iska na qoqarin yaye lullubin kanta,wanda dole ta kasa
hankalinta biyu,saidai bata cimma nasarar riqe mayafin ba saboda ta bada qarfi wajen kashe kiran iskar
ta debi mayafin ta kuma yi cilli dashi gefe guda,baqar sumarta me santsi yawa da tsaho ta warwatsu
saman fuskarta,hakan sai ya zamana tamkar ado ga saman fuskartata,qamshin hair mist din da take
using dashi shima ya fara fita tare da iskar. Qaramin tsaki taja idanunta akan wayar

"Allah yasa a cikin gida ne da na cutu" ta furta tana qoqarin saving number, idanunta kuma akan wayar
tana takawa direction din da taga mayafin ya tafi ya fadi da zummar ta dauka ta wuce cikin.

Yana sane,ya kuma ga tahowarta,don haka ya taka a nutse idanunsa a kanta har ya isa gaban
mayafin,ya kuma tsugunna ya sanya hannayensa ya dauki mayafin. Hannu ta miqa ba tare data kalli
wajen ba,saboda ta gama gane inda mayafin yake,can qasan zuciyarta kuma tana wani irin bugu saboda
mugun qamshin turarensa da takeji dab da ita sosai. Qasa taji ta debo,wannan ya sanyata barin saving
number din don dole ta maida dubanta ga wajen. Sauka idanunta sukayi kan zaratan qafafunsa dake
sanye cikin wani flip floppy masu taushin gaske, charcoal color da suka haska farin skin dinsa sosai.

Da sauri ta miqe cikin rashin sanin yana dab da ita, hakan ya sanya tayi gware da katafaren
qirjinsa da ya mamaye tsahonta. Haduwar jikinta da qirjinsa yayi sanadin sa saura kadan numfashinta ya
kubce mata,da wani irin hanzari taja da baya tana watsa masa wani irin kallo,tuhuma da bacin rai fal bisa
fuskarta.

Abinda bata sani ba manyan fararen idanunta da take jifansa da kallon tsana ya dinga ji suna
ratsa kowanne sashe na jikinsa,sai yakejin kallon kamar wani kallo ne na musamman bawai na bacin rai
ba,idanunsa suka shagala da kallon sassalkan gashinta da yake tunanin shekaru da hankali data qara
suma abun ya shafesu,don ya qara cika tsaho da kuma santsi.

Kafeta da yayi da lion eyes dinsa sai taji kaman yana watsa mata wuta ne cikin sashen jikinta,ba
abinda idanuwansa ke tuna mata sai waccar ranar da wancan LOKACIN. Ba abinda suke tuna mata sai
yadda ya gwada mata zallar qarfi da rashin imani......baya tuna mata komai sai sanda take jifansa da
kalaman da take tsammanin zasu sanyashi fusatar da zaya rabu da ita ba tare da yayi mata komai
ba,ashe a nata rashin sanin......a nata rashin wayon rashin imaninsa yakai har inda baya jin kiran.

Bata qaunar koda hada idanuwa daya dashi bare wata magana ta hadasu,ta gwammaci ta koma
cikin gida a haka akan tayi masa maganar ya bata mayafin,ta sanya hannunta ta maida gashin dake tsone
mata idanu baya,sannan tayi taku biyu gefe da zummar kewayeshi ta wuce,don ya tokare kowacce
hanya daga gabanta da zata bata damar wucewar.

Cikin sauke qafafunta da tayi sau biyun tare suka sauke shi da ita,a fusace ta daga idonta zata
sauke masa,saidai kuma yana tsaye kaman wani zane ya sake kafeta da kakkaifan kallon nasa da suke
sanya kowacce laka ta jikinta zarewa a shekarun baya,suke kuma cire mata duk wani taurin kai qwarin
gwiwa da tsiwar data tsammaci yi. Ga mamakinta ko a yanzun ma tasirin wadannan idanun masa masu
kama da idanun zaki basu fasa galaba a kanta ba, saidai kuma bacin rai dake sidar zuciyarta ya rage kaifin
tasirinsu. Hannun hagunta ta sake takawa don neman hanya still ya sake tareta,wannan karon ya motsa
siraran labbansan nan dake da wani irin color me birgewa

"J'ai besoin que tu m'écoutes s'il te plaît(ina buqatar ki saurareni don Allah)" ya fadi cikin tattaccen
harshen faransanci da zai nuna maka zallar qwarewarsa a ciki da kuma nuna da yaren yayi saman
harshensa

"ne bloque pas la route(kar a taremin hanya)" ta maida da harshen da sukafi magana dashi din dai
still,cikin lafuzzanta akwai kakkaifan sound na gargadi tayi kuma maganar ne ba tare data kalli idanunshi
ba,don ko kusa ko alama bata da sha'awar hakan. Bai damu da wannan ba,don lokaci da hankalinta
kawai yake da buqata

"je cherche des faveurs(ina neman alfarma)" ya sake fada yana zaro hannayensa daga aljihun wandonsa
ya hadesu guri daya👏🏽.

"Ka matsamin na wuce nace!" Tayi maganar da tsawa zuciyarta na mata zafi. Tsam ya runtse idanunsa
yana jin saukar siririyar muryarta har tsakiyar kanta. A nutse ya bude idanun nasa sanda yaji tana takawa
da gaske zata wuce ciki. Kai tsaye ya sanya hannu yayi caraf da tsintsiyar hannunta,abinda ya bata shock
qwarai,ta kuma tsaya cak da tafiyar da takeyi,ta waiwayo tana kallon tsintsiyar hannunta dake cikin
tafukan hannunsa daya runtse tsam. Maida dubanta tayi ga fuskarsa
"Ka sakarmin hannuna.....baka da hurumin tabani" ta fada tana qoqarin controlling hawayen daketa
turereniya suna son bayyana kansu take son hanawa,batason ko sau daya ta sake kuka a gabansa a
rayuwarta,tanason nuna masa she's strong......fiye da yadda yake tunani

"corrige tes mots(ki gyara kalamanki)" ya maida mata amsa. Maganar tasa sai taji zallar raini ce a ciki,ta
tattara dukkan qarfinta da nufin son zame hannunta saidai kuma inaaaa......wutsiyar raqumi tayi nesa da
qasa,ita kanta tasan ba abu bane me yiwuwa don riqon bana ragwagwen maza bane. Shi kam yana tsaye
hankalinsa kwance,yanata qare mata kallo da kuma yadda take fafutukar qwace kanta

"Kinyimin tsaki jiya.....saboda na qyaleki shine yau kika dora da yimin tsawa?,Ai-je ton âge ?(ni tsaranki
ne?"

"Je ne sais pas, parce que c'est ton souci et pas le mien(Ban sani ba, domin matsalarka ce ba tawa ba!")
Ta amsa masa still da tsawa hawayen da take boyewa suka sillobo ta gefen oily eyes dinta da hawayen
suka qarawa sheqi

" assez !(ya isa!)" Ya fadi cikin tsawar data bada amsa kuwwa a dukka wajen da husky and deep voice
dinnan nasa,zuciyarsa nason hasala da harzuqa,idanunsa a hankali na son fara sauya launi,tabbacin ya
fara shiga bacin rai kenan. Kaman an watsa ma sassan jikinta ruwan sanyi haka tsawar tasa ta saukar
mata,tayi mugun ratsata fiye da yadda take tsammani,har dai data kaita ga runtse idanunta gam saboda
yadda sautin ya shiga kunnenta da kyau

"Wuce ki zauna!" Ya sake fadi cikin gigita,sai kuma ya kasa tsaiwa jiranta,ya sake sanya hannunsa ya riqe
nata hannun da kyau ya soma yin gaba. Sai a sannan ta bude idanunta,so take ta tirje masa amma kuma
qarfinta da gabbanta ke dashi sun gaza bata hadin kai,da sauri sauri yake riqe da ita har zuwa qofar
babban falon,ya sanya qafa ya tura qofar da dan zafinsa ya shige yana jan hannunta zuwa ciki

"Ka sakeni nace!" Ta sake fadi itama tana bude muryarta da kyau,zuwa lokacin hawaye ya gama wanke
mata fuska
"Cool down maina......kabi a hankali.....kabi a sannu" abinda zuciyarsa ta soma nanata masa kenan. Sai
ya fara furzar da iska da sauri sauri daga bakinsa yana fatan zuciyarsa ta saisaita,daidai sanda ta sake
juyawa da sassarfa,sumar kanta na lullube fuskarta ta nufi qofa. Taku biyu rak ya cimmata,ya rigata dora
hannu akan handle din,ya maida qofar ya kulle ya murza key ya zare ya jefa aljihunsa,falon ya qara
duhu,shuru ya sake ziyartar wajen,ba motsin komai sai bugun zuciyoyinsu guda biyu,abinda ya darsa
tsoro a zuciyarta kenan,ta shiga tuna wadancan ranakun da abinda ya faru da ita,sai taja da baya tsoro
yana cika zuciyarta,amma tana qoqarin bawa kanta qwarin gwiwa.

Ta ritsashi da dukka idanunta kamar yadda shima ya ritsata da da shanyayyun idanunsan nan da
suke birkice,birkicewar da taso yima sultana kama da birkicewar wancan lokacin,abinda ya dinga qara
adadin tsoronsa cikin zuciyarta kenan.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[15/06, 11:54 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 64
Kaifin idanunsa ya rage mata ta hanyar lumshesu,yayi qoqarin yin gyaran murya koda kalaman
da yakeson gaya matan zasu fita dai dai

"Zan barki ki wuce ciki ne kawai SULTANA idan kika tsaya kika saurareni mukayi magana" ya fada da
muryarsa data lanqwashe qwarai tayi wani irin sanyi. Kai ta girgiza tana jin tsanarsa na sake kai mata
iyaka,to me zai ce da ita?,me zai gaya mata ma?,wanne bayani garesa?,batajin akwai wata kalma da zata
fita daga bakinsa wadda zata yi daraja ko ta samu matakin yarda a wajenta

"Bazan saurareka ba Aliyu,bazan taba sauraronka a nan dakin ba,don kai ba abun yarda bane......da
shigen wannan salon ka cutar da rayuwata a baya" ta furta kukan gaske yana qwace mata ba hawaye ba
irin na dazu

"Cutar dake kaman yaaya?" Ya fadi da sigar tambaya fuskarsa na nuna gaskiyar rashin sanin cutarwar.
Wani kallo ta bishi dashi harara takeson gasa masa 'yar gaske da zai fahimci a yanzun shi ba kowan kowa
bane cikin rayuwarta amma kuma idanunta sunqi bata hadin kai

"Kince fyade nayi miki wancan karon,amma zuwa yanzu ina fatan kinyi gamsuwar da zaki fahimci
haqqina na na karba......tunda da gumina......da kudina a matsayina na dan makaranta na biya
sadaki.......zan iya yarda idan kikace nayi abun ne ta yarda ya dara shekarunki......but har a gurin Allah
bani da laifi.......wannan kuma bazai zama hujjar da a yanzun zan dinga baki dama kina gayamin dukka
maganganun da suka zo kanki ba,bazanyi tolerating rubbish ba.......dole dole kisan matsayin da Allah ya
bani a kanki......ina buqatar zama muyi magana dake ta fahimtar juna.......zan nema afuwa a duk guraren
da kike ganin na saba miki" batayi shirin zama ba amma sai data koma da baya ta zauna saman
kujera,batayi tunanin yana da zarra da qarfin hali har haka ba,batayi tunanin akwai lokacin da zayazo ma
ya tsaya a gabanta ba bare ya fadi mata ire iren wadannan maganganun,yanzun yana ganin laifinsa da
qanqanta har haka?.

Kaman yasan me take saqawa a ranta sai ya maida hannayensa yana goyesu a bayansa,sannan
ya fara takowa zuwa kujerar da take zaune a kai, tahowar tasa data sanya hanjinta kadawa,zuciyarta
kuma na saqa mata tsaf zai iya maimaita aikata abinda ya aikata a baya. Wani irin hautsinawa tayi
gefe,sai gata ta sauka a qasa,zata miqe ya cimmata,ya sulale shima a hankali ya tsugunna a
gabanta,tsugunnon da ya basu kusanci qwarai
"Kar ka aikata" ta fadi kuka yana qwace mata sanda ya miqa hannu da nufin janye mata gashinta daya
warwatsu har kusa da idonta

"Halalina ce fa" ya fada calmly

"Bani da wani miji.....ni ba matar kowa bace!" Ta fadi tana jin zafin kiranta da matarsa da sukeson gwada
mata qarfa qarfa shi da goumar

"Am really sorry.......kowanne kalan ban haquri kikeso ki fadi zan miki shi SULTANA" Kaf gidan yafi kowa
iya furta sunanta,kaman saboda shi aka halicci sunan,kaman sunan yasan shine wanda ya zaba mata shi.

"Bana buqatarka a rayuwata......ka fitamina a rayuwa"

"Am so sorry sultana.......ni benazeer da batoul muna da buqatarki......kiyi haquri ki yafemin,let build a
home ni dake for our kids please" sosai ta bude fararen idanunta da suka koma kalan manja a kansa

"Which kids?,baka da wasu yara,yara yaranane......kaman yadda ni ba matar kowa bane.......zasu samu
wani iban,nima zan rayu da duk mijin da na zabawa kaina wanda yasan darajar rayuwa da mutuwa" wani
ciwo maganar take ji masa a zuciyarsa har yanajin kamar bazai iya ci gaba da dauka ba

"don't say that please 🙏" ya fada idanunsa a rufe gam

"Bazan daina fada ba!.....bazan daina ba,that's my truth!" Dole ya sake bude idon nasa a kanta a Karo
kusan na uku

"Baki canza ba har yanzu sultana?,da gaske akwai sauran wani gyaran?" Tambayar da yayi mata kaman
ya sanya sarqa ya kulleta ne,tanason ta fahimci abinda yakeson cewa ta kuma gaza fahimta din,sai kawai
ta sanya hannayenta duka biyun ta dafe qasa taja da baya sannan ta miqe tana son dosar qofa
"Ba abinda zai canza a maganata hukuncina da kuma ra'ayina,you better to stay away from me........"

"How can I do that?,dukka rayuwata tana tattare da ke,'ya'yana gudan jinina......matata....."

"Baka da mata.......kalamanka ba zasu taba rusunar da zuciyata ba........ saboda kai din azzalumi
ne.......me take......" Labbanta basukai ga qarasa cewa komai ba suka tsinci kansu tsakiyan tausasan nasa
labban,kafin tayi kowanne yunquri ya hadeta da bango sosai ya kuma sakar mata qarfinsa,sannan ya
sanya hannayensa ya riqe kanta da kyau yana sake kamo labbanta sosai cikin bakinsa.

Kamar ya samu sweet haka ya dinga sarrafasu daga lips nata har zuwa harshenta. Wata muguwar
gigicewa tayi,saboda yadda abun yazo mata a bazata,ta sanya hannayenta ta dinga dukan qirjinsa da
yunqurin qwacewa amma sam bai saurara ba bai kuma dakata ba,duk abinda tasan zatayi don ta dakatar
dashi tayin amma hakan baiyi tasiri ba,sai kawai ta tattara dukka yawun bakinta ta tura masa bisa
tsammanin zai janye. Zut taji ya zuqeshi gaba daya,ya kuma sake zura harshensa cikin bakin nata kaman
ma me neman qarin yawun nata,abun sai ya zafafeta ta fashe da kuka gaba daya.

Sai daya tabbatar dukkan tsoro da mutuwar jiki sun mamayeta sannan ya zame bakinsa daga
nata,tana zaton zata tureshi ta zille sai ya riqe qugunta sosai yana kallonta da lion eyes dinsa da sukayi
matuqar yin laushi. Sosai qirjinsa ke bugawa fat fat har kana iya hangen hakan ta saman rigar kaftan din
jikinsa,hawaye sun wanke mata fuska sosai,yayi mata riqon da ba abinda ke faruwa sai musayar
numfashi da sukeyi shi da ita,ya fidda nasa ta zuqa ta fidda nata ya shanye,idan kuma ta kawar da
fuskarta wani gefen ya sanya hannun ya tallafota,tanata bitar kalma guda da zata gaya masa da zata
sanyashi jin haushi ta qona masa zuciya ya saketa ko bai shirya ba,tana kuma tunanin abinda zata fada
din me zaya haifar mata

"Idan baka sakeni ba zan maka ihu na rantse da Allah" duk ya yadda idanunsa ke lullumshewa amma sai
da maganar ta sanyashi fidda wani sassanyan murmushi me qaramin sauti,riqonta ya qarayi da kyau
yana duban tsakiyar qwayar idanunta. A hankali yakai yatsansa gefen idonta guda dayan yana rayawa a
ransa wataqila wannan shine tabon da ya kusa illata mata idanu. Idon nata ta runtse hawaye sabbi suna
fita. Sosai yaji zuciyarsa ta matse,yaji zafin kansa da kansa sosai,shaidan tabbas yayi tasiri a lokacin,ya
kuma iza masa wutar zafin kai data zuciya sosai a sannan,but......yayi alqawarin shafe wannan tabon
dama lalurar gaba daya muddin yana numfashi
"Da kin kyautamin,kin kuma gajarcemin wahala......anyways......daga yau duk sanda kika taba lips dinki
ko kika kalleshi a madubi zaki tuna cewa ke matar aure ce,kuma uban jarumin uban 'ya'yanki yana
nan......na yarda ni din me laifi ne......duk wata tuhuma zan karbeta hannu bibbiyu......but tsiwa......da
barranta kanki da yarana daga gareni wani abune da zuciyata ba zaya iya dauka ba" harara sosai take
balla masa wannan karon,ta sake tattar qarfinta ta tureshi tana rushewa da kuka sai ya saketa wannan
karon babu ja,ta nufi qofa yana yunqurin budewa

"Nop.....jirana zakiyi ai tare zamu shiga cikin gidan" ya bata amsa yana tattare hannun rigarsa sannan ya
bude toilet din falon ya shige.

Sulalewa tayi ta koma gefe ta zauna tana sake sakin kukan,gaba daya abun nasa yazo mata da
rainin hankali,ta yaya shike da babban laifi ko tace manyan laifuka irin wadannan dukka ya zauna yana
qanqantar dasu a idanunta?,yana abu kaman baisan girman abinda yayi mata ba?.

Ya jima cikin toilet din yana ajiyar numfashi idanunsa kan fuskarsa daya bayyana tar gaban
madubi,emotions da yawa yake gani saman fuskarsa

"Alhamdulillah" ya furta can qasa amma a fili,lallai addu'a ba abun banza bane,bare addu'a gaban dakin
ka'aba?. Ya tsammaci bore fiye da wannan daga wajenta,sai gashi komai da alama zayazo masa da sauqi

(Nidai nace uhmmm malam aliyyu haidara,ba girin girin ba dai tayi Mai,kabi a hankali da sultana😂).

Alwala ya dauro sannan ya fito yana warware hannun rigarsa, idanunsa yakai kanta,sai baice
komai ba ya fara takawa yana nufar qofar.

Key ya zura ya bude qofar sannan ya waiwaya a nutse ya dubeta

"êtes-vous prêt à aller?" Ya tambayeta yana tsareta da kallonsa hadi da miqa mata mayafinta. Kaman ba
zata karba ba amma ta daure ta miqa hannu,sai ya gaza zare idanunsa daga dogayen hannun nata dake
dauke da farar fatar da kamar ka wanke hannu kafin ka taba. Ganin kamar baida niyyan bata sai ta saka
hannu tana zare shi daga hannunsa,dab da zata kammala zarewar yayi caraf ya riqe mayafin yana duban
cikin idanunta

"Daga yau......kada ki sake fita bada izini na ba" haushi takaici,kaman tayita zunduma ihu haka taji,ta
gaza jurewa sai data watsa masa wani kallo. Koda batayi magana ba yasan sarai meye a cikin ranta,shi ya
raineta,duk wani motsi nata koda batayi magana ba yana fahimta,don haka ya sake riqe mayafin da kyau
cikin hannunsa yana kuma sakar mata wani kallon da ya tabbatar sai ya isa har tsakiyar zuciyarta

"Idan da ba'asan inda nake ba,kuma ba laifi idan kinyi hakan,a yanzun ina nan,kuma ina shirye da sauke
duk wani hakkina.....kema kuma dole ki sauke hakkinki"

"Dole?" Ta tambaya cikin salon mamaki tana kallonsa da rinannun idanunta,kai ya daga mata don son
tabbatarwa

"Qwarai kuwa" so takeyi ta gaggaya masa maganganun da zasu yiwa zuciyarsa nauyi amma tata zuciyar
sai ta kwabeta

"Kada ki fara,a nan din daga ke saishi.....karki maimaita kuskuren da kikayi a baya" wannan ya sanya ta
tattaro dukka kalamanta ta hadiyesu,sannan ta sake zare mayafin sai ya sakar mata. Yana tsaye ya
tsareta da kallonshi har ta lullube kanta saidai baiga ta motsa ba,ya fahimci me take buqata,don haka ya
matsa daga bakin qofar yana cewa

"Bismillah" a nutse ta tako zuwa shiyyar ta kuma giftashi, iskar data kwaso din ta watsa masa lallausan
qamshin jikinta wanda ya sanyashi sakin wata ajiyar zuciya yana lumshe idanunsa tamkar yaron da yayi
kukan neman mamarshi har ya gaji. Ko kafin ya bude idanunsa sai ya taras har ta fice ta kuma fara nisa
da inda yake,sassarfa takeyi tamkar wadda ke gudun tserewa mayunwacin zaki. Murmushi ya qwace
masa,kwata kwata sauri bai dace da tsarin halittarta ba,amma sai yayi tsaye,sai data qurewa saurinta,sai
gashi a qididdigaggun taku ya cimmata.

Kamar ko yaushe,qamshinsa kadai ya sanya ta fahimci yana dab da ita,koda ta waiwaya ta ganshi
saita fara qaramin gudu tana nufar sassan bibi,abinda ya bashi mamaki kenan,sai ya qara saurin tafiyarsa
yana biye da ita......baisan me bibin zata dauka ba idan ta gansu a hakan sun shigo tare,koma meye a
yanzun zatace ko zatayi bibin ko a kwalar rigarsa,kome dai meye she's his wife......kuma bazai taba bari
damarshi ta kubce masa ba. A shirye yake ya fuskanci kowanne qalubale ta dalilin haka......komai
tsanani,komai runtsi......

_maina fa da gaske yake_😂

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank
_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[15/06, 11:54 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 65

Bibi na daga tsaye tana qoqarin karbar daffafiyar nonon raqumi me dumi da takansha daga
hannun bilki taji sautin sheshsheqar sultana din,ko kafin ta waiwayo ta iske bibi din ta kuma rungumota
ta baya tana sauke kanta a bayan bibin tana kuma sake fashewa da wani kukan.
"Meye haka?,lafiyarki?" Ta jefa mata tambayar dai dai sanda maina ke shigowa falon. Idanunshi a kansu
kaman yadda bibi itama take kallonsa,saita rasa bakin magana,ta dubi bilki

"Ajjiyemin madarar ki tafi abinki" ta amsa mata cikin girmamawa,ta qarasa kan daya daga cikin tables na
glass dake tsakanin kowacce kusurwa ta kujerun falon ta aza akai sannan ta wuce.

A nutse abinsa ya qaraso cikin falon,ya samu daya daga cikin kujerun ya zauna ya kuma miqa
hannu ya dauki daffafiyar madarar ya kurba. Sosai yayi missing al'adunsu,sosai yayi missing komai da ya
shafi abzinawa,sai yanzu yakejin komai din yana dawowa cikin jikinsa

"Me kayi mata?" Bibi ta tambayi maina tana dubansa ganin yadda kukan sultana ke qara yawa. Sauke
cup din da yakai bakinsa yayi yana dan juyashi a hannu sannan yace

"Ki tambayeta mana bibi.....nidai bansan wani abu da nayi mata ba......"

"Aliyyu" bibi ta kira sunansa na aihini kai tsaye

"Banason a samu matsala ko maimaicen kuskure"

"Ba za'a zamu ba bibi......ba wani abu nayi mata ba,kawai nasan na ja mata kunne ne kadan,tana yimin
tsaki tana kuma gayan magana ba ta hanyar data kamata ba,ina cewa kun koya mana girmama babba
ko?......to don Allah bibi ki sake karanta mata kafin ta fara zaman aure cikin gidanta ta gyara dukka
wadannan dabi'un" maganar tasa saita zama kamar turin wuta,da sauri ya daga fuskarta daga kafadar
bibi zuciyarta tana zugi cikin kuma muryar kuka tace

"Kinji ko?,kinji ko bibi?,ki gaya masa ya fita sabgata ya fita rayuwata,don ba abinda ya hadani dashi,bani
da wata alaqa dashi,kuma ni ba matarsa bace na gaya masa,yaje ya nema matarsa,ki gaya masa yayi
nesa da lamurana,tunda nidai ban shiga nasa hurumin ba" tana kaiwa nan ta saki bibin ta wuce ciki da
sassarfa tana ci gaba da sakin kukanta.
Da kallo dukkansu suka bita,saidai sanda bibi ke dawowa daga nata kallon shi ya dauke idanu ya
fuske din baiso ma bibin ta gani. Rai ta hade tsam tana dubansa

"Waikai din wanne irin yaro ne?,ka dawo da wannan manya manyan laifukan kuma kake tunanin kawai
kai tsaye zamu baka ita?" Idanu ya zubewa bibin ga mamakinta sai taga ya saki murmushi

"To bibi idan baku bani ita ba dafata zakuyi ku cinye?,ni kadaine zan iya da ita bibi,sannan bugu da qari
ma ai nasan kuna buqatar ganin wasu twins din ko?" Turqashi!,bibi ta fadi a ranta,yaushe aliyu ya soma
komawa haka?. Bai taba gwada magana irin wannan ba don haka duk furucin sai ya sanyata ta daburce

"Qaniyarka.....ni kake gayawa irin wannan maganar aliyyu?,zaka maimaitata ne a gaban hamidou
kuwa,kaga shi sai ya dauketa ya bakan" siriryar dariya ya saki,yasan a nan wajen bibi din nasararsa take

"To kece bibi mana,kun dameni da cewa na tafka laifi,laifina daya na rashin bayyana kaina ga kowa na
karbi laifina a bayyane,amma duka sauran abinda ake tuhumata akai ban karba ba ban kuma yarda ba,ke
kika sanya su aba da oncle bashar suka bani lasisin aikata komai fa,sannan a yanzun ki dawo kina min
qorafi bayan abinda kikeson ji da gani kenan,gashi kinji kin gani harda result ma"

"La'ilaha illallahu muhammadur rasulullahi sallallahu alaihi wa sallam" bibi ta jawo dogon salati kai kace
mutuwa ce akayi mata

"To da alama wannan shari'ar nema takeyi tafi qarfina,bari ka gani" ta fadi adan diririce tana juyawa
kaman zata bar falon. Cikin zafin nama ya miqe ya tareta,ya kuma riqeta da kyau yana cewa

"Haba bibita......zo kiji,ai ba za'a yi haka ba" ya qarashe maganar yana zaunar da ita saman kujera,shi
kuma ya koma saitin qafafunta ya zauna yana dan tausa mata qafar a tausashe.

Idanu ta zuba masa,sai yayi mata shuru ya qyaleta har sai da tayi hararar me isarta sannan ya
sake matsowa kadan murya a tausashe
"Duk ki gama hararata bibi..... Allah dai ya rufa miki asiri kawai da baki zubda min cikin yara ba,da
wataqila yanzun ina nan ina shari'a dake" baki ta bude galala,kunya kuma tana dabibayeta,saita watsa
masa daquwa

"Ungo nan.....qaniyarka,wanne shaidanin ne ya gaya maka wannan maganar......nasan ba aikin kowa


bane wannan saina wancan dan banzan goumar baqin buzu" yadda a yau din tayi amfani da sunan da
sultana tafi kiransa dashi ya sanyashi sakin murmushi me sauti

"Kinyi zaton bana bibiye da rayuwar sultana?,kin dauka na watsar da ku da ita ne gaba daya?" Tambayar
da ya jefa mata ta sanyata tsaiwa kawai tana dubansa

"To bari na baki labari" sai ya sauke qafafunta qasa,ya kuma fara gaya mata abubuwan da tayi imanin da
gasken yana tare dasu,da gasken yana bibiye da motsin sultana lokutta da yawa. Haihuwarta tafiyarta
Hassan gwarzo,metron asabe da ya bawa kwangilar kula da sultana da duk abinda takeso tsahon
shekarun da zatayi ta kammala,wanda daga nan ne sadarwashi da ita ta yanke,ya tafi karatun da ya
dauki alqawarin ma daddy daya kubutar dashi daga hannun mutanen da suka so tilastashi shiga aikin
S.S.....ya kuma zo ya rasa number goumar tun ranar da shima yaje visiting hassan gwarzo

"Kowa bai ganni ba amma goumar ya ganni,har yayi wata magana a sannan da na tsammaci zaki dauki
haske(inama kina iya ganin abinda nake gani)" fes maganar ta dawowa bibi,ta kuma tuna sanda goumar
ya fadi hakan yana kallon wani guri daban,duka ta zaci iya shegensa ne kawai,ashe magana yake mata
me harshen damo.

Hirarsu dashi din a yanzun ta sanyayawa bibi jiki,ta kuma fahimci a kame yake a hannun wasu da
sukayi masa dauri me kamar sake don su sakashi cikin aikin da baiso qarfi da yaji.

Ajiyar zuciya ta saki tana lanqwasa yatsunta sannan a nutse tace

"Duk na fahimceka,kuma ka sani bana goyon bayan raba aurenka da sultana....... saidai ko kadan bazan
tilastata zama da kai ba,bazan kuma baka izinin takurata ba,kabi hanyar data kamata ka shawo kanta ka
amintar da ita,sannan kuma uwa uba ka sanya soyayyarka a zuciyarta".
********Tun daga wancan ranar da abun ya faru ta yima kanta alqawari ya daina ganin koda gilmawarta
bare ya samu qwarin gwiwar tsareta da wasu kalamanta da sam basu da tasiri a gareta. Ta gwammace ta
kwanana a daki sannan tayi wuninta gaba daya a dakin. A yanzun hatta da gilmawar benazeer da batoul
ya ragu sosai cikin gidan,saboda bini bini suna tare da maina din,tana sane da komai,amma ta barsu ne
ta zuba masa idanu taga iya gudun ruwansa. Abinda yafi komai yi mata dadi shine,kwanakin da zasuyi
cikin gidan ba masu yawa bane,tasan komai ya kusa zuwa qarshe,da zarar ta wuce Paris ina zaya ganta
bare ya gallabeta?. Bataga wani sakewa tsakaninsa da ama ba bare ta sanya ran zata zauna tayi dogon
zancan da ya shafeta dashi,su benazeer kuwa ko kadan bata taba bari sun san lokacin komawarsun
ba,don tasan su kadaine hope dinsa da zaiji komai daga garesu,musamman benazeer da bakinta
bayaniya shuru,rawan kanta akan daddynta kuma ya fara bawa suktanan tsoro,ko shigowa sukayi
gaidata in sha Allah kafin su fita a dakin sai ta mata zancansa,saidai ta koreta ko ta rakata da harara
sannan ne zata ja bakinta tayi shuru. A zaman da takeyi ta maida kai sosai wajem research yadda zata
zama good presenter akan program dinta, research akan abubuwan da suka shafi al'adun qabilu daban
daban,saidai ta fi bada qarfi akan qasarta ta nijer,don da ita take son farawa,wannan ya sanya duk sanda
ta fahimci bibi ita daya ce a zaune zata je ta dameta da tambayoyi da son sanin wasu tsaffin al'adu da ita
batasan su ba.

Duk wata magana da maina din ya gaya mata a wancan ranar ta azata a mizanin qarya ne,don
bataga wata hanya guda daya zancansa zai zama gaskiya ba. A yanzun ba maina take kallo ba,aliyyu take
kalla,duk wata kalmar damuwa da ita da yake furtawa tana kallonta ne a mazaunin labarin qanzon
kurege,ko kadan zuciyarta ma bata qaunar wani lamari da ya shafeshi,a yanzun da zai sake bacewa bat
kaman wancan karon tayi imani dari bisa dari itace number ta daya a gidan da zata fara murna da hakan.

Su aminata sunyi mita sun kuma yi qorafin rashin zuwanta gidansu har sun gaji,abinda basu sani
ba shine,ita ba zuwa gidansu ne matsalarta ba,damuwarta ta fita farfajiyar gidan tsautsayi ya hadata
dashi.

**********K'arfe takwas na daren ranar tana tsaye cikin kitchen din ama tana qoqarin kammala miyar
tuwon aba. Tun safiyar yau data shigo gaida ama don ba'a sassanta take kwana ba kwana biyu ta karanci
ama din bata jin dadi,wannan ya sanya da yammaci liqis ta fito ta karbi girkin aba wanda bata baiwa
kowa yayi masa sai ita da kanta sai kuma sultanan. Bata kuma baro sassan bibi ba sai data tabbatar baya
gidan shi dasu batoul da a yanzun suka zama qafar yawo,kowacce rana akwai inda suka nufa,guraren
shaqatawa daban daban cikin marad'i harma da niamy kamar wadanda suka kawo yawo duniya. Abun
yana bata haushi, musamman yadda taga kowa cikin gidan ya xuba musu idanu,kamar ma sun samu
goyon baya kenan,wani gun idan sunje su kwana,wani su dawo a ranar, goumar idan yana free kuma
shima ya zama dan rakiya dan iza wuta. Haka zata zauna tayita baqin rai,abun da yake sake bata haushi
hatta da bibi tana yin kamar bata san me yake damunta ba,kusan tanja ce kawai ke tankata,ita dimma
tana bin tanja da ba komai,don tana ganin idan ta furta wani abu game da yaran kaman tayi rashin
kunya ne,amma yana da kyau a dinga duba mata basai tayi magana ba.

Lafiyayyen tuwon shinkafa tayi masa miyar shuwaka da taji agushi. Tadan qara yawan abincin
saboda ama tace tana da buqatar tuwon itama. Ta kammala komai tana shiryawa cikin warmer's tanja
tana tayata.

A nutse yake takowa zuwa sassan ama daga nashi sassan don yayi dinner,yana sanye da wata
baqar hoodie abaya ta maza wadda aka yiwa adon golden din zare,bai sanya hular saman kanshi
ba,wannan ya sanya baqin nannadadden gashinsa na asalin buzaye ya bayyana bisa tsari saman kansa.
Suma ce da ba'a gajiya da gyaranta da kuma kashe mata muggan kudade gurin siyan kayan
gyaranta,kama daga mayuka hair mist da sauran tarkacen kula da gashi na maza.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800
UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[21/06, 9:23 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*


*H U G U M A*

Book 02 page 66

Duk inda ya gifta sai yabar sassanyan qamshin nan nasa me kwantar da zuciya wanda yakan jima
a waje kafin yabar wajen. Tunaninsa da kuma hankalinsa suna karkasuwa,ya gama noticing nata tsaf,duk
wani zaman daki da boyewar da takeyi ya tabbatar don saboda shi ne,shi kuma yana ji cikin jikinsa akwai
wani abu da zai girgizashi ko ya sanyashi janyewa daga qudurinsa. Duk kuwa da cewa ba wani sauyi daga
wajen aba,gaisuwa ce kawai take hadasu, gaisuwar ma zaya amsa masa ita ne da qyar,bibi kuwa tana ji
tana gani ya mata qarfa qarfa,duk abinda zaiyi wanda zai saka ta kulashi shi yakeyi,to kuwa koda batayi
niyyar kulashin ba sai ta kashi. Ama kam zata amsa masa gaisuwa ne ba yabo ba fallasa,daga haka koda
zaman awa nawa zasuyi a wajen muddin dai bai sake cewa komai ba itama bata sake cewa. Zuciyarsa ba
zata iya daukan hakan daga ama ba koda kowa zaiyi masa,don haka ya soke kawo mishi dinner da akeyi
har sassansa,ya tsiri zuwa suyi dinner tare koda ba abinda zai hadasu har su gama. To bare zaiyi wuya su
gama dinner din sun tashi haka,musamman da yake su benazeer suna zuwa ayi tare dasu,sai ya soma
ganin alamun zuciyarta tana sanyi daga daukan zafin da tayi,saidai tanata boyewa ne taqi ta bayyana
hakan akan fuskarta,to koda bata bayyana ba shidai hakan ma ya masa dadi,ya sani kuma tsakanin uwa
da danta sai Allah,tabbas zata sassauto kaman yadda yake fata.

Sanda ya shiga falon babu kowa,baiyi mamaki ba saboda dukka masu aikin cikin gidan daga
kowanne sashe daga magariba tayi suke komawa sassansu,saidai idan kuma an buqacesu,sai na jiki sosai
irinsu tanja da ba'a rabo dasu. Fes falon yake wanda girmansa ya sanya yake dauke da rukunin kujeru
biyu,amma duk da hakan sai yake neman rainsu,ko ina qamshi yake fiddawa dake gauraye da sanyin a.c.
qatuwar tv plasma din dake girke ce kadai keta aikinta. Takawa yayi a hankali ya dauki remote yana rage
sautin ta,yayin da hancinsa ke shaqo masa daddadan qamshin miyar shuwakan. Ajjiye remote din yayi
yana duba lokaci. Bakwai da hamsin da takwas,masallatai dake sallah da wuri dukka sun idar. Kewar
yaran gaba daya ta isheshi,tun dazun suka fita da goumar da yammaci yawonsu saboda yau din shi bai
samu fita ba yana daki yana duba wasu takardu da sardauna ya turo masa ta email dinsa,gashi har
yanzun basu dawo din ba. Bude wayan yayi ya kira goumar din

"Mun kusa da gida,nasan yaranka ka biyo" abinda goumar ya furta kenan yana qaramar dariya cikin
salon tsokana. Qaramin murmushi ya subuce masa,yadan cije lips nashi kadan yana katse wayar. Shi
goumar din baisan banda shi ba ba wanda zai iya lamuncewa yaran har a fita dasu daga gidan har haka
su dade ba?. Number ama ya laluba ya kira,bugu biyu ta daga,muryarta a qasa tayi sallama,ya amsa
mata cikin tsananin kulawa a ladabce

"Na shigo ban ganki ba ama" boyayyar ajiyar zuciya ta sauke. Haidar dinnan dai me tsananin nuna mata
kulawa da kuma kula da damuwarta,har yanzun shine dai,komai har yanzun halayen da dabi'unsa game
da ita da take tunanin sun barshi suna nan ba inda suka je

"Zan fito yanzu zan shiga wanka ne"

"A fito lafiya" ya bata amsa yana komawa saman kujerar dake facing dining area ya zauna yana dan
sauke idanunsa a wajen. Yanason duba me suka dafa din yau amma sai yaji yana gandar haka,ya bude
wayarsa ya kunna data dinsa,sai ya shiga IG yana duba hotunansu benazeer da baya gajiya da kalla.

Kiranta shi ya katse masa kallon hotunan da yakeyi

"Sister" shine sunan da ya bata,wanda ya tabbatar bata taba ganin hakan ya sanya mata ba. Doguwar
numfashi yaja ya sauke qafansa da a dazu take daya saman daya ya gyara zamansa yana tunanin yadda
zai kaucewa doguwar waya da ita,don a yanzun yana da buqatar lokacinsa qwarai,akwai abubuwa kuma
masu muhimmanci da har yanzu bai gamasu ba. Yana shirin dagawa ta katse,yana kuma yunqurin bin
kiran wani kiran nata ya shigo,sai ya daga yana saka wayar a kunnensa

"Hello" ta fada cikin karyayyar muryarta

"Assalamualaikum" ya furta kaman yadda ya saba a duk sanda zai daga waya. Gyaran murya tayi kadan
tana tuno kuskurenta,yasha gyara mata amma saboda sabo tana mantawa.

"Wa'alaikumussalam........zuciyata tanata gayamin cewa da gaske yaa maina bai damu dani ba" ta fadi
har tsakiyar zuciyarta kalaman suna fita,tana kuma ji da gasken bai damu da ita din ba.

"Kada kice haka mana.......ya mummy take?"


"Tana lafiya,amma wunin yau na cikata taf da qorafi a kanka,har sai da daddy ma yaji hakan" idonsa
yadan rufe kadan,bayason abinda mahaifinta zai ga kaman bai damu da rayuwar diyarsa ba,diyarsa mace
guda daya daya dorawa dukkan buri da gatan duniya

"Me yasa?" Ya tambayeta shima

"Saboda abinda idanu da zuciyata suke gani kenan.......yaa maina......inaso ka bani dama na shiga
rayuwarka sosai......nayi maka alqawarin baka dukkan farinciki da kuma soyayya,ka bani dama na soka
yadda ya kamata,soyayyata kadai zata samar maka da kalar farincikin da baka taba riskar irinsa ba" A
yadda take maganar ya shanshano tana fesar dasu ne da gaske daga zuciyarta,yaji mata babu dadi
sosai,ya kuma kasa gane sai yaushe zata fahimci inda shi yafi karkata ne?,sai yaushe zata fahimci
pretending da reality?.

"Wannan damar da kike magana a kanta sai nake gani kamar na baki ko?......but duk da haka kiyi tunani
da kyau laila....karkiyi pushing kanki zuwa abinda zai dinga hurting mind dinki..... please laila" ya fada
cikin kwantar da murya yana fatan kalamansa masu harshen damo zasu warware cikin kwanyarta har ta
fuskanci ina ya sanya gaba.

"Ya maina" ta furta a marairaice

"Laila" shima ya kirata da salon murya kaman me begging wanda ya furta sunan ne yana bude dukka
idanuwansa,idanuwan da basu sauka a ko ina ba sai a kanta sanda take fitowa da qawataccen kwandon
da aka saqashi da wani kalar ciyawar turawa me azabar kyau kalar green.

Sanda ta sanya dukka qafafunta waje zuwa cikin falon taji fitar sunan fes daga bakinsa,bata
gama fahimtar waye a wajen ba sai data kammala fitowar daidai lokacin da ya aza nasa idanun cikin
nata. Janye kallon nata tayi daga kansa,ta kuma dauke kanta zuwa gefe zuciyarta na ayyana mata yau
tayi baqar rana.

"Zan kiraki later" ya furta a nutse


"Is okay....... but ka cika alqawari"

"Zan qoqarta" ya sake amsa mata a gajarce yana zame wayar daga kunnensa. Zuwa lokacin har ta kusa
qofar falon da nutsatsen takunta tamkar ma batasan da wata halitta a falon ba. Bai debe idanunsa daga
kallonta ba har sai data kammala ficewar,sai ya maida idon nasa ya lumshe yana jin wani iri a zuciyarsa.
Ko ba komai,koda bata kuma sanshi ba gaba ai take dashi ko?,kuma ya cancanci gaisuwa

"Kana nan har yanzu?" Ya tsinci muryar ama abinda ya sanyashi ware idanunsa a hankali sannan kuma
ya miqe tsaye yana duban ama din

"Ina jiran fitowarki ama"

"Lafiya" ta jefa masa tambayar tana duban qwayar idanunsa da ta sauya launi,alama qwaya daya tak
dake nuna somi somin bacin ransa kenan

"No.....ba komai, I can't take my lunch bakya kusa" ya fadi yana shafa sumar kansa.

Komai da ya faru kusan a kan idanunta ya kasance,tun fitowar sultana daga kitchen har zuwa
ficewarta daga falon. Idan akwai abu daya da ama keson sultana da gyara a yanzun shine gaida
maina,badon komai ba sai don idanun su batoul,kuma batajin zata bar haka yaci gaba da tafiya kodon
tarbiyyar yaran

"To bismillah mana" ta furta tana nuna masa table din ba tare da tasan tayi hakan ba. Da sauri ya daga
idanunsa ya dubeta,yau din ama ke masa magana haka a tausashe tamkar shekarun baya da yake little
maina dinsa?. Wani abu me sanyi ya tsarga ta tsakiyar bacin ransa,sai yaji zafin da zuciyarsa ta fara yana
raguwa.

"To mu qarasa ama" ya amsa mata yana janye mata wata qaraman kujera daga hanya. Fuska yaga tadan
bata
"Ka fara yin gaba mana". Yadda tayi maganar ya kusa bashi dariya,wato ta gano kanta da kanta,wannan
tausayin dake danqare a zuciyarta yana don fallasa kanta,ita kuma ba yanzu ba,yanzun bata shirya
barinsa ya fahimci haka ba,tanaso yasan martabar sultana sosai.....tanason yaji ciwo akan 'ya'yansa,tana
so kuma PLAN dinta da zai kaishi ga jin wannan ciwon ya tafi dai dai.

Shikam ko iya haka a wannan daren ta biyashi,don haka ya soma takawa har zuwa wajen dining
din,yaja mata kujera yana jiran isowarta ba tare da shi ya zauna ba.

Key ta zura ta bude sassan aba tunda tasan baya nan,ta dauki kwandon tana shiga falon da
sallama duk kuwa da tasan ba kowa a ciki. Tana qoqarin jera ma aba abinci fuskarsa tana mata yawo
cikin idanunta

"Ya salam.....ya salam" ta furta tana yarfar da hannu,ko kadan ko alama batason tunawa da sunansa
bare ta dinga ganin gilmawar fuskarsa,wannan ya sanya take jin dadi sosai yadda take killace kanta

"Mugu" ta fadi qasa qasa tana murguda qaramin bakinta,tamkar wanda takeyi don shi yana zaune a
wajen.

_"Laila........zan kiraki later"_.ta tuna kalaman guda biyu da taji yana furtawa sanda take fitowar. Siririn
tsaki taja tana tabe baki

"Yo daman mutumin da yabar gida ya tafi yawon duniya shekara biyar aiba abun mamaki bane hakan ta
faru dashi" ta samu kanta da fadi qasan zuciyarta. Sai kuma ta sake jan tsakin zuciyarta na mata wani
sabon qunar

"Me ya kaika jiyo abinda bais shafeka ba?" Tace da kunnenta cikin jin haushi jiyo sautinsa ma da tayi har
ta jiyo wadannan kalaman. Tsakin dai ta kuma,ita in banda ama da bata jera mata nata tuwon ba bataga
abinda zai maidata sassan ba,amma dole ta koma din,ama ta cancanci dukkan wata kulawa,domin itama
babu wani nau'in kulawa da bata bata ba sanda take da matuqar buqatar hakan.
"Ama me zan zuba miki?" Ya tambayeta bayan ya tabbatar ta zauna. Wannan din al'adarsa ce dama tun
ba yau ba,daya dawo kuma bai manta da ita ba yaci gaba

"Nan duk abinda zanci yanzu diyata zata kawomin tuwon data yi min". Maganarta kaman jirwaye me
kama da wanka tayi masa,ko bata fada ba yasan tana nufin sultana,don haka sai ya koma ya zauna ya
rungume hannayensa yana jiran dawowarta.

Da wannan muryartata dai da bata taba bacewa kunnuwansa da kuma mafarkansa ba ta sake
sallama a falon. Dukka tsokar zuciyarsa ta motsa,don kafin ta iso jarabbaben qamshin nan nata da baisan
yaushe ta juye haka ba y soma riskarsa. Kamar zuciyarsa tana narkewa haka yaji sanda takunta ke isowa
inda suke,yana muradin juyawa ya kalli takunta da kyau......yanason ganin takun tafiyar wannan sultanar
shine har yanzu ko kuma ya sauya?,amma haka kawai cikin jikinsa yake jin kamar ama na ankare da duk
motsinsa,wannan ya sanya dole ya cinye wannan da jawo wayarsa ya buda yana ci gaba da duba
Instagram dinsa.

"Kin kammala?" Ama ta tambayeta sanda ta iso wajen tana maida al'amarinsa gefe guda gami da tattara
hankalinta akan ama kawai

"Eh ama" ta bata amsa tana ajiye na ama din data fito dasu daga kitchen ta ajjiye qasan dining din

"Sannu da qoqari,ban kula bama ashe abincin yana kusa dani" dan qaramin murmushi maras sauti tayi
tana bude warmer's din

"Sultana" ama ta kira sunanta da wani sauti da yaja hankulansu dukka su biyun,saidai still dai shi din bai
kallesu ba yana ci gaba da danna wayarsa tare da qoqarin kokawa da sabon yanayin da yakeji a dukka
sassan jiki da zuciyarsa

"Naama ama"
"Kin tuna?,duk garin kafiran da ma'aiki yaci da yaqi yana ci gaba da girmamawa dattawan kafiran?,ya
kuma ce maja duk wanda baya girmama manya baya kuma tausayin qanana na qasa dashi tabbas baya
cikinmu?" Fes ta karanci karatun ama din,saita sadda kai a karon farko taji kunyar ama din ta dan kamata

"Kiyi haquri ama"

"Ba laifi kikayi ba" ta tareta da wannan amsar fuskarta Na bayyanar da zallar jin dadinta. Cikin jin wani
irin nauyi da takura tadan juya jikinta sassansa kadan. A zahiri wayarsa yake dannawa,yanayinsa sai ya
tuna mata da shekarun baya,sanda take gaidashi yake bawa banza ajiyarta,bata gaidashi ba kuma ya
zam wani laifi me girma,a zuciyarta ta dinga jin kamar ta bace daga wajen don ta kubucewa
gaidashin,amma kuma ama tafi gaban haka daga gareta

"Barka da dare.....ina yini" ta hada gaisuwar dukka gaba daya. Kansa ya daga yana kafeta da lion eyes
dinsa

"Barka kadai alhmdlh" ya amsa mata shima,sai shigowar batoul da benazeer ya kawo qarshen gaisuwar
qeqe da qeqen.

Kamar ko yaushe da rigimarsu suka shigo,ama ce ta karbi rabiyar fadan. Tanaso ta wuce tabar
wajen amma sai taga rashin dacewar hakan. Da qyar ama ta raba fadan,yana zaune yana
murmushi,saboda hakan bai tuna masa komai ba sai fadan attah da almu. Bata ko bi ta kansu warning
daya take basu a sannan,amma sai gata yanzun tana lalacewa wajen raba fadan jikoki,wannan kadai ya
isa ya gaya masa yawan adadin son da take ma yaran.

Ta qasan idanunsa yake satar kallonta yana kuma qare mata kallo son ranshi ba tare da kowa
dake wajen ya karanci hakan ba. Totally wannan ba sultana bane hatta da zara zaran yatsun hannunta
sun sauya. Ta zama wata miskila ta gaske ba da ruwanta da abinda ke faruwa a kewayenta,don ko
yanxun ma a zaune take tsaf saman kujera tana danna waya sanda ama ke rabon rigimar yaran.

Qarar wayarsa ne ya katse masa daddadan yanayin,iya morewa kallonta kawai daya fara ya
saukar masa da nishadi. A kasalance ya sanya hannu ya dauki wayar dake gabansa,sai ta tsinci kanta da
satar wayar da kallo,ta janye idanunta da sauri tana miqewa. Buqatarta tabar wajen,sam batason
kunnuwanta su dinga ma sha'aninsa shishshigi,hakan tamkar tana batawa kanta da tunaninta lokaci
ne,da hakan gwara taje ta karanta abu qwaya daya da zai zameta jagora a aikin jaridarta

"Na fara jin bacci ne ama" yaji tana bawa ama din amsa sanda ta tambayeta sai ina?,sai ya janye
idanunsa yana maidawa kan wayar.

Suhail ne yake kira,ya kara wayar a kunnensa lokacin da take sauka a hankali daga step din area
din,ya dauka dubansa daga kanta a hankali daya fahimci tana shirin hardewa

"Surprise" suhail ya soma fada yana dan dariya

"For what?"

"Ina nijer"

"Bana wasa dakai" ya fadi kansa tsaye

"Tuwo ne a idonka da baka fahimci code din NIJER ne a number na ba?"

"Ma sha Allah..... but munyi da kai ni xan daukoka a airport fa?"

"Kada ka damu,tunda na sauka a qasar nan karsashina ya qaru......haka kawai jikina yake bani kaman
zanga crush dina fa, yarinyar haram" dogon tsaki maina yaja,har ransa yana jin haushin tada
zancan,baisan me yasa ba,amma yana haushin yaga namiji na yima mata rawan qafa. A nashi ra'ayin ba
kowacce mace namiji ya kamata ya budewa zuciyarsa ba,qalilan ne suka cancanta

"Zaka iya qaryata zancena ko ka gasgata,nidai gaskiya na gaya maka......ka turon Adress zan taddaka har
gida,zan baro niamy gobe in sha Allah"
"Karka damu,kana isowa airport ka kirani zanzo na daukeka"

"Yayi......godiya,sai na qaraso".

*_Tofa,ga suhail nan zuwa,ko ya zata kaya?_*

[21/06, 9:23 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 page 67

Tsaye yake jikin motarshi dake cikin tashi da saukar jirage na garin marad'i cikin shigar cikakken
buzu da ta fidda sigar kyau da cikakkiyar kamalar da yake dashi,yadda rawanin ya zaunawa kansa kadai
abun burgewa ne,kyawawan idanunsa da hancinsa da bai cika tsaho ba sun zauna das saman fuskarsa.
Sumar fuskarsa na kwance luf, zakayi tsammanin usulinsa balarabe ne bawai ba'abzine ba.

Wayarsa ce a hannunsa yana sauraren laila,sam ya rasa amsar da zaya bata,daga jiya zuwa yau
gaba daya ta soma rikice masa kamar wadda ake mintsinin zuciyarta

"Na fara kaiwa stage din da bazan iya juriya ba......ban taba cewa inason kowanne namiji ba saikai please
maina......ina gaya maka da gaske ne,i really love you......kuma zaka iya ganina a nijer any moment"
zagayayyun lion eyes dinsa yadan fidda kadan,tazo nijer ta qara wuta fetur?,yana kan lallaba aba fa har
yanzu?,yace masa meye?.

"Cool down laila.....na fahimceki,amma banason kina zafafawa haka da yawa......kibi komai a sannu"
idanunta ta lumshe tana dora hannunta saman qirjinta hadi da fidda siririyar iska daga bakinta
"Don bakasan yadda nakeji bane ya haidar......shi yasa kake cewa haka,ni dama kawai nake buqata ka
bani cikij rayuwarka,basai ka tayani ba"

"Ki nutsu please......ga suhail can ya iso,zan daukeshi mu wuce gida,zamuyi waya in sha Allah"

"Nadai kiraka as usual" ta fadi murmushin yaqe yana fita daga fuskarta,sai ya rasa amsar da zaya bata.
Cikin kafatanin rayuwarsa sam sam bai bata soyayya ba,bai kuma san ta yadda zai tattaro wannan kaya
da laila keson aza masa ba,shi dukka dabararsa akan aikinsa take,a kanta ta qare,so baqo ne shi ta
wannan fannin

"Ba damuwa,kiranma wata damar ce,na gode da ita,bye......take care dear" ta furta a hankali tana katse
kiran.

Iska ya furzar shima yana gimtse kiran,ya sake daga kai yana hango tahowar suhail,sai ya dan
tashi daga jikin motar ya soma nufarsa tare da qoqarin sanya murmushi kan fuskarsa.

Wayar ta ajjiye gefe tana cusa yatsunta cikin sumarta hadi da jan iska sosai cikin hunhunta. A
hankali Sarah ta miqa hannu ta dafa ta

"Duka wannan daga qafan da zagaye zagayen idan nice bazan iya shi ba......aliyyu yana ganin kima da
martabar mahaifinki ya yayanki,me yasa ba zakiyi amfani dasu ba?,ina kyautata zaton wannan kadai ce
hanya da zaki samu yadda kikeso ba wani dogon kwana kwana,ba cutar dashi kikayi ba ai,sonshi
kike,kuma kina da tabbas a soyayyar da kikeyi masa,sannan kuma zaki bashi duk wata kulawa data
dace,anayin aurenku ya samu yadda yakeso namiji ne fa,nan da nan zai mance matsayarsa ya biye miki
kuyi soyayyarku me dadi" daga fuskarta Laila tayi tana duban sarah

"Nafison ya nutsu ya gamsu da kanshi kafin akai wannan matakin sarah......amma kuma na fara sarewa
da haka, zuciya ta ina jin tana min ciwo lokaci lokaci,inajin zaiyi wuya gaba kadan muddin ban shawo
kanshi ba......komai zai ya samuna" ido sarah ta fiddo
"Me yasa?,da gatanki?,kuma da chance hundred percent na samunsa a hannunki ki bari ciwo ya
kamaki?,ni zan gayawa mummy maganar nan tabbas" ta fadi tana miqewa. Caraf sarah tayi ta riqo
hannunta

"Kada kiyi haka sarah don Allah,aminci na dake yasa na gaya miki sirrin da ya shafeni,a zaton mummy
yayi accepting soyayya na ne, soyayya mukeyi,please ki barsu a haka" a sanyaye ta dawo ta zauna,saita
kasa cewa komai daga ita har laila din.

Hannu ya miqawa suhail sukayi shacking,idanun suhail a kanshi ya soma magana

"Kai mutumina......ya naga kaman nijer na shirin karbarka fiye da ko ina?,kaga yadda kake zama fresh?"
Dan tureshi baya kadan yayi yana amsar luggage dinsa ya soma ja sannan ya bashi amsa

"Indai kaine zaka fadi fiye da haka,ka wuce muje ko na tafi da iya jakarka" ya amsashi yana fara takawa
don barin wajen

"Baqonka annabinka dai,muddin kace zakamin wannan halin naka zan koma inda na fito"

"Ga fili ga me doki ai" ya kuma bashi amsa,sai suhail din ya saki dariya sosai. Indai shida maina ne sun
saba irin haka,sardauna ne sam baya jurewa irin wannan wasan,wani lokacima shi yake zama dan rabiyar
fada a tsakaninsu.

"Bayan wancan BMW din wannan kuma yaushe ka siyeta?" Suhail ya furta bayan ya zauna a seat me
zaman banza yana shafa gaban motar,saboda sosai ta tafi dashi,sabuwar shigowa ce da duka duka batayi
wata biyar da bayyana ba

"A satinnan,wannan ne hawa na na biyu gaba daya" ya amsa amsa yana tada motar,sai suka zarce da
hirar motar,qirar motar na sake burge suhail din don shima ma'abocin son hawa motoci ne.
Hayaniyarsu benazeer ne ya farkar da ita daga baccin data koma a sassan ama,hayaniyar tasun
ce kuma ta sanyata baro sassan bibi tunda safe ta dawo sashen ama din,sai gashi bata tsira ba sun sake
biyota da kalar rigimarsu. Qaramin tsaki taja tana saukowa daga gado,ta jawo hularta data dace da
cotton night gown dinta me kauri ta lullube gashinta me santsi,ta zura flip floppy dinta ta miqe tana
nufar qofa,sai tayi punishing nasu yau,tabarar da sukeyi tanason ta fara yawa hakanan.

Tana bude qofar dakin nata ta hangesu suna fita daga lobby din,duka su biyun kamar ko yaushe
kamar kuma kowanne lokaci sanye da pink pyjamas masu wando kawunansu fake da tafkeken pink
ribbon da yazo cikin mahadin kayan, qafafunsu wasu lausasan slippers ne rufaffu duka cikin set din
kayan sukazo,wannan kusan shine shigarsu daga dare zuwa safiya,tana kuma kalla tasan lallai basuyi
wanka ba sai uban karadi da suka cika gidan dashi,basa ma duba cewa ama bata jin dadin. Maida qofar
tayi ta rufe bayan ta fito daga dakin,kai tsaye tabi qofar fita daga lobby din inda zata sadata da falo.

A tsaye ta hangesu a dining area kowannensu dauke da mug dinsa wanda ke dauke da sunansa
baro baro a jiki,tanja na tsaye tana qoqarin hada musu juya madarar data zuba musu a oat,su kuma baki
abun magana sai sambada mata zance sukeyi

*BB" ta kirasu da sunan da goumar ne ya fara rada musu,zaiyi kuma wahala kaji ta kirasu dashi din. A
tare suka daga kai suna dubanta,sai ta daga hannu ta yafitosu,ba jinkiri suka soma saukowa daga dining
din suna nufota.

Kamar yadda suka koya suka kuma tashi dashi,dukkansu rusunawa sukayi suna gaidata da
harshen faransanci da ya zauna a bakunansu

"bonjour, tu t'es réveillé sain et sauf ?"

"bonne santé" ta amsa musu tana murza goshinta saboda hatta gaisuwan ma kowa so yake yaga shine
ya fara yi mata

"Ihun mene ne kukeyi haka?,kowa yana bacci?" Junansu suka kalla,don a wajensu yanzun sha dayan
safiya ba za'a kirata safiya ba,basu iya baccin safe ba Sam,barsu da baccin rana dai
"Batoul ce......"

"Allah bani bace aunty........bena"

"c'est assez(ya isa haka)" ta fadi yana daga musu dogayen yatsunta,don ta tabbatar idannta tsaya tana
kallonsu sunyita yi kenan.

"Banason na sakejin hayaniya,yau zamuje gidan tante aminata da tante yasmine......but.....duk wanda ya
qara cika mana kunne zaiyi gidan gidan nan ne" murna sosai ta kamasu harda tsallensu,duk kuwa da
cewa already goumar ya kaisu.

Qarasowa tanja tayi tana murmushi

"Ai gwara kije din gaskiya kafin lokaci ya qure"

"In sha Allah yau zanbi mutanen gidan......ina kwana tanja?"

"Kin tashi lafiya?"

"Lafiya alhamdulillah ya yaran?" Ta tambayi tanja data fara raba musu oat din,don kullum tanjan takan
tambaya kwanansu tare dayi musu sannu ko ita ko ama

"Lafiya qalau alhmdlh"

"Ma sha Allah......ama bata samu fitowa bane?"

"Tana ciki kam,tunda ta fito tare dasu batoul ta barsu a nan"


"Badai jikin ba?" Ta tambayi tanja cikin kulawa tana takawa zuwa tsakiyar falon tana qoqarin daukan
madarar dake ajjiye tana tsatsafar sanyi,da alama an ajjiyeta ne tasha iska. A kwanakin shan madarar ne
yakeson dawo mata sosai,wani abu data bawa shekaru sosai rabonta dashi

"A'ah jiki alhamdulillah mana,naji ma tana waya dazun kamar tace zata leqa shagonsu benazeer don
tana da lissafe lissafe dasu"

"To alhamdulillah,bari na dubata " ta furta tana wucewa kai tsaye zuwa dakinta dake benen saman
sashen,don tasan aba baya nan,tun daren jiya sukayi sallama akwai gajeruwar seminar da zasuyi,koda
kuma yana nan din sunfi zama a sassansa dake manne da babban falon ama din.

Da sallama ta tura dakin ta shiga,ama dake zare tattausan socks din dake qafarta ta amsa
mata,idanunta akan sultana din. Duk sanda zata kalli fuskarta sai ta samu kanta da yi mata addu'a,Allah
ya dawwamar da farinciki cikin rayuwarta,dukkan wani qalubale da cakwakiya da basu da mafita a kanta
Allah ya bada hanyar warewarta.

Da kwantacciyar fara'arnan me laushi saman fuskarta ta qarasa gefan sofa bed din ama ta rusuna
har qasa kaman yadda ya zame mata al'ada tana gaidata,can qasan zuciyarta tana jin wani dan nauyinta
da a yanzun takanji kuma har yanzun batasan meye dalilin hakan ba,tadai alaqanta hakan da girma da
kuma gankali dake sake lulluneta kullum kwanan duniya,sannan uwa uba takan tuna da wasu abubuwa
da suka faru tun kan cikinsu benazeer din zuwa haifesu da tayi. Bayan bibi da tanja da tayi rainonta duk
gidan ama itace mace ta biyu data taba ganin jikinta zahiri,tayi biqinta ta kuma yi jegonta kamar jaririya.

[22/06, 1:28 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 68

sannan ta bita da tambayar jikin nata


"Alhamdulillah na samu sauqi" itama ta amsata cikin kulawa

"Allah ya qara afuwa yasa kaffara"

"Ameen ya hayyu ya qayyumu" ama ta amsa mata tana shafa cleanser a fatarta,da alama shirin shiga
wanka takeyi.

Tadan dauki mintuna suna tattaunawa da ama din wanda kusan duka akan komawarsu ne da
kwanaki kadan suka rage,sannan ta miqe tana cewa

"Zanyi wanka ama,yau din naji kaman yaran gidan nan suna cewa zasu gidansu aminata,zan daure na
leqa kada mu wuce banje ba,bansan kuma sai yaushe zan dawo ba" kai ama ta gyada

"Eh gaskiya yana da kyau,saura kadan atta ya karbi key din motar da kike hawa,na hanashi nace ya dauki
wata wannan din duk bubbugemin mota yakeyi,bai iya tuqi a hankali ba" murmushi ta danyi kadan

"Da kin bar masa ama,nima tunani nakeyi nabi motocin gida"

"A'ah bashi yiwuwa,nex time idan mun dawo ma dole a siya mota a ajjiye miki,ko don su benazeer da
suke tasowa" ama tayi maganar tana cirar key din ta miqa mata

"Idan bakijin driving ma ai almu yana nan,saiku fita tare" hannu biyu ta saka ta karba,koda yaushe
kulawar ama a kanta daban take,ta banbanta da wadda take bawa 'ya'yan cikinta ma.

Tana komawa daki ta wuce bandaki,don tana fitowa suka hadu da ummeeta dake shaida mata
"Tante.....ba zamu wuce sha biyu zuwa daya ba zamu dawo" tace da ita. Cikin nutsuwa ta fidda bath set
dinta,tsadajjen shower gel da sauran tarkacen wanka wanda kusan ama ce nauyin komai,sai daga bisani
da tayi hankali ta soma saving abinda take samu take wuf tayi wasu hidindimun kafin ama din takai ga yi
mata.

A nutse ya wuce gate din farko na gidan,ya kuma zarce sashen ajiyar motoci dake gidan ya fara
yiwa motar tasa mazauni. Tunda suka shigo gidan suhail ya kasa cewa komai,yana dai bin sassa sassa na
gidan da kallo yana mamakin ya za'a yi mutumin da ya fito daga mansion house na alfarma irin wannan
ya zabi yayi rayuwa qarqashin wani kuma yazo masa a yaronsa?.

Sanda ya kashe motar yake qoqarin cire seatbelt suhail ya kasa haquri lokacin da wasu security
dake sanye da uniform suka gaidashi suka wuce

"Mamaki na yaketa kamani fa haidar,na kasa nayi shuru" qaramin murmushi na gefan baki maina ya
saki,ya sani dole ne suyi mamaki,tsahon zamansu tare shekara kusan hudu ba wanda yasan asalin
wayeshi,ba kuma wanda yasan komai daya danganceshi,illa dai ama aba da sunan sultana da suka
sani,shima din cikin mafarkanshi ne da yakeyi wadanda sukan bayyana masana a zahiri wani lokaci idan
yana baccin har ya ambaci sunansu.

"Zaka sani ai yanzun ko?"

"Sardauna zaifi kowa yin mamaki" suhail ya fadi yana bude murfin motar kamar yadda maina ya bude na
bangarensa.

Cikin atamfa ta shirya kanta riga da skirt me launin army green da adon light orange kadan a
jiki,ya lullube kanta da Chantilly veil daya dace da shigarta,siraran abun hannu da wuya ta sanya da sue
mahadi da agogon da zoben hannunta,kaman yadda jakarta da takalminta dukka suka kasance na
kamfanin Hermes brand hakanan turarenta dukka na kamfanin ne. Kusan komai nata tafi ta'ammali da
wadannan Brand din guda biyu Hermes ko saint Laurent. Sosai fuskarta ta fita das cikin daurinta data
kawoshi gaban goshi,qirar jikinta ta fita da kyau saboda yadda driver din ya qware sosai wajen fidda
shape din dinki,ta fita a bahaushiyar nigeria zam,ta kuma yi kyau ainun,saboda shiga ce da ba kasafai ta
fiya yinta ba. Tafi ganewa dogayen riguna a yanzun abayas sai English wears masu skirt ko budadden
wando irinsu palazzo.
A nutse ta fito daga dakinta ta samu ama tana shirin yin makararren breakfast dinta saboda bata
sauko da wuri ba. Dubanta ama din tayi,a yau din karon farko taji kishi ya darsu a ranta. Irin kyan da
sultana din tayi tasan ba kowanne namiji bane zai iya dora idanu a kanta yaso janyewa ba tare daya sake
marmarin kallonta ba,komai nata cif da cif Masha Allah,kama daga yanayin tsaho da halittar qibar
jiki,batayi qiba ba kaman yadda sam sam bata da rama,idanunta sun sake fitowa sun kuma qara wani
haske sosai,santala santalan qafafunta da hannayenta dake dauke da shimfidaddiyar fata dake nuna
zallar hutu da ta samu

"Tun dazun suke jiranki,amma nace musu suyi gaba baki kammala shiryawa ba,su benazeer din ma
maybe sun bisu,don an shiryasu,nasan kuma zaiyi wuya su iya tsayawa jiranki"

"Shikenan kam,na huta da rabiyar fada" ta furta tana dariya. Murmushi ama ta saki tana mata fatan
dawowa lafiya tare da binta da kallo. Ajiyar zuciya ama ta sauke sanda ta fita din,a wannan yanayin ta
tabbatar idan haidar ya ganta zaiyi wuya ya iya shanyewa,tasan tsananin kishinsa,wanda shine yayi
musabbabin tilastawa qannensa sanya atamfa ya kuma sanya aka bayar da duk wani English wears
nasu,suka kuma dinga fada da samun sabani da sultana.

"Mu wuce ka fara hutawa tukunna saika shiga cikin gidan" maina yace da suhail yana nufar sassansa

"A'ah,a ina ake haka?,kazo baqunta kaqi fara duba kowa?,fara kaini wajen grandma tukunna sai mu
wuce wajen ama din" qaramin murmushi maina ya saki

"Bibi rigima,Allah yasa ta barmu mu fito da wuri,kasan dai zuwa yamma zamu shiga company mu duba
engines dinnan ko?"

"Ina sane"

"Alright" ya furta a taqaice,sai yayi kiran daya daga cikin security din gidan,ya bashi luggage din hade da
key din sassan nasa yace ya saka masa a ciki yabar gurin a bude yanzu zai shiga.
Tare suka jero har suka isa sasaan bibi,sun sameta a falo tana ta fada,fadan kuma da maina
yasan rigima ce kawai irin tata,kayan sawa take warewa tana fadin wannan batason ayi musu guga,a
qyale mata abunta haka

"Ayita danawa kaya wuta b gaira ba dalili" ta sake jaddada mitarta daidai sanda suka shigo falon,ta daga
kai tana amsa sallamarsu.

Tun asali mutum ce meson baqi da kuma girmamasu,wannan ya sanya ganin maina tare da wani
saita dan saki fuska,maina din ya qaraso kan kayan yana duban yaron dake musu gugar

"Kwashe kayan gaba daya,kaje ka fidda duk wanda tace bataso a goge din a dawo dashi ciki"

"In sha Allah" matashin ma'aikacin ya fadi yana duqawa ya tattare kayan yana fita dasu,sai ta koma ta
zauna idanunta akan suhail

"A ina ka sake samo mana bafullatani?" Maganar ta bawa suhail mamaki, baiyi zaton zata gano
bafulatani bane shi nan da nan,lallai tsohuwar nada kula sosai

"Hala bai baki labarina ba?"

"Shin kaine suhail?" Ta jefa masa tambayar sai ya qarasa sakin murmushi

"Nine bibi,barka da warhaka" ya soma gaidata cikin girmamawa yana murmushi,qarasa sakin fuskarta
tayi tana amsawa,sai tahau shelanta kiran masu aikinta

"Nayi baqo,a kawo masa abun tabawa". Tace da masu aikin nata.

Yadda suke gaisawar kamar sun jima da sanin juna ya bawa maina mamaki,daga dai yanayin
yadda ta saki jiki da suhail har hira na gudana tsakaninsu ya tabbatarwa maina haduwar jini ta qullu
tsakanin bibi da suhail,sai maina kawai ya sanya kunne abinsa yana jin yadda suhail ke kwasar bibi suna
hira,da yake shima gwanin barkwanci ne idan taku tazo daya,itama kuma ama din tana da son
barkwancin.

Har ta sanya key ta bude motar ta kuma zura jakarta a ciki sai ta tuna aminata tace tana da
ajjiya wajen bibi. Murfin ta maida ta rufe,ta soma takawa zuwa cikin gidan tana gyara yafen mayafinta.
Dab da zata shiga sasaan bilki data karbo maqullan sassan baqi a wajen bibin za'a gyara ta fito,ta bawa
sultana hanya tana fadin

"Kece qarshen tafiya kuma kece wadda kadai bata taba zuwa ba" murmushi sultana ta saki

"Yanzun zan wuce in sha Allah,yauwa......don Allah ina samun daffafiyar madara idan na dawo?"

"In sha Allah za'a hadata"

"Na gode,bari na qarasa" ta fadi tana sanya kai falon.

"Shekar kusan hudu bibi wannan jikan naki gashinan,bai tab......." Maganar ta tsaye masa a maqoshi
sanda sassanyan muryarta tayi sallama cikin falon.

Kusan a tare idanunsu suka sauka a kanta,suhail da maina,mabanbantan feelings kuma suka
sauka saman zuciyar kowannensu.

Da kallo daya tak ya gama karance shigar dake a jikinta,don shi din mutum ne me kaifin basirar
dauke komai hadi da ankara,sai ya maida idanunsa ya lumshe zuciyarsa tana bugawa,wani irin kishi yana
mintsinarsa har kaman zai kasa controlling kansa.

Suhail kuwa gaba daya idanunsa ya zube mata,sam bata lura dasu ba dukka su biyun har sai data
qaraso tsakiyar falon. Kasa haquri yayi yakai hannu yana tabo maina zuciyarsa tana bugawa. Fes ya bude
idanun nasa,saidai basu sauka a ko ina ba sai akan sultanar. Sarqewa da tafiyarta ya fara yi ya tabbatar
mata da idanu da yawa a kanta,tun shigowarta falon qamshinsa ya shaida mata akwai mutum ta
wajen,inma yazo ya tafu ko yana zaune a wajen,ta watsa fararen idanunta cikin falon don batason tabi ta
gefan da yake yayin da take cema bibi

"Bibi ta.....zan wuce duk sun tafi sun barni,saqon aminata". Kaiwa qarshen maganarta yayi daidai da
tuntube da tayi hakanan

"Subhanallah......kula kada ki fadi" suhail ya fada da hanzari har yana dagowa daga saman kujerar da
yake kai kaman zai tallafe ta. Maganar da yayin yasa ta lura da zamansa a wajen,ta juya fuskarta
sashensa ta masa kallo daya tak sannan ta janye idanunta tana ji a jikinta kamar tasan fuskar,kamar sun
taba haduwa a wani waje daban taci gaba da takawa gaban bibi. Dukka kaifafan idanunsa ya zubewa
suhail,motsin da yayi kadai a yanzun ya harbawa maina kokwanto da shakka a kansa cikin zuciyarsa

"Why he was so bothered?,don tayi tuntube meye na nuna damuwa qarara haka?" Ya fadi a ransa yana
duban tsakiyar qwayar idanun suhail din.

Idan ya lura,idan kuma idanunsa da gaske suke nuna masa to tabbas kallonsa nakan
sultana,kuma idanunsa na manne da ita tana zama a gefen bibi

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[22/06, 1:28 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 69

"Dama ni ke nake jira,ki shiga dakina daga cikin cupboards din kusa da bandaki ki bude zakiga baqin leda
ki ciro,bansan meye ne a ciki ba aka qulleshi haka" murmushi ta saki wanda ya sake qarawa fuskarta
ainihin kyau,murmushin da ya sanya suhail murmusawa shima yana jin tana qara burgeshi da duk wani
motsinta,ya kuma sanya maina lumshe ido yana jin bugun zuciyarsa yana qaruwa musamman da ya
maida kallonsa kan suhail yaga yadda ya maida hankali a kanta

"Ba fada meye ya kawo gaba?" Suhail ya kasa jurewa ya furta,maganar tashi a karo na biyu ta sakata
waiwayowa tana kallonsa

"Sorry?" Ta furta da alamun rashin ganeshi qarara a fuskarta,saita juya zata wuce ciki amma idanunta
sukayi kuskuren fadawa cikin na maina.

Janye idon nata tayi da sauri hadi da fadin

"Barka da rana,ina wuni" ta furta masa sabo tunawa da girman ama a wajenta,gaisuwar duk a hade
lokaci guda tana wucewa ciki

"Alhamdulillah" yayi qarfin halin fada yana ci gaba da monitoring suhail har sanda ta wuce ciki.

Ajiyar zuciyar da suhail din ya saki dukka tsakanin bibi da maina saida suka dubeshi
"Lafiya ko?" Bibi ta wani abu ya darsu a ranta ta fada tan kallon suhail, murmushin qarfin hali ya saki
yana shafa kansa

"Ba komai,kawai akwai wani abuna ne daya bata nake tunanin kamar na tuno inda yake"

"to alhamdulillah,ai haka akeso" bibi ta fadi tana kawar da maganar gami da jefa masa wata tambayar,ya
nutsu kuwa yana bata amsa tare da sake qanqan da kanshi,don yana da tabbacin zaiyi wuya sultana ba
jikar bibi bace,daga kuma yadda bibi din ta amsheshi o bibbiyu tabbas alamu sun nuna yana cikin nasara.
Ya matsu ta sake fitowa daga dakin ya samu yabi bayanta,a yau basai gobe ba zai sake gabatar mata da
kanshi. Yadda ta kalleshi dai ya nuna sam bata ganeshi ba,amma jikinsa bai bashi haka ba yana ganin
kawai jan aji ne irin na isassun mata irinta.

Zafin da zuciyarsa ke masa ya sanyashi kasa ci gaba da zama a wajen,sai ya miqe tsam yana zube
hannayensa a aljihun rigarshi

"Ina zuwa?" Bibi ta daga kai tana kallonsa qwayar idanunsa na nuna tasirin fushi kadan kadan daga
zuciyarsa

"Zan samu ruwa nasha" ya bata amsa yana nufar hanyar kitchen. Taso ta dago wani abu,saboda indai
ruwa ne gashinan a nan wajen gaban suhail,ta san maina din sosai,tasan kuma akwai abinda ya
tadashi,uwa uba kuma ta karanci mugun kishin nan nasa kwance cikin idanunsa,taga kallon da suhail
yabi sultana dashi,tayi imani wala'alla abinda take ganowa cikin idanun nasa yana da tasiri da wannan.
Tasan halin 'yan kayanta sarai,tsoronta daya kada sanadin kallon ya sanya ya yiwa dan mutane diban
karen mahaukaciya duk da matsayinsa na baqonsa.

Freezer din ya bude ya ciro ruwan gora me sanyi har yana tsatsafa,ya balle murfin ya kafa kai ya
soma kwankwada. Duk kuwa da cewa shan ruwan sanyi sam baya cikin dabi'arsa amma sai daya shanye
shi tasa sannan ya buga ribar ta daki kitchen cabinet din ta fado qasa,sanyin da yakeson ji a zuciyarsa bai
sameshi ba kwata kwata,ya furzar da iska ya ciro handkerchief daga aljihunsa yana share zufan data
tsatstsafo masa a goshinsa,sai ya juya kawai gadan gadan zuciya tana ingizashi yana fita a kitchen din.
Daga qofar kitchen din yana hango bibi da suhail suna ci gaba da hirarsu abinsu. Wani abu ya
tsaya masa a wuya daga kallon fuskar suhail kawai,abinda bai taba ji ba tsahon zaman tarensu. Kanshi ya
kawar sannan ya nufi sashen dakin bibi din kansa tsaye,babu tsoro ko shayin bibi ta ganshi ko wani cikin
masu aikinta.

A nutse ya murda handle din qofar dakin sannan ya tura yana shiga. Tana duqe tana qoqarin
jawo ledar tana mita qasa qasa yadda bakajin abinda take fada din sai dan sound na lallausar muryarta
dake dan motsawa cikin dakin. Jingina yayi da qofa yana qare ma qugunta kallo wanda ya turo sosai
saboda duqawar da tayi,gaba daya qamshinta ya cika dakin,wani irin lallausan qamshi me kwantar da
zuciyan. Baisan ya akayi ba sai siriryar ajiyar zuciya data kubce masa,wani mahaukacin kishinta ya sake
taso masa ya dinga ji kaman zuciyarsa zata zauce,wannan ya sakashi sakin hannayensa daya goye a
qirjinsa ya soma takowa cikin dakin zuwa inda ta ajjiye handbag dinta da key din motar.

Shaqar iska ta gaba da zatayi saita gauraya da qamshinsa,abinda ya haddasa mata mummunar
faduwar gaba,ba shiri ta saki ledar data jawo din,ta miqe tsaye sosai sannan ta waiwayo a nutse fuskarta
a dinke tsaf.

Yana tsaye daga bayan nata,duka duka taku shida ne adadin tazarar dake tsakaninsu su.
Idanunsu suka gauraya waje daya kaman yadda qamshin jikinsu ya cika dakin bibi din.

Yadda take kallonsa fuska a hade haka shima,asalin fuskar maina take gani yanzun a tattare
dashi. Dakiyar nan da hadaddiyar girar nan da yakan cure guri guda duk sanda zai musu hukunci,bakinsa
yakan tsuke kadan a wancan LOKACIN to yanzun ma haka,saidai wannan karon siraran labban nasa dake
da wani irin launi me kyau zagaye suke da gyarraren saje daga qasan habarsa zuwa qasan hancinsa. Haka
kawai taji bugun zuciyarta ya sauya,sai ta janye idanunta tana gargadar zuciyarta da kada ta kuskura taji
shakka ko tsoronsa,don haka sai ta juya tana yunqurin ci gaba da jawo ledar ba tare data ce masa kanzil
ba,duk da yadda tsoro ya mamayeta,kwarjininsa a yau yakeson mamayar dukka qarfinta yakai qafafunta
qas,abinda bata jin zata bada damar ya faru

"Waye kika tambaya da kike shirin fita baki nemi izini na ba?" Har cikin kwanyarta taji tambayar ta mata
banbarakwai,ta ciro ledar daidai lokacin,don haka ta miqe tsaye riqe da ledar tana fuskantarsa

"Izinin wa kika nema?,ko kina rayuwa ne on your own?" Ya maimaita mata tambayar a karo na biyu.
Dara daran fararen idanunta da hasken qwayayen dakin bibi ya qara haskawa,suka kuma fidda ainihin
oily eyes dinta ta zuba saman fuskarsa. Qaramin bakinta ta motsa da niyyar maida masa da dumi,sai
kuma dukka kalmomin data tattara don yaba masa suka fara sulalewa sunayin nasu guri,saboda takowar
da yakeyi zuwa gareta ya haifar mata da fargaba. Batason ya sake taba jikinta ko ya sake kusanto inda
yake,to amma kuma tana jin asarar tsaiwa bashi amsa. Duk taku daya idan yayi fargabarta ce take
daduwa,amma kuma kaman wadda aka kafe a wajen ko aka qullewa baki taqi cewa dashi kanzil.

Sai daya rage tazarar dake tsakaninsu sosai sannan ya miqa hannunsa,miqawar data sanyata
qanqame jikinta a tsorace. Tsaiwa yayi da abinda yayi niyyar yi din yana qarewa fuskarta kallo. Baby face
dake dawo masa da shekarun baya fes cikin kwanyarsa, fuskar sultana sosai ta bayyana,har baisan sanda
wani siririn murmushi maras sauti ya qwace masa ba,ga tsoro ga ban tsoro,ga tsiwa ga kuma tsoron
hukunci.

Tas ya zare mayafin daga jikinta,tana tsaye tana jin yadda kowanne sashe na mayafin ke fita a
jikinta yana barinta gaya,sai daya gama zareshi duka sannan ya dunquleshi cikin hannunsa,yayi kaman
zai cillar sai ya fasa,ya sanyashi saman kafadarsa, lallausan qamshinta kuwa yace salamu alaikum,yadan
lumshe ido ya bude

"Wannan din ba mayafin yafawa bane,duk randa kuma na sake ganinki dashi na rantse da Allah sai na
hukuntaki ko a gaban waye" daga haka ya juya yana takawa a hankali,sai a sannan ta samu nasarar bude
idanunta da suka cika da hawayen takaici tana binsa da kallo,tana mamakin kuma me zaiyi ta qofar
bayan sassan bibi?,bazai fita ta normal qofa yadda kowa ke fita ba?,salon ayi zaton suna tare a dakin?,to
ta yaya ma zata iya iya fita a haka ba mayafi,wanne kallo bibi da baqonta zasuyi mata?,bayan kuma ta
tabbatar sunga shigowarsa?.

Duk sai taji kunyar fita a hakan,ta koma ta bude wardrobe din bibi tana bincike ko zata samu
wani abu da zata yafa itama tabi ta qofan bayan ta fice,don dai ba zata iya fita a haka ba. Allah ya
taimaketa ta samu wani sabon mayafi a ledarsa,da alama cikin kyaututtukan da akewa bibi dinne cikin
'ya'yan 'yan uwa da kuma surukai saboda qarfafa zumunci. Sosai ya dace da kayan jikinta tamkar dama
ta ajjiye ne saboda ita,ta farke ta yafa,sai taga yafi haskata ma akan wancan. Da sauri ta zari handbag
dinta da ledar aminata ba tare data tsaya duba key din motar ba,burinta ta isa gidan ta kuma dawo da
wuri,Allah Allah take kwanakin da zasu bar nijer ta cika ta fice daga qasar,ta gaji da ganinsa kwata
kwata,ya soma shiga rayuwarta wanda ita kuma ba zata lamunta ba.

Da yake tabar qofofin a bude ne sai ta bude front seat,ta zura hannunta da zummar ajjiye
ledan,wanne tudu wanne gangare ta tsinci kanta a ciki, kafin ta gama daidaita nutsuwarta ya miqo
hanunsa har yana shafar qirjinta ya jawo qofar ya rufe,abinda ya sanya numfashinta daukewa na wucin
gadi. Wutar jikinsa ce shima ta dauke tsaf!,sai wani irin shock da ya ratsa kowacce jijiya ta jikinta yabi
jininta,ya furzar da zazzafar iska daga bakinsa yana qoqarin dage dukka baqaqen glass din motar sama.

Tsaf ya dagesu ya miqa hannu a kasalance ya kunna ac din motar sannan ya fara yunqurin tayar
da ita. Sai a sannan hankalinta ya dawo gangar jikinta,tsoro sosai ya mamayeta,qamshinsu da
numfashinsu kawai ke karakaina cikin motar,sai bugun da zuciyarta keyi wanda take kyautata zaton shi
dake zauna a seat dinsa tana iya jiyowa.

*_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875
Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[23/06, 11:19 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 70
Dukka dauriyarta ta tattaro cikin dakiya da son ragewa kanta tsoron dake damunta

"Ban fahimci abinda kike shirin yi ba?,ina zaka kaini?" Ta tambayeshi tana qoqarin duban tsakiyar
idanunsa. Da idanunsa da sukayi laushi qwarai saboda yadda qamshinta ke kassarashi ya kalleta

"Shshshs......fyade zan miki" ya furta kalmar gatse gatse kansa tsaye. Karon farko ta janye idanunta daga
kanshi tana jin wani nauyi yana ratsata. Karom farko da taji nauyi da girman kalmar har tsakiyar
kanta,irin girma da nauyin da bata taba ji tayi mata ba,bugun zuciyarta ya sake daduwa har taji kaman
iska tana mata wahalar shaqa.

Ya zaci zata ce wani abu amma sai yaji batace komai ba,duk da yana iya ganin yadda qirjinta
yake dagawa ta saman mayafin jikinta.

Tana ji tana gani ya tayar da motar,maganganu ne fal cikin bakinta takeson furta masa su masu
tsananin zafi,saidai duk sanda ta motsa labbanta da nufin tofar masa sai wancan ranar ta dawo mata,sai
taji kaman abunda ya faru wancan karon shine zai sake maimaita kansa,haka ta runtsen ido kawai tana
jin yadda motar ke gangarawa tana ficewa daga gidan zuciyarta na mata tsananin zafi.

Sanda yahau kwalta sosai sai ya figi motar kamar me tashi sama,irin dai tuqin nan nasa daya
saba a baya,dama shi din bai iya yiwa abun hawa ta sauqi ba.

Shuru ne ya ratsa motar sosai,ba me cewa da dan uwansa wani abu. Ita din tayi shuru taga
iyakar gudun ruwansa ne,yayin da shi kuma yake fatan taci gaba da zama a haka cikin laqwas din da
tayi,wannan ce kadai damarsa da zai samu furta dukan abinda yakeso ya furta din ya kuma aiwatar

"Sulthana" ya kirayeta da wani irin sauti daya sanya jinin jikinta harbawa da gudu. Sake runtse idonta
tayi tana jiyo yadda qasan zuciyarta ke zafi akansa,yana kuma tuna mata da abubuwa masu yawa da
suka shude. Bakinsa ya bude zai kuma kiran nata saidai kuma kiran wayar laila ya dakatar dashi. Shuru
yayi yana jin wayar tana ringing har ta katse,ta sake kira,dole ya danna accept ya kuma maida wayar a
free.
"Hello dear....." Ta furta da salon karyar da murya tana langabe kai daga can barin da take tana jin
zuciyarta na sake samun rashin madafa game dashi,wanda muddin hakan yaci gaba da kasancewa tasan
tabbas......indai tanason tsira da rayuwarta to takai batun gaba bro da daddy. Muryar tata ta fita tas ta
kuma karade motar har kaman tana amsa kuwa.

"Am on the way laila......i will call you" ido ta runtse,wannan kalmar ta gama haddaceta tsaf a bakin
maina,kuma ta fahimci dukka salo ne na koreta daga yin doguwar waya dashi.

"Alright" ta amsa masa a taqaice tana katse kiran.

Gaba daya ji take kaman ta sauke glass din ta fita ta window din motar,laila.....laila.....bashi da
aiki sai zancanta?,shi ko kunya ma bayaji?,ya gama yawon duniyarsa ya dawo da abokiyar shashanci har
ya bari ta dinga kiransa?.

"Mtseww" taja tsaki tana gyara yafen mayafinta. Sam sam bata dauka tsakin zaya fito ba,saidai ya fita
din da sautinsa sosai. Ido ya runtse yana jin kaifin tsakin kamar an zura masa abu cikin kunnuwa.

A nutse ya rage gudun motar,sai ya koma tafiya slow kafin ya sanya signal ya fara sauka gefan
titi. Mamaki ya cikata ganin yana qoqarin parking qasan wata bishiya cikin bishiyoyin da aka qawata
gefan titin dasu. Bataga wani shop ko masu saida wani abu a wajen ba bare tayi tsammanin wani abu zai
siya. Sanda ya tsaida motar cak ya kuma kasheta sai mamaki ya hanata sukuni,sai data juyo tana
dubansa da fararen idanunta.

A lokacin ya nutsu ne gaba daya ya zuba mata lion eyes dinsa yana kallonta,dauke idanun nata
tayi tana kauda kanta hadi da hadiye abinda takeson fada. Tana ganin bata bakinta da lokacinta ne ma ta
tsaya yi masa magana,shuru shi yafi dacewa dashi.

"Waye kika yima tsaki?" Kasa bashi amsa tayi sai qeya data juya kasa,kwantankwacin abinda takeyi masa
a shekarun quruciyarta sosai duk sanda yake mata fada

"Look!" Ya fada da kakkausar muryarsa


"Kinyi tsaki na farko a waya.....nayi warning dinki,kinyi na biyu yanzu a gabana......karkiyi kuskuren
maimaita na uku......am not your mate..... uban 'ya'yanki ne....yayanki kuma mijinki,hope i made it clear
to you?" Wani haushi ya sake saukar ma zuciyarta,yadda yaketa jero wadannan bayanan da matsayinsa
mataki mataki tana jin kamar ta fasa motar ta fice,saidai tunda suka shiga taji qarar saka security a kulle
take. Bai damu da amsarta ba don yasan tsiyar daya qulla mata a yau din,sai ya juya sosai ya soma
kwantar da kujerar motar ya miqe qafarsa ya kuma yi relaxing bayansa abinsa bayan ya kunna sauti can
qasa.

Shurun da taji yayi yawa ba motsinsa ba kuma alamun kunna motar shi ya sanya ta fara
tambayar kanta da kanta ko lafiya?,banda sauti da AC din da ya bari a kunne ba abinda ke motsi cikin
motar. Ta dinga qoqarin kallonsa ta gefan idanu,saboda batason ta juya ta kalleshi ta bada kanta,da qyar
ta hangeshia a kwance abinsa sambal tamkar yana cikin dakinsa a kan gadonsa

"Wannan wanne irin mulkin mallaka ne?" Ta tambayi kanta da kanta bayan ta duba agogonta taqa a
qalla sun share mintuna talatin a wajen shi bai motsa ba itama bata ce masa ta tafas ba. Ci gaba tayi da
duba agogonta akai akai,taci alwashin ba zata masa magana ba har dai ya gaji da kansa ya tashi motar
sun tafi,saidai kuma duk sanda ta kalli agogon sai ranta ya kuma baci akan wancan bacin ran. Wanne irin
mulkin mallaka ne wannan?,hankalinsa kwance yanata sauya tattausan busar guitar din dake tashi a
motar xuwa nau'i daban daban?,ita ya barta zaune ya kuma tsareta?,bai barta ta tafi ba bayan bata
gayyatoshi cikin rayuwarta ba?.

"Zaka iya bani key din motata ka sauka ni na wuce,ina da wajen zuwa" ta karya billenta daga qarshe ta
furta murya a cunkushe kamar wadda aka yiwa cushen tsumma.

Sirrintaccen murmushi daga can qasan zuciyarsa ne ya subuce masa,dama so yake gaya iya nata
taurin kan da kafiyar,batasan yanzu aka soma ba

"Ni bani da abunyi.....don mun kwana a nan ma ba damuwata bane indai ba zaki koyi manner na magana
dani ba" sake baci ranta yayi,me yake nufi?,ta qasqantar masa da kanta kenan ko.meye?,lallai tarin
neman fitina ce kawai qasan ransa,banda haka na meye zai dinga shiga gonarta har haka?.
Sai daya mula don kansa sannan ya miqe ya zauna sosai,yasa zara zaran yatsunsa yana maida
sumarsa baya,sannan kuma a nutse bakinsa yana ambatar

"Bismillah" ya tayar da motar,saidai a yanzun ya rage gudun da yakeyi sosai dukka hannuwansa dafe da
sitiyarin motar.

Idanunta nakan hanya,tana kallon shimfidaddiyar kwaltar zuciyarta kuma cike fal da tunani iri
daba daban. A hankali ta fara lura hanyar da yake bi din kamar ba hanyar gidan amaren bace,don ta riqe
kwatancen da dunan street din nasu. Tsoro ya sake kamata,wannan karon kuma kai tsaye ta kasa shuru
ta magantu

"Ina zaka kaini?,nan ba hanyar bace" juyowa yayi idanunsu suka hadu waje daya

"Nace miki fyade zanje nayi miki karo na biyu tunda wancan ya amsa sunansa" yayi maganar yana dauke
kan motar suka shiga wani titi na daban da wani irin zafin nama.

Ido kawai ta zuba suna ci gaba da wuce wurare har suka iso babban ginin daya tsaya a gabanshi
yana karbar binciken security kafin wucewarsa ciki.

Idanunta ta daga tana qarewa ginin kallo,sunan data gani daga qarshen sunan dake kafe a
tsororuwar babban ginin ya sanya gabanta harbawa

"Hotel?,to me sukazo yi s hotel?" Ta tambayi kanta da kanta. Kafin ta lalubi amsa har ya gama da
security ya wuce cikin babban harabar hotel din.

Ko ba'a gaya mata ba da ganin tsari da girman wajen tasan hotel ne na manyan mutane masu
hannu da shuni,komai bisa tsari tun daga farfajiyar har tsarin ginin wajen

*_KWANKWASON JIMINA_*
*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261
*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[24/06, 5:14 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 71

Bayan ya daidaita tsaiwar motar,ya zare seatbelt dinsa yana dubanta,kaman zaiyi magana sai
kuma ya fasa,ya bude side dinsa ya fice. D

Bata koda kalli sassan da yake ba har sai da taji ya maida murfin ya rufe, second biyu ta bayar ta
waiwaya da kanta tana duban gefanta.

Cikin takun nan nasa me cike da ginshira da qasaita yake takawa zuwa main entrance na hotel
din,hannunsa guda daya zube a aljihun wandonsa,daya hannun kuma wayarshi da key din motar ya riqe.
Idanunta ta kawar tana tabe tana jan tsaki,tana mamakin irin qarfin halinsa,yanayin komai kamar baisan
ya aikata komai ba,kamar kuma bame laifin komai ba,yanata maimaita kalmar fyade zaiyi mata kamar
wata kyakkyawar kalma me dadin ji da sauraro?,baya ma ko kunyar idanunta bare abinda ya aikata a
baya da ita har yanzun sunan fyade ta bashi?,duk da ta fahimci da gasken ba fyaden bane,sadakinsa na
saifa daya bayar ya sauyawa abun suna a musulunce. Yanxun daya kawota nan din me zaiyi a ciki?,
Tambayar data yiwa kanta kenan kuma bata da amsarta.

Tunaninta ya katse sanda kira ya shigo wayarta,ta bude handbag dinta ta zaro wayar tana gyara
ajiyar cards dinta masu amfani dake ciki. Yasmin ce sarkin zaquwa da gaggawa

"Shuru.....shuru sultana lamarinki sam babu kara fa" yasmine ta fadi cikin zumudi

"Afwan yasmine...... kin ganni nan......" Da sauri ta katse abinda da farko tayi niyyar fadi,sam ta
mance,tana shirin dabawa kanta da kanta wuqa

"Ina hanya bazan wuce awa daya ba in sha Allah"

"Shikenan,ina jira,aminata ma ke take tsumayi"

"In sha Allah" ta amsa mata tana lumshe ido saboda bacin rai daya taso.mata. gaba daya ya sauya mata
akalar tafiya?,wai anya ma ba sassauci ya gani saman fuskarta yake neman rainata har haka ba?.

Tana katse kiran tare da qoqarin sauka daga call logs dinta taji ya bude murfin motar a hankali.
Sam batasan da isowarsa wajen ba don hankalinta baya kai. Idanunta ta daga a hankali ta sauke dubanta
a kansa. Yana tsaye gabanta,cikin cikakkiyar tsaiwar nan tasa dake sake fidda diga da zatinsa. Cikakken
tsayayyen ba'abzine dogo fari tas. Shima ita din yake kalla,hasken rana daya haska qwayar idanunta
dake da sheqi kamar an diga zaiba sai ya bada wani irin haske me kyau,abinda ya masa kwarjini
qwarai,mazantakarsa ta sanyashi shanyewa,ya sassauta kafin nasa qwayar idanun cikin nata
kadan,sannan ya rusuna yana dauke handbag din take saman cinyarta,wanda kafin tayi kowanne
yunquri ya soma takawa yana barin wajen
"Taso mu qarasa"

"ina?" Ta tambayi kanta tana fidda ido waje. Ganin bai waiwayo ba ci gaba yakeyi da shiga ciki,ga idanu
da sukayi yawa a kanta dole ta zura qafafunta waje tabi bayansa. Tana biye dashi saidai ta cika tayi fam
da bacin rai da baqinciki

"Wai me wannan yakeji dashi ne?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar. Yadda suka dinga wuce security
ana checking nasu duk inda suka wuce ya sanya ta sake shiga nutsuwarta sosai amma kuma ranta cike
yake fal da fargabar shigarta wajen,batasan me yazo yi ba,batasan me ya kawosu yi ba.

Elevator taga ya nufa,ya danna ta bude ta shige,sai a sannan ya waiwaya yana kallonta. Ja tayi
ta tsaya,abun ya isheta haka,ya maidata kaman wata raqumi da akala?. Yana tsaye daga bakin qofar ta
yadda bazai bata daman rufewa ba ya kuma tsareta da ido.

"Idan kika qara minti daya a nan wannan karon nine zan miki ihu na kuma tara miki mutane kaman
yadda kika yimin wancan karon" hanjin cikinta taji ya dunqule guri daya,daga yadda taga wajen yadda
yake cike da matakan tsaro idan ya aikata mata hakan ta kade daga ita har ganyenta

"Idan kin damqani a hannun police har na kwana ni a hannun da zan damqaki ko?......." Bai qarasa ba illa
yatsansa daya nunata dashi wani shu'umin murmushi na mugunta na kubcewa daga saman labbansa.

Babu shiri tayi taku biyu xuwa gaba,sai yayi taku biyu baya har ta shiga elevator din ya rufe dasu
suka fara wucewa zuwa floor din daya zabar musu.

Tana tsaye daga bakin qofar dakin take qarewa dakin kallo. Babban daki ne wanda aka wadatashi
da komai na alatun rayuwa. Kana ganinsa kasan vip suit ne na isassun mutane. Idanunta ta dauke daga
kallon dakin ta maida kansa sanda yake qarasawa ciki yana ajjiye key din motar saman bedside drawer
din dake dauke da bed lamp. Wani abu ta sake hadiyewa me tauri daya tsaya mata a wuya tun dazun

"Amma dai kasan inda zanje ko?" Ta jefa masa tambayar muryarta na bayyanar da bacin ranta
"Na sani......ina da buqatar na huta tukunna kafin mu wuce"

"Bana buqatar wani hutu.. wannan abun da kakeyimin ya isheni haka,ka bani key dina na tafi,idan kaso
ka bari sai wata shekarar sai ka taho wannan ba damuwar sultana bace" ta fada tana yarfa hannu cikin
fusata. Sosai ya zauna saman sofan dake dakin,ya kuma dora qafanshi daya saman daya yana qare mata
kallo tsaf har takai aya.

Murmushin gefen baki ya saki yana kada kai

"Taurin kai da rashin kunyar nan naga alama da sauranta har yanzu......yayi kyau......haka nakeson gani"
ya fadi yana sauke qafafunsa qasa,sai ya miqe cak abinsa ya qarasa bakin window din dakin,ya zuge
labulen yana hangen view me kyau daga nan cikin dakin. Abun sai ya fusata ta,wato ya maidata wata
mahaukaciya ma,ta hasala sosai,kawai sai ta fara masifa idanu rufe. Yi yayi kaman baiji ba har minti
kusan biyu. Ya saki labulen ya juyo a tsanake. Kallo days yayi mata sai yakau da kai,ya sanya hannunsa a
nutse ya fara balle botiran rigarsa.

Da farko bata ankara ba har sai daya gama ballesu tas,fara qal din vest dinsa dake ciki ta
bayyana kanta,ya saka hannunsa ya fara zare rigar a nutse,ya cireta tsaf ya ajjiyeta a gefe.

Kallo daya tayi ma qirar jikinsa wata shakkarsa me qarfin gaske ta shigeta. Murdadden jiki me
cike da baqa sidik din gargasa. Ba tare da yace mata kanzil ba sai gashi dukka maganganun da take
zubarwa tana musu muhalli tare da maidasu cikin cikinta ragowar da bata ida furtasu ba. Tsoro sosai ya
shigeta sanda ya zare ragowar vest din data rage a jikinsa ya waiwayo kuma yana dubanta.

Guri daya idanunsu suka sarqe,ya lumshe idanun nasa yana mata nuni da dogon wandon jikinsa
yana riqe hannunsa a qugunsa. Ba qaramar yarinya bace ita,hakanan tun ba yau ba yayi mata sabo da
body language,don haka sarai ta fahimci me yake nufi. Cikin dakiya ta aje masa wani kallo zuciyarta na
tsananta gudu kaman zata fasa qirjinta ta fito

"Muqulli na kawai nake da buqata......kada ka yarda kaci gaba da shiga hurumin........" Bata qarasa ba ta
tsinceshi gabanta,yayi mata katanga da faffadan qirjinsa. Dukka tsahonta ya shanyeshi,bata kuma tsaya
ko ina ba sai daidai qirjinsa dake a waje cikin ni'imatacciyar lallausar suma.
Baya tayi niyyar ja da sauri,saidai kuma kafin takai ga aiwatar da hakan ya sanya hannu daya ya
fusgota. Batayi masauki ko ina ba sai saman qirjinsa,fuskarta ta samu kyakkyawar tarba tsakiyar
kwantacciyar sumar qirjinsa. Wani dogon matsoracin numfashi taja wanda ke cakude da sassanyan
qamshin dake fita daga cikin gargasar tasar. Kafin tayi tunani na biyu ya sanya dukka hannuwansa biyu
ya warware mayafinta tas.....bai barta ta gama nutsuwa ko tattara hankalinta waje daya ba ya sauke
mata dankwalinta,wanda cikin sa'a ya hada harda ribbon dinta,abinda ya bawa doguwar sumarta daman
bajewa gaban fuskarta zuwa gadon bayanta.

Tana cikin qoqarin tattara sumar nata cikin tashin hankali da tunanin me yake shirin
aikatawa,fit......taji ya sauke zip din gaban rigarta gaba daya tun daga sama har qasa,abinda ya sakata
sakin gashin nata kenan a muqar gigicewa da kuma razanin yadda ya iya aikata hakan kamar qiftawar
idanu

"Mm......meyeh.....haka?,wanne abunne wannan?" Ta tambayeshi a gigice tana qoqarin tattaro gaban


rigar tata don hana bayyanuwar jikinta muraran

"Ladabi zan sakeyi miki,don na fahimci yara biyun ma da kika haifa basu sanya kin sauya hali ba......
karatu kawai kikayi ba ilimi ba, yanzun zan baki cikakken ilimi,and yanzun yara uku nakeso na baki ajiya!"

"Maina!...... don't......" taja sunansa da wani irin amon sauti me dauke da tashin hankali......Sai ta kasa
qarasa fadin abinda takeson fada din saboda tsintar tausasan tafukan hannayensa da tayi cikin ainihin
fatar jikinta yana yawo dasu daga saman cikinta ya zagaya har zuwa gadon bayanta sannan ya zarce yana
neman maballin bra dinta

"Don't what?.......ehhh?,ba zaki daina bani warning akan abinda yake halali na ba?,karki damu wannan
karon nayi hankali nima,na sake girma.......you will enjoy it......babbabn ALBISHIR dinma tare zamuyi
rainon cikin,tare kuma zamu shiga labour room din".

Rawa dukka jikinta ya dauka cikin matsanancin tashin hankali,bakinta ya kulle gam,sai kawai ta
sakar masa muka sanda taji d'as! Ya balle bra din. Jikinta ta cukuikuye waje guda tana girgiza masa kai
sanda taji yana qoqarin zare rigar da bra din duka daga jikinta,yana nufin ya ganta a tsurarta
kenan?,abinda bata taba yi ba gaban wani d'a namiji
"Please......don Allah,i beg you.....kayi haquri" ta jefa masa roqon ba tare data shiryawa hakan ba tana
girgiza kai kaman ba gobe.

Cak ya dakata daga abinda yake shirin yi,yayi komai ne akan plan da son cimma wani abu na
sanyata ta sakeyin laushi,amma kuma sai abun ke neman zame masa na gaske,don ba wata kafa a jikinsa
da bata mutu ba,gaurayuwar jikinsu waje daya da kuma yadda fatarta keda tsananin taushi sulbi da wani
irin qamshi na musamman sun masa wata irin mummunar illar da basuyi masa a baya ba cikin qasa da
minti daya.

Sake mata komai yayi sannan ya juya a nutse abinsa yana wucewa toilet. Da gudu gudu sauri
sauri ta dinga maida komai muhallinsa,ta mayar din amma kuma komai a hargitse ta maidashi,ta lullube
jikinta da mayafinta,saita sulale a wajen tana sakin qaqqarfan kukan da take ta riqewa.

Ya jima sosai a bandakin sannan ya fito,sanye da gajeran wando zalla abinda ya sanyata sake
cusa kanta tsakanin cinyoyinta tana jin wani bacin rai da weakness suna ratsata. Baice da ita komai ba ya
isa ga windows din dakin dukka ya sauke labulayen,abinda ya qarawa dakin duhu kenan,ya isa ga
makashin qwayaye dukka ya kashesu,sannan ya qarasa saman gadon a matuqar kasalance yabi lafiyarsa
yana cewa

"Zan huta na wasu mintuna daga bisani na kaiki.....ki kwanta ki huta kema" ya furta yana tattare pillows
din saman gadon ya matsesu gam a jikinsa yana sauke numfashi a wahale.

Bata amsa masa ba,hakanan bata motsa ba,taci gaba da rera kukan bacin rai a hankali. A qalla
mintuna ashirin da daukan shirun da dakin yayi,wayarta data watse a gefe ta soma haske. Kaman ba zata
daga ba sai kuma ta miqa hannu ta janyota

"Ama ta" shine sunan dake yawo saman screen din. Riqe kukanta tayi da kyau tama share hawayenta da
bayan hannunta sannan ta daga kiran

"Karki jima sultana sosai,ki dawo da wuri ki fara hada kayanku,kwana biyu kawai ya rage mana zamu
koma" kamar bushara haka taji maganar ama,ta bude idanunta da suka jiqe da hawaye tana hangensa
daga inda take a zaune,wani irin farinciki ya soma mamaye damuwarta,lokaci yayi da zata sake masa
nisa,nisan da idan tayishi ba zata sake bashi daman zuwa kusa da kta ba bare ya dinga walagigi da
rayuwarta yana mata Iko yadda ranshi yakeso ba

"In sha Allah ama" har ama din ta buda baki zata tambayeta inda ta tsaya don yasmine tace bata qarasa
ba sai kuma ta fasa ta yanke kiran. Wata wawiyar ajiyar zuciya ta saki fuskarta na kallon sama

"Alhamdulillah" ta samu kanta da furtawa,tana ji a nan kusa zata yakiceshi ta huta. Bashi da
communication me kyau da ama bare aba ballantana ya isketa a inda take din. Sai ta miqe a hankali ta
taka zuwa qofar toilet din tana ji har jikinta da zuciyarta ta samu qwarin gwiwa.

_ba'a nan naso tsaiwa ba,amma yanayin yazo a haka,in sha Allah idan na samu yadda nakeso hutun zai
kasance asabar da lahadi ne zuwa litinin kawai,daga nan zamu dora_

_da alama qullalliya sultana ke shirin qullawa maina ta hanyar amfani da ama ba tare da ama din tasan
da haka ba,shin ya zata kasance?_

_ayi sallah lafiya cikin aminci,ubangiji ya maimaita mana ya karbi ibadunmu ameen ya hayyu ya
qayyumu_

[28/06, 9:29 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE page 72


Alwala ta daura ta goge fuskarta da kyau cikin toilet din,ta fidda powder da bata rabo da ita ta
shafa,ta kuma gyara lips dinta. Har cikin zuciyarta tana jin sanyi,bacin ranshi kuma ya ragu sosai,tunda
tasan kwanaki biyu rak suka rage mata tayi adabo dashi.

Tayi zaton data fito zata sameshi a shirye ko yana ma shirin su tafi din,maimakon haka samunsa
tayi a kwance lakadan abinsa,kamar ma wanda ke bacci. Ta saci kallonsa sai tayi hanzarin kauda
kai,saboda ta tunashi da shegen saurin karantar mutum. Taci alwashin ba zata ce dashi komai ba,don
haka ta koma saman kujera ta zauna,ta fidda wayarta daidai sanda take ringing kira ya shigo.

Ko data duba sai taga kiran yasmine ne still

"Ya salam" ta furta cikin damuwa,don batasan amsar da zata bata ba

"Oya..... bani wayar nan" muryarsa can qasa kaman wanda yasha wani abu ya ratsa kunnenta. Tadan
tsorata don ta tsammaci bacci yakeyi,amma sai ta tada kai tana dubansa. Bai ko kalli wajen ba,amma
hannunsa suna saitinta yana jira ta kawo din.

Har tsakiyar zuciyarta taji zallar raini kawai yayi mata,banda haka meye hadinsa da wayarta
dama ita kanta da zai dinga qoqarin control dinta da komai nata

"Kada na maimaita fa?" Ya furta har yanzun muryarsa da wani mugun laushi. Bacin rai ya kawo mata iya
wuya,ta motsa qaramin bakinta da niyyar masa tsiwa kuma saita maida dukka maganganunta ta
hadiye,don tasan furtasu bazai haifar mata da d'a me ido ba,kuma a wannan wajen da suke komai ma zai
iyayi mata babu me ganin laifinsa. Wannam tunanin ya sanya ta tattara duk wata tsiwa tata da bacin
ranta ta hadiye,ta kuma yunqura a nutse tana isa inda yake din.

Wayar ta miqa kamar yadda ya miqa hannunsa ba tare da tace masa komai ba,tana kuma
qudurcewa a ranta ba zata ce masa ta iso ba,duk sanda ya juyo ya ganta.

Hannunta da aka cafka ya sanya zaren tunaninta katsewa,kafin ta sake tuna komai ya jawota
zuwa saman gadon ita da wayar gaba daya.
Birkitota yayi sosai yana zare wayar a hannunta ya danna switch ya kasheta,idanunsa a lullumshe
muryarsa na dauke da wani irin lallausan amo yana cewa

"Ba zuwa nayi kawai na kashe kudin daki kina niamy ina marad'i ba.....dole ki tayani hutawa,bacci nakeji
sosai.......baccin da kikayi shekara da shekaru bakya barina inyisa cikin nutsuwa.......duk sanda na jefar da
kaina na kwanta to tabbas sai wannan muryar taki me cike da tsiwa ta biyoni har cikin mafarkina tana
sake jaddadamin abinda ta gayamin a baya......zaimin fyade.....Allah ya isa ban yafe ba...... it's so
annoyed" ya qarashe fadi da salon muryartata sannan ya cusata tsakiyar qirjinsa a tausashe yana maida
hannuwansa ya lullubeta da kyau.

Wani irin abune taji ya mamayi dukka ilahirin jikinta wanda ya haifar mata da tsatstsafowar
gumi ta kowacce kafa ta jikinta

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta furta jikinta yana rawa,wani irin tashin hankali yana rufto mata

"Shshshsh!" Ya fadi da qaqqarfan sauti yana dora yatsansa saman lips dinta,wanda a sannan fuskokinsu
sunyi matuqar kusaci da juna. Ji tayi kaman zata shide sanda ya busa.mata iskar bakinsa a fuskarta,iskar
dake dauke da qamshin mint na mouthwash ne kona meye bata sani ba.

Dukka qarfinta ta tattaro ta turashi baya,sai ya ware lion eyes dinsa yana kallonta

"Ehnnm......bance miki fyade zan miki ba dama?,yanzun wa zaki kira cikin wadanda ke tare
miki?,uhmmm?" Ya sauke maganar yana duban tsakiyar idanunta dake kawo gudunmawar hawaye.
Labbanta rawa suke tanason fidda maganar dake zuciyarta tare da qoqarin qwatar kanta,sai kawai ya
saki siririn murmushi ya maida kansa ya kwanta bayan ya tabbatar ya zagayeta da hannayensa. Ya barta
taci gaba da yunqurin qwatar kanta,bai hanata ba bata fasa ba har sai da dukka qarfinta ya qare,yayi
amfani da wannan damar ya jata jikinsa sosai,sai ta fashe da kuka ganin babu sauran wata dama data
rage mata kenan,bata da sauran zabi sai hada numfashi dashi,ba wata mafita ko garkuwa saita hada
gangar jiki dashi,abinda bata sake mafarkin faruwarsa ba,abunda take gani bazai taba hadata dashi ba
har qarshen numfashinta. Wanne irin tsaurin ido gareshi haka.,wanne irin taurin kai da kafiya ce dashi da
har ya ya iya zare duk wani tanadi data yiwa haduwarta dashi?,ya yake neman rusa komai ya kuma ci
galaba a kanta?. Abune da ba zata taba bari ya faru ba yayi iya yinsa na yau ne kadai,saidai duk yadda
yakai ga qwarewarsa wajen yaudara bai isa yakai inda yake hari ba.

_nikam nace mmmm🤐

Tun tana lissafa minti biyu biya har goma sai gashi ta tafi lissafin awa daya,sannu a hankali awar
tana shudewa tana zarcewa awa ta biyu. Idanunta fes tana zagaye da cikin dakin tana muma biye da fitar
numfashinsa da kuma bugun zuciyarsa. Ko yaya ta motsa da zummar zare kanta sai taji ya sake maqaleta
da kyau,murya can qasa kuma ya furta

"No" har abun ya fara bata tsoro,a qa'ida ya kamata idan baccinsa yayi nisa dukkan gabbansa su saki ta
yadda zata iya zare kanta,amma nasa qawa zucin bai bar hakan ya faru ba.

Tayi kuka tayi kuka har dantsensa daya dora kanta akai ya jiqe,idanunta dukka suka tasa saboda
tsabar bacin ran da takeji cikin ranta,ga wayarta daya kama ya kashe mata,tsoronta daya kada
hankalinsu ya tashi da neman inda take tunda dai ita bataje gidansu aminata din ba,sannan kuma bata
koma gida ba.

Dai dai sanda muhtarin sallar la'asar ya shiga ya motsa. A hankali ya bude zagayyayun idanunsa
da duka qara girma suka. Dan kada kadan ya zubesu akan fuskarta. Kamar an qara mata qarfi saboda
yadda zuciyarta ta motsa da rainin hankalinsa,shi ashe ma baccinsa yakeyi da gaske?. Sanda yake
qoqarin tashi saita rigashi tashin,tana tunanin shammatarsa ne batasan miqewa shima zaiyi ba. Tsam ta
miqe tana gyara dankwalinta da mayafinta,sai ya miqe a nutse ya zauna ya zuba mata idanunsa. Can
qasan ransa dariya ce sosai take kamashi,yasan ya gama da ita,wannan din wani assignment ne ya bawa
zuciyarta da gangar jikinta,ya basu wani aiki ya kuma ajjiye musu wani yanayi da zaiyita kai kawo cikin
kwanyarta koda batason hakan.

Abu na biyu yadda taketa wani gyara jikinta tana gyara yafen mayafinta tamkar wadda taga
wani muharraminta. Taurin kanta da yadda har yanzu take masa kallon ba mijinta ba yana burgeshi,don
yana hango ranar da zai sanyata ta qaryata hakan da kanta,ba da bakinta ba,zata qaryata ne tun daga
qasan zuciyarta har ya bayyana a dukka ayyukanta.
Kau da kansa yayi kaman baiga abinda takeyi ba ya miqe a nutsensa ya wuce toilet yana boye
dariyarsa,ya azawa fuskarsa wata muguwar daurawa da cin mur.

Har ya fito ya maida rigarsa ya dauki key zai fita tana zaune,sai da taga da gasken yayi hanyar fita
sannan tayi hanzarin miqewa

"Ina zaka tafi ka barni?" Tayi masa tambayar wadda a zahiri murya da fuskarta dukka sun juye sun koma
kalar shagwaba,irin tsohuwar shagwabar nan tata da take tatawa sanda take ganiyarta,yayin da can
qasan zuciyarta kuma ba shagwabar bace. Wata tsana da haushinsa ke yunqurin hallaka zuciyarta.
Muryartata saita kashe masa jiki gaba daya,ya daki handle din ya tsaya sosai yana kallonta,kaman zaiyi
magana sai wani abu ya fado a ransa,sai yasa hannu yaja qofar ya rufe yayi gaba. Duk taku daya
kunnuwansa na cikin dakin yana wani murmushin mugunta,zayaso wannan LOKACIN ya qaraso,sanda zai
dafa zuciyarta da gangar jikinta da soyayyarsa,yana tausaya mata,daga mata qafan da yakeyi a yanzun
yana yinsa ne kawai saboda yanason ya fara sauke zafin kanta da kuma zafin fushin da zuciyarta ke ciki a
kansa.

Yadda ya zata hakance kuwa ta faru,sulalewa tayi a wajen qwalla masu zafi suna fita mata a
fuska,wannan wacce irin baqar rana ce gaba daya a wajenta?,tayi nadaman fitowa a yau,inda tasan
wannan ranar zata qareta dashi ne qarqashin daki guda,zata gwammace ta wuni a daki da zazzabi a
jikinta,tasan koma meye duk inda za'a je a dawo shi zazzabi kankarar zunubi yakeyi.

Baiyi mamaki ba daya dawo ya sameta a wajen,shima yi yayi kaman bai ganta ba a wajen,ya
koma ya zauna ya gama azkar dinsa na yammaci,yana ankare da ita baiga ta tashi tayi sallah ba.

"Ki tashi kiyi alwala kiyi sallah" ya furta yana miqewa sanda ya hangi wani a bakin qofar dakin yana jiran
a bude mishi ta cctv din dake maqale a qofar dakin. Bayansa ta ballawa harara siraran hawaye na karyo
mata,ta sanya hannu ta daukesu a zuciyarta tana cewa

"Ba za'a yi sallan ba,sai kace da can kaike sakani sallar" amma yana waiwayowa ta kwashe kallonta daga
kansa zuciyarta nadan bugawa tamkar tana tsoron yaga tana harararsa ne

"Allah ya kiyaye ni.ba tsoronsa nakeji ba" ta baiwa kanta da kanta amsa cikin fushi.
"Bazan zake maimaita kije ki sallah ba........kawai nasan idan na tashi zan saki kiyita koma ta yaya ne" ya
fadi yana bude makararren lunch din da aka kawo musu

"Fashi nakeyi......" Ta furta a dan tsiwace tana tura baki gaba rai bace,na meye zai takura lallai sai yaji
sirrinta. Tsaiwa yayi daga abinda yakeyi yana dubanta

"Fashi kaman yaaya?,kina nufin har yanzu baki daina wasa da sallah ba ashe?" Ya fadi seriously

"Menstruation......" Ta furta da sauri harda dan daga murya hawaye na balle mata ganin yana niyyar yi
mata mummunar fassara.

Siririn murmushi ya kubce masa duk da bai shirya ba,dama abinda yakeso yaji kenan daga
bakinta duk da ya fahimci tun farko abinda take nufi. Waskewa yayi yana shafa tattausar sumarsa

"Oh..... okay,ashe ma a bule kike kiketa wani tutturjemin....." Kasa riqe bacin ranta tayi sai kawai ta rushe
da kuka,abinda ya sanyashi boye kansa tsakiyar tafukan hannunsa kenan yana sakin asirtacciyar dariya.

Ya yadda babba babba ne kuma duk wanda ya girmeka ya riga ya girmeka,duk yadda yaketa
qoqarin hargitsata dinnan bata fahimci da biyu yake komai ba,sai quruciya da suka sanyata a gaba taketa
sake tunzura.

Sau uku yana mata maganan tazo taci abinci taqi,sai ya qyaleta ya bude yaci.nashi,duk da shima
din ba wani me yawa bane.

Magariba tayi taga ya daura alwala ya fice,ya dawo yaci gaba da sabgarshi abinshi. Yana
haramar fita Isha'i ta sanya masa kuka. Kunya takeji da kuma nauyin dukka jama'ar gidan. Duk duniya
duk wanda ya gansu tare babu wanda bazai fassara da goyon bayanta ba kuma tana sane ta biyoshi. Ta
tabbatar kuma zuwa yanzun nemanta kowa keyi, musamman da wayarta ke a kashe. Yasan me yake
damunta,amma yaci alwashin ba zasu tafi ba har sai ta buda baki ta roqi su tafi, zaiga qarshen gudun
ruwanta. Abu daya ke damunsa yadda taqi yarda taci ko tasha komai kaman me azumi.
Yana hanyar dawowa masallacin kiran suhail ya shigo,kusan kira na biyar kenan da yayi masa
yana shareshi. Sai daya hadiyi wani abu yakai kuma zuciyarsa nesa,yaja numfashi har cikin hunhunsa
sannan ya daga kiran

"Ina ka tafi ne haka?,haka ake tarbar baqo a gurinkun?" Ya fadi cikin muryarsa akwai alamun wani abu
yakeci

"Komai kake da buqata nasan ka sameshi......wani uzuri ne ya fiddani amma ina hanyar dawowa ko
yaushe"

"Uhunn......yayi kyau,banda Allah ya hadani da tsohuwar nan me kirki da kuma dattijuwar arziqi ama
haka zaka kwasoni ka yasar ko?......kasha zamanka ma ni na samu abokiyar hira me kirki ba me shegen
baqin rai irinka ba......amma kasan wani abu?"

[24/06, 5:14 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 73

"Nop" ya fada a gajarce don ba abinda ke dawo masa sai kallon da ya dinga bin sultana dashi
dazu"

"Na samu komai......amma wannan balarabiyar sister din naka......kasan itace naketa nema tsahon
wannan shekarun......tunda na ganta a haram ban sake ganinta ba sai yau a gidanku?,kuma tunda naga
ta shige dakin bibi nayi imanin kuna da qaqqarfar alaq......."
"Wait mana......wai me bibi ta baka kasha ne kaketa zuba haka kaman lalataccen famfo?" Dariya suhail
ya tuntsire da ita

"Giyar soyayya nasha....... maganar gaskiya ina neman taimakon ka haidar....... I really really love her,na
kamu sosai"

"Stop mana suhail.......soyayya kazo neman nijer ko zumunci da aiki ya kawoka?"

"Dukka ukun" ya maida masa amsa muryarsa tana komawa serious. Dif maina yayi yana karanto yadda
suhail ya koma magana da gaskensa ba kamar daxun da yake magana da wasa wasa a ciki ba

"Alright......sai ka nema mai taimaka maka,ka kuma nema wata matan ba wannan ba...."

"Why?" Ya tambayeshi a mamakance

"Saboda bazan iya ba"

"Gashi kuma ni ita nakeso.....ita na jima inaso,na ganta kuma saika haramta min ita?" Ido ya lumshe yana
jin zuciyarshi kamar zata fashe duk sanda suhail yace masa ita yakeso

"Meye dalilinka haidar?,ko kaima kana sonta?,idan sonta kake hakan bazai hana a bawa wani dama
ba,tunda mace allura ce a cikin ruwa ko?."

"U are very stupid suhail,damnit!" Ya furta a fusace yana katse wayar. Sauran kadan yayi cilli da wayar
sai kuma Allah yasa ya jefata cikin aljihunsa.

Baisan wanne tsautsayin ne ya kawo suhail nijer ba,amma yayi imanin muddin zaici gaba da
fadin wadannan maganganun akan sultana komai zai iya faruwa tsakaninsu.
Bai koma cikin dakin ba saboda bayason ta ganshi a wannan mode din,sai daya zauna na wasu
mintuna masu yawa a waje ya daidaita kanshi sannan ya samu qarasawa ciki.

Yana bude dakin kiran goumar yana shigowa wayarsa. Da sallama ya daga kiran goumar din ya
amsa

"Ina kyautata zaton tana tare da kai yaa maina right?"

"Yeah,me ya faru?" Ajiyar zuciya ya sauke

"An fara nemanta fa......har an sanarwa aba.....don bataje gidan yasmine ba bare aminata,wayanta kuma
switched off,kayi qoqari ku dawo please kafin su ankara kaine ka dauketa,kasan har yanzu aba ba'a huce
yake ba,itama ama din haka" siririyar iska ya fidda daga bakinsa. Me yasa ake masa hakan?,kamar dai ya
saci diyar mutane?,ko kuma ya dauki diyar da ba muharramarsa ba?,bai manta bafa har yanxu,ba wanda
ya bari ko a sannan ya biya mishi sadaki,da kudin school dinsa ya biya sadakinta...... Me yasa suke manta
wannan?. Gefe guda kuma goumar din masoyi ne,yasan yana cikin masu sonsa cikin gidan,kome zaiyi
yana yine saboda kawo gyara da daidaito,don haka ya sassauta fushinsa ya amsa shi a gajarce

"Okay" kai goumar din ya jinjina

"Na gode da fahimta" sai ya sauke wayar.

Yana takawa zuwa dakin yana ji a ransa inama zasu gansun su fusata da hakan?,shi kam da yafi
kowa jin dadi,yafiso su fahimta ma da kansu shikam bazai taba iya yi musu abinda sukeso ba idanma
kora da hali suke masa a kanta.

Wannan karon a dakensa ya shiga dakin,ya kuma kasa ya tsare da tsukakkiyar girar nan tasa da
idan baiso ba yake juyewa wata irin fuska me ban tsoro. Abincin ya jawo ya bude yace kuma ta taso
taci,kaman yasan me ta qudurta yi ya dora da
"Duk musu daya da zakiyi kuma dai dai yake da kwananmu nan wajen,dama kudin kwana din na
biya,choose wisely.....but zanfi so kiyi taurin kan" ya qarashe maganar yana buda dukka hannayensa ya
dora saman makarin kujerar yana yakuma yi relaxing bayansa jikin makarin kujerar bayan ya miqe
qafafunsa sosai.

A yadda yayin ta tabbatar ya fadi ne har cikin zuciyarsa. Dole taja abincin ta kuma juya masa
baya taci spoon uku da qyar. Data maida masa sai daya mula don kansa sannan ya miqe ya tattara komai
da yasan nasa ne sannan ya bude dakin ya fice ta bishi a baya tana jin kamar tayi tsuntsuwa ta ganta a
gida.

Shuru ne ya ratsa motar,shi da ita din babu me cewa komai. Itakam ko qwaqwaqwaran motsi
batayi,ta gama yarda maina kawai ya qaro ta'addanci ne,a yanxun idanunsa sun sake soyewa fiye da
baya,ta tabbatar zai iya aikata komai,koma dai meye Allah ya kusa nesantata dashi.

A nutse kuma hankali kwance yake tuqinsa,yasan yau din ya samawa kansa memory masu
dadi,duk wani motsi laushin fatarta da kuma qamshinta ne yake dawo masa sabo,zaqin da laushin
labbanta sai yakejin kamar a duniya babu wani abu da yakai lips dinta sulbi.

Cikin qwarewa ya sauka daga saman titin ya gangara layin nasu dake shimfide da tsararriyar
kwalta. Dai dai qofar gate din mansion house din nasu ya tsaya ya kuma danna horn daya tak saiga daya
daga cikin security na gidan ya bayyana tamkar dama dawowarsa ake jira.

Tsaf ya wangale qofar,hasken fitilar gaban motar da ya sanyata a full light ya haske masa
farfajiyar farko ta gidan da kuma mutanen dake tsaye a wajen. Shi da ita dukkansu zubawa wajen idanu
sukayi,tata zuciyar ta tsinke ta fara luguden bugu cikin firgita,yayin da tashi zuciyar take a nutse tamkar
ma baiga komai ba,ya sanya hannunsa saman steering din ya soma murzashi a nutse kuma cikin
qwarewa yana sanya hancin motar cikin gidan game da rage kaifin hasken motar.

Tsananin hasken ne yana hankulansu dukka zuwa bakin qofar,ama ce tsaye sai aba da goumar
kusa dashi,sai kuma oncle issoufou da alamu ke nuna yanzun nan suka suka shigo gidan shi da aba. Idanu
dukka suka zuba musu,har zuwa sanda ya isa da motar parking lot na gidan,ya daidaita ya kasheta ya
zare key din. Juyowar da zaiyi sai suka hada idanu da ita,hawaye ne kwance cikin idanun nata,ta kuma
zuba masa ido kafin ta janye kallonta ta maida gefansu inda su ama ke tsaye,kuma dukkansu hankulansu
suna kan motar kamar masu jira suga wanda zai fito daga ciki.

Ya fahimci me take nufi,wani murmushi ya taso masa daga qasan zuciyarsa,shi kam wannan
incident din yake da buqata ako da yaushe,sai ya dage mata dukka girarsa biyun yana tambayarta da
idanunsa

"Kaga irin abinda zaka janyomin ko?,yanzu me kakeso nace musu?,waye zaice ba nice na bika ba?,wanne
irin shiga haqqine wannan?" Ta jefa masa tambayar muryarta yana rawa kukan da takeson daqilewa ya
fara yin kansa da kansa.

Hannayensa dukka biyu ya daga yana kallonta da zagayayyun idanunsa daya fiddo waje

"No.....kinga kada ki sake shafamin baqin jini banda wanda na diba......idan suka qaraso yanzun kuma
sukaga kina kuka,ba rape zasuce nayi miki ba tunda sunsan an riga na wuce wajen tunda ga result nan
kin basu......i think wannan karon kidney dinki zakice musu naje na saida ko?" Haushi kaman ta dora
hannu ta rusa ihu,amma ba zata iya hakan ba don batason asan tana ciki tare dashi,don haka idanunta
sai suka zarme da jefa masa harara cikin maqurar bacin rai

"Gyara kallonki babe.....if not wallahi zakisha mamaki a gabansu...... okay har kin manta dokan dana kafa
miki saboda kin dawo gaban masu sangartaki ko?" Ba shiri ta janye idanun nata saita maida bakin
qofar,still suna tsaye saidai magana aba yakewa ama wanda batasan me yake ce mata ba. Kafin ta
ankara ya bude murfin motar ya fita,ta zaro idanu saboda data lura da kyau handbag dinta na
hannunsa,baiko waiwayo ba,hakanan kuma ko a jikinsa yake takawa yana nufarsu. Fitowar tasa taja
hankulansu,shi kuma ya basar yana takowa dai dai har ya iso dab dasu.

"Ama barka da dare" ya fadi a ladabce yana rusunawa

"Yauwa" ta amsa shi a taqaice. Ya waiwaya wajen aba ya buda baki da zummar gaidashi sai yayi hanzarin
juyawa yana duban almu da ya iso wajen yanzu
"Ka bude bayan motata ta fiddowa bibi cukui kakai mata"

"Attah......kaima sultana handbag dinnan nata tana fitowa yanzu" maina ya fadi da biyu cikin dan
taqaicewa,don bayason aba yabar wajen baiji abinda ya fada ba.

Sarai aba din yaji abinda yace din,amma sai yaci gaba da takawa yana wucewa ciki baiko
waiwayo ba. Yana miqawa atta jakar ama ta bita da idanu,sai suka hada ido dashi,nauyi yaji yadan
saukar masa,ya sanya tafin hannunsa yana shafa kwantaccen sumar dake qeyarsa yana dan basarwa.
Itama nata idon ta janye,daidai sanda sultana ke takowa wajen,don dole saita wucesu zata isa qofar
sassan ama din ko sassan bibi.

Dukka idanunta qasa suke kalla,don batasan yadda zata iya hada idanu da ama din ba duk da
tana jin idanunta a kanta,haushi takaici da baqincikin maina ya kamata,cuta yau kam ya riga ya gama da
ita ya kuma cuceta,amma daga yau ai zata yiwa tufkar hanci,da wanne ido zata kalli ama?,da kuma
wanne baki zata yi mata bayanin yadda suka hada tafiya da maina?.

Ta karanci fuskarta fes,don haka tun kafin takai ga isowa sai ama din ta juya abinta ta wuce ciki
itama,wannan ya sauqaqa tsananin nauyi da kunyar da takeji din,kallonsa kuma sai ya koma kanta,yana
kallonta tsaye kallon tsaf,yadda take takawa cike da kunya sai abun yaji ya masa,ta masifar tafiya dashi
gami da burgeshi,kamar ya dauketa su kuma suci gaba da kasancewa tare kaman dazun,koda ba zata
buda baki tayi masa magana ba,koda zata masa tsiwa ne,koda masifa zatayi masa

"Ki tafi a hankali mana please" ya furta a tausashe sanda take giftawa ta gabanshi. Ji tayi kaman ta sanya
abu ta tureshi ya fadi,a sanda ya hada wata cakwakiya me zafi sai yasan yadda ya zame kanshi,sai yasan
yadda ya maida komai ba komai ba,yasan duk yadda zai sauke laifi duk girmansa izuwa qaramin mataki.

[24/06, 5:14 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 74
Sassanyan murmushi ya saki yana furzar da iska me sanyi daga bakinsa,ba qaramin dadi yaji ba
da ganinsun da aba da ama sukayi,wani abu ya darsu a ransa sanda yake wucewa zuwa sassansa yana
sake sakin qaramin murmushin,yakai hannunsa ya shafa lallausar sumarsa yana cije lips dinsa na qasa.
Nishadi da farincikin da zuciyarsa ta samu wunin yau kawai ya wadatar dashi lafiyayyen bacci a daren
yau me cike da kwanciyar hankali.

Kai tsaye ya fidda kayan jikinsa bayan isarsa bedroom dinsa,ya hada ruwa me zafi ya shige cikin
bathtub dinsa yana rufe idanunsa,dumin ruwan yana ratsashi zuciyarsa na masa haske.

Koda ya fito a nutse ya sharce kansa ya kuma shirya cikin wata cotton doguwar riga ta maza
maras nauyi saqar qasar india,kewar benazeer da batoul yakeyi sosai,yasan kuma ko su din sun
nemeshi,yanzun haka yana da tabbacin sunyi barci,to amma kuma bazai iya kwanciya har zuwa safiya bai
gansu ba,don haka ya zura wasu slipper nashi masu taushi off-white kalan rigar yana fita a dakin.

Daga sassan bibi har na ama suna da dakunan kwanansu a ciki da komai da komai,ko ina suna
iya kwana cikin gidan,don haka ya rasa wanne sashe suke. Daga bangaren ama harna bibi din ba wanda
yakeson shiga,sassan ama yana dan jin nauyin abun dazu ne, sassan bibi kuma bayason ya taras da suhail
a can,ko yaya yayi misbehaving masa yasan sai bibi ta tanka,don ya fuskanci ta karbeshi hannu bibbiyu.

Kamar an jeho masa saddi,ya tako a hankali ganin yayan nasu tsaye a wajen,yadan rusuna cikin
ban girma yana fadin

"Barka da dare"

"Barka saddi,BB fa?"

"Suna sassan ama" ya amsa masa yana masa nuni da sashen da yatsansa

"Yayi jeka abunka" ya furta yana nufar sashen.


Duka a rude take sanda ta wucesu,ta rasa ina zata dosa wajen ama ko bibi?. Idan ta tafi wajen
bibi hakan yana nufin fa kenan ya tabbata ita din me laifi ce,amma kuma zuwanta wajen ama din kuma
fa?,kunya takeji yau din matuqa, tilas ta hadiye tunda tana jinta aba me laifi ba tayi sassan ama din,ta
bude dakinta ta tura ta shiga. Sai data maida qofar sannan ta fidda numfashi tana jinta safe,ta soma
tariyo abinda ya faru dukka wanin yau din,sai taja dogon tsaki

"Bazan sake bashi daman da zai ganni ba bare ya rainamin hankali haka ba" ta fada tana jin zafin walagigi
da ya dinga yi yau din da ita. Wanka ta shiga itama don gaba daya kayanta da jikinta taji sun fita mata a
rai,don ba abinda sukeyi sai qamshin wannan mayataccen turaren nasa,tana ciresu ta jefasu a laundry
basket ta fiddashi qofar dakinta,tasan me hada musu kayan wanki zuwa gobe da ssfe zata iso tayi gaba
dasu zuwa laundry room dinsu.

Tsaye tayi gaban madubi,lallausan gashinta da yaji ruwa ya kwanta mata lambas a goshinta zuwa
wuya,ta goge fuskarta da qaramin towel sannan ta jawo cream dinta ta fara matsa tana shafawa. Sanda
tazo daidai bakinta saita tsaya tana zagaya yatsunta akai,turo lips din tayi gaba ta kuma jan qaramin tsaki
tana dauke ido daga saman kyakkyawar fuskar tata. Sai yanzun takejin wai yama akayi ta tsaya yayi mata
dukka irin wadannan abubuwan kaman me jin tsoronsa?,ya raina mata wayo da yawa, sa'a dai kawai
tasan ya taka,amma tabbas nan gaba ko meye zaiyi mata bazai sake samun dama a kanta irin haka ba.

Wasu pink pyjamas ta zaqulo masu hade da cap ta sanya,ta taje gashinta da kyau ta nannadeshi
ba tare da ta sanya band ba saboda batason abinda zai takurata idan zata kwanta,tabi dukka jikinta
dukka da sassanyan body body mist me qamshin strawberry,ta zauna daga saman stool ta dauki wayarta
da zummar turawa aminata da yasmine apology tex akan rashin xuwanta,sai benazeer da batoul suka
fado mata a rai. Zura wayar tayi cikin dan qaramin aljihun pyjamas dinta dake maqale ta qasan
rigar,kwana biyun sai takejin wani sabuwar qauna da kewar yaran,ta sanya takalmanta ta rage hasken
dakinta ta fito. Ta tabbatar suna sassan,don yawanci irin wannan ranar sunfi kwana sasssn ama,don
itama a sassan take kwana,ba kasafai ta fiya zuwa sassan aba ba a irin wannan ranar,su kuma sunfi son
su kwana idan tana cikin sashen.

Ba kowa falon ama din har ya ratsa ya isa dakin yaran,ya murza handle din ya tura ya shiga,dim
light ne duka dakin,ya gauraye da sassanyan qamshin da kusan ya kama jikinsu da ma dakin zuwa sassan
ama gaba daya. Makunnin babbar fitila ya laluba ya kunna. Tarwai fuskokinsu suka fito,ruqunqume da
juna cikin duvet kamar wadanda aka ce za'a rabasu. Murmushi ya subuce masa,qaunarsu da alfahari da
yaran yana ratsashi,a yadda yake ganin sun damu matuqa da al'amuran juna da tsananin kama da juna
da sukeyi yana kyautata zaton a mahaifa daya suka rayu.
A nutse ya qarasa ya haura saman gado,tsakiyarsu ya zauna sosai,ya miqa hannu yana shafa
fuskarsu sannan ya gyarawa kowacce kwanciya,ya hada hannayensu biyu waje daya ya musu addu'o'i ya
shafa musu. Hannunsa saman kan batoul,yana jin wata soyayya tana sake ratsashi. Shi kadai yasan me
yaji sanda ya fahimci mamansu na dauke da cikinsu,a lokacin da bashi da iko ko daman taimaka mata da
komai,a lokacin da kowa ke masa kallon ya gudu ne da gangan,a lokacin da kowa ke kallon yayi komai ne
akan bada qarfi,ba wanda ya kalli K'ADDARA cikin lamarin.

Zamannan da yayi a tsakaninsu sai yaji tamkar yana hira ne a tsakanin zukata biyunsu da tashi
zuciyar,tamkar yana gaya musu damuwarsa wadda kowa ya kasa fahimtar sa,kowa yaqi bashi uzuri
tamkar su din suna fahimta suna kuma tayashi alhini.

Bude idanunsa yayi a hankali,cikin jikinsa yakejin kamar tana tahowa dakin saboda yadda bugun
zuciyarsa ke qara yawa,sai ya miqe tsam,ya tafi bayan qofa yayi tsaiwarsa,don ya tabbatar muddin ta
ganshi ba zata qaraso ba,shi kuma yana da buqatar ganinta da gaske,ganin da zai zame masa dan rakiya
har zuwa gadon baccinsa.

Can qasan maqoshinta tayi sallama da siriryar muryarta duk da tana da tabbacin sunyi bacci

"Ya akayi sukabar wuta akunne kuma?" Ta fadi da tattausar muryarta tana takowa zuwa ciki. Fes yake
qare mata kallo cikin pyjamas din da suka fidda shatin bra da kuma pant dinta, yalwataccen gashinta
nata sheqi a hasken qwan dakin,qamshin strawberry body mist dinta ya gauraye dakin duka ya sauya
masa qamshi.

Wani yaarr taji yaji tun daga yatsun qafarsa har tsakiyar kwanyarsa lokacin da take takawa a
nutse tana nufar bed din yaran. Kowanne sashe na jikinta motsawa yakeyi da salon tafiyarta tamkar
wadda takeyin tafiyar a qididdige ko kuma take motsa jikin nata da gayya. Baby sultanansa ta bude sosai
ta zama babbar mace,irin isassun matan nan da qirar jikinsu keda wahalar samu,duk da kusan a rurrufe
yake ganin komai har yanzu,amma shi din a yanzun ba yaro bane qarami,yayi yawo a duniya yaga
halittan mata kala kala,uwa uba likita ne shi din dake mu'amala da kowanne irin jinsi ko yare. Wani irin
kishi ya taso ya saukar masa,maza nawa ne sukaga irin haka a tattare da ita?,ko dai abinda suhail ya gani
din kenan ya rude masa har haka a kanta?, tambayar data ida rikita mode dinsa gaba daya,yaji kaman zai
fita hayyacinsa saboda wani irin kishi daya sauko masa,hakan ya sanyashi kulle idanunsa yana zuqar iska
sosai don takai hunhunsa, rufe idanun da suka sanya har ta musu nata addu'o'in ba tare da tasan yayi
musu ba ta sake rufesu ta juyo zata bar dakin bai sani ba,sai da tazo dab da qofar ya shaqi qamshinta da
kyau ya miqa hannunsa a tausashe ya fusgota zuwa inda yake tsaye din.

Bata zaci haka ba kwata kwata,don haka abin ya matuqar tsoratar da ita,ta kira sunan Allah da
qarfi abinda ya saukar mata da nutsuwa kenan nan da nan. A tare suka ware idanunsu akan juna,cike da
zafin nama ta sanya hannu zata turasa baya,ya nuna mata namiji gaban mace yake ta hanyar kamo
qugunta ya riqe sosai,ya kuma janyota jikinsa ya hade qugunsa guri guda,abinda yayi sanadiyyar
daukewar numfashinta na wucin gadi saboda saqon daya aika mata a fakaice. Dukka jikinta ya soma
rawa kamar wadda aka tsoma cikin ruwan qanqara,tsoratar tata sai ta sake qarawa idanunta kyau a
idonsa,ya saki boyayyen murmushi don yasan saqon da yakeson ya aika din ya isa,ya gyara tsaiwarsa da
kyau yana duban tsakiyar idanunta suna musayar numfashi

"Ina roqonki..... please..... please,daga yau ki dinga saka jilbab idan zaki fita.....bazan iya jurewa ba naga
ana kallonki.......you are not a baby now......kin zama babbar mace.....zuciyata ba zata iya dauka ba.....ki
killacemin please"

"N killace maka me?,waima......meye hadinka da dukka rayuwata iyeee...... please stay away from me" ta
fadi da qwarin gwiwa tana son banbare hannunsa daga qugunta,don wani mummunan saqo me tsayawa
a zuciya da qwaqwalwa kawai yake aikewa gangar jikinta a haka. Tana jin wayarta na vibration amma
bata ma da qarfin duba me kiran.

Hankalinsa kwance yake kallon qwayoyin idanunta,akwai wani kakkaifan abu a ciki da yake
sanyashi nazari yadda zai kaudashi daga zuciyarta,ta riqi abubuwa masu yawa a ranta da alama,and shi
kuma bazai iya kallonsu tattare da ita ba,dole ya kawo qarshensu. Sakinta din yayi a hankali saidai kuma
ba salin alin ba,don sai daya zira hannunsa cikin aljihun rigar tata ya zare wayarta,wanda bata lura da
hakan ba sai daya daga wayar yana qoqarin cire code din kai.

A tsiwace ta bude bakinta zatayi magana amma sai maganar ta koma inda tafito sakamakon
turo qofar dakin da akayi da dan sauri.

A tarw suka juya suna duban bakin qofar,ama ce sanye da qaramin hijab mahadin pyjamas
dinta,fuskarta tayi kyau qwarai cikin kalolin kayan,sun kuma fidda quruciyarta sosai saika dauka duka
duka bata wuce shekara talatin ba.
Wani irin abu sultana taji kaman an watsa mata cikin jikinta

"Subhanallah" ama ta furta qasa qasa da sauri,sai sultana din tayi hanzarin ja baya cikin zafin nama tana
nesanta jikinta daga maina. Zuciyarta na bugawa kamar wadda aka kama da laifin sata dumu
dumu,idanunta dukka sun nuna tsantsar tsoronta da ganin da ama tayi musu tsaye cikin mugun kusanci
da juna ita da maina din. Daga subhanallah ama bata qara komai ba ta saki handle din ta juya tana
ficewa daga dakin cikin abinda duka bai wuce second biyar ba,dama zuwa tayi taga yanayin yaran ta
wuce itama ta kwanta,wanda hakan sabonta ne,duk dare takan dubasu kusan sau hudu ko
biyar,musamman idan aiki yama tanja yawa ko ba'a nan zata kwana dasu ba.

A fusace ta juyo tana duban maina wanda ko dis babu wani alamun tashin hankali tattare
dashi,hasalima sai taga kaman wani tattausan murmushi ne yake fita daga saman fuskarsa. A yadda taga
hankalinsa na akwance tasan ko meye zata fada ma batawa kanta lokaci ne kawai zatayi,sai kawai ta juya
da gaggawa tabi bayan ama kamar wadda keson cimmata.

Wani murmushin ya kuma saki bayan ta bacewa ganinsa,ya matsa gaban yaran ya sake
dubasu,ya saita musu ac din dakin sannan ya kashe duk wasu kayan wuta ya rufe musu ya fice abinsa.

Yana ratsa farfajiyar gidan iskar dake kadawa tana sake sanya masa nishadi har cikin
zuciyarsa,idanunsa ya dinga lumshewa yana tuna qamshinta da laushin fatarta,wani irin dumi da fatarta
ke dashi wanda kusan ya jima da haddace wannan,tun tana mitsitsiyarta ma......lokaci na farko da ya fara
saninta a matsayin diya mace,sanda tana sultana qwaila. Wani murmushin ya sake subuce masa daya
tuna ranar,rana ce da tazo musu a rikice ba tare da shiri ba,rana ce da bai taba hasashen faruwar abinda
ya faru din ba a sannan,tana dauke da wani irin memories masu nauyi da bazaiyiwu zuciya ko kwanya su
manta dashi ba.....amma duk da haka yakan tuna wasu baiwawwaki da ya sameta dasu da suka girmi
shekarunta.

"Lafiya kake murmushi kai daya?" Muryar suhail dake zaune cikin falon yana duba wata jaridar qasar
France ya fadi yana kallon fuskar maina.

Sai a sannan ya lura dashi,yayi qoqarin gyara mode na fuskarshi yana neman wajen zama
"Lafiya mana....." Tashi suhail yayi sosai ya zauna yana ajjiye newspaper din

"A'ah,inafa lafiya,kafimin kama da mutumin da soyayya ta yiwa mummunan kamu fa malam" harara ya
watsa masa yana qoqarin bude wayar sultana din daya taho mata da ita

"Hakane.....tunda kowa ma irinka ne wanda bashi da aikinyi sai soyayya" sai ya gyara zamansa sosai yana
shiga cikin wayar ya soma dube dubensa. Baku suhail ya sake yana kallonsa kafin ya saki murmushi daga
baya

"Ni ka tunamin,i got her phone number......bari na gwada kiranta" kaman an fusgeshi ya daga idanu yana
duban suhail,so yake ya tambayeshi wacece amma kuma ya kasa,sai idanu kawai daya zuba
masa,zuciyarsa na harbawa kadan kadan.

"Yeey.....ta shiga" ya furta with excitement yana gyara zamansa. Ga mamakinsa wayar sultanan dake
hannunsa ne ya fara harbawa,a nutse ya dauke dubansa daga kan suhail ya maida kan wayar,saiga
numbers a jere reras suna harbawa.

Iya adadin yadda suke harbawar haka zuciyarsa ke bugawa fiye da kima,a nutse ya maida
dubansa ga suhail bayan kiran ya katse yana sake qoqarin kuma kira.

Kaman dai dazun haka yaga kiran ya sake shigowa,da gaske ne wannan ba wasa ba, numbers din
sultana ke gareshi,kuma ita din yake kira,waye ya bashi number wayarta cikin gidan?,ya yiwa kansa
tambayar da baisan amsarta ba

"Still dai taqi dagawa.......tana da aji da yawa,da gaske sai nayi yaqi da gasken gaske zan sameta......
lemme try again" ya furta yana duban screen din wayarsa yana sake qoqarin kiran.

Hannu ya sanya ya latse wayar gaba daya ya kasheta duka yana jin wani abu yana riqe masa
waya
"Oh no!" Ya sake ji suhail ya fada da sautin damuwa cikin muryarsa

"Ta kashe wayar.......wai man.....me yasa ba zaka shigemin gaba ba?,na tabbatar sister dinka ce don
akwai kamanni a tsakaninku......i love her wallahi with all my heart.....zan kula da ita i promise"

"Mahaukacin da ya baka digit nata bai gaya maka matar aure bace!" Ya fadi a tsawace har sautin tsawar
nasa na fita farfajiyar corridor dinsa. A mamakance suhail ya fidda idanu yana duban maina,kafin daga
bisani ya rage kaifin kallonsa a kanshi,ya kuma tattaro dukka jarumatarsa yana masa duba nakai tsaye

[24/06, 5:14 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 75

"Please banason irin wannan wasan,wanne magana kake haka?,matar aure kamar yaya?,ta ina ta zama
matar aure?,ina mijin?"

"Eh.....yes matar aure ce harda yaranta" dariya suhail ya saki yana doka qafanshi a qasa

"Kaga,cool down man.....kawai kacemin kaima kana cikin 'yan takara bawai kayimin qaryar matar aure
bace...."

"Na taba maka qarya?" Ya jefa masa tambayar yana jin zafin jifansa da qaryar da yayi

"No.....amma akan mace ai ba abinda mu maza ba zamu iyayi ba muddin dai muna sonta"
"Shut your mouth please suhail......sultana matata ce..... benazeer da batoul are my kids!" Yakai qarshen
maganar yana dukan hannun kujerar da yake kai.

Sak suhail yayi yana kallonsa cikin mamaki,yayin da shima maina din suhail yake kalla fuskarsa na
sake bayyana zallar kishinsa.

Qaramin dariya suhail ya saki yana komawa baya ya zauna sosai

"Nasan ka qware wajen dakiya,cin magani,zafin zuciya da kuma zallar miskilanci......to amma bansan
sanda ka zama dan wasan kwaikwayo ba,yaushe kukayi auren?,har ta haifa maka wadannan bula bulan
twins din ma sha Allah tubarkalla,son kowa qin wanda ya rasa?,idan su din yaranka ne me yasa tsahon
shekarun kaketa begensu kake sonsu amma kuma muke yawan maganar bakasan inda suke ba a fadin
duniya?,ko nufinka duk cikin rainin hankalinka ne?" Ya amsa tambayar cikin salo na shashantarwa. Tsam
ya miqe daga inda yake zaune din

"Duka wannan bani da lokacin maka bayaninsa,kaje wanda ya baka phone number din ya maka
bayanin,kuma ka gaya masa nace ya warware maka komai ta yadda a Karan kanka zakasan bakin rijiya
ba wajen wasan makaho bane.......zan iya jure komai amma banda abinda zai tabamin mutuncin iyali
na.......kada ka kuskura mu ssmu matsala dakai akan haka,je répète(na sake maimaitawa)sultane est ma
femme(sultana matata ce),reste loin d'elle(ka fita hanyarta)" daga nan ya tsugunna a nutse ya dauki
wayoyinsa da nata ya soma takawa kai tsaye zuwa bedroom dinsa.

"Wannan duka matsalarka ce,ko ba wajenka ba zan zauna a gidan MAYAK'I,sannan idanma kayi hakanne
don ka hanani sonta so yanzu na fara sonta......" Maganar ta sakashi cin burki sanda ya sanya qafarsa a
dakin ya waiwayo ya zuba masa wani kallo me cike da kashedi da gargadi ba tare daya sake tofa masa
kanzil ba ya juya ya qarasa shigewa ciki.

Saman bedside drawer ya zube wayoyinsa,ya cusa hannunsa cikin sumarsa yana
yamutsata,wanne irin jarrabawa ce wannan takeson kutso kai tsakaninsa da abokinsa na kusan shekaru
hudu?,Ta yaya zai iya ci gaba da mu'amala dashi?,yanason matarsa?,uwar 'ya'yansa?,me yasa suhail yaqi
yarda da bayaninsa ne?,bayan yasan tsahon zamansu da shekarun da sukayi tare bai taba kwatanta yi
masa qarya ba?. Kiran sunan Allah yayi a jejjere yana fatan zugin da zuciyarsa ke masa ya sassauta.
Bayason yayi treating suhail in a wrong way,koba komai kusan qarfin zuwansa marad'i saboda
shine,ya baro familynsa a niamy ya zabi zuwa wajensa,bai dace ace yayi masa wani ba dai dai ba,amma
shima ya dace ya fahimceshi,ya fahimci maganarsa da kyakkyawar fahimta.

***********Kaman wata maras gaskiya haka take takowa zuwa dakin ama,tun daren jiya data samu ta
shige daki ko motsi me qarfi bata sakeyi ba saboda nauyi da kunyar ama din. Batasan me zata ce mata
ba,duk da komai data gani kawai yazo ne ba zata,amma sai abun ya zamana kamar an tsarashi ne,bataso
ama ko wani cikin gidan ya fahimceta bai bai.

Wata off-white gown ne a jikinta chiffon da aka yiwa budadden dinki,sosai kalan yayi mata
fatarta kyau wadda keta fidda qamshin milk cream nata da take amfani dashi. Da safen sumarta ya
dameta,ta zauna bayan ta fito daga toilet ta rabashi gida biyu ta kalbace kowanne,sai jelar ya biyo ta
bayan kunnenta, fuskarta yayi wani irin kyau kai kace daga qasar hindu ta fito.

A falon ama din su zuwaira keta kai kawo suna kawar da abubuwan dake buqatar a kauda su
din,tabbacin dai da gaske goben tafiya ta tabbatar musu. Don duk wani abu da zai iya datti ko qura anata
cireshi ana alkintashi. Ta gaisa dasu cikin mutuntatawa suka amsa mata cikin girmamawa da kuma qauna
da sanin darajar juna,sai ta zarce dakin ama, wanda tun daga bakin qofa takejin muryoyinsu benazeer,da
alama yauma sammakon tashi sukayi kenan.

A kunyace ta tura qofar dakin bakinta dauke da sallama. Ama dake yiwa batoul stretching da
mini stretcher dinsu ta amsa tana waiwayowa. Suna hada idanu sultana tayi saurin dauke idanunta
saboda sosai takejin nauyin ama,itama ama din saita basar taci gaba da tsaga sumar batoul tana cewa

"Uhm.......sai kuma me ya faru?" Da zumudi take ci gaba da bata labarin,wanda sai data zauna sannan ta
fahimci labarin daddynsu take bawa ama din,ita kuma ta tattara dukka hankalinta tana saurararta.

"Barka da safiya ama" ta fadi kaman wata baquwa

"Barka kadai.....mun tashi lpy?" Ta amsa mata yadda suka saba gaisawa ba tare data juyowa ba
"Lafiya alhamdulillah" zamowa dukka benazeer da batoul sukayi suka gaidata,ta amsa musu tana dan
dubansu. A kullum cikin zuciyarta sake jin alfahari takeyi da yaran,a kullum kwanan duniya wani kusanci
zuciyarta take samu da yaran,ko yaushe nutsuwa da tarbiyyar da suke samu yi mata dadi takeyi a rai,ba
wani guri da zasu baqunta su zauna ko su gifta saisun samu masoya,wani irin farinjini garesu,sai kuma
Allah ya hukunta suka zama wasu irin nutsatstsu masu hankali,idan ka dauke surutun benazeer wanda
shi din kaman a halittarta yake,saidai kuma duk surutun nata yana da limit,bata soki burutsu KO
maganganun da suka shallake shekarunta.

"Dame dame ama za'a hada?" Sai a sannan tadan waiwayo

"Ni kuma?,ai na kammala komai,saidai ke,abinda kikasan baki hada din ba ki hada,goben in sha Allah by
10 zamu tashi zuwa Nigeria,four kuma zamu wuce in sha Allah" ta fadi sanda benazeer da batoul keta
hayaniyarsu basuji ma me take fada ba. Kunya tadan sake kamata,ta sadda kai qasa tana matsa
hannayenta,sai ta miqe sum sum

"Zamuje lalle,ba zakije ba?" Ama ta tambayeta. Batajin zata iya hada wajen zama da ama na wasu
awanni,don ame laifin take jin kanta,don haka tace da ita

"A tahomin da kayan hadin kawai duka,koda mun isa can zan saka da kaina"

"To yayi" ta amsa mata tana qoqarin hadewa batoul gashinta guri guda.

Agogon fata na kamfanin D&G shine abu na qarshe daya daura a hannunsa,kuma shine
cikamakin kwalliyar da yayi cikin bugaggiyar shaddar qasar mali fara qal dake jikinsa. Shadda ce da aka
zubawa wani irin kwantaccen aiki daya dace da kalar dakakkiyar hular kansa,ya daga zagayyayun lion
eyes dinsa yana duban fuskarsa ma'abociyar sassanyan kyau da wani irin shinfidadden kwarjini wadda ta
qawatu da baqiqirin gashi daga gefe da gefen kumatunsa zuwa habarsa.

Comb ya dauka yana sake gyara gashin fuskar tasa da kyau,duk kuwa da cewa a kwance yake
yana sheqi,sheqin da zai gaya maka qololuwar tsafta da kulawar da yake samu. Siririn murmushi ne ya
subuce saman labbansa dake da wani irin color me jan hankali daya qarawa habarsa da kyakkyawan
hancinsa kyau,daren jiya ya tuna,yayi mafarki sosai da ita,mafarkin da ya sakar masa da matsananciyar
sha'awarta me cakude da wata iriyar narkakkiyar qauna da ya tashi da ita da safennan. Wani irin so ne
me nauyi da yaji tamkar an qara mizanin nauyin zuciyarsa,t bashi memory me dadi da ya tabbatar zaiyi
masa rakiya zuwa niamy ya bashi kuma dukkan karsashi har yaje ya dawo. Abu daya zuciyarsa ta tsaida
masa,wanann tafiyar idan yaje ya dawo,zaya zauna ayi komai ya qare tsakaninsa da aba ama harma da
sultana din. Bazai juri yana rayuwa da ita gida daya ba amma batasan girma da nauyin igiyarta dake
kansa ba.

Knocking qofar da kuma fitar sautin suhail shi ya Katse masa komai

"nous allons rater le vol(zamu rasa jirgi)" ya fadi da harshen faransanci. Bai amsa masa ba sai ajjiye comb
din da yayi,ya dauki wayarta data kwana a hannunsa ya zura a aljihunsa,sannan ya saka hannu ya jawo
luggage dinsa dake dauke da kayan sawarsa na kwana daya tak da zasuyi ya fito.

Zuciyarsa yakai nesa sosai ya miqawa suhail hannu. Ga mamakinsa shi kaman ma komai bai faru
ba ya bashi hannu shima suka gaisa yadda suka saba

"petit-déjeuner(breakfast)" suhail ya fada yana nuna masa warmer din kayan karin kumallon da Bibi tasa
aka shirya musu. Kai ya kada alamun a'ah

"Kasan yayi safiya yanzun,zan shiga muyi sallama da su ama"

"Saika fito don ni already ma munyi,har 'yar tsohuwa ma ta bani wata kyauta wallahi,naji dadin.kyautar
nan" ya fadi yana murmushi gami da satar kallon maina. Sarai ya ganshi,amma sai ya share kaman bai
ganshi din ba,ya taka a nutse yana fita daga sassan nasa.

[24/06, 5:14 pm] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 76
A gaggauce yake amsa gaisuwar masu aikin saboda shi kansa yasan lokaci yana dab da
qauracewa. Sanda yake duban agogonsa yana nufar dakin ama kai tsaye lokacin ta sanya santala
santalan fararen qafafunta da suka dan nuna ta qasan material din jikinta. Qafafun nata ya soma gani
kafin ya kai idanunsa har zuwa qaurinta don rigar bata sauka har qasa sosai ba. Tsigar jikinsa ya
zuba,wani abu ya tsarga mishi har cikin jininsa da ganin kwantaccen baqin gashi saman qaurinta,wanda
bame yawa bane,wannan din sai ya zama tamkar ado saman farar fatarta.

Da sauri ta kauce masa sanda yake sauke idanunshi a kanta. Kalbar kanta ta dauki hankalinsa
sosai lokacin da take giftashi da hanzarinta,don batason ma wani abu ya hadasu. Da kallo ya bita har ta
bacewa ganinsa,sai ya maida idanunsa ya lumshe,yana jin tsananin kewar tattausan qamshin da jikinta
ke fiddawa,ya qarasa ya murza handle din dakin ama ya shiga.

Tana amsa sallamarshi ta dauke kanta tana ci gaba da hada hadarta,ta fahimci gaba daya
kaman kunya ce takeson yin qaura daga jikinsa,shi yasa ta hade ranta da kyau. Daga benazeer har batoul
basu barshi ya qarasa shigowa dakin ba suka taho da gudu,kowacce na qoqarin fara hawa jikinsa.
Murmushi ya subuce masa,wani farinciki yana ratsa zuciyarsa,ko iya wadannan princess din da sultana ta
bashi kadai ya isa ya siya mata matsayin da bayajin duk duniya baya ga ama akwai wata mace data isa ta
sameshi,ya tsugunna dukkansu ya basu daman hawa kanshi da kyau kamar bai damu da farar shaddar
dake jikinsa ba,sannan ya miqe dauke dasu yana qarasawa wajen ama.

Har qasa ya tsugunna bayan ya ajjiyesu yana gaidata,ta amsa masa ba yabo ba fallasa,shuru ya
biyo baya sai kokaye kokayen benazeer da batoul. Agogonsa ya kalla yana cewa

"Akwai aikin bude wani company din ubangidana a niamy da zamuje ama,kwana daya zamuyi gobe zan
dawo in sha Allah,ayimin addu'a" maganar taji tayi mata banbarakwai har ta kasa hadiyewa,ta waiwayo
tana duban idanunsa

"Company din uban gidanka?" Ta tambayeshi cike da mamaki. Kai ya gyada

"Eh ama"
"Kana jinin gidan mayak'i?,jikan ABDU ME KANO?,ubangida fa aliyyu?" Ta kuma furtawa tana jinjina
abun. Qasa yayi da kansa,yasan sarai dukka tambayoyinta abinda suke nufi,ya kuma san meye ya taba
zuciyarta,to amma kuma shidin ya riga ya yiwa kansa alqawari ne,zaya dawo musu a cikakken mutum
me dogaro da kansa,wanda yasan zafin nema da rashin,wanda bai dogara da kowa ba,wanda kuma bai
aza nauyin rayuwarsa akan kowa ba.

"Allah ya bada sa'a" kawai tace dashi a taqaice

"Na gode" ya amsa mata yana miqewa dukka jikinsa a sanyaye. Ya sani don dai sunqi bashi cikakkiyar
damar da yake da buqata ne,amma akwai abubuwa masu tarin yawa da suke buqatar su sanar da juna
su kuma fahimtar da juna,saidai komai lokaci ne,yana sanya ran zuwa da wucewar komai a kurkusa.

A gaban benazeer da batoul ya tsugunna ya kama hannayensu ya sanya cikin nasa

"Ayima daddy Addu'a zaiyi tafiya" murmushi dukka sukayi,benazeer ta hade hannayenta waje daya ta
fara karanto ire iren addu'o'in da ake koya musu. Murmushi ya dinga yi yana amsawa da ameen,har sai
data gama suka shafa a tare,ya durqusa yayi kissing goshin kowaccensu sannan ya soma tafiya da baya
da baya yana daga musu hannu suna maida masa,tamkar yasan idan yaje ya dawo din ba lallai ya
taddasu,a haka ya fice a dakin.

Kamar zai wuce amma sai taji kaman ana jansa da magnet zuwa dakin nata,a nutse ya juya akalar
tafiyar tasa zuwa dakin nata.

A tausashe ya murza handle din ya tura,tana tsaye gaban madubi da madaidaicin mug dauke
coffee me dumi tana kurba a hankali. Har cikin jiki da zuciyarta taji shigowar tasa,amma wata zuciyar ta
bata shawarar dakewa,don haka ta basar,tayi kaman bata ganshi ba tana ci gaba da kurbar coffe din nata
da a yanzun taste dinsa ya sauya gaba daya a bakinta.

Maida qofar yayi ya rufe sannan ya murza key yana qarasowa cikin dakin hannayensa zube a
aljihun wandon rigarsa.
Ta qasan idanu take satar kallonsa,zuciyarta taci gaba da harbawa tana qoqarin dannewa.
Karon faro taji ya mata kwarjini sosai,shigar ta sake sakashi ya zama babban mutum kuma magidanci
zam,taci gaba da dannewa cikin nuna dakiya da juriya,shi kuma yaci gaba da qarasowa,bai kuma tsaya ba
har sai da yazo dab da bayanta. Cikin zafin nama taso zillewa,saidai ina ya fita ta wannan fannin,caraf ya
riqota,ya kuma sanyata cikin jikinsa da kyau yana dora habarsa saman kafadarta,wannan ya bashi damar
sakar mata numfashin da ya sanya dukkan wata tsiga ta jikinta tashi. Kici kicin qwacewa ta fara yi,ya
mata namijin riqo muryarsa can qasa da wani irin laushi tamkar wanda ciwo ya yiwa sassan jikinsa illa
yace

"Relax mana......zuwa nayi muyi sallama zan danyi tafiya,ayimin addu'a"

"Meye hadina da tafiyar ka?,wancan karon da zaka tafi din ka gayaminne?,yanzun ma Allah yasa kafi
ruwa gudu" wata malalaciyar dariya ya saki wadda ta sanyashi sakinta yaja da baya qaramar dariyarshi
nadan fidda sauti. Muddin a yadda yakeji a jikinsan nan yanzu da yadda lokaci ya qure musu yace zaya
biye mata tafiyar ba zata yiwu ba,yana da burin ya jigatata ainun ta yadda zata rasa bakin maida masa
martani

"Na fahimci tafiyata ta wancan lokacin ta miki zafi sosai......"

"Allah ya sawwaqe" ta maida masa a tsiwace. Murmushi ya sake qwace masa,shi daya yasan tanadin da
yayi mata yana tarata ne kawai,sai ya kalli agogon hannunsa sannan ya maida dubansa tsakiyar fararen
idanunta

"Idan ta miki idanma bata miki ba.....duk ba damuwa.....Allah ya dawo dani zan wanke kaina yadda ya
dace" ya fadi yana dage mata girarsa guda daya. Kai ta dauke da sauri saboda wani nauyi da ya aje mata
ta cikin idanunsa,ta soma nufar qofar toilet ba don tana da abunyi a can din ba

"Basai idan ka taras dani ba?" Har ya soma taku sai ya tsaya cak ya waiwayo a nutse yana dubanta,wani
abu ya darsu a zuciyarsa,ya sauke numfashi sannan a nutse cikin jerarrun kalamansa da kuma wani
yanayin sound dazai nuna maka da gasken gaske yake magana ya furta
"Idan kina ganin kin bacewa ganina a wancan karon......wannan lokacin kiyi gudu dukka iya yanda kike
ganin zaki iyayi cikin fadin duniya.....ni aliyyu maina mayak'i ina me baki tabbacin zan taddoki na kuma
zaquloki......i promise" ya furta yana daga yatsunsa. Da idanunta fes take kallonsa daga qofar bandaki,bai
qara daga haka ba ya juya a dan gaggauce yana ficewa a dakin bayan ya aje mata wayarta saman sofa
bed.

[25/06, 11:11 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

BOOK 02 PAGE 77

Numfashi taja me qarfi matuqa daga hancinta zuwa cikinta sannan ta fesar,yanayin yadda yayi
magana ya ratsata qwarai,har taji kowacce kalma na sauka a kowanne gaba na jikinta,ta dinga jin abinda
ya fadi din kamar dahir ne,amma kuma wani sashe na zuciyarta sai taji ya kasa aminta da hakan. Ta ina
zai zaqulota?,ta yaya zai taddota?,bayan inda zata shiga din zata guje masa ne da nisan tazarar tafiyar
awanni da kwanaki ma?,ba zata taba bari ya zaqulota ba, tabbas!.....itama zata tabbatar ta cika wannan
alwashin da taci. Da wannan tunanin ta fito daga bakin bandakin don dama bawai wani abu zatayi a ciki
ba,mafaka kawai take nema,ta dawo cikin dakin jikinta na neman mutuwa amma ta bawa kanta qwarin
gwiwa,ta sauke suit case dinta guda biyu,ta soma hada komai nata waje daya,tana ji a ranta da zuciyarta
muddin yana nijer batasan ranar sake zuwanta ba.

Shi daya cikin mota suna a hanya amma dukka jikinsa ya mutu murus,irin qiyayya da tsanar da
yake hanga cikin idanunta tana taba zuciyarsa sosai,baisan me take buqata daga gareshi ba wanda zai
wanke dukka laifin da yayi mata. Kamar me magana a radio din yasan me yake tattaunawa cikin ransa ya
soma magana kaman haka

_ba kowacce matsala ce tsakanin masoya sulhu ke maganceta ba,wani lokaci sai ayi fada,wani lokacin sai
anyi qarfa qarfa an saka qarfin iko_ a nutse ya lumshe idanunsa yana digesting maganar a
kwanyarsa,tsahon mintuna kusan talatin kafin wani murmushi ya subuce masa

"Na fahimta" ya furta can qasa yana jinjina kai.

"Me ka fahimta yallabai?" Suhail dake zaune gefansa yana duba newspaper da alama shidin makarancin
labarai ne ya fadi yana duban maina. Juyowa yayi suka hada idanu dashi ta cikin eye glasses dinsa
"It's not your own business" idanu suhail din ya dan fiddo sai kuma ya maidasu yana rufe jaridan

"U right.....abinda yafi damuna rashin samun layin crush dina......kaine nake ganin zaka taimaka min kana
neman watsa min qasa a idanu,ka qirqiri wasu labarai duk don ka nesantata dani......ni kuma nayi
alqawarin bazan bar marad'i ba sai da soyayyarta" ya fadi yana dunqule hannunsa guri guda. Da qyar
maina yawu ya wuce ta maqoshin maina,ya dauke kansa a hankali yana qoqarin tausar zuciyarsa kan
kada ya yiwa suhail mugun bugu cikin motar,muddin yace zai daki suhail to saidai buzunsa,don ko a qirar
jiki suhail din dan kalankashi ne me jikin fulani. Hannunsa ya tura cikin qaramar jakarsa ya fiddo
headphones ya dora saman kansa ya toshe kunnuwansa,yayi connecting da wayarsa ya soma sauraren
wani abu na daban,sai suhail yayi sak yana kallonsa kafin daga bisani ya dauke kallonsa yana girgiza kai.

**********Washegari sukayi sallama da dukkan wani family din MAYAK'I suka wuce airport suka bar
al'ummar gidan cike da kewar iyalan ama musamman BB. Bibi harda qananun qwallar wucewar yaran

"An daukesu an dauke uwarsu" ta fadi cikin falon nata tana qananun qwalla. Kusan dariya ta bawa
kowa,bibi din bata iya sabo da mutum ba idan ta tashi sabo dashi din,bare sultana da take tamkar wani
bangare na jikinta,ga yaran suma sun dosano farinjininta da kuma soyayyar data samu din.

"Sai da nace ki shirya mu wuce tare bibi,yanzun a miki shiri ki biyo bayanmu?" Ama ta furta cikin lallashi.
Kai bibi ta girgiza

"A'ah hamdiyya,barni a nan cikin ahalina,shekaruna turawa sukeyi,na gaji da yawo a qarfen nasara,irin
haka ne mutuwa zata riskeka a qasar wasu azo ayita tiri tiri da gawarka,ko mutuwa ne gwara ka mutu
cikin sutura a dakinka" maganar tata sai tadan taba zuciyar kowa amma sai suka bita da dariya,sultana
tace

"Mutuwa bibi ba yanzu ba,Allah ya qara miki dogon kwana me amfani"


"Ameen" aba dake duqe shima a gabanta ya amsa. Nutsuwa sukayi bibi ta musu addu'o'i sosai sannan
suka miqe,har sun fita ta sanya aka kira mata aba,ya dawo gabanta ya tsugunna

"Hamidou"

"Na'am bibi?"

"Rayuwa bata da tabbas,hakanan duk dan adam bai wuce kuskure ba,shine cikar dan adam din,abinda
nakeso dakai don Allah ina roqonka ka sassautawa yaron nan koda a iya fuska ne,ya dawo da dukka
qwarin gwiwarsa da kuma daidaita rayuwarsa,bai kamata mu rushe komai nasa ba akan kuskuren da ya
riga ya afku,kuma Allah ya kawo yankewar komai ba tare da an samu mummunan sakamakon lalacewar
rayuwar wani cikin su biyun ba" kai ya gyada a ladabce

"In sha Allah bibi"

"Allah ya albarkaci rayuwarku gaba daya" ya amsa da ameen.

Lokacin da jirginsu ya daidaita a sararin samaniya sai ta furta

"Alhamdulillah" cikin wata cikakkiyar nutsuwa,ta rufe idanunta tana jinta ta zama comfortable,
murmushi ya kufce mata,can qasan maqoshinta ta fadi

"Naga ta inda zaka nemo ni" tayi maganar cikin mugunta da jin ta tsere masa har abada.

A nutse ama ta dauke dubanta daga fuskarta tana sauke tata ajiyar zuciyar,tun daxun ta
fahimci yadda take cikin walwala da barowarsu nijer,ta sani koma meye zai sakata walwala baya rasa
nasaba da gujewa maina,batasan yadda wannan qaddara ta samo asali ba,kuma Allah shine masanin
lokacin qarewarta,bata taba ganin irin wannan mummunar rashin jituwar kamar tasu ba,tun abun be
damunta har ya soma tabata,abu daya ya rage mata wannan addu'ar zata ci gaba dayi
"Allahumma khir li wakhtarli". Maida dubanta ta sakeyi ga benazeer da batoul,basuyi sallama da
mahaifinsu ba don basusan inda zasu koma din wani guri ne da zasu jima basu ganshi ba,duka lissafinsu
Nigeria zasu sake zuwa suyi wani hutun na kwana daya ko biyu kafin daddynsu shima ya dawo daga
tafiya.

Iska ta kuma furzarwa,Allah ya sani taqi shaida masa ne saboda tana son ya sake sanin maqurar
muhimmancin mace a wajen d'a namiji,tanason yasha wahalar samo kanta wadda bai sha ba sanda aka
aura masa ita sama taka yana zaune cikin inuwa,tanason ya jigata yadda bazaiyi wasa da ita ba,bazai
kuma yi wasa wajen nemo soyayyarta ba. Murmushi yadan qwace mata tana hangoshi sanda zai duba
kaf gidan yaga ba ita ba benazeer ba batoul ba kuma sultana din. Ta tabbatar sai yayi musu qaramar
hauka,to amma kuma tana dan shakkar anya zaya dauki lokaci mai tsaho me gano inda suke ba?. Ta
sanshi farin sani tas ma kuwa,tunda dai ya fita daga jikinta ne,yana da naci da bin qwaqwafi akan dukkan
abinda yakeson aiwatarwa ya kuma sanya a gaba,uwa uba ko da can yana da wata fikira da basirar
saurin gano abu,to amma koda ya gano inda suke din,tasan bazai gano su a banza ba,dole energy da
kudaden aljihunsa suyi aiki,idan yazo kuma ya kawo mata kanshi,don ba zata zake bari yayi aiki
qarqashin wasu ba,bayan a abinda kakanninsa ita da aba suka tara masa yana da dukiyar zai dauki
mutum Dari aiki a qarqashinsa da cikakken albashin da zai riqe kowanne ma'aikaci da iyalinsa.

Kwana daya rak suka daidaita cikin qasar France a garin paris. Ba wani dauda ko qura me yawa
suka samu,don haka cikin awanni qalilan suka gyare komai,komai kuma ya koma kan muhallinsa,abu na
gaba data fara shiri shine fara aikinta a sati na gaba a gidan tv ta qasar paris,wanda zata zama jagorar
shirin daya shafi al'adun africa gaba daya. A satin suka tura mata kudade masu yawa daga gidan tv din na
wardrobe allowance. Bata da buqata ba abinda kuma zatayi dasu,don suttura kam wata ma sai ta
shekara biyu bata sakata ba. Ta bangaren aikinta da zata fara kuwa komai aba ya tanadar mata,ga ama
itama a gefe data tsaya mata kan ta lissafa duk abinda take da buqata ko takeso,buqata kam saidai idan
bata fadi wadda takeso ba,don haka hanakalinta kwance take shirye shiryen kama aikinta.

*_MAINA FA?_*

[28/06, 9:29 am] Karymart🥰🥰: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 78
*ALIYYU MAINA*

Cikin qwazo da kuma qwarewa ya jagorancin aikin duba kamfanin da gabatar da abubuwan da
suka zama dole a buqata a cikinsa don samun ingantattun abubuwa da zasu dinga fitarwa. Haka kawai ya
samu hankalinsa da tunaninsa suna karkasuwa kashi kashi,wani a niamy wani a marad'i,duk bayan wasu
lokuta sai benazeer da batoul sun fado masa a rai,ta wani gefen kuma sultanan ce gaba daya tayi masa
tsaye a rai,yana tuna abubuwa masu yawa da suka faru a tsakaninsu,bama iya sultana kawai ba hatta da
yaran,wani abun ya saki murmushi wani ya girgiza kai,daga qarshe yakai tafin hannunsa saman
qur'aninsa saitin zuciyarsa ya dafe yana fidda wani sihirtaccen murmushi.

Ya yadda yayi imani sannan kuma ya tabbatar a yanzun sune rayuwarsa,sune Kuma duniyarsa
gaba daya,bayajin zaya iya rayuwa ba tare dasu ba,haqurin da yayi na wancan shekarun,ya rayu babu
su,a wannan karon baya jin zuciyarsa zata dauke wannan. Wannan tunanin ya sanyashi yin overwork a
ranar,suhail nata mitar ya gaji,ba sauri sukeyi ba,me zaya hana su isa masauki su kwanta, gobe su qarasa
zuwa jibi,ko gata ne sa koma marad'i din,ai suna da enough time.

Juyawa yayi kawai ya kalleshi,shi daya yasan me yakeji a zuciyarsa,yana ji kaman ya raba
zuciyarsa ne gida biyu yabar rabi a marad'i,a wannin da yaketa spending a nan din yana ji kaman ya
maidosu marad'i,bazai taba iya kaiwa jibi a niamy ba,yana buqatar komawa ya hada kan iyalinshi waje
guda,ayi duk abinda za'a yi a gama,zai rungumi kowanne irin tsanani,don wannan karon bawi da wasa
yakeson maidota cikin rayuwarsa ba.

"Ban hanaka zuwa ka kwanta ba......abinda na sani dai kawai shine,gobe in sha Allah a marad'i zan
kwana,ko mun gama ko bamu gama ba,bare ma inda tabbacin na sanya dukkan effort dina,gobe azahar
yayi yawa mun gama in sha Allah.....idan ka gaji kaje ka huta zan iya kammalawa" bai sake cewa komai
ba ya maida kansa yaci gaba da magana da ma'aikatan.
Satar kallon maina din kawai yakeyi,he's so hardworking,tun farkon haduwarsu abinda yaja
raayinsa game dashi kenan,bashi da wasa,ko meye ya saka a gabansa sai ya cimma nasararsa. Iya
wannan daya tuna din,sai shima ya kakkabe dukkan wata guntuwar kasala ya miqe sosai suka ci gaba da
aikin tare.

Kaman yadda ya yiwa kansa alqawari washegarin qarfe sha biyu na rana sun kammala
komai,zuwa qarfe daya ya kammala rubutawa daddy report ya tura masa ya kuma turawa sardauna
ragowar,kai tsaye suka koma masauki,ya koma toilet ya sake watsa ruwa,ya kuma shirya tsaf cikin wani
lallausan farin yadi,saidai kuma dukka wannan gaggawar tashi dole ya jira akwai ragowar lokaci,don
jirginsu sai qarfe hudu zai tashi,yana ji yana gani ya fita corridor din dake manne da dakinsu ya zauna
samam couch yana duban suhail dake zaune d'ai d'ai abinsa ba alamun shiri tattare dashi.

Kanshi ya dauke yana zuqar numfashi,zayaso suhail din yayi zamansa a nan ba tare daya bishi
marad'i din ba,duk da haka sai ya danne zuciyarsa ya tambayeshin yana duban wani guri na daban

"Hala ka dawo gida kenan?"

"Me ka gani?" Suhail dake shan yoghurt ya fadi

"Banga alamun tafiya tattare dakai ba,na dauka zaka kammala hutunka a nan,zamu hade kawai a
France"

"Inaaaa" ya furta yana miqewa da hanzari kamar wanda aka mintsina,har sai da maina dole ya juyo ya
kalleshi.

Fararen danunsa fes cikin na maina din yana kallonsa

"Banga ta zama ba,ka manta har yanxu ko cikakken magana bamuyi da crush dina ba?,yaya zan koma
ban samu soyayyata ba?" Idanunsa ya mayar ya lumshe.
yanajin kamar suhail yana diga masa wani abu saman zuciyarsa,baisan me yasa ba,ba halin
suhail bane qin fahimtar mutum da gangan ba,amma sai yaga kaman idanunsa ya rufe a wannan karon

"Idan ma akwai wanda ya sanyaka kakemin haka......ina me baka shawarar kabi a hankali,idan har ka bari
na fusata zan manta da matsayinka a wajena,na gaya maka ina kuma sake gaya maka,sultana is my
wife......" Yana kaiwa nan ya miqe a nutse yana bar masa wajen. Da kallo suhail ya bishi,shi fa har yanzu
yana tantama akan hakan,ta yaya hakan zata kasance?,shekarunsu nawa dashi?,amma koda wasa bai
taba zancan wata ba?,yaran da yake iqirarin nashin ne sau nawa suna zancan baisan yaran wanne qasa
bane?. Kai ya girgiza,shi kam har yanzu bai gamsu da zancansa ba.

Kafin lokacin ya cika sai ga suhail din ya shirya tsaf harda jakanshi da wasu kayan daya musanyo
daga ainihin masaukinsa gidan kakanninsa. Maina din baice masa komai ba,don haka ko cikin jirgi ma
kowa sabgar gabanshi yakeyi.

Awa biyu rak ta iso dasu marad'i,cikin drivers na gidan mayak'i daya daga ciki yazo ya daukesu
daga airport cikin daya daga cikin motocin maina dake gidan.

"Wanne kalan malalacin tuqi kakeyi ne?" Maina ya tambayi driver din yana kallonsa ta cikin madubin.
Waiwayowa suhail dake qoqarin kunna wayarsa yayi ya kalli maina,sai ya maida dubansa ga driver din
wanda yake qoqarin take motar ya qara mata gudu

"Kada ka damu tuqinka yayi dai dai ba laifi,muje a haka" sai ya juya ga maina. Ya fahimci kaman bashi da
nutsuwa daga jiyan zuwa yau

"Fake wife din naka ka matsu ka gani ne?" Ya tambayeshi cikin muryarsa akwai sautin tsokana me yawa.
Wannan karon gaza daurewa maina yayi,ya kaima suhail wani mummunan duka a kafadarsa,saiga suhail
din ya gantsare yana runtse idanu hadi dayi masa nuni da driver dake cikin motar. Dukka girarsa ya daga
yana nuna masa ko a jikinsa

"Gaba idan ina sabgogi na nida iyalina ka sake shiga,na rantse da Allah da Allah saidai su sardauna suzo
su daukeka a kakkarye"
"Amma dai kai mugu ne wallahi,koda yake na fuskanci inda ka dosa,kishi ne yake dawainiya dakai,kuma
kada ka manta......ba sauke kafada ba,ko meye zaka yimin idan tace saini saini din" tafin hannunsa kawai
ya sanya ya lullube fuskarsa,ya fuskanci ko meye zai cewa suhail bazai daina fadin abinda ke ransa ba,tun
ba yau ba,yasan shi din dan kai tsaye ne,amma yanzun ya soma fahimtar abinda yakeyi masan kamar
akwai wata a qasa.

Ana kiraye kirayen magarib motar ta daidaita a farfajiyar babban gidan nasu,ya sauke ajiyar
zuciya yana dan yawo da idanunsa wai ko zai hangi benazeer ko batoul. Yanason shiga ciki ya gansu,to
amma kuma muddin ya shiga din zai iya rasa jam'in sallah,don haka ya daure ya cire agogonsa da sauran
kayayyakinsa ya miqawa attah yace ya shiga masa dashi wajen ama. Atta din nason masa bayanin saidai
ya kaiwa bibi yaga har ya juya yana amsar ruwan alwala daga hannun daya daga cikin ma'aikatan
gidan,don yace bazai qarasa famfunan dake jere a farfajiyar gidan.

Tare suka wuce masallacin shi da suhail almu atta da saddi. Sukayi sahu daya har aka idar,bai
zauna azkar ba yasan kafin ya isa gida ya kammalasu a hanya,suka sake rankayawa cikin gida tare.

Sassan ama ya soma wucewa kai tsaye,saidai tun bai isa ba ya fuskanci sashen a kulle yake,ya
dubi almu da suke tare

"Ina ama?"[7/3, 11:10 PM] +234 906 707 5191: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 81

*_SULTHANA_*
**********Dukka wani mayuka zuwa qananun engines na gyaran gashi ta zube cikin bathroom dinta
tana hidimar gyara dogon gashinta. Dole ta zama wata 'yar gayu ta musamman,komai nata ya
canza,wani irin feleqe gareta yauqi da ya hade da wani irin aji kyau da kuma zallar kulawa na gyara da
take samu. Zama da ama din ya zame mata kamar wata jami'a ta musamman,tayi naso da dabi'unta
masu tarin yawa.

Tana tsaka da taje kanta ta soma jiyo hayaniyarsu,sharewa tayi taci gaba da abinda takeyi saidai
kuma hayaniyar tasu kaman qaruwa yakeyi,dole ta ajjiye comb din ta dauki qaramin towel ta rufe kanta
ta fito.

Tsaiwa kawai tayi riqe da qugunta tana kallonsa,harda ama,tana cikinsu,sun baje kaya masu
uban yawa tsakiyar falon sunata zabe zabe. Batoul ce ta fara ganinta,tana ta dariya ta kalleta

"Guess what mummy?" Sunan mummy din data kirata dashi ya sanyata tayar da kai ta kalleta sosai. Sau
daya suka taba fadi ta hanasu, w sunce daddynsu ne yace mummynsu ne,sunanta mummy not aunty.
Haushinsa ya kamata a sannan,meye nashi da wani shishshigi zai sauya mata suna daga sunan da yaran
suka saba kiranta

"Mummy ki canka" benazeer ta fada da qarfi tana boye abu a bayanta. Wannan yaja hankalin ama
daketa tara kaya gefe guda ta waiwaya tana kallonta

"Ki canka din mana.......suna birthday month dinsu ne,saiki gaya mana date muga idan kin riqe" ta fadi
tana ciro wani kwali dake dauke da wasu kids wears designers na wani kamfani ta aje gefe.

Murmushi tayi tana dan jin kunyan ama din,saita qaraso din ta zauna,sun sanyata a tunani

"Yau 25th......kaman......kaman on 28ne"

"Kaman ko kuma haka ne?"


"Hakanne ama,28 sixs years kenan?" Ta fadi cikin mamaki tana dan fidda idanu. Murmushi ama tayi,taji
dadi cikin ranta,don batayi tsammanin ta riqe ranar ba

"Wanne kaya zaki saka mummy,ama zata hada mana birthday party?" Benazeer ta tambayeta cikin
murna

"No......ranar da na fara zuwa aiki washegari ne zakuyi,maybe ma ina gurin aikin...... but zan bada gift na"
fuska suka bata dukkansu su biyun, benazeer ta karyar da kai

"Please mummy" waiwayowa tayi ta zaro mata idanu

"Ni ko ama?,......ama ne mummy"

"Ama grandma kece mummy" ta amsa mata tana nunata da yatsa. Ama da ta kauda kai kaman bata gani
dariya ya kamata,yayin da mamaki ya kama sultana sosai,wato duka yayi brainwashing yaran?. Bata
gama wannan mamakin ba ta sake ballo mata wani ruwan

"Daddy fa zaizo?,uncle goumar yace zaki gayyato mana shi" ai batasan sanda ta qarasa fiddo idanun nata
dukka waje ba,wannan din kuma bai hana benazeer ci gaba da zubo da surutunta ba

"Na daukama dashi zamuzo?,don Allah mummy ki gayyaceshi,we missed him a lot......ko batoul?" Tayi
tambayar tana juyawa wajen batoul din. Da sauri yarinyar ta gyada kai itama,qarasa daburcewa tayi,sai
kawai ta juya ta wuce ciki ba tare data samu amsar basu ba.

Guri ta samu ta zauna,ta kasa qarasawa toilet din,wai anya kuwa maina zaibar rayuwarsu yadda
ya kamata?,tana tsoron faruwar wasu abubuwa nan gaba. Dukka kayan da tasan sunyi cakudedeniya
dashi a nijer ta waresu guri guda,don duk wanda ta dauko babu abinda takeji a jiki sai qamshinsa. An
wankesu kusan sau uku kenan,amma bata daina ji ba,kawai saita sanya kuka tana rufe fuskarta,kukan da
ita kanta batasan meye dalilinsa ba.
*_MONDAY_*

Da dukka karsashi da qwarin gwiwa ya tashi ranar duk don kada yayi disappointing daddy. Ya shirya
tsaf shi da sardauna da zai wakilci daddy ranan farko da za'a fara amfani da asibitin.

*_SULTANA_*

Ta bawa ranar muhimmanci me yawa cikin tarihin rayuwarta,ranar nasara kuma ranar sa'a a
wajenta. Tun bayan sallar asuba bata koma ba,ta kasa zaune ta kasa tsaye,hatta da kayan da zata sanya
daga gida zuwa tv station din,da wanda zata saka yayin gabatar da program din a dakin da aka tanada
don buqata irin wannan.

Qasa ce ba irin tamu ba,suna matuqar bawa lokaci muhimmanci,don haka kafin cikar lokacin
dukka iyalan hamdiyya abdu me kano suka isa gidan tv din don yiwa sultana rakiya a ranar farko ta kama
aikinta,a matsayin cikakkiyar 'yar jarida da zata shugabanci sashen al'adu na gidan tv din.

Ama aba benazeer da kuma batoul din dukkansu,sauka ta musamman akayi musu,bayan
tattaunawa a wani qaramin hall na musamman dasu ama din a matsayinsu na iyayenta,sun basu
tabbacin cewa zata samu dukkan kulawa da mutuntawa data dace da addininta da al'adarta da kuma
mutuncinta,uwa uba kuma sun sani tana da qananun shekarun da take buqatar hakan,daga qarshe suka
rankaya tare aka sadar dasu zuwa ga office dinta.

Sam bakin sultana ya kasa rufuwa, murmushi ne zalla kwance saman kyakkyawar
fuskarta,kyawawan tausasan labbanta sun fadada qwarai da mayalwacin murmushi. Madaidaicin office
ne dake dauke da toilet da kuma balcony domin shan iska,ga spare din daki don changing kaya,an zuba
mata komai don qawata wajen da kuma bata damar gudanar da aikinta hankali kwance.
Aqalla sun kusa awa daya wajen,aba ya mata addu'o'insa sosai ya kuma bata taqaitacciyar
nasiha data ratsata sosai ta kuma sanyaya mata jiki,sannan ya fiddo key din mota ya ajjiye mata a
gabanta

"Don sauqaqa zirga zirga,ranakun da kikejin qyuya kuma zaki iya bin train" hawaye ne suka fara digo
mata,ta zame zuwa qasa saman gwiwarta sai ya dakatar da ita

"Tashi ki koma ki zauna,kada kicemin komai,jinin mohmoud yafi qarfin komai a wajena,rayuwarsa
mohmoud ya sadaukarmin,banda Mahmoud da yanzun haka ba'a san waye hamidou bama,abu daya
zakiyimin shine,ki kula da kanki,ki karemin tarbiyyarki da mutuncinki.....bazan lamunci duk wani abu da
zai zama cutarwa ko cin zarafi a tattare dake ba" dan dubansa kadan ama tayi,sai taji kaman yana
magana a fakaice ne akan aliyyu,amma sai ta share zancan daga ranta,tunda bai kama suna ko kwatance
da zai nuna shine ba. Duka suka tattara suka tafi suka barta ta fuskanci ayyukanta,wanda sai kusan
yamma sannan zata dawo gida.

A nutse ya maida qofar ya rufe yana ajiyar numfashi,baro mutanen da wajen hayaniyar da yayi
sai yakejin kamar ya tserewa wani mugun abu. Kwata kwata baya son hayaniya ko surutu me
yawa,yanzunne kanshi zai fara yi masa ciwo.

A hankali ya zare suit dinsa na saman ya maqale,ya wuce toilet ya daura alwala ko zaiji mode
dinsa ya daidaita,kasancewarsa kuma mutum da baya rabo da zama da alwala(hakan yana da matuqar
muhimmanci,don tana bawa mutum kariya sosai daga dukkan sharrin wani abu me sharri mutum ko
aljan).

Saman sofa din da aka shirya daga wani sashe daban na office din ya zauna,yayi relaxing sosai
yana fidda numfashi da kyau,har sai da yaji ya fara komawa dai dai. Qafafunsa ya sauke yana lissafa
adadin kwanakinsa a paris,yana ganin kamar yayi nawar gano inda ama suke,don haka ya sanya hannu
cikin zafin nama ya jawo system dinsa dake aje saman table ya bude.

Aiki sosai ya shiga yi da ita,lokaci lokaci yana magana ta wayarsa,sau biyu ana masa knocking
yana neman excuse akan wani aiki yakeyi me muhimmanci.
Kimanin awa guda da wasu mintuna kusan arba'in din kafin hannunsa ya tsaya cak saman
board din system din,yana duban sunan qasar dake yawo saman screen din. A fili fuskarsa shimfide da
wani shauqi da farinciki,zuciyarsa fari tas ya furta

"Paris!" Sunan ya fita tar a bakinsa da wani irin accent tattacce.

Baya ya koma ya jingina sosai da kujerar yana tallafe da qeyarsa,wani sassanyan abu ke masa
yawo cikin zuciyarsa,ama benazeer da batoul dinsa dukka suna Paris?,suna qasa daya?,jaha
daya?,wannan shine dalilin da ya sanya yakejin raguwar qunci kenan daga zuciyarsa tunda ya sauka a
qasar?,wannan shine dalilin da yasa ya dinga jin ya nutsu sosai da qasar?.

"Komai yazo qarshe,zai kuma zo da sauqi" ya furta a fili yana jin kaman ya gansu ya gama.

Knocking da akeyi shine ya katse masa tunaninsa,sai kuma kira ya shigo daga wajen sardauna

"Am done.....yallabai a daure a budemin qofan" ya fada da sauqin kan nan nasa har sai daya bawa maina
dariya,ya aje wayar baice komai ba ya tashi ya nufi qofar.

"Done and dusted" sardauna ya furta yana saluting maina. Murmushi ya sakeyi,ya miqawa sardauna
hannu

"Daddy ya kamata ka bawa wannan salute din sardauna...... he's our mentor"

"Harda kaima haidar......mafarkan daddy na shekara da shekaru dana gaza cika masa su yanzun ka zama
silar cikarsu........ thanks for coming into our lives" jijjiga hannun sardauna yayi ya jashi zuwa kujera

"Kowacce kaddara da silarta sardauna.......sanda duk wani abu ya sameka qila sila ce kuma ta samuwa ko
faruwar wani abu ga rayuwarka,Allah shine abun godiya" kai sardauna ya jinjina
"Haka maganar take......kunyi waya da suhail"

"Karka ambatarmin shi,tunda ya bini ciwon kai kawai yake bani,na rantse saina ragargaza maka dan uwa
watarana" dariya ya kubcewa sardauna,ba kasafai maina yake biyewa suhail ba,amma kuma duk randa
ta hadosu to da zafi zafi abun yake zuwa

"Indai suhail ne kayi duk yadda kakeso dashi,hasalima ni zan tayaka" ya bawa maina amsa yana isa
gaban babbar tv plasma dake maqale a bango ya tsugunna ya kunnata,sannan ya juya zuwa wajen fridge
yana cewa

"Bari muga me zamu samu a office din likitan zuciya" cikin dan tsokana da jan wasa.

Sanda ya bude bakinsa zai bashi amsa,daidai lokacin muryarta ta karade dakin,cikin tattausar
muryarta me dauke da tataccen harshen France,wanda daji kasan ba tsintarsa tayi a hanya ba,don ya
kama bakinta radam.

Idanunsa nakan wayarsa a sannan yana duba saqonnin ayana da na laila da suka kusan yin
gware wajen shigowa wayarsa,kowacce na tura masa saqon fatan alkhairi ne da fatan nasara.

Da sauri ya cira kansa daga screen din wayar zuwa screen din tv din,idanunsa sukayi kuwa
kyakkyawan gani.

Beautiful sultana,farar ba'abziniya wadda dukka kamanninta sukafi karkata da jinin arab,fara sol
me wata irin ni'imtacciyar fata me azabar sulbi da sheqi,sanye cikin ainihin kayansu na al'ada,kayan da
aka san kowacce mace ba'abziniya da sakasu,kalar shuni da sukayi masifar fidda kyawunta suka dace da
jikinta,hatta da kyawawan qwayoyin idanunta a yau sun fidda kyansu,brown din qwayar idanu me wani
irin sheqi tamkar an diga mai a cikinsu,siraran labbanta sunsha nasu adon,kamar yadda zara zaran
yatsunta da hannayenta suka sha adon banguls na azurfa da tagulla da wasu irin duwatsu irin nasu.
Gashinta kawai bai fito ba,ta sayashi cikin daurin kallabin dake kanta.
Da qyar ya zuqo numfashinsa,da mugun wahala da kokawa da rai ya zaquloshi ya maidoshi cikin
qirjinsa. Me yake shirin gani haka?

"Ba sultana bace" wani sashe na qwaqwalwarsa ya gaya masa

"No" ya furta a sarari wanda banda hankalin sardauna nakan wayar da yake amsawa fes zai jishi. Sultana
ce,babu wani yanayi da zai hanashi gane sultana,babu shi a duniya!,tsanani wahala ko dadi.

"Ma sha Allah,wannan kamar shigar gargajiyarku ko haidar?,da alama presenter din expert
ce......wannan program din zaija jama'a gaskiya" sardauna ya fadi bayan ya dauke idonsa daga saman tv
din yana lalubar wajen zama.

Kasa hadiye abinda ya taso masa yayi,ya sanya remote ya kashe tv din gaba daya. Dago kai
sardauna yayi da zummar tambayarsa me yasa ya kashe?,ya barshi suga gargajiyar nijer a paris
mana?,sai maina din ya rigashi tambaya

"Wanne gidan tv ne wannan?,a ina kuma yake?"

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/3, 11:10 PM] +234 906 707 5191: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 page 82

"ga logo dinsu can a sama,kaman national TV ne ai ko?" Sardauna ya fadi yana kai cup din
bakinsa.

Remote din ya ajjiye ya sake daukar wayarsa cikin karsashi,gefe guda yana jin ranshi yana
sosuwa,yana hasaso dubban miliyoyin jama'ar dake kallonta yanzu haka live

"Ya salamu ya Allah" ya furta qasa qasa bayan dukka bayananta sun fito a page din gidan tv din a
matsayin sabuwar ma'aikaciyarsu ta sashen al'adu.

Iska ya sake furzarwa,kusan ya gama samun komai,a yanzun samun adress nata ba shine a
gabansa ba,don yasan bazai zama damuwarsa ba. Bai sauka ba sai daya gama bincika dukkan abinda
yake da buqatar bincikawar,wanda ya daukeshi dogon lokaci,don har sai da sardauna ya tafi ya bashi
cikin office din.

A nutse take driving cikin takatsantsan dabin dokokin qasar,gefe guda kuma ranta fes,nishadi
takeji sosai a ranar,komai yayi successful,su kansu suna yabawa da yadda ta gabatar da program din
cikin zaar qwarewa,babu wani abu da zai sanya kayi tunanin farin shiga ce ita din,ta samu yabo
sosai,hakanan a iya ranar kawai gidan tv din ya sake samun qarin viewers da sukw bibiyarsa ta kafafen
sada zumunta da sauran kafafen sadarwa.
Ta cikin speaker din motar ta jona take sauraron VN din aminata da ta bibiyi shirin sanda ake
gabatar dashi. Kalmomin yabo ne sosai da kuma alfahari da ita da family MAYAK'I keyi,ba aminata kadai
ba,ta samu saqonnin cousins dinta da yawa da ayanzun take saurara yake kuma sake sanyata nishadi,
kyakkyawan fuskarta tattausan murmushi kawai take fiddawa wanda yake qara mata wani irin kyau da
kuma kwarjini.

A nutse ta isa qofan gidan,ta ajjiye motar a muhallin da gwamnati ta aminta da ajjiye ababen
hawa,ta bude motar a nutse ta cire wayarta tana daukan hand bag dinta idanunta ya sauka akan pack na
snacks da abokiyar aikinta 'yar qasar nijer ta bata dioura. Zuwan sultana ya yiwa dioura dadi sosai,don
sai ta jita tamkar a gida nijer,ta samu 'yar uwa abokiyar aiki. Wunin ranar nan nan ta dinga yi da
sultana,ganin farko dama Allah ya hada jininsu,gashi kuma suna qasa daya.

Daukan pack din tayi tana murmushi tana tuna kirkin dioura,a yau din tana jin duk wani baqinciki
da bacin rai dake ranta ya goge fes,sai ta soma takawa cikin gidan riqe da Jakarta.

Sau daya tak ta danna bell aka bude kaman ana jiranta ne dama. Wani abu taji an watsa mata
tadan kauda kai kafin ta bude idanunta tana duban benazeer da batoul dake tsalle a gabanta

"Happy happy mommy,first day a gidan tv" benazeer dake fama tsalle ta fada

"Mun ganki mommy Allah" batoul itama ta fada tana dariya. Murmushi ya qwace mata,abun nan da
bahaushe ke cewa diyoyin sanyin idaniyar iyayensu shine ya saukar mata,tadan saci kallon ama dake
tsaye tana murmushi,saita ajjiye kayan hannunta ta tsugunna ta rungumesu dukansu

"Thank you,na gode sosai" sai kuma ta miqe a kunyace ta qarasa gaban ama tana kallon dam decoration
din da suka yiwa falon da rubutun congratulations

"Barka da warhaka ama,ya gida ya yara?"

"Barkanki dai ma fille('yata),tu as travaillé dur(kinyi aiki sosai),nayi alfahari sosai dake yau,ina fata Allah
ya qara haska miki rayuwa,ya haska miki kuma dukkan kyakkyawan abu,ya haneki da fadawa hanyar da
ba dai dai ba" ama tayi mata dukkan wadannan addu'o'in tana dafa kanta. Kunya ta sake kamata,ta
rusuna tana sunkuyar da kanta qasa,sai ama din ta dan janye baya.

"Ki shiga ciki ki huta kafin aba dinku ya dawo ki bamu labarin yadda aikin ya kasance"

"To ama na gode" ta amsa mata. Da kallo ama din ta bita,dai dai da rana daya bakinta bai tana gajiya ba
wajen roqon ubangiji ya daidata dukkan al'amuran rayuwarta,kai ta kada tana maida dubanta cikin
falon,saita nufi benazeer da batoul da suka tasa cake din da ta sa aka kawowa sultana din a matsayin gift
a gabansu suna lakata suna ci ta soma musu tsiya

"Tofa ga shazumamu me bakin shan zaqi"

*_Aliyyu maina_*

Sake juya fuskar system din masa yayi a karo na babu adadi wai ko arrow din dake masa nuni da
direction din arean da phone number din yake aiki zai sauya akala,saidai fa ina,duka adress din da arrow
din suna masa nuni ne da gidan dake kallon nasa gidan. Tsananin mamakinsa ya qaru,ya kashe system
din ya sake kunnata,ya koma kan aikin nasa still abu daya yake nuna masa.

Tsam ya miqe daga inda yake zaune ya sauke qafafunsa a hankali,ya zura takalmansa ya taka a
nutse har ya isa gaban babban window din dake facing gidan da arrow din ke nuna masa.

Hannu biyu ya saka ya yaye labulen yana sauke idanunsa akan gidan. Kamar kowanne gida dake
qasarma gaba daya zai iya cewa,a rufe yake ruf baya iya hangen komai da zai bashi satar amsar
tambayarsa. Dukkanin idanunsa ya zubawa gidan kamar yana fatan ganin gilmawar wani,saidai shuru ba
motsi ko gilmin komai. A qalla ya kusa kashe awa biyu kenan daga aikin zuwa tsaiwarsa a wajen yana
neman hujja,tunda ya dawo daga office bai bar gurin ba,ko abinci bai nema ba daga wajensu
Ahmad,ruwan lemo kawai yake dirkawa cikinsa. Sakin labulen yayi da zummar komawa ya sake
bincikawa,amma sai kuma yaji zuciyarsa ta kasa yarda da qaryata binciken da takeyi. Sake juyawa yayi ya
kalli gidan,sai ya taka a hankali ya koma mazauninsa ya dauki wayarsa ya fara laluben number ahmad.

Bugu biyu kacal ya dauka,komawa yayi ya zauna yana amsa gaisuwarsa da harshen faransanci

"Ina da aike da zanyi maqota,akwai dan aike da zan samu?"

"Eh akwai,nan da mintuna biyar zai iso yallabai"

"Da kyau,na gode"

"Ba godiya yallabai" ahmad din ya fada yana murmushi. Shi daya yasan zallar karamci irin na maina,ya
jima bai hadu da mutum me karamcinsa ba,amma kuma da sardauna yake gaya masa halin dattako irin
nasa sai gaba daya ya qara sallamawa lamarinsa.

A nutse ya miqe yana binciken me zai aika dashi gidan a mazaunin saqo?,me zaya bada wanda
zai bashi damar fahimtar su waye mazauna gidan?.

Tunawa da yayi da su benazeer ya sakashi bude fridge yana laluben chocolate din da ahmad ya
zuba tun randa yazo gidan,shi din ba gwanin shan zaqi bane,wannan ya sanya ya manta da lamarinsu
gaba daya. Dukka kwalayen ya debo ya shiryasu saman table,dai dai sanda yaji ana danna bell sai ya taka
ya bude qofan. Matashin saurayin bature ne dogo siriri,ya gaidashi cikin girmamawa,ya amsa masa yana
masa nuni da kwalayen,sannan cikin yaran faransanci ya nuna masa gidan da zai miqa din.

Bakin window din ya koma ya sake budewa yana dafe window din da hannayensa,yana biye da
takun matashin har ya isa qofar gidan ya kuma soma danna qaraurawa.

Tana zaune tsakiyar benazeer din da batoul tana musu adon gashinsu. Dole suka sakata gaba
akan ita zata gyara musu kansu saboda goben sunsan zata fita aiki ne tun da safe. Ama na zaune a gefe
tana duba wani littafi daya shafi hikayoyin gargajiya da aka rubutashi da yaren faransanci,sultana ta
yunqura zata miqe saboda qarar door bell din,sai ama ta ajjiye littafin tana cewa

"Yi zamanki" ta jawo wani madaidaicin farin hijab ta sanya ta miqe tana nufar qofar,a nutse ta murza key
din sannan ta Murda handle din ta bude.

Tarwai fuskar ama dinsa ta bayyana a gaban qofar,ya lumshe lion eyes dinsa yana jin wani abu
yana tsarga masa,ya sake budesu da sauri dai dai sanda ta waiwaya bayanta tana magana,da alama da
sultana take magana,yadda kuma take kallon saqon bayan ya miqo mata ya bashi tabbacin ta dago haske
ne,ko kuma ranta ya darsa mata wani abu.

"Merci" ta furta da yaran faransanci bayan ta karbi kwalin dake da sanyi alamun daga gidan sanyi aka
cirosu.

Tunda ta karbi kwalin jiki da zuciyarta ke raya mata wani abu,alamu da motsin aliyyunta takeji
all over her heart......tana jin kamar yana kusa dasu ne,tana da yaqini kaso tamanin cikin dari cewa daga
hannunsa wannan ya fito.

"To idan bashi ba waye?" Ta tambayi kanta sanda zuciyarta ta soma mata wasi wasi. Daga ita har sultana
ba wanda yayi ordering wani abu daga waje,hasalima sun gama siyan komai na birthday din
yaran,goumar baya nan bare tace shine, after all shi daya yake wannan gift din ma yaran,tun sanda ma
yake mutumin boye.

"Indai kuwa shine tabbas d'ana ya cika sadauki......ya kuma cika namiji sannan ya nuna mazantaka daya
lalubo family dinsa da kansa" ta furta qasan ranta murmushi yana qwace mata a sirrance,don tana da
yaqinin bai samu goumar ba kwata kwata ko a waya ballantana tace shine ya bashi haske.

Dukka idanun yaran yana kan kwalin saboda ganin masoyiyarsu wato kayan zaqi

"Ama namu ne?" Benazeer ta tambayi ama. Rasa amsar da zata basu tayi,batason tayi wata magana da
zata razana sultana ko ta sanyata dasa zargi a ranta kamar yadda zargin ya dasu a nata ruhin
"Naku ne,ku diba kadan ku sanya raguwar a fridge karku sha ya muku yawa" cikin murna suka amsa din
suka baje suna zaba. Ama na zaune tana binsu da kallo tare da hasaso ta ina maina zai bullo indai shine?.
Yayin da sultana ma sam bata kawo komai cikin ranta ba,saboda tayi imani dari bisa darin cewa bai isa ya
cimmata ba. Tattare kayan kitson ta farayi,don tanason ta shiga daki ta qarasa abubuwan dake gabanta
ta kwanta da wuri,don tanason fita aiki da cikakken energy da kuma nutsuwa.

"Nikam na gaji,tunda kun samu abunyi sai da safenku"

"Goodnight mommy" suka amsa mata a kusan tare ba damuwa tunda sun samu abun maqulashe.

Da baya da baya ya koma ya zauna a hankali yana furta

"Alhamdulillah" murmushi ya qwace masa saman fuskarsa,dukkansu yayi missing dinsu,yayi kewarsu
kaman hauka,shi kadai kuma yasan me yakeji. Agogo ya kalla,dare ya fara yi,amma kuma yana da
muradi,yanason ya isketa a wannan daren,idan da hali idan kuma zai yiwu,yana sha'awar raba dare da
ita,ya kamata a karon farko ya bata wani lesson me wuyar mantawa,ya bata wani babban karatu da
kowanne motsinta zai dinga tuna mata

"She's belong to him"

Hannunsa ya damqe qam qam guri guda tsigar jikinsa na zubawa saboda tunawa da yayi da
komai nata,lallausar fatarta me qamshin nan,lips dinta dake da wani irin sulbi da sanyi,sassalkar sumarta
dake da wani irin sulbi,uwa uba dumin jikinta dake da wani irin tasiri cikin qasusuwansa tun tana
mitsitsiyarta.

Sake duba lokaci yayi,sai ya miqe a nutse yana komawa bakin window din,zuwa yanzu babu
haske kwata kwata da yake iya hangowa,tabbacin sun wuce zuwa ga kwanciya,uwa uba qarin mota guda
daya daya gani ya bashi tabbaci aba ya riga da ya dawo.
Juyawa yayi cikin nishadi ya wuce bedroom dinsa. Wayoyinsa ya kashe dukka gaba daya,ya
jawo drawer din madubin ya zubasu,sannan ya soma zare kayan jikinsa ya wuce zuwa toilet ya hada
ruwa me yawa da dumi. Kwanciya sosai yayi cikin bathtub,yana shirya komai cikin kwanyarsa,dole yau ta
tsaya ta fuskancesa ko kuma yayi forcing nataa ta fuskanceshi ta dolen dole.....zabi ne guda biyu.
✌🏽

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank
_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/3, 11:10 PM] +234 906 707 5191: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 83

Sai data dan sake bata lokaci gefen gado tana duba aikinta na yau,tare da dan qaramin research
kan program dinta na wani satin da zata fara practicing dinsa tun daga gobe. Ta kusa awa daya sannan ta
kashe system din ta mayar ta ajjiye,ta miqe tana miqa saboda gajiyar dake bin sassan jikinta. Tunda ta
tashi yau din bata huta ba,yawan mutanen da yau tayi magana dasu da murmushinta a yau ya zarta na
kullum. Mutane ne su masu son mutumin da yake da talent,wannan ya sanya suka yita zuwa ganinta
tare da yabawa program din a iya yau kawai,dole kuma ta sakarwa kusan kowa a fuska kaman yadda
ama tayi mata fadan haka sosai.

Kayan jikinta dukka ta zare ta daura babban towel,ta bude jakarta ta ciro sabbin bath set dinta
daya hada da shower gel bath mist da sauransu,ta zare ribbon dinta ta azashi saman madubi,ta dauki
qaramin towel ta dora saman kanta don tasan wankan tsarki zatayi,don kafin ta fita dinner ta duba taga
al'adarta ya dauke. Ta zura slippers dinta na wanka ta wuce toilet bayan ta daidaita sanyin dakin.

Tun tana wankan takejin idanunta suna mata nauyi kaman zasu rufe saboda bacci da kuma
gajiya,wata irin kasala takeji tana bin duka sassan jikinta,wannan ya sanya ta jima sosai a toilet din fiye
da yadda ta saba dadewa.

A hankali ya tura qofar dakin ya shigo,sanye yake da wasu fararen hoodie pyjamas masu
matuqar taushi da sulbi,ya dora hulan saman kanshi amma hakan bai hana bayyanuwar sumar nan tashi
me tsaho sulbi da kuma baqi ba. Duk da kayan farare ne amma yayi wani irin sassanyan kyau,fuskarshi
tayi fes tayi tarwai kaman an qara masa hasken fata ne. Hannayensa duka biyun zube a aljihun wandon
pyjamas din nasa,yana qarewa dakin kallo a nutse. Hankali kwance kuma yake shaqar daddadan
qamshin da dakin yake fesarwa,qamshin wani irin freshener ne da ya cakuda da qamshin sassanyan
turaren nan nata da yake mutuwar so.

A nutse yaci gaba da nazarin dakin,daga qarshe idanunsa ya sauka saman gadonta dake dame a
gyare abun sha'awa game kallo. Saman gadon nata ta yasar da fari qal din under skirt dinta hade da
brazier dinta data zare. Cike da nutsuwar nan tamkar ba kutse yayi cikin gidan jama'a ba tare da saninsu
ko izininsu ba ya soma takawa zuwa gefan gadon. Dab da kayan ya zauna,ya miqa hannunsa ya dagasu
yana kallo. Qamshi suie fitarwa tamkar bata sanyasu ta fita zirga zirga dasu ba,ya lumshe idanunsa yana
jin wani abu yana fara sauka masa yarr a jikinsa. Hannu ya miqa,ya dauki remote dake controlling dukka
qwayayen dakin ya kashesu,sai guda daya daya bari wanda yake daura da mirror dinta.

Gaba daya qamshinta ya gama kashe masa jiki,a hankali ya koma da baya yayi relaxing saman
pillow din dake ajiiye fuskan gadon,ya daga undies din a hankali ya aza saman fuskarsa yana shaqar
qamshin dake fita a jiki.
Dadewar da tayi ya sanyata fitowa a dan gaggauce,kanta daure da towel din tana yamutsa
sumarta da takeso ta ragewa danshi saboda batajin zata iya tsaiwar sanya drayer ta busar dashi.

Dan qara kadan da qofar toilet din ta bayar ya sakashi juya kanshi sashen bandakin. Da dan
sauri sauri taja qofar,tana takowa zuwa tsakiyar dakin. Jajaye lips dinta ke motsawa a nutse,da alama
akwai abinda take karantawa. Lumshe idonsa yayi yana jin wani nauyi na raguwa a qirjinsa,gudun
zuciyarsa kuma yana sake qaruwa. Cikin kallo me kama dana qurilla ya soma sauke qwayoyin idanunsa
daga saman lips dinta zuwa fararen kafadunta masu sulbi da suka kasa riqe ruwan da tayi wankan dashi
saboda santsin fatarta.

Sarqafewa idanunsa sukayi a saman qirjinta data daureshi da towel,wanda sosai tudu da
tsaiwarsu kyam ta nuna ta saman towel din. Yadda yaji yana neman fara kokawa da numfashinsa ya
sanyashi qarawa kallonsa gaba,yanason ya more kallonta da kyau kafin lokacin da zata Ankara da
wanzuwarsa a dakin.

Santala santalan cinyoyinta suka sanya tsigar jikinsa zubawa,suka kuma tuna masa da wani
dadadden yanayi da ya kasa manta irin duniyar da ya tsinci kansa a ciki,dole ya miqe ya zauna,sannan ya
tattara dukka qarfinsa ya tashi ya soma takawa zuwa inda take tsaye.

Ko kusa ko alama jikinta bai bata da mutum cikin dakin ba,tunda tasan qasa ce dake da doka da
qa'idar da ba wanda ya isa ya haure maka gida,uwa uba kuma ta sani hatta su benazeer basu shigo mata
daki sai sunyi knocking bare ama da bama shigowar takeyi ba idan ba kamawa tayi ba.

Abu daya hancinta ya iya fahimta,kamar atmosphere na dakin ya sauya,da kadan da kadan taji
kaman qamshin sake mamaye dakin yake,sai taja qaramin tsaki. Batasan me yasa hancinta ke yawan
saurin tantance qamshinsa ba,batasan me yasa hancinta yake gane kowanne qamshi nasa ba,ta tsani
wannan saurin gane duk wani qamshi na jikinsa,sai ta miqa hannu ta dauki comb ta zame towel din
saman kanta ta zummar fara taje sumarta don ta samu tasha iska da wuri.

Comb din taji an riqe kafin kuma ya kama qugunta yadda ya saba ya manne da jikinsa.
Muguwar razana tayi wadda kadan ya rage ta fadi banda ya tallafota da hanzari
"Ya salam.......take it easy mana......bakiyi zaton zuwa na bane?" Ya furta mata cikin kunnenta da wani
sound da ya sanya ta kusa loosing control nata. Idanunta kawai ta mayar ta lumshe tana kiran sunayen
Allah tare da qoqarin daidaita bugun zuciyarta,don kowacce laka ta jikinta tsoratar da tayi yabi ya
kassarashi,taja numfashi da kyau sannan ta tattara dukka sauran qarfinta ta turashi. Abun takaicin ko
gezau baiyi ba,sai hannuwan nata ma daya riqe da kyau yana dubanta. Fuskarsa a nutse tsaf yake
dubanta

"Cool down......ba fada nazo nayi muyi ba......duk da kinyimin laifin da ki wajen Allah idan baki nema
afuwata ba sai Allah ya qonaki" ya fadi a tausashe,qamshin man data wanke kanta zuwa qamshin da
jikinta ke fiddawa yana son fara rarraba masa hankali.

Maganar tashi taji ta mata nauyi qwarai,wani abu me zafi ya tsaya mata a wuya,tanason ta fesar
masa da maganganu ne to amma tana jinta a tozarce da yadda take tsaye haka a gabansa daga ita sai
towel,duk wani sashe na jikinta yana nuna kansa.

"Ka sakeni" ta fadi idanunta a lumshe da tsiwa cikin muryarta

"I said calm down.......ki zauna ki fahimceni"

"Bazan fahimceka ba,ta hauro mana gida ka.ketomin daki,ka tsaidani a gabanka kana qarema tsiraicina
kallo?,kana tunanin idan nayi qararka akan hakan ba za'a karba min haqqina ba?"

"Tsiraici?......haqqi?......,for sure kin manta waye ni cikin dictionary din kanki?"

"Who are you?" Ta furta tana ware masa fararen idanunta.

"You asked in the right place" abinda kunnuwanta suka jiye mata kenan,abu na gaba data iya ji shine
damqar towel dinta da soma warwareshi tsaf daga jikinta.
Iya gigicewa ta riga ta yishi,tayi imanin muddin ya cimma muradinsa na rabata da dan towel din
da shine kawai garkuwar da ya mata katanga daga bayyanar jikinta ta kade,ta tattara dukka qarfinta cikin
tashin hankali tana fadin

"Stop it....." Baiko nuna kumnuwansa suna ji ba bare ta sanya ran ya fahimta,gigicewarta ya hanata
fahimtar hakan,bakinta ya gaza kama kowacce kalma sai fadin

"Stop it"

"Stop it" data dinga maimaitawa,wanda duk fitar kalma guda daya daga bakinta kamar yana daidai da
warwarewar towel din jikinta nata. Hawa daya tak ya rage masa ya kammala zareshi,bakinta na rawa ta
sake maimaita masa kalmar cikin furucin da take sanya ran shine na qarshe da wata raunanniyar murya

"Stop it......pleeeeassseee" kalmar qarshe din sai ta zamana kamar wata gaba ta karya lago a wajensa,ya
dakata cak yana maida numfashi. Baya jin a yau zai iya barin sultanar.......baya tunanin zai iya qyaleta ko
ya daga mata qafa,kowanne sashe na jikinsa muradinta yakeyi,hakanan yana son ya tuna mata wani abu
data manta,yanason yabar mata abinda zata dinga jin kanta ko yaushe a MATAR AURE ce ita din kaman
kowacce mace.

Ragowar towel din da kowanne ya riqe a hannunsa yana son hana dan uwansa cikar burinsa ya
jawo da wani irin zafin nama,sai gata gaba daya cikin jikinsa,sauran abinda kuma ya rage na towel din ya
zame yayi nasa waje,abinda ya haukata kwanyar maina cikin qasa da second biyu,ya kuma gigita sultana
gaba daya data fahimci garkuwarta ya fadi,ba wani sauran abu da ya rage da zata rufe tsiraicinta
dashi,sai kawai ta dunqule cikin jikinsa kuka yana qwace mata. Dunqulewar da tayi a jikin nasa da
zummar samun kariya sai ya zamana kamar turi tayi masa,tamkar fami ne ta yiwa wani tsohon miki
kamar kuma susa ce ta yiwa kowanne gaba ta jikinsa,ragowar nutsuwar da tayi saura a jikinsa ta soma
sulalewa,ya soma gagara kama hankalinsa........

_tom......qaqa qara qaqa_

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*
*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*
09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/3, 11:10 PM] +234 906 707 5191: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 84

Kyakkyawan tarba yayi mata cikin faffadan qirjinsa,ya lullubeta tsaf irin lullubar da inda
zuciyarta a sake take zata jita cikin aminci ne da nutsuwa tamkar kwanciyar d'a cikin mahaifiyarsa. Cusa
kansa yayi tsakanin fuskarta da kafadunta

"Calmez vous s'il vous plait(ina roqonki ki nutsu)" ya furta mata cikin taushi dason bata
nutsuwa,maimakon nutsuwa sai maganar tasa ta qarasa hautsinata,don yana sauke mata hucin
numfashinsa da tasirin muryar nan tasa da tun ba yau ba suke daya daga cikin abinda ke sanya mata
tsananin shakkarsa. Yadda yaga taba sake curewar jikinta ko ina yana rawa ya bashi tabbacin ta tsorata
ne,yana buqatar nutsuwarta fiye da kowanne lokaci,bayason ya maimaita abinda zataji ya qarasa fice
mata a rai,baya son taci gaba da kallon mu'amalar aure a wani abu me kama da horo azaba ko wahala
cikin rayuwar diya mace,he needs to show her me ainihin mu'amalar ke nufi,yanason shi da kansa ya
tabbatar mata isn't a rape.......ba abinda take tunani bane.
Tayi imanin zamanta cikin jikinsa a irin wannan yanayin kuskure ne babba,amma bata da wani
sauran mafaka daya wuce wannan,zuciyarta ta gaya mata ta gwada masa barazans ko zai
qyaleta,muryarta na shacking sosai kaman wadda sanyi ya kada tace

"laisse-moi(ka rabu dani),ama da aba dukka suna kusa.......ihu daya zai kawos......su dakin.....na,ka sani
ai" ta fada da qarfi tana daga murya wai ko zaiji abun ya tabashi ya barta.

Siririn murmushi ya saki a galabaice,sai ya sauketa saman sofa bed,ya sanya hannunsa yana
qoqarin banbare hannunta data cukuikuyeshi dashi. Sam taqi sakin nasa,saboda ta fuskanci janyewa
zaiyi daga gareta alhalin bai bata wani abu da zata maye gurbin jikinta dashi ba. Tsaiwa yayi cak yana
murmushi

"Ahaaannn......kince na fita na tafi,but kuma kin riqeni......idan kuma nace zanyi abun kice nayi raping
dinki.......cela montre qu'il y a quelque chose que tu veux(yana nuna cewa akwai abinda kikeso)"ya
qarasa fadi da harshen faransanci

"You missed me the way I missed you" ya sake fada da muryarsa na sake qanqancewa,yana jin kamar
tana fita ne daga maqoshinsa da qyar saboda yadda jijiyoyin jininsa ke sake budewa,suna kuma aika jinin
da sauri da sauri zuwa ga kowanne sashe na jikinsa.

"Nooo....." Ta furta da muryar kuka. Kai ya girgiza mata shima alamar a'ah,cikin wani irin taushi ya zame
jikinsa don yana da buqatar ganin abinda take boye masan gani na zahiri.

Tunda yake idanunsa basu taba ganin wani abu daya fusgi dukkan hankali tunani da nutsuwarsa
ba irin jikin sultanar,komai ya bayyana muraran,wani irin tashin hankali ya sauko mata ta fara qoqarin
samun wajen buya tsakanin pillows da duvet. Da wani irin zafin nama ya cimmata a tausashe ya
riqota,ya dagata gaba daya ya sauketa cikin jikinsa yana qoqarin cusa hannunsa tsakanin wuyanta zuwa
qirjinta.

"Nooooo pleeeeassseee" ta sake fada da sheshsheqar kuka,saboda iya riqon da yayi mata kawai ya soma
gaya mata lallai abinda ya faru shekara biyar zuwa shida baya ne yake shirin maimaita kansa.
Dukka haqurinsa yaji yana sulalewa,rashin haqurin nan nasa na asalin halittarsa ya fara taso
masa yana tasiri wa ruhinsa,yadda take kame jikinta guri daya da kyau tana dukkan qoqarinta na ganin
ta hana hannuwansa isa inda yake da muradi...... ta hanashi yakai gurbin da suka fi ko ina tsone masa
idanu......ba haka ya sansu ba.....ko a wancan lokacin da komai ya faru cikin fushi zafin rai da fitar hayyaci
amma kuma yana iya tunasu......ba haka suke ba,yaushe suka koma haka?,sun maida kansu yadda yake
gani cikin mafarkinsa,sun koma yadda yake buri da muradi,burinsa a kansu masu yawa ne,yana cikin
jerin mazan da suke da haushin wannan wajen,suke kuma da tanadi me yawa a kansu,tsananin kamun
mai da zallar miskilancinsa ya sanya kosu suhail da sukan taba zantuka irin wannan bai taba sanya musu
baki ba,basu kuma taba sanin kowanne plan nasa akan kalar matar aurensa ba.

Juyeta yayi kawai saman tattausar katifar,ya kuma yi mata wata da faffadan qirjinsa cikin salon
da bazai hanashi kallon fuskarta da qwayoyin idanunta da suka qara sheqi saboda ruwan hawayen dake
kwance a ciki.

Da gaske ihu takeso tayi masa amma sai takejin kamar an kame harshenta an riqe,a wannan
yanayin idan tayi masa ihu ama ko aba suka kawo mata daukin da take da buqata da wanne idanu zata
kallesu a gobe?. Fuskarta ya kawo cikin tafin hannunsa,ta sanya hannunta da ture hannun tana kauda
fuskartata,cikin zafin nama ya kama hannuwan nata ya aza musu nauyinsa,sai ya zamana bata da wani
sauran abu da zata kare kanta dashi,shi kuma yi ya bash damar zube hannuwansa a inda yaketa harin.
Abinda ya sanya ya qarasa birkicewa gaba daya,muryarsa ta sarqe gaba daya,sultana kuma ta sake masa
kuka na gasken gaske,tana jin wani abu yana yawo cikin sassan jikinta.

Har tsakiyar kansa ya dinga jin saukar sautin kukanta,sautin daya dinga so ya tuna masa da
abinda ya faru five yrs back,cikin birkitacciyar muryarsa data qanqance kamar wanda mura ta yiwa kamu
ya fara magana,yana yi yana jan numfashinsa da kyau don yana jin kaman zai qwace masa ne.

"s'il te plaît(please)Sultan give me a chance....no more aba,no more ama..... Aliyyu haidar kawai.....ki
fahimceshi......ki bashi zuciyarki da tunaninki......all this while sultana zuciyata bata taba samun hutu
ba,ban taba hutawa ba sultana......ban taba kwanciya nayi bacci cikin nutsuwa ba dukka shekarun nan
saikin hanamin sukuni cikin bacci na......ban taba samun cikakken nutsuwar ruhi ba dukka shekarun
nan......,pleeeeassseee sultana,ki yafemin......dukka laifin da kike tuhuma na dashi na yarda na
dauka......zan gyara kuma.....ki bani Chance mu gina gobenmu......ki bani Chance na koya miki
soyayyata,ki bani chance na inganta rayuwarmu data 'ya'yanmu"
"Bana sonka.......bana......i hate you...." Ta fada cikin gunjin kuka sanda ya mata wata wawiyar runguma
tamkar zai tsagata gida biyu.

"You are a liar.......idanma da gaske kike daga yau zan koya miki yadda zaki fara sona" daga wannan bai
sake bata daman magana ba,ya toshe labbanta da harshenta da nasa bakin da wani irin salon
kiss.....wani irin tsotsa yakema lips nata da harshenta,sai daya tabbatar ta galabaita ta kuma haqura da
yunqurin magana da takeyi,duk wani cizo da take kai masa da haqorinta ya shanye,bai qyaleta ba sai
daya zuqe duk wani yawan bakinta tas,ya tabbatar numfashin dake kai kawo a qirjinta ya soma sauyawa
sannan ya gangaro zuwa wuyanta.

Wani irin zazzafan numfashi ya dinga sauke mata yana sansana wuyan kamar zai
hadiyeta,saqonnin da yake sakar mata a iya wuyan kadai suka fara qoqarin rikita mata lissafi,ta bude
baki zatayi magana amma numfashinta rawa yakeyi yana kai kawo tsakanin qirjinta da zuwa
maqogaronta,koda zatayi maganar ma ta tabbatar ba wani sauti me kyau da zata bayar.

Ita ce macen farko kaf rayuwarsa da ya fara sani a matsayin diya mace......amma kuma yana da
sani me yawa akan mata.......duk wani sani nasa daya tara tashin shekaru saboda ita a ranar ya bude
mata su babi babi,zafafan saqonni dake tafi da imanin me imani,ya kuma sauke dukka zafin kai da na
zuciyar kowacce irin diya mace......izza taqama da kuma qasaitarta. Tun tana qoqarin qaryata abinda
gabbanta keji har ta fara tsoron maina din......ya hanata kowanne motsi,zafafan 'yan aike kawai yake
tura mata da suka sanya kwanyarta ta fara zafi,hannunsa zuwa harshensa kawai takeji suna yawo all
over her body.......bai qyaleta ba sai daya tabbatar kowacce gaba a jikinta ya aje mata saqo me dumi da
gigita tunani......a sanda kunnuwanta suka soma dodewa ta daina fahimtar kowanne sauti daidai,sanda
gangar jikinta tayi nisan nisa cikin wata duniya daban da maina ya aikata......lokacin da ta soma tunanin
dama tana da irin wannan feeings din cikin jikinta?,wanne irin shaidani ne mainan har haka da yakeson
fiddata daga saitin hankali zuwa wani layi da yafi kama da mutumin da yasha wani abun bugarwa ya
bugu?,sanda tayi nisa wajen tunanin ta yaya zata dakatar dashi......a lokacin ta jishi yana yunqurin kaita
azababbiyar duniyar daya taba kaita tsahon shekaru biyar da suka shude......duniyar data aje ma
rayuwarta tarihi.....duniyar da ko sau daya bata taba gushewa ko ta subucewa tunaninta ba. Daidai
lokacin hankalinta yayi mummunan tashi,ta kuma yi azamar dawowa daga inda ya kaita din,cikin
galabaitacciyar muryar da ko maqoshinta bata kaiwa ta soma magana kai kace magen data sha wahala a
hannun yara

"Don Allah.......kayi haquri...... please Allah bazan sake komai ba....suis désolé pleeeeassseee" ta qarashe
maganar tana jan wani dogon numfashi sanda ya cimma gaci.
Daga shi har ita ba wanda zai iya tantance meye ya biyo baya,kimanin wasu mintuna ta sake
dawowa hayyacinta karo na biyu,ta fara sauka daga layin amasar saqonninsa,ta soma hawa wancan layin
da take tsoro. Zuwa lokacin bashi da katabus din kansa bare nata,tuni ya sake mata hannayenta,wanda
dasu tayi amfani ta tattarasu saman qirjinsa tana turashi

"Leave me......i beg you.....don Allah" ta kuma fadi hawaye karo na biyu suka soma cika mata idanu. Me
yasa tayi gangancin qyaleshi har yakai ga wajen? Taji wata tuhuma daga can qasan zuciyarta.

"Don Allah ya maina...." Ta sake fada tana sakin kuka. Yana iya jiyo muryarta sama sama cikin
kansa,amma kuma qwaqwalwarsa bata aikin da zata rarrabe me take fada. Sake qanqameta yayi da kyau
muryarsa na rarrabewa kamar zai shide mata

"Don Allah sultana......." Shima ya fadi yana sake qanqameta kamar za'a rabashi da ita,tamkar zata
bacewa ganinsa.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800
UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/6, 7:46 AM] +234 810 626 2369: *_GUDUN ƘADDARA_*


*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 85

Abinda bata lura ba duk sanda sautin muryarta ya fita sai ya zamana kaman qara masa qaimi
takeyi,abun ya soma bata tsoro saboda ta fara karbar gashi yadda ya kamata,zuciyarta ta cika da
fargaba,ta tuna yadda ta qwaci rayuwarta da qyar a wancan lokacin,sai ta saki kuka da gasken
gaske,yayin da ya sake tattarata zuwa jikinsa sosai muryarsa na sake yin rawa kamar wanda aka yiwa
wanka da ruwan qanqara yana fusgar kalmar

"Am sorry.......am sorry please help me......" Idanunta ta maida ta kulle gam tanayin surrender,ta sani
yau ma Allah ne kadai macecinta. Dakatawarta daga dukkan wani yunquri ya sake bashi nutsuwa qwarai
da gaske,ya kuma zame masa tamkar wani taimako a gareshi da zai isa wata duniya me matuqar tarihi
cikin rayuwarsa.

Ji tayi kamar zata amayar da 'yan hanjinta lokacin da ya sake rungumeta tamkar zai ballata gida
biyu

"Wayyo Allah" ta fada murya a karye hawaye masu dumi suna sauko mata. Har cikin jikinta taji zafin
yadda ya matsetan. Da sauri ya sassauta riqon,ya kuma daga fuskarsa da ta sauya launi,zagayayyun lion
eyes dinsa sun wani jirkice,jirkicewar da bazata iya kallonsu ba,saita maida qwayar idanunta ta lumshe.
Hannunsa ya Sanya da sauri saman idanun nata,gumin daya jiqe masa fuska yana diga saman fatarta

"Please open your eyes.......ban ji miki ciwo ba ko?" Ya fadi a dan rude yana tsoron maimaituwar wancan
tsautsayin.

Wani nauyi takeji a zuciyarta,kunya haushi da takaici dukka sun cikata,wannan ya qara yawan
ruwan hawayen dake bulbula ta qasan idanunta. Sosai ya rude,da sauri kuma ya rage mata nauyinsa
daya aza mata dukka. Fuskarta ya dago da kyau yana duban fuskarta da take fes tarwai,babu komai sai
digon guminsa da nata da suka gauraya waje daya. Ko a haka da idanunta ke a rufe yana iya hangen
zallar kyan da suke dashi
"Sultana" ya kirata da wani sauti me matuqar sanyi da sanin yadda ake furta ainihin sunan

"Please open your eyes.. kalleni sultana"

"Idan ka gama zaka iya wucewa" abinda tace dashi kenan cikin muryar kuka. Wani abu ya hadiye,sannan
kuma yayi qoqarin daidaita kanshi

"Ban gama ba.......and bazan gama ba muddin ni dake muna raye......ki soni ki koyi haquri dani,wannan
shine shawaran da zan baki" daga hakan bai tsaya saurararta ba ya yunqura ya miqe cikin mazantaka duk
da yadda jikinsa yake a mugun mace. Cak taji yayi sama da ita,abinda ya tilastata bude idanun nata
kenan tana kallonsa

"Ka saukeni......"

"Shshshs" yace da ita yana hade fuskarsa,irin hade ran nan da ya zama jinin jikinsa,tamkar ba shine a
yanzun ya gama rawar jiki da roqon ganin qwayoyin idanun nata ba

"Kada kice zaki fiya sa'insa dani......idan kika daga murya da yawa ma akaji aka shigo ba raping naki nayi
dis time ba.......dan aike na aika kika kuma karbeshi hannu bibbiyu" . Wayyo ina rami ta shiga ta
huta?,ina wuta kuma ta cilla maina?,wanne sauka tayi daga layi har zai fara goranta mata?,tabbas ya
gama da ita,batasan kuma me zatayi masa ta huce ba,kawai sai ta saki kuka sosai harda shashsheqa.

Ko ta kanta baibi ba sai daya tabbatar ya sanyata cikin bathtub dake cike da ruwa me dumin
gaske. Sai ya juya ya fara zare ragowar abinda yayi saura a jikinsa. Ta matuqar kaduwa da ganin zai
qarasa bayyana mata abinda bata iya buda idanu ta kalla ba,ta qame gaba daya cikin bathtub din
zuciyarta na mugun harbawa. Ya juyo yaga kuma yadda tayi, silently ya saki murmushi,shima baiyi niyyar
shiga ba,sai ya wuce Jacuzzi abinsa ya kunna shower ba tare da yace da ita komai ba.

Tsaf yayi wankansa ya gama,duk wani motsinsa idanunshi a kanta,a tsorace take da gasken
gaske,don tunda ta rufe idanunta bata bude ba. Ya jima ruwan yana sauka a kansa yana morewa kallon
fuskarta da tayi jazur saboda kuka,wani irin yanayi yakeji cikin gangar jikinsa da zuciyarsa,duk yadda ya
hasaso zai samu pleasure abun ya wuce nan,yana mamakin kansa qwarai idan ya tuna wai baby
sultanarshi ce ta tsaye ma rayuwarsa?,ita din wadda ya raina da hannunsa ce ke son juya akalar
zuciyarsa dama rayuwarsa gaba daya?.

Da babban towel ya daure qugunsa,ya qaraso inda tayi mutuwar zaune,ba zato ba tsammani ta
jishi cikin ruwan yana tsiyaye na ciki yana kuma tara wani,saita sake hade jikinta tana kuma sakar masa
kuka

"Ka fita ka bani waje......Allah zankai qararka.....zankai qararka wajen Allah" idanu ya zaro yana kallonta

"Da nayi miki me?,don kawai na taimakeki na miki abinda kikeso?,karki manta kema fa kindan san dadin
abun......ko kin manta shi ya sakaki suma" ji tayi kaman ta hadiyi zuciya ta huta,maina ya gama kasheta
yau gaba daya bata da sauran abinda xata masa a yanzu dai ta huce. Zata masa gardama ya fidda mata
idanunsa yayi warning nata

"Duk taurin kai ko musu guda daya yana dai dai da na sake raping naki ne cikin toilet dinnan tunda sunan
rape kika bawa abun ko?,wanka kuma ai ba yau na fara yi miki shi ba" Yadda yake mata maganar kai
tsaye ya saka shakkarsa cikin ranta,tanaji tana gani ya wanketa tas kamar wata baby doll,ya kuma
daukota zuwa bedroom ya laluba Wardrobe dinta ya fidda kayan bacci ya saka mata.

Kwanciya ya sanyata yi ta dole,don ba zata iya zama taci gaba da kallonsa ba,hawaye kam yaqi
barin fuskarta,gashi dukka gabbanta ciwo sukeyi mata,ita kuwa me ta yima yaa haidar haka kaf cikin
zuri'arsu yafi sanya ma rayuwarta idanu?.

Tana jinsa ya koma toilet din,yayi alwala ya dawo ya shimfida abun sallarta,ya sake matsawa
gaban madubinta ya dauki tutarenta ya fesa,sannan ya kabbara salla abinsa cikin nutsuwa.

Raka'a biyu rak yayi,amma kuma ta kusa daukansa mini talatin kafin ya kammalata zuwa
addu'o'i,ya shafa ya miqe yana dubanta. Tana nannade cikin duvet tana jin zuciyarta kaman zata
fashe,daga pillow din har duvet din qamshinsa suke fiddawa,zataso ta miqe ta sauya daki ma gaba daya
ba pillow case da duvet ba,to amma da wanne ido zata miqe su kalli juna?,yau din ya ganta haihuwar
mahaifiyarta?,ya ganta ganin da rabon da yayi mata irinsa tun kafin takai munzali.
A tausashe yake takowa gareta,yaso qwarai ta fahimceshi ya bata first night dinta me dadi a
wannan ranar,saidai ya gama fahimtar da gaske har yanzu sultana zuma ce sai da wuta,jan ido yafi
sanyata tayi laushi wasu lokutan.

Saman kanta ya tsaya,ya miqa tattausan tafin hannunsa saman sumarta,ya sunkuya ya bata
wani hot kiss a wuyanta da goshinta,muryarsa da wani irin sanyi yace

"merci pour cette belle nuit(na gode wannan dare)" ido ta lumshe sauran hawayen dake maqale suka
zubo mata. Ba dole yayi mata godiya ba?,ya gama tozartata har cikin dakin baccinta?,tsakanin ama da
aba da yaranta

"Ki rage wannan kukan kada da safe mutanen gidan su fahimci abinda ya faru,thought dai zanso su
fahimta din,may be su gane cewa kin balaga sosai,kina buqatar namiji kusa dake......and bafa raping naki
nayi ba in jaddada miki.....nasan bakisan bada kanki kikayi ba" ya fadi yana danne dariyar dake qasan
ranshi,don yasan wannan kalmar kadai zata tabata,yana kuma kaiwa qarshe ya juya yana furta

"Have a sweet sleep" ya maida qofar a nutse ya rufe mata.

Kanta ta cusa cikin pillow tana sake sakin wani tsumammen kukan.

"Wayyo Allah na" ta furta can qasa tana jin qamshinsa tako ina,hakanan kowanne sashe da hannunsa
yakai a jikinta tana jin tamkar yanzu ne komai yake faruwa,ya akayi ya shigo gidan?,shine babbar
tambayar data dinga yiwa kanta. Ta jima tana sharar hawaye,sai data tabbatar bazai maganta mata da
komai ba sannan ta miqe tana cije labba saboda yadda jikinta ke dada ciwo.

Toilet ta koma ta zare kayan jikin nata ta musanya da wasu,ta dawo ta zare komai dake saman
gadon tabar katifar da pillow din ta koma ta kwanta tana kyautata zaton qamshinsa zai tafi,saidai kuma
babu wani abu daya canza. Daga qarshe saita sauke pillow din qasa ta koma can ta kwanta. A can dinma
dai duk ba wani sauyi da taji,saita miqe ta zauna kawai ta rushe da wani kukan.
Tayi kuka sosai har sai dataji ba dadi sannan ta haqura,a hankali bacci ya soma rinjayar
idanunta,tun tana sharar hawaye a sannu a sannu har bacci ya rinjayeta.

Yayi zaton zaya samu bacci yadda ya kamata,amma kuma sai ta sake tsaye masa rai duka
daren,duk wani juyi da zaiyi ita yake hangowa cikin idanunsa,irin pleasure din daya samu da wata irin
nutsuwa da bai taba samun kamarta ba daga gareta.

Knocking din ama ne ya sanyata bude idanunta da taji sun fara mata nauyi

"Anyi sallar asuba sultana banji motsinki ba" ama din ta fadi daga bakin qofar tana juyawa ba tare data
shiga dakin ba.

"Alhamdulillahil lazi ahyana ba'a da ma amatana wa ilaihin nushur" ta furta can qasa tana motsa
labbanta. Juyawa tayi hannun damanta,idanunta ya sauka kan wayarta,sai taga wayar tana haske,ta
miqa hannunta da yayi mata nauyi tana jawo wayar. Text ne daga number da bata santa ba,kaman zata
ajjiye sai kuma ta bude. Tun kafin ta qarasa karanta saqon ta fahimci daga ina ya fito

*_Stay at home_*

Maimaita saqon tayi har kusan sau biyu,to me yake nufi?,kada taje wajen aikinta?,kada taje wajen
aikinta sai yaushe?,yana son yace ta ajjiye aiki ne fakaice?.

"Tabdijan" ta fada qasa qasa,ta tattara dukka qarfinta ta miqe ta zauna sosai,ko zata lamunci komai
banda abinda ya shafi aikinta,cikar burinta?,burinta na shekara da shekaru?,burin data cimma cikin wani
irin yanayi da baisan ya akayi takai ba?,ba zata lamunta ba ko kusa ko alama,aikinta alfaharinta
ne.....cikar farincikinta kuma.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*
*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107
*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 86

Ko Ina a jikinta ciwo yake mata,zata kuma buqaci hutu a qa'ida,amma ko don ta nuna masa
iyakarshi sai ta fita aikin,ba zata zauna ba,don bataga meye alaqarsa da aikinta ba.

Sau uku tana attempting tashi amma ta kasa,an hudun ta miqe tana cije labba,dukka jikinta ya
mata tsami,ta soma takawa a hankali tana wucewa bandaki. Tana shiga idanunta ya sauka a inda ya
tsaya, Jacuzzi da bathtub din daya wanketa tsaf a ciki,idanun nata ta janye tana jan qaramin tsaki,haushi
ya cikata,wai me yasa ma bata tada masa ama da aba din ba?,tunda dai tasan duk tsiya idan ta tashesun
ita keda gaskiya,kunya kuma sai ya fita ji?.

Ruwa me mugun dumi ta hada ta shige bathtub din tana sake gasa jikinta da kyau,ta dade a ciki
har sai da taji dadin jikinta sannan ta fito.

Zaune kawai tayi gaban madubi daure da towel,batajin dadin yanayinta gaba daya,sake jan
qaramin tsaki tayi,shi ya jawo mata komai,me yasa dole saiya cusa rayuwarsa cikin nata?,bayan ita ba
damuwa tayi da lamuransa ba?. Agogon dake manne a bango dai dai saman mirror dinta ta kalla,mamaki
ya kamata saita dan fidda idanu,ta miqa hannu zata dauki cream dinta sai ama ta turo qofar.

A nutse tayi sallama,idanun ama din a kanta,amma saita samu kanta wannan safiyar da kasa
kallon fuskar ama din,ta kauda idonta tana dan sunkui da kanta qasa. Kallo daya aman tayi mata taga
sauyin yanayi a tattare da sultana din,mutuwar jiki da rashin kuzari,hakanan fuskarta ta dan tasa kadan
ta danyi jaa kuma

"Hala yau ba aiki sultana?" Kai ta girgiza

"Makara nayi ama"

"Yauwa nifa ince,koda asuba baki leqo ba,har su batoul sun wuce school" bata iya amsa mata ba sai
rusunawa da tayi ta gaidata,har yanzun dai taqi su hada idanu,gani take tana kallon ama din aman zata
fahimci abinda ya faru da ita daren jiyan.

"Lafiya Lau mun tashi lafiya?" Ta amsa mata tana shirin zama gefan gadon,sai kuma ta fasa tayi sak tana
kallon gadon yadda ya yamutse gaba daya,hatta da bedsheet din ba'a dai dai yake ba,pillows din dukka a
qasa. Abune da bata taba gani ba wajen sultana,saita kwanta a gado ta kuma tashi ka ganshi lafiya
Lau,don akwai tsafta,ba zaka taba ganin gadonta a yamutse ba,wanann ne ya sanya ko su benazeer bata
bari su hau mata gado musamman idan ta gyarashi.

"Lafiya....lau ama" ta amsa mata tana dan daburcewa saboda yadda ta fahimci idanunta na saman
gadon,gabanta yana dan faduwa,kada dai ta dago wani abu,Allah yasa ba wani abu saman gadon da zai
tona mata asiri,ta fadi cikin ranta da dan fargaba

"Lafiya kika kwana ko?" Ta tambayeta a fakaice don son tabbatar da ba wani abu ne ya sameta na lalura
ba

"Lafiya.....lafiya qalau ama" ta sake fadi tana sake kauda idanunta sosai daga kanta.
"To ma sha Allah,idan kin kammala ina parlor saiki fito kici wani abu kafin ki wuce ko?" Ta furta qasan
ranta tana kokwanto,sinqe sinqen da sultana keyi na meye?,saidai kuma tunda tace mata lafiya lau din ai
lafiyarce,don dama ita ke buya,don haka ta miqe ta fice daga dakin.

Dogon numfashi ta sauke kamar me laifin da ya kubuta daga hannun alqali,ta maida idanunta
saman gadon,ya yamutse qwarai,kuma dole ama taga abun wani iri,harda towel dinta na jiya daya zare
ya watsar,warin dan kunnenta da kuma pant dinta. Ta miqe a hankali ta isa gadon,ta sanya hannu ta
tattare bedsheet din,sai takeji ya fita a kanta,ta hada duka da pillow case din data cire jiya ta watsa a
laundry basket,ta duba wardrobe dinta ta ciro wani ta sauya.

A gurguje ta gyara dakin,abinda ya sanyata ta sake makara kenan,ta sake buda wardrobe
dinta ta fidda wasu English wear skirt and blouse na yadin chiffon me dan kauri ta shirya kanta tsaf,ta
yane kanta da madaidaicin scarf daya sake fidda kyawun fuskarta wadda a yau daya taga fuskartata
tadan ciko,tayi dam tsakiyar scarf din,har sai data sake duban kanta. Cikowar da fuskar tayi ya qara sawa
idanunta labbanta da hancinta dukka sun sake fitowa sunyi kyai,ta dauki turare ta fesa,sannan ta daura
agogon fata na kamfanin blancpain,da hand bag nata da takalminta dukka set ne daga kamfanin Hermes
da suka siya a nan French cikin shagonsu,gift ne kuma daga aba cikin siye siyen fara zuwa aikinta.

Wani mahaukacin sassanyan kyau tayi,wanda ko mai hassada idan ya kalleta bazaiyiwu ya
dauke idanunsa a kallon farko ba,ko makaho ya shafata yasan lallai komai na rayuwa ta hada,ba abinda
ya rage mata sai neman lahira. Dakin ta jawo ta rufeshi ba tare da ta saka key ba don bata sakawar.

A nutse take tafiya cikin yanayin kasala zuwa parlor din tana duba saqonnin data taras cikin
wayarta,duk inda ta gifta sai tayi ajiyar sassanyan qamshinta,a haka ta isa dining area saidai batakai ga
zama ba saboda bataga ama ba,tana a tsayen tana replying massages din wayarta aka danna qararrawa.

Ta daga kai tana duban qofar da zummar tambayar waye taga an turo qofar da alama ba'a
rufeta ba gaba daya.

Itace abu na farko da idanunsa ya fara kaiwa kanta,kamar yadda itama dashi ta fara tozali,
zagayayyun lion eyes nashin nan da taga sunyi wani irin haske a safiyar,kamar kuma an qara musu girma.
Sassanyan kyansa dake kwance saman ba'abzinar fuskar nan tasa dake wannan kwarjinin na tun
asali,tun duniya na kwance,gayun nan dai da duk wanda yasan aliyyu maina na kwance a yanxunma a
jikinsa,irin gayun dake nuna zallar wayewa kwanciyar hankali da kuma tarin ilimin da ya mallaka,ilimin da
ya qarawa fuskarsa kwarjini,ya kuma haifar da zallar nutsuwa cikin kowanne taku da kuma motsi nashi.
Suit din jikin nashi tamkar kamfanin sun qirqireta ne kawai saboda shi,idan ka kalleshi babu abinda zaya
hanaka rantsewa wani balarabe ne.

Sai da yaji kamar an harbi zuciyarsa da ganinta a tsaye,kyanta ya bugeshi sosai,ya kuma
motsa masa ainihin kishinsa da yaketa qoqarin dannewa a kanta. TAURIN KANTA da sauransa kenan har
yanxu?,bazai gaya mata taji ba?,sai ya gyada kai,shi daya yasan me ya shirya mata.

Sake maimaita sallamarsa yayi yana tsugunnawa a nutse yana sabule tsadajjen sau cikinsa daya
sakaya qafafunsa a ciki. Kafin ya dago yaji muryar ama tana amsawa,wanda sai data iso cikin falon sosai
sannan ta fahimci waye?.

Dagowa yayi suka hada idanu da ama, murmushi zai kubce mata ta danne,saita buge da fadin

"Kaine?" Nasa murmushin ya sake mata,wai ala dole sai tayi fushi itama da fushin wani?,banda abun
ama meye alaqar dake tsakanin dangantakarsa da ita da kuma dangantakar sultana dashi?. Duk da haka
sai ya dake shima,yana sake dauke idanunsa sosai daga sultana kaman baisan da tsaiwarta a wajen ba

"Nine ama......ko na koma?". Baki tadan tabe

"Banason sanabe,idan zaka qaraso ka qaraso,kaga abanka?" Kai ya girgiza duk kuwa da cewa yaga
wucewarsa,to amma yanzun bai shirya haduwa dashi ba,so yakeyi su hadu ranar da zai kasheshi da
mamaki

"No,bamu hadu ba"

"Yanzun nan ya fita" ta fada tana nufar dining. Qasan ranta sai takejin wani sanyi da dadi suna
ratsata,amma kuma bata bari hakan ya nuna a kan fuskarta ba.
Kanshi tsaye shima dining din ya nufa,don bazai bari yayi Missing abincin ama dinsa ba. Tana
qame a wajen har ya qaraso,ya jawo kujerar dake kusa da tata ya zauna yana fadin

"Barka da safiya ama,fatan kun tashi lafiya,ashe nan ne location naku"

"Lafiya alhamdulillah"

"Ya hanya?,bansan zaku taho ba ama......har yanzun baki dawo dani bane cikin 'ya'yanki?" Yayi maganar
cikin karyewar murya da nuna rauni. Batajin yanzunne right time da zasuyi irin wannan maganar
dashi,don haka ta bashi amsa a dunqule da cewa

"Kai kaso....in ka shirya cin abinci ne bismillah,tunda ka iskemu magana ya qare ai" murmushi ya saki,ya
fahimci inda tasa gaba,don haka baice komai ba ya miqa hannu yaja butar shayi

"Amma zan wuce" ta fadi tana jinta duk a takure. Mamakin qarfin halinsa takeyi,kaman ba shine ya
hauro musu gida daren jiya ba yazo ya muqurqusheta,amma yanzun don qarfin hali da qwarewa a rainin
wayo wai shine yake tambayar ashe nan ne location nasu?. Ita kanta yadda ya dubeta a gaban ama din
ba zaka dauka cewa ya taba ganinta ba,ya basar yayi zamansa

"Ban gane zaki wuce ba?, c'mon zauna kici abinci,haka akace miki ana zuwa aiki da empty stomach?" A
hankali ta matso tana jan next chair,ta haqura da wadda ta fara ja din saboda tayi kusa dashi sosai

"Ina kwana" ta furta a hankali kaman wadda batason yin magana sanda take shirin zama.

Sai daya daga kanshi suka hada idanu,ya faki idanun ama ta yadda ba zata ganshi ba ya sake
mata wani irin narkakken kallo yana lumshe idanunsa sannan yace

"Alhamdulillah" labbansa na wani irin motsawa. Ta fahimci ma'anar gaisuwar tasa,saita kau da kai taja
itama butar coffee din ta soma zubawa.
Sam kaman baisan da ita a wajen ba,dukka hankalinsa ya tattara yana jan ama da hira,tadan
soma dojewa daga baya tadan sake masa kadan. Yayi kaman ya manta da ita ne,amma duk wani spoon
ko mug da zatakai bakinta yana lissafe da adadin. Har yanzun tana nan da wannan halin na yiwa abinci
riqon sakainar kashi. Sanda ya fahimci dab take da qoshi sai ya fiddo wayarsa daga side pocket din jikin
rigarsa.

Saqo ya tura mata cikin hikima ta yadda ama ba zata fahimta ba,ya maida wayar ya ajjiye yana
ci gaba da duban ama cikin tsananin kulawa yadda ya saba mata.

Tayi zaton wani Tex ne me muhimmanci,wannan ya sanya ta jawo wayar ta buda

*_zanyi warning naki a karo na qarshe,muddin kikayi kuskuren fita aiki.......bazan gaya miki what's going
to happen ba.......but zaki gani a aikace_*. Maimaita saqon ta sakeyi tana satar kallonshi,abu nashi taga
alama yama wuce gona da iri,wai ana dole ne?,lallai sai ya maidota cikin rayuwarsa?,lallai sai ta maidashi
itama cikin rayuwarta?.

Tsaf ya karanci meke reading saman fuskarta,sai ya miqe a nutse

"Nayi mantuwa ina zuwa" yadan sauka daga wajen yana fita da 'yar sassarfa. Ajjiye pork din hannunta
tayi ama ta bita da kallo tana furta

"Ma sha Allah" qasan ranta,sai yanzun sultana ke zama cikakkiyar mace,shekarunta suke kaiwa dai dai
shekarun cikar 'ya mace,ita kanta tayi mata kyau sosai

"Na qoshi ama,zan tafi yau na makara sosai,akwai abubuwan da zan duba na program dinmu na next
week"

"Allah ya taimaka,saikin dawo" har ta fara barin wajen idanun aman yana kanta
"Ki kula da kanki sultana" ama din ta fadi. Sai taji maganan ya ratsata sosai,har sai daya waiwayo ta kalli
ama sannan a sanyaye tace

"In sha Allah" juyawan da zatayi ya shigo,bata yarda ta kalleshi ba ta sanya kai zuwa ba.

Lips dinsa ya cije yana sakin wani boyayyen siririn murmushi,yaro man kaza ya fadi a
ransa,hankalinsa kuma kwance yake dawowa wajen amansa,don sosai yakejin dadin hira da ita a
wannan safiyar,ta dan sake masa ba kaman yadda take masa a baya ba.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/6, 7:50 AM] +234 810 626 2369: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 87
A nutse ta bude motar ta ta shiga tana ajjiye hand bag dinta daga gefe,ta tattara hankalinta ta
sanya muqulli ta kunnata sannan ta tayar da ita ta soma barin unguwar a nutse.

Radio ta kunna don ta rage mata kewa,zantukan ama ke dawo mata da wasu tunanuka da suka
shafeshi keson kutso mata kai wanda bata da buqatarsu. Tana mamakin qarfin halinsa da yadda yake
abubuwan kanshi tsaye,duk da halinsa da dabi'unsa ba ta jima da saninsu,amma a yanzun yana shirin
zame mata sabon mutum. Yadda ya sake girma ya sake zama cikakken mutum haka take sake ganin
wasu sabbi da baqin halayya daga gareshi,koma meye dai oho,damuwarshi ne,ita ba wannan ne a
gabanta ba,gina kanta takeyi a yanzun,lokaci ne da shekarunta suke dai dai da sanda kowanne dan adam
ya kamata ya maida hankali ya gina gobensa,tanason ta sake yiwa rayuwarta ta baya nisan tazara sosai
fiye da tazarar da tayi mata a yanzu.

Daren jiyan ya fado mata a rai,tsaki taja,har yanzu haushi da baiken kanta take gani,tana ganin
kaman tayi sakaci da har haka ya faru da ita,abun ya maqale mata a rai,tana jin tayi abun kunya da har
tayi saken da ta sake hada jiki dashi,yadda akayi yaci galaba a kanta abune da bazata iya tunawa ba,ta
sanya yatsanta guda daya a baki tanason second guda daya daya bashi dama ya shawo kanta amma ta
kasa tunawa. Dan dukan steering din motar tayi tana tura baki gaba cikin alamun jin haushi tamkar yana
a gabanta.

Batayi wani nisa ba can danja ta tsaidasu,ta tsaya kaman yadda dokar qasar yake,tana yi tana
duba adadin mintunan da suka rage a basu daman wucewa. Tsaki ta kuma ja,duk shi yaja mata koma
meye,wannan lattin batasonshi,bataso ta fara aikinta da saba alqawari da kuma saba lokaci,tunda ta
sani,su din mutane ne masu girmama lokaci da kuma alqawari.

Gefan hannun damanta tadan kalla,har ta dauke kai tayi saurin maida dubanta wajen. Maina
ne,zaune cikin motarsa hankalinsa kwance,ya manne qwayar idanunsa da baqin eye glasses wanda suka
yiwa farar fatarsa mugun kyau. Kallo daya zaka masa kasan cool guy ne a ido,amma a idanun sultana can
qasan zuciyarta sai ta furta

"Wicked" sannan ta dannan madanni tana dage glass din side din,don bata qauna ko fatan ya ganta
ma,kowa tashi ta fishsheshi,hanyar jirgi daban ta mota daban. Ana sakinsu kuwa taja motarta tana dan
qara speed kadan akan na dazu duk kuwa da yadda take tsoron gudu a mota,koda kuwa driving nata
akeyi bare ace ita keyi da kanta.
A nutse take dan bin waqar da suka sanyo cikin gidan radio din da harshen faransanci,saita
waqar ta dinga tuna mata shekarun baya,sanda tana sultanar bibi,me bala'in son rawa da waqa,me bin
duk wani gida da ake shagali walau gida ko hotel. Waqar na daya daga cikin waqoqin da take mutuwar
so, murmushi ya dinga kubce mata a hankali tana bibiyar waqar.

Dan speed ta qara ganin ta hau doguwar hanyar nan wadda daga ita zata shiga titin gidan tv
dinsu,hanyar ta fiya shuru,ita kuma tun dacan tana da tsoron wajen daya fiya shuru haka.

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ta furta tana zaro idanu lokacin da gudun motar ya fara ja baya,ta kuma
fara tafiya slow. Dukka idanunta ta fiddo waje ciki tsananin fargaba tana duba ma'ajiyar dake nuna dadin
man fetur dake cikin motar. Mamaki ya kamata qwarai ganin cewa wai mai ne ya qare,bayan shekaran
jiya aba yayi mata full tank da motar tata.

Bata saku damar kai motar gefan hanya ba ta mace mata,ta sake kiran sunan Allah tsoro da
fargaba yana cikata,ta kalli hagu da dama dukka ba motsin kowa sai kukan tsintsaye da iskar dake kada
dogayen bishiyun da suka yiwa hanyar qawa.

Hannayenta ta hada waje daya ta karanta addu'o'i ta shafa a jikinta,ta bude murfin motar a
darare tana fitowa wai ta duba gaban motar ko zata gane inda matsalar take,duk da cewa ba wani abu
data sani akan matsalar data shafi mota,don shi kansa driving ma bata dade da farawa ba,ko ina zata
akwai mai kaita akwai me daukota.

Koda ta bude kaman yadda ta zata bata fahimci komai ba,haka ta qarewa wayoyi kallo ta mayar
ta rufe,saita jingina da motar zuciyarta na bugawa tana kiran sunan Allah.

Waige waige taci gaba dayi,mintuna kusan goma amma bataga gilmawar kowa ba,ta lumshe
ido ta juya da sauri ta bude motar,ta dauko jakarta ta fidda wayarta da zummar kiran ama ko aba ko can
tv station din nasu ko akwai wani dauki da zasu iya kawo mata.

Wayam ta gani,babu komai cikin jakar sai dan tarkacenmu na mata da bama rabo dashi,kulle
idanunta tayi da qarfi tana cewa
"Innalillahi" tabbas saman dining din ama ta manta wayar. Zuciyarta dukka ta karye,ta koma ta window
tana cilla jakar,daidai sanda ta soma jiyo sautin tahowar mota

"Alhamdulillah" ta fadi tana gyara yafen scarf dinta,ta matso bisa titin sosai ta sanya hannu sanda motar
ke dab da isowa inda take tsayen,saidai abun haushin wucewa motar tayi. Cikin sarewa ta sake komawa
ta tsaya tana fatan samun dauki,cikin sa'a ta sake jiyo wata motar,sai ta sake matsowa tana saka hannu
wannan karon harda bayani

"s'il vous plaît, aidez(please help)".

Murmushi ya kamashi amma ya danne,har yanzun halayyar nan ta tsoro tans nan bata barta
ba?,target dinsa ya fada a dai dai kenan. Yana sane yadan take motar kamar zai wuce,har yayi gaba sai
ya rage gudu,ya danna reverse ya dawo da baya da gudu.

"Alhamdulillah" ta fada tana aje numfashi ganin motar data wuce din ta fidda ran tsaiwarta itama tana
dawowa.

Ganin an tsaida motar kuma ba'a fito ba saita soma takawa zuwa gaban motar,duk dadai a
tsorace take amma tana da yaqinin qasa ce me aminci da iren iren abubuwa masu cutarwa haka basu
fiya faruwa da mutane ba,uwa uba kafin ta fito daga gida tayi addu'a,tana da tabbacin tana cikin kariyar
ubangiji.

Yana zaune daga cikin motar yana qare mata kallo son ranshi,idanunsa da kansu suka dinga
rusunawa suna budewa,yadda take takowa zuwa gareshin yana sake tada masa wani sabon tsumammen
feelings a kanta,tamkar daren jiya dama baiyi komai ba. Yana iya ganinta tarwai,amma ita bata iya
ganinsa saboda baqin glass ne dashi. Sanda ta tsaya jikin window din ta masa knocking sai yayi kaman
baiji ba,yana ganin yadda fuskarta ta nuna alamun qosawa,ta sake knocking glass din,sai yadan sauke
glass din kadan ta yadda zai iya jinta kawai ba tare da taga fuskanshi ba
"Pouvez-vous m'aider? La voiture ne fonctionnait plus(zaka iya taimako na?,motata ce ta daina aiki)" kai
kawai ya gyada,ya maida glass din ya kulle. Sak tayi tana tsammanin mamallakin motar na shirin yin gaba
ne abunsa,sai taga an bude murfin side din da yake,ya zura qafafunsa ya fito gaba daya.

Baya taja da sauri tana dubanshi yayin da shi kuma ke gyara zaman suit din jikinsa kamar ma bai
santa ba. Sake ja tayi da baya sanda ya fara takawa yana nufar motar .

Turqashi!,ita sam batasan shi bane tunda batasan wanne kala ne motarsa ba,tsoro ya hanata
motsawa,har ya bude gaban motar ya gama tabe tabensa,ba kuma tare daya kalleta ba yace

"Wannan motar bazai tashi ba yanzu ya tafi hutu,ki nema abun hawa ki wuce" ya fadi yana karkade
hannayensa kaman wanda yayi wani abun arziqi.

Tayi zaton zaice mata ta taho suje,amma sai taga yana nufar motarsa,har yanxun kuma bai
kalleta ba, sanda ya shige ya maida murfin ya rufe ta tabbatar tafiyar fa zaiyi,saita kalli hagunta da
damanta,su kadai suka rage a wajen,dole ta sake matsowa gaba da sauri ta daga masa hannu.

Kaman bazaiyi kowanne motsi ba sai kuma taga yana sake sauke glass din har ya kammala
saukeshi tas,idanunsa a kanta,ya sanya hannu a nutse ya zare baqin eye glasses dinsa

"Ya akayi?" Ya jefa mata tambayar yana mata wani irin kallo. Idanunsa sun fiya dafi da yawa,sai ta kauda
kanta gefe sannan tace

"Ka qarasa dani bakin hanya...... please" ta qarasa maganar tana jin dacin neman alfarma yau a wajensa.
Kaman ya qyalqyale da dariya to amma yanzun ba muhallinta bane,don yana hango yadda roqon ya
mata daci. Murya can qasa ya amsa mata yana maida glass dinsa

"Bismillah" yace da ita. Rai a bace ta qarasa wajen motar tata ta fidda kayayyakinta,ta tako cikin
nutsuwar nan tata zuwa bakin motar.
Bayan motar take da muradin shiga,to amma kuma tun duniya tana kwance tasan halinsa
sarai,dole badon taso ba ta bude gaban motar ta shiga,ta maida murfin ta rufe,ya saki boyayyen
murmushi cikin ranshi yana cewa

"Mission accomplished" ya tayar da motar a nutse yana qarawa fuskarsa daurewa,daurewan da ya qara
mata wani irin kwarjini daya fitar da ainihin kyanshi.

_su maina sarkin wayo,ina zuwa?_

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_


6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/6, 8:05 AM] +234 803 066 5772: *_GUDUN ƘADDARA_*

[7/6, 8:05 AM] +234 803 066 5772: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 88

Cikin nutsuwa yake driving motar,wani irin calmness yana nunawa saman fuskarsa. A jikinsa
yakejin addu'a tana mugun tasiri ga bawa baya ga irin sa'arshi a rayuwa,yanajin wani sukuni idan ya tuna
tana a gefansa,ta shiga kuma tarkonsa sai yadda yayi da ita a yau dinma,amma idan ka kalleshi zakayi
tunanin yana wani lissafi ne daban bawai tana a gabansa bane.

Tafiyar mintuna goma kacal suka fita a titin,sai ta sauke ajiyar zuciya tana jin sasaauci a
ranta,sun wuce wajen da take mutuwar tsoron,kuma a nan ya ajjiyeta hakan ya mata. Tadan motsa
kadan tana tunanin zai faka motan ne gefan hanya ya ajjiyeta,sai kuma taga yaci gaba da tafiyarsa lafiya
lau kaman ba kowa cikin motan sai shi kadai.

Kusan hanyar tasu daya ce,don haka bata fuskanci wani hannun ya dauka ba sai da sukazo dai
dai titin da zaka tadda TV station din nasu,maimakon ya saka signal ya shiga sai taga ya wuce.

"Zaka iya ajjiye ni a nan" ta furta tana gyara riqon jakarta

"Kinyi zaton driver kika samu da zaki tsaidashi a duk sanda kika so?,na riga dana wuce,sai kuma idan na
dawo" ya fadi yana basarwa ba tare daya kalli fuskarta ba.

Fuska tadan motsa tana maida idanunta ciki,kai tsaye take dubansa,bata fahimci abinda yake
nufi ba,ta hadiye maganar dake ci mata a rai tace

"Bance ka qarasa dani ba,zan iya kai kaina daga nan" ta amsa masa da dan qwarin gwiwarta

"Shut your mouth mrs maina" ya fadi yana saka signal zuwa hannun hagunshi titin da asibitinsa yake.

"Mrs maina?" Ta maimaita sunan a fili saidai can qasa tana jin abun banbarakawai
"Yes......maina MAYAK'I", ya qarasa mata ba tare da ya waiwayo ba. Shuru tayi yatsunta qasan habarta
tanason wassafo zallar rainin hankalin da yakeson yi mata. Maganganu ne cikin ranta na bacin rai masu
yawa da takeson gaya masa amms kuma tana jin wata shakkarsa tana ratsata. Bata manta yadda ta
gurzu ba a jiya,wanda tasan wani abun da gayya yayi mata,ta kuma ji a jikin nata,don har yanzun akwai
guraren da basu daina ciwo ba a jikinta. To amma ita bata nema komai daga wajensa ba banda rage
hanya.

"Kada dai ace hanata zuwa aikin yayi niyyar yi da gaske kaman yadda ya haramta mata zuwa gidansu
aminata har ta baro nijer?" Ta tambayi kanta sanda ya tsaya bakin gate din katafaren asibitin yana
neman izinin shiga.

Ranta yayi qololuwar baci sanda ta cusa hancin motar zuwa harabar asibitin,ya tsaida motar a
wajen ajiyar motoci na musamman dake asibitin. Qasa ya danyi da glass dinsa,ma'aikatan dake wajen
suka fara qarasowa suna gaidashi cikin girmamawa. Wasunsu da harshen France,wasunsu da
English,wasunsu da Arabic,sai wasu masu yare biyu daban da batasan wanne yare sukeyi ba,amma kuma
da mamaki da taji maina din ya iya.

Zare key din motar yayi ya juyo kaman zai kalleta sai kuma ya dauke kai,ya bude side dinsa ya
fito ya zagaya nata seat din. Hannunsa ya zura ya sauke glass din motar sosai,hakan ya bashi damar
dogara gwiwar hannunsa saman window din idanunsa zube fes cikin nata idanun da hasken rana ya
sanya sheqin qwayar idanunta fita sosai,ta kuma sake fidda kyan idanuwan,saidai kuma rauni da karaya
me tarin yawa ya hanga cikin idanun nata.

"Zaki fito salin alin?,ba tare da mun tarawa kanmu jama'a ba?,ko kuma in sauqaqe miki na daukeki zuwa
ciki a hannuwana?" Tsoro maganar tasa ta bata,hae ta zaro qwayar idanunta waje ba tare data shirya ba.
Ya fahimci me take nufi,sai ya dage dukka girarsa yana sake kafeta da shu'umin kallon nan nasa da
zagayayyun lion eyes dinsa

"Yes........ya halatta a nan qasar koda ba couples bane mu,ballanta ne da kike halaliyata,ko a cikin motar
nan na buqaci ki bani haqqina indai kinason kaucema tsinuwar mala'iku haka zaki gyar........."
"Subhanallah" ta fadi a fili tana kuma janye idanunta daga cikin nasa numfashinta yana neman sauyawa
saboda fargaba da mamaki.

Kalamansa sun mata matuqar tsauri,Wani abu me kama da nauyinsa taji ya saukar mata tun
daga saman zuciyarta,don haka ta janye idanunta gefe. Shi ko sau daya bai taba jin nauyij gaya mata irin
wadannan kalaman ba?,shi baya jin kalaman cike suke da tsauri da kuma nauyi?,ya sake lalacewa daga
ya maina din data sani sanda tana nijer,sultanar nijer wadda batasan rayuwa ba,sultanar nijer da bata
taba zuwa ko ina ba banda Nigeria.

"Fito....." Ya fadi yana ja baya,ya kama murfin motar ya bude mata yana tsaye ata wajen.

Bata sake cewa komai ba saboda shawarar da zuciyarta ta bata,ta bishi ta lalama ko ta zuba
masa idanu taga iya gudun ruwansa,ta miqa hannu zata dauka jakarta ya miqa nasa hannun sai ta janye
nata hannun,ya riqe jakan ta sako qafafunta ta fito daga motar. Murfin ya maida ya rufe,taku uku ya iso
gabanta,bata tsammani ba sai taji tafin hannunta cikin nashi soft and warm tafin hannun. Wani yarrr taji
kaman an watsa mata kiyashi

"Karkiyi taurin kai.......banason musu,i hate it.....indai da musu tsakanina dake ba zakiji dadi na ba
sultana" lips dinta na qasa ta dan cije kadan,ga maganganu fal cikin ranta,amma yanzun neman kubuta
daga hannunsa takeyi kada abun jiya ya maimaita kansa.

Abinda ta lura dashi kafin su isa reception din yadda idanu suka yi musu yawa a ka,eh su ba
qabilarsu bane......amma kuma mutane ne kaman kowa,idanun haka na meye?. Bata da amsa saita
taqaita ganinta kawai,bata da wani sauran kuzari saboda abinda takeji a jikinta.

Tunda ya sanya hannunshi cikin nata yake yamutsa hannun a hankali,fatar tafin hannunshi
yana gogar bata softly,sau uku tana qoqarin janyewa yana warning nata da idanunsa,sai tayi sak kawai
tanason taga iya gudun ruwansa.

Tun daga reception taga kalar girmamawar da ake masa,wani girma ake bashi na musamman
wanda ya tabbatar mata tabbas shi din wani ne cikin asibitin. Duk wanda ya gaidashin kuma sai ya kafeta
da kallo,kwarjininsa ya hanasu tambayarsa ita din wace?,at last suna dab da shiga elevator sukayi
kacibus da daya daga cikin doctors na asibitin. Da alama shima babba ne cikin asibitin,saidai kuma yana
da shekaru ba kaman maina din ba,shi dinne yayi qarfin halin tambayarsa,murmushi yadan saki yana
gaya masa matarsa ce. Murmushi sosai likitan ya saki ya juya yana gaidata,daurewa tayi ta saki
murmushin yaqe tana amsa masa,sukayi sallama ya sama musu elevator suka shige.

Ko kammala rufe kanta elevator din batayi ba ta zame hannunta cikin zafin nama,batasan me
yasa ba amma tunda ya soma murza mata tafin hannuwa gaba daya nutsuwar jikinta ya fara yin
qaura,wani abu me kama da yanayin data tsinci kanta a daren jiya yake mata yawo a jiki,kasala da
mutuwar jiki tana mamaye dukka gabbanta,har idanunta tana jin sun fara wani iri.

Baice komai ba sai tsaiwa da yayi a gabanta da dukka tsahonsa,ya zube hannayensa cikin
aljihun trouser na suit dinsa,ya kafeta da mayatattun idanunsa dinnan da har yau bataga idanun da suka
kai nashi nauyi ba.

Baya taja kadan saboda yadda tsahonsa ya kere nata sosai,karon farko data fahimci lallai da
gaske yaa maina din yana da tsohon da murjewar jikinsa yake hanawa a gani. Cikin rashin sa'a taku biyu
kacal tayi ta tokare da qarfen elevator din,saita juya baya da sauri,no more space kenan?,sai ta sake taku
biyu Left side dinta don burinta kawai ta bashi tazara. Duk hanzarinta batakai shi ba,batakai ga aje
sawayenta ba ya tare gurin da hannu yayi mata katanga,ya qara taku biyu kawai sai ya hade gap din dake
tsakaninsu gaba daya.

Musayar numfashi suka fara yi,daya daga cikin abinda ya karanci yana cikin weakness dinta tun a
daren jiya. Hannayensa ya sanya dukka ya kamo hannayenta cikin nasa ya riqesu da kyau,ya kuma yi
musu matsaya saman qirjinta still yana riqe dasu,wannan ya bawa bayan hannunsa damar gogar
qirjinnata a dabarance.

Cikin magudanar kowanne jini na jikinta ya sakar mata wani irin feeling na babu zato wanda ke
cakude da fargaba kafiya da taurin kai,fes yaga komai cikin idanunta,wannan taurin kan ya
tsana,yanason ya qarasa cisgeshi gaba daya daga ruhi da gangar jikinta,don haka ya danna hannayensun
duka da kyau cikin qirjinnata,abinda ya sanyashi tabo muhallin sosai,hakanan itama saqon ya sake isa ga
sassan jikinta fiye dazu,lamarin daya sanya zuciyarta karyewa saboda komai ya fara kai mata ko
ina,wannan ya karya zuciyarta,oily eyes dinta suka fara hidimar tara ruwan hawaye ta fara girgiza masa
kai don abinda ta soma gani cikin qwayar idanunsa tana jin kamar zai kassarata,sauyawar kalolin qwayar
idanunsa kadai abun tsoro ne a wajenta,yadda ya kafeta da idanunsan nan masu kaifi ya sake kassara
duk wani kuzari da karsashinta.
Abinda bayan hannunsa ke iya ji din su suka zama jagoran baiwa dukka sassan jikinsa wani irin
feeling me matuqar qarfi,har yana jin kamar bazai iya skipping minti daya ba a haka,numfashinsa ke son
fara masa wasa,yayin da cikinsa ya harba,ya tabbatar somi somi ne na murdawar ciwon
cikinsa,matsanancin ciwon cikin da tun daga wancan ranar daya fara saninta diya mace yake zame masa
barazana a rayuwarsa. Duk inda zaya samu magani magana daya suke gaya masa,yana buqatar mace by
his side. Ya riga ya fara yiwa halittarsa dan dani haukaci,tarin sha'awar da take cikin jini da halittarsa ya
fara mata hanya daga bisani kuma hanyar ta datse,yana ganin komai cikin kowanne mafarki,yana ganin
komai cikin kowanne dare,amma a zahiri bashi aikatuwa. Bai tana sha'awar zina ba,koda wasa kuma bai
taba sha'awar tana diyan kowa bada sunnar annabi Muhammad ba,wannan ya sanya yake cikin azaba
tsahon shekarun. Daga baya ya gayawa kansa,ciwon cikin yana daya daga cikin hukuncin da Allah zai
masa ne tun a duniya na nesantar gida da yayi,har yanzun kuma yana aza ciwon a mizanin hukuncin
Allah a kansa. Sauqin daya samu zuwansa umra biyu na qarshe daya yawaita addu'a,sannan kuma yasha
zam zam sosai,sai gashi a wannan rana a kuma wannan lokacin yana niyyar tasan masa.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200
_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/7, 3:58 PM] +234 906 049 8204: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 89

A hankali jikinsa ya fara shacking abinda ya tilas masa sake mata hannu,ya kuma yi amfani da
hannayen nasa ya jawota cikin jikinsa sosai sanda take neman yadda zata qwace,saidai ko kusa ko alama
ya hanata hakan,dai dai sanda elevator dinsu ya isa floor din da ya buqata,sai ya jawota gefen qugunsa
sosai ya riqota da kyau ya soma takawa da ita a hankali suna fitowa daga elevator din.

Dogon lobby ne dake dauke da office a jere cikin tsari da tsafta da kuma wadatar haske,waje ne
dake da cikakkiyar nutsuwa don babu hayaniya ko kadan a wajen,a nutse yake takawa da ita bai saketa
ba hakanan bai sassauta mata riqon da yayi matan ba,sai dan cije lips dinsa kadan da yakeyi saboda
yadda yaji mararsa na murdawa,da gasken gaske ciwon keson motsa masa kenan.

Inda so samu ne,kuma inda ciwon yayi shawara dashi bazai taba bari ya motsa a irin wannan
lokacin ba,saboda shi kansa yana tsoron zuwa irin ranar akan kowacce diya mace ma game dashi,yasan
baqar wuyar da yakesha a baya,irinta dinne ya tabbatar duk sanda ya sameshi zai juye akan koma
wacece.

A nutse duk da yadda jikinsa keson ya fara shacking ya bude qofar office na uku dake jere cikin
jerin office din,yana riqe da ita da daya hannun ya tura qofar ya shige,sannan ya maida qofar ya kulle ya
juya a hankali yana dubanta.

Tana tsaye a tsorace,ta raba hankalinta biyu,da farko tayi zaton office ne kaman kowanne
office,sai da suka shigo sai ta fahimci office ne amma kuma na musamman dake dauke da wasu kujeru
da kake iya maidasu gado a duk sanda kk da buqatar hakan,akwai lallausan carpet daya mamaye ko ina,
kyakkyawan table dake dauke da takardu,fridge da manyan throw pillows masu taushi farare qal,
corridor daga waje sai toilet daga ciki,gefe guda kuma kayan tarkace cups ne cikin wani drawer na glass a
shirye,harda plates da spoons masu azabar kyau duka gold color. Basarwa tayi ta kama scarf dinta tana
gyara zamansa saboda dan zamewa da yayi. Hannuwansa ya goye a qirjinsa yana takowa inda tadan
bashi baya. Sam bataji tahowar tasa ba saboda lallausan carpet din dake wajen,saiji da tayi yayi caraf da
hannunta a tausashe. Juyowa tayi adan hasale,saidai kuma

Kallon da yake mata ya banbanta da na kullum,mamaki da dan tsoro yadan kamata ganin yadda
idanunsa sukayi laushi cikin lokaci kadan,a hankali idanunsa suna lumshewa suna kuma budewa kusan
lokaci guda,sai ya sanya hannuwansa ya soma warware scarf din dake kanta
"Am burning with jealousy.......am envying sultana" ya qarasa fada muryarsa a tsananin karye,ya kama
hannunta da daya hannun nasa yana kaiwa saitin qirjinsa daidai zuciyarsa, idanunsa cikin nata. Hannunta
taso janyewa,amma kuma sai taji bugun zuciyar tasa da gaske ya wuce kima,dukka wata laka ta jikinta ta
fara tsinkewa,sai ta gaza aiwatar da komai sai idanunta dake qirjinsa data zubawa idanu

"Am a cardiologist......kinji yadda bugun zuciyata ya banbanta da na masu lafiya ko?.......inaji a jikina
indai haka yaci gaba da faruwa......zan iya samun heart failure sultana" ya qarasa maganar ta sigar rada
yana lumshe mayatattun idanunsan nan tamkar wadda bacci ya yiwa illa.

Mutsu mutsu ta fara yi da hannun nata tana son qwace kanta,yanason yayi amfani ne kawai da
harshensu na maza da suka qware wajen zaqin zance yasa ta mance yadda yayi rugu rugu da
rayuwarta,ta dinga daukan rayuwarta da zuciyarta a pieces da qyar ta iya hadeta waje daya,sai kuma
bayan ta tsallake kowanne tsanani,tayi moving forward yakeso ya dawo ya sake rabar rayuwarta?.

"Me yasa kika sake fita sultana bayan na gaya miki banaso?" Ya jefa mata tambayar yana qoqarin
komawa mode dinsa na dazu. Fararen Idanunta ta daga ta kalleshi abubuwa da yawa cikin ranta.

"I can't take it......duk duniya suna kallonki,fuskanki,muryarki dama mo......." Kasa qarasawa yayi saboda
ciwon daya mugun murda masa,sai kawai ya sanyata cikin jikinsa gaba daya ya dunqulesu waje daya har
sai data ce

"Wayyo Allah na bayana" saboda wawiyar rungumar da yayi mata,kusan mintuna biyar sunana haka yaqi
sakinta,ya kuma hanata motsawa,kamar yadda itama tsoron gudun da zuciyarsa takeyi ya hanata
aiwatar da komai,tana jin yadda take bugawa sosai har saman qasusuwan qirjinsa.

Idanu ta shiga rabawa saboda gumin da taji yana ratso sumarsa yana gogar gefan wuyanta,shiri
ne ko da gaske ne?. Ta tambayi kanta,da sauri ta zare jikinta daga nashi tana dan turasa kadan,abinda ya
sanyashi yin baya yayi kaman zai fada saboda yadda jikinsa yayi laushi,sai ya sanya hannayensanya dafe
bayan kujerar yana yin qas da kansa gami da runtse idanunsa da kyau. Labbansa na motsawa yana kiran
sunan Allah yayin da sautin baya fita da kyau,shi kadai yasan abinda ke yawo tsakanin mararsa da jikinsa

Bata lura ba don gaba daya yadda yake behaving dinta ya sanya lissafinya na neman
kwancewa,saita qarasa saman table inda ya yiwa jakarta ma'ajjiya ta dauka tana gyara riqonta gami da
fadin

"Ka budemin na wuce na makara" ganin bai ko motsa ba saita tuna taga key din saman table,ta koma da
sauri ta dauka ta dawo ta zura tana qoqarin budewar.

Lausasan tafukan hannayensa taga ya saka ya riqe hannuwanta dake murza key din,ya dagasu a
nutse yana zare muqullin daga tsakiyarsu

"I need you......i really need you" ya fadi yana yin jifa da key din,kai tsaye kuma ya fada wani guri ko
irinsa bata gani. Fuska a narke ta dauke idanunta daga key din daya bacewa ganinta ta maida
kansa,yayin da yake tsare ya tsareta da nasa idanun

"Amma......hanya kawai nace ka ragemin,ka daukoni ka kawoni nan" ta fadi zuciyarta na karyewa. Tana
tsoron haduwa dashi,iya jiya kawai tasan zaren ba kalar yadin bane........fitinar dake idanunsa a yanzu
kuma suna sake nuna mata yana da buqatar qarin wani abu na daban.

Maimakon ya amsa mata sai ya saki wani tattausan murmushi,ya kamo fuskarta yana duban
qwayar idanunta da ko yaushe suke tafiya dashi,tun da can,tun yana matsayin uncle dinta idanunta
yasan na dabanne,bare yanzun da suke haifar masa da wani yanayi mai matuqar gaske a jikinsa

"How can you turn me on so much just for looking at me?". Fidda idanun nata waje tayi tana mamakin
abinda yace din,sharri kenan zaiyi mata?. Buda masa idanun da tayi sai ya sake kunnashi din

"Ya salam" ya furta yana yarfar da hannu, tsigar jikinsa tana tashi,yafiso duk sanda zasu kasance din a
tare ya zamana tana cikin shauqinsa kamar shi,ko yanzun ji yakeyi kaman yayi mata yadda zuciyarsa ke
raya masa,amma ba wannan yake da buqata ba,ba jikinta kawai yakeso ba,yanason harda zuciyarta
nutsuwarta dama yardarya,yardar ce kadai yasan zatayi masa wahala muddin ta kai tsaye ce
"Let me go......" Ta fadi tana son tsaurara muryarta

"No.....ba zaki shigamin mota a bati ba,kinsan ba'a aikin banza dai ko?"

"Me kakeso na biyaka dashi?" Can qasa yayi da muryarsa yana jifarta da wani irin kallo,kamar me rada
kamar kuma wanda bayason kowa yaji me yake cewa,ya qara taku yana hade tazarar tsakaninsu

"Money?" Ya tambayeta yana dage mata gira,tayi taku biyu zata ja baya ya sake hadr gap dinsu

"Inason wani abu da yafimin kudi daraja......yafi duk wani abu me daraja daraja a wajena......." Sai ya
sake tausasa muryarsa yana qoqarin saita kansa saboda ciwon cikinsa dake qara gaba

"I need to re_taste that body of yours.....i can't wait to kiss every inch of your body.......my hand wants
to feel every inch of you". Maganganunsa gaba daya suka sanya taji qafafunta ba zasu iya daukan gangar
jikinta ba,sai tayi qasa ta sulale tana dunqulewa waje daya. Bai qyaleta ba,don abinda yakeson ya samu
kenan lagonta,sai ya bita suka qarasa sulalewa gaba daya,ya jawota jikinsa ya mata wani irin kyakkyawan
riqo yana fusgar numfashinsa da qyar saboda tsananta da ciwonsa yayi,magani kawai yake nema,don
haka cikin qasa da second uku ya zame mata kamar wani mahaukaci ko mayunwacin zaki. Saboda wasu
irin saqonni masu mantar da dan adam sashen tunani da tuna abinda ya kamata na qwaqwalwarsa ya
shiga aike mata. A zafafe,a yunwace a kuma shauqance.

Duk yadda taso kaucewa wani saqo nashi abun ya faskara,duk yadda taso ta kauce kada ya
lalata mata tunani abun yafi qarfinta

"Yaaya maina ne wannan?,ya haidar ne?" Tambayar da zuciya da kwanyarta suka hadu suna aike mata
kenan a sanda yake dab da fiddata daga hayyacinta.

Ba zatace ga yadda aka fara ba,dukkansu daga ita sai shi sai bude idanunsu sukayi sukaga
komai ya wakana a nan gurin,dab da bakin qofa,sauqin abun carfet din wajen me tsananin taushi
ne,sannan wajen office ne na musamman da akayi musu bayan office dinsu na ainihi dake first
floor,wannan din kaman ya zamana wajen hutawa ne kawai a garesu su manyan likitoci.

Ko motsin kirki ta kasa tayi bare ta yarda ma su hada idanu,sai hawaye kawai da take
tsiyayarwa,wanne irin yaudara ne haka yake mata?,wacce irin shammata ce wannan?,wanne irin kuma
rashin adalci da qarfa qarfa yake mata?.

Dariyarsa yake qunshewa kawai,shi daya yasan yadda ya sanyata ta sauka daga kan layi,shi
daya yasan me yaji me kuma ya gani?,duk da yadda take dojewa a hakan saboda kafiya da taurin kai irin
nata,amma koma meye ya sani yayi winning,ta kuma sama masa magani yau cikin qasa da mintuna
goma,abinda a baya sai ya shafe kwanaki yana kwance saboda babu matallafi,babu me tayashi fidda
cutar dake danqare a mararsa.

Har ya fito a wanka tana duqunqune a wajen,ta cure cikin lallausan blanket har baka iya
hangota,sai sheshsheqar kukanta. Tsaye yayi gaban madubi yana kallon fuskarsa,ita kanta fuskar tasa
tayi wani fresh ta qara haske,irin haske da qyallim goshin da ake cewa angwaye sunayi,wani murmushi
yasubuce masa ya miqa hannunsa zuwa lallausar sumarsa da tasha ruwa har yake diga ruwan,yanxun
yana mata magana yasan rigime masa zatayi,solution shine kawai yayi mata yadda ya saba.

Tsane kansa yayi da kyau ya maida trouser dinsa da shirt din ciki ta suit dinsa,ya balle maballan
rigar yana nannadesu,sannan ya taka zuwa gabanta.

Tsugunnawa yayi sosai yana bada qarfinsa a qafar damansa,tsugunnon sai ya masa kyau yana
sake nuna cikar zatinsa da haibarsa.

"Kukan nan ya isheni, gate up kije kiyi wanka,ina cewa aiki na miki kika biyani........I didn't do it by force"
ido ta rufe da kyau,zai sake raina mata wayo irin na rannan kenan?.

"Ko meye ka yimin Allah zai saka min" ta fadi qasa qasa,saidai mugun ji gareshi din haka ya jiyota

"What?" Ya fada dariya na qwace masa


"Kinga malama,ji mana,ni zaki rainama wayo?,inda bakiso me ya hana ki qwace kanki koda ta qarfi
ne?,ba abinda kika tsinana sai cewa da kikeyi 'ka bari mana,banaso' kuma nasan it is hypocrisy, gate up
idan ba haka ba na wankeki tas........abun ma da ba wani dadi da yayi?" Ya qarasa fada yana miqewa.

Batasan me yasa maganarsa ta qarshe ta sauka a kunnuwanta da ciwo fiye da dukka


maganganunsa ba,sai kawai ta saki kuka me sauti,sautin daya dinga jinsa yana masa dadi don ya jima
baiji kukanta me sauti kama haka ba,sautin yana tuna masa da yadda yasha fama da its lokacin
quruciya,koke koken banza da tsokana,idan kuma akafi qarfinta ranan aka zaneta ta buwayi kowa cikin
gidan.

"Idan nayi counting daga daya zuwa goma baki wuce toilet ba,na rantse yanzu zan tube mu tafi second
round,kuma second round dina bashi da dadi ni kaina na sani......it will take more than twenty to thirty
minutes" ba shiri ta tattara blanket din tana boye kanta a ciki,ta soma takawa zuwa bandakin,har yanxu
bata bar kukan da take ba.

Da idanu ya bita yana jin wata zazzafar qauna da tausayinta cikin zuciyarsa. Xayaso shi zai mata
wankan,ya lullubeta cikin qirjinsa,ya shiryata,yayi mata tausa a dukka guraren da yasan ya wahalar da
ita,to amma ita din zuma ce sai da wuta,qilau zata iya jawo bau,gwara dai ya bita a haka.

Sai data shige toilet din ya dauke idanunsa yana fidda iska daga bakinsa,yana mata uzuri sau
da dama,kowa da yadda Allah ya halicci zuciyarsa,wani mutumin yana da saurin manta abu ya
wuce,wani kuma koda ya yafe abu baya saurin barin zuciyarsa,bashi da mantuwa kwata kwata,kuma
hakan ba yana nufin bai yafe ba,any way yaci alwashin sai ya sanyata tayi rushing zuwa gareshi sooner or
later.

Yanason ya fara gyara wasu abubuwa da yakejin lokaci yayi da zasu gyarun,don haka ya miqa
hannunsa ya dauki jakarta,ya kuma fiddo wayarta ya bude, zuciyarsa fes,ruhinsa tas..........

_KWANKWASON JIMINA_*
*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*
09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/7, 3:58 PM] +234 906 049 8204: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 90

Mobile app nashi ya bude bayan ya gama caje wayar ya lalubi account number dinta,kudi ya tura
mata masu yawa,ya kuma zuba mata numbers dinsa dukka yayi saving da

"Dad BB" wasu kuma ya saka sunan masoyi da yaren faransanci,wata kuma ya saka sunanshi haka nan.
Duk abinda yake da buqata,kama daga pictures dinta da sauransu ya tura sannan ya maida wayar
aljihunsa.

Ta jima tsaye a bakin qofar lullube ruf da towel tana jin nauyin fita,batasan da wanne ido zata
kalleshi ba,wani irin kunya takeji ba dan kadan ba,ta dinga juya kalamansa a kunnenta
_idan bakiso me ya hana ki qwace kanki koda ta qarfi ne?,nasan it's hypocrisy_ idanunta sukayi rau rau
da hawaye tanason tuna da meye da meye ma tayi a lokacin,saidai kuma oho ta kasa tuns komai.

Hakanan tayi shahada ta murda handle din ta sanyo qafafunta waje. Yana tsaye kyam yana
fuskantar qofar tamkar me gadinta,dukka idanunsa ya zuba mata, murmushi yana son qwace masa,gaba
daya ta tsargu,sai ta koma ta bayansa tana cire towel din da sauri tana maida dankwalin kanta.

"Nooo" ya fadi yana ajjiye wayoyin hannunsa saman mirror,fara takowa yayi wajenta yayin da tayi tsuru
tsuru tana kallonsa. Ita totally a firgice take dashi,ko qanqani batason ya matso kusa da ita,saboda ta
fahimci ko yaya jikinsu ya samu connection sai mode dinsa ya sauya,sai ya buqaci kuma kebewa da ita.

Ta bayanta ya tsaya,ya sanya hannu ya zare scarf din yana cewa

"Bai bushe ba ta yaya zaki rufeshi?" Kafin tace komai har ya sanya hannayensa biyu ya fara ware gashin
zuwa gadon bayanta wani kuma zuwa fuskarta. Da sauri ta miqa hannu ta riqe hannun nasa,sai ya kada
kai

"Ko ki sakarmin hannu ko kiga matakin da zan dauka....." Ba shiri ta sakar masa hannun idanunta na sake
hada hawaye. Ta gaji da hawaye,batason kuma tayita zub dasu tunda bataga ranar tsaiwarsu ba. Kaman
yaji abinda ta raya itama ya sake tabbatar mata yana sake janyota cikin jikinsa

"Ki rage yawan kuka kada ki rasa hawayen xubadawa a labour room". Qarasa kashe mata bakinta yayi,ta
rasa ma meye zata ce masa taji dadi,sai kawai ta gwammaci tsuke bakinta amma ta kasa tsaida hawayen
idanun nata.

Janta yayi ya zaunar gaban madubi,yasa drayer ya busar mata da kan nata,yana aikin yana
cewa

"Tunda nine silar jiqewarsa ai gwara na gyara abuna kada laifin nawa yayi yawa" harara takeson watsa
masa amma tana shakkar abinda zaya biyo baya a matsayin horo,ta tabbatar idan yace zai sake wani
round din a yanzu babu abinda zai hanata ziyartar gadon asibiti,don dukka gabobinta motsi sukeyi mata
yanzun da wani irin ciwo,mada ma cinyoyinta suji labari,haka nan lips dinta da suka sha tsotso kaman
babu gobe. Kanta ta dauke gefe tana tsuke bakinta gefe,bakin da zuciyar fal da tsiwa,amma tana tsoro ta
furta,so take ya fiddata daga wannan office din,batasan wanne tsautsayi bane ya sanya tayi trusting
nashi ta shiga motarsa ba,bayan ko jinyar jiya bata gama yiwa jikinta ba,gashi yanzun ya sake hada mata
wata gajiyar.

Tsaf ya gyare mata kan,ya kuma dameshi da band dinta.

"See" ya furta yana dan ja baya kadan cikin murmushi yana duban fuskarta ta cikin madubin,fuskartata
ta fito sosai tayi fes,kyawunta ya sake fita ainun,hakanan oily eyes dinta sun sakeyin haske sosai.

Sau daya ta daga kai ta kalla na duka duka baifi second biyu ba ta dauke kanta. Ita kanta taga
yadda yayi qoqari,kyan yayi kyau kaman an mata retouch ne.

"Ni dama badon ke nayi ba,koki yabani ko karki yabani.....dama aikina ne tun kina 'yar mitsitsiyarki" yayi
maganar yana kama hancinta.

Tana shirin kauda fuskarta kira ya shigo wayarsa,sai ya sake mata hancin yana duba me kiran.
Tare idanunsu shi da ita suka kai kan screen din wayar

"Laila" ya furta bayan duka sun karanta sunan dake saman screen din a zukatansu. Ta gefen idanu yake
kallonta a sace,kanta yaga ta dauke tamkar ma bata ga komai ba. Murmushi ya saki dan qarami,ya haye
saman dressing table din qafarsa na gogar tata sannan ya daga wayar yana sanyata a handsfree

"Hello nijer man......" Laila ta fadi cikin sanyin murya da mutuwar jiki gaba daya. Yana sane ya danyi
delay na amsawar,sai ta sake magantuwa

"Hello........dear" ta sake fadi cikin lanqwasa murya har tafi ta dazu zaqi da qarfi.

"Hi......kina lafiya?" Narke murya tayi


"Yanzu kuma?......dear ban cancanci hakan ba,me yasa?" Yasan sarau akan me zatayi complain,ya fara
satar kallon sultana sannan yace

"Am sorry.....,am was so busy ne,but....zanyi qoqari naga na gyara"

"Kayi alqawari?"

"Zan duba in sha Allah.....ina fata ranki bai baci ba?" Ya fadi da gayya yana kuma sane.

Tsam ta miqe tana maida scarf dinta saman kanta,ta tsani jin sunan yarinyar gaba daya,ba don
komai ba sai don yadda ta fahimci a yawon duniyarsa ya hadu da ita,babu kunya kuma a tattare dashi
yake ci gaba da mu'amala da ita?,ko babu komai ita din ba d'iya ko qanwa take a wajensa ba?,wanda ya
kamata ace kome zaiyi ya kaucewa idanun sani ai.

Ji tayi an jawota an kuma zaunar da ita,wanda bata zauna ko ina ba sai saman cinyarsa,don
juyota yayi sosai ya kuma yi mata masauki a nan din. Hannuwansa taso zamewa amma yayi mata riqon
tsauri yana kuma ci gaba da wayar,tana iya jin sanda lailan ta bashi amsa

"Ba'a fushi ai da masoyi......yana da wani daraja da ya cancanci ayi haquri dashi a kowanne situation"
hannu ya sanya yana juyo da fuskar sultana gareshi lafazin laila yana ratsashi. Idanu suka hada,ta kauda
kanta tana jin zuciyarta na mata susa. Ne meye zai riqeta haka?,lallai dole sai taji zancansa da yarinyar
da ta tabbatar bata da kamun kai?.

"Thanks.....na gode sosai, za'a yimin uzuri yanzun?"

"Me zai hana.....ba damuwa bane"


"Thanks my little sister" murmushi tayi tana jin dadin hirarsu,yau din sai taji ya sake mata sosai ba
kaman yadda ya saba amsa mata a daddake ba,ya sauke wayar tana kissing dinta,tana tunanin nan da
next week ta siya ticket gaskiya taje ta ganshi,me yiwuwa addu'ar ta ne Allah ya amsa mata.

A nutse kaman baiyi komai ba ya aje wayar a gefe,ya dauki tata wayar yana buda tafukan
hannayenta,taso damqesu amma tasan wahalar banza zatayi da ranta,qarfinsu ma ba daya bane,ya
sanya mata sannan ya dubi idanunta

"As from today.....ki gayawa ama da aba,bana buqatar su sake miki komai,ke ko su benazeer,dukka
nauyinku a wuyana yake,ko abinci zanso kuci daga wanda na siya da kudina......amma shima din with
time zaku koma qarqashina" sam ko kadan abun baiyi mata ba,sai ta soma qoqarin zame jikinta daga kan
cinyarsa ranta na baci sosai. Bai hanata ba har ta gama zamewar. Tazara ta bayar tsakaninta dashi tana
dubansa

"Shekara nawa munaci daga taskar tasu?,ka taba tunawa da mu?" Ta fadi wani abu me tsauri yana
nunawa daga qasan idanunta.

Tsakiyar idanunta yake kalla,ko kadan maganar bata bata masa rai ba,a yau sai yake gano wani
abu daga tsakiyar idanun nata,wani abu daya sake sanya masa hope sosai a kanta,sai ya maidata kaman
tv sanda take motsa dan qaramin bakinta. Tsiwa takeyi amma batasan idanunta suna tona wasu sirrika
da yayi imanin ita kanta batasan dasu ba, murmushin gefan baki ya subuce masa,ya maida hannuwansa
ya goye a qirjinsa

"Na lura tafiya ta tana miki zafi da yawa a rai right?" Ya qarashe da sigar tambaya yana dage mata dukka
girarsa

"Saboda me zan damu?,bayan sai daka tabbatar na mutu ne sannan ka gudu ka barni"

"Ya salam......" Ya fadi yana kuma saki qaramin murmushi


"Yes.......kudadenka basa nufin komai a wajena......bani ya dace na cisu ba,yammatanka sune sukafi
dacewa dasu" dole wani murmushin ya sake qwace masa. Kishi!,ya fita sosai cikin zantukanta,so yake
taci gaba da maganar,saboda ya tabbatar tana fitar da duk wani ciwo da rauni Dake qirjinta,maganar
yakeso tayi tuntuni amma ta qiya,shi yasa ta gaza hucewa,amma a yanzun maganarta tana zame masa
tamkar wata nasara a tattare dashi.

"Cool down.....ki gayan hukuncin da kikeso na yiwa kaina da kaina"

"Leave me alone please, stay away from me...... that's all i want" ta furta da wani irin zafi.

Bai barta ta sauke numfashin data debo ba yayi mata wani kyakkyawan kamu,bai kuma bata
second chance ba ya mata masauki cikin jikinsa,ya mata riqon tsauri yana same tsotse lips dintan nan
masu sulbi da baya gajiya dasu.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200
_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/9, 8:52 PM] +234 803 546 4710: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
Book 2 page 91

Hawaye kawai take fiddawa ta gaza aiwatar da komai,itakam me ya maidata ne?,tun daga sanda
suka hadu a France bashi ds aiki sai luguguitata,ya maidata kamar wani babyn wasa?,meye ya rage ne a
jikinta bai taba ba?,meye ya rage a jikinta hannunsa da bakinsa baikai wajen ba.

Bata da qarfin qwatar kanta don haka hawaye da idanu sune kawai nata,har sai da yayi me
isarsa ya gama,ya saketa yana maida numfashi amma kukan da yaga tanayi ya sanyashi sake kamota har
zuwa saman sofa din dake dakin. Qafafunsa ya raba ya sanyata a tsakiya,bayanta ya jingina da qirjinsa
yana sauke numfashi a hankali idanunsa a lumshe,har sai daya daidaita numfashin nasa ta yadda zai iya
magana.

"Inata tabaki bakiso ko?, I can't control my heart.......if you know what double means to soyayyarki
ce.....na soki tun kina zallar jini a jikin nafessa.......na soki lokacin da kika wanzu a mahaifarta,na soki
sanda kika shaqi iskar duniya,na kuma dora da sonki tun daga wannan ranar kawo yau........abinda ya
faru tsakaninmu na tabbatar ubangiji ya hukunta hakan saboda ya mallakamin ke......banda hakan ya
faru da bazan taba ganewa cewa ina sonki so na soyayya ba......bazan taba gane ina sonki so na
auratayya ba,zanta dauka cewa so nake miki na 'yan uwantaka,so irin na uba da 'yarsa ne kawai,zan yita
fafutukar mallaka miki miji na gari ne ba tare da nasan cewa ni din nine nafi cancanta dake ba.....ke
jinina ce sultana kuma ruhina,ko baki sona,koki yarda ko kada ki yarda ke din BUGUN ZUCIYATA CE......I
can't stop loving you till my last breath........Tu es mon bonheur, tu es ma vie(kece farincikina kece
rayuwata" ya furta yana sakin gauron numfashi da ya motsa zuciyarsa.

Wani irin takejin kalamansa cikin zuciya da jikinta,gaba daya yanzun bata fahimtar kusan
komai,siririn kukanta kawai ke fita yana ratsa kunnuwa da zuciyarsa,duk sanda take kuka irin wannan
wannan kukan nata na quruciya yake tunawa,wanann kukan data dinga yi masa sanda ya karbe jaririn
budurcinta da bai gama cika ba

"Me kikeso?" Ya tambayeta calmly don bai qaunar kukan

"Ka maidani....."
"Ya isa.....muje" ya fadi a taqaice yana miqewa. Tsam ta miqe itama,cikin jin nauyi da kuma jin tur da
abinda ya faru ta tsinci kayanta da suke d'ai d'ai cikin dakin. Jikinta ba qwari ta maida scarf dinta saman
kai,ta lalubo hand bag dinta da sauran tarkacen agogo da dankunnenta da ya ciresu daya bayan daya ba
tare ma da yasan yayi ba. Dukka bata da lokacin maidasu jikinta,don haka ta tattarasu ta watsa cikin
jakar,ta xura takalminta tayi tsaye a bakin qofa tana jiransa,kamar wadda za'a ce ket ta zura da gudu

A nutse ya isa wajen saqale suit,suit dinnasa ya dauka ya maidasu jikinsa,ya gyara musu zama sosai
a jikinsa,ya tsaya gaban mirror din dake saqale a kusurwar office din saman dressing table ya dauki comb
yana gyara hair style dinsa. Cikin second goma ya koma tsaf abinsa,tana tsaye tana satar kallonsa,cikin
ranta tana gulmarsa sanda yake daura agogon hannunsa saman lafiyayyar fatarsa me wadatar gargasa

"Har yanzun wanann shegen iyayin da gwallin kamar mace yana nan" ta fadi a ranta tana tuna sanda
yana maina dinsa,dan jami'a cikin jami'ar niamy,yama akayi ne ya zama likitan zuciya?,bayan ya taso a
matsayin soja kuma likita?.

Murmushi me sanyi ya saki ta gefen bakinsa yana daura agogon,ya kamata sosai tana satar
kallonshi amma ita din bata sani ba,sai ya kauda kai har sai daya gama daura agogon nasa sannan yadan
yardar da hannunsa yana cewa

"Idan baki qoshi da kallona din ba...... ni ba sauri nakeyi ba,mu zauna ki qarasa saimu wuce", mugun
firgita tayi dataji ya fadi hakan,ta wani basar tana juya masa baya,ko zata yarda da kowanne sharri nasa
amma banda wannan,bakinta ta murguda cikin jin haushin me zata kalla?.

"Allah ya sawwaqe,me zan kalla?"

"To ni na sani ne?,kinsan ance tsakanin miji da mata ai sai Allah ko?,na sani ko kewar......." Kaman tasan
me zaya fada tayi hanzarin tararsa da fadin

"Pleeeeassseee......." Tana dora hannunta saman kunnenta gami da runtse idonta da kyau. Tilas siririyar
dariya ta kubce masa,ya dauki wayarta data manta ya fara takowa har ya iso bakin qofar,sai yasa dukka
hannunsa saman kafadarta yadan matsar da ita gefe,ya zura hannunsa cikin Jakarta ya ajjiye mata wayar
sannan ya zura key din daya lalubo yana bude qofar,dukka idanunsa bisa fuskarta yana hango yan
qananun kamanni tsakaninta da su batoul can qasa qasa,yayin da idanun nata suke a rufe,amma kuma
tana iya feeling idanun nasa cikin jikinta.

Nishadi yakeji sosai cikin ransa tare da wani energy cikin jikinsa,don haka ya saka slow music
dake tashi da wani sassanyan sarewa,wannan ya taimaka qwarai wajen kashe mata jiki,tayi relaxing sosai
jikin kujerar tana aje numfashi,qamshinsa da takeji duka ya buwayi hancinta,ko ina na jikinta idan ta
motsa qamshinsa yake bata.

Idanunta a rufe saidai batasan inda suka nufa ba,tadai dauka zaya kaita ne TV station din. Duk
bayan wasu mintuna sai ya juya yadan kalleta,hira yakeso suyi koda fada ne,koda tsonakarta yayi amma
kuma yadda ta tsume din yasan ba zatayi magana ba,don haka yana sane ya dauke kan motar zuwa
babban titin dake da yawaitar shops a wajen.

Daya daga cikin shop din da yafi siyayya a ciki ya tsaida motar,sai a sanann ta bude fararen
idanunta a hankali,ta zauna sosai tana duban wajen,sai taji zuciyarta na narkewa. Da gasken yake bazai
kaita ba,kalaman bakinta dukka ya qarar dasu,batasan ta yadda ma zata fara roqarsa ba.

Dubansa tayi sanda ya zagayo ya miqa mata hannunshi.

"Koda sau daya ya kamata mu siya gift na birthday din su benazeer tare......ko don farincikinsu......na
tabbatar zasuji dadi" kanta ta kawar gefe,kaman ba zata ce komai ba,kaman kuma ba zata motsa ba,sai
kuma ta juya a hankali ta zura qafafunta waje yasa hannunsa ya riqe hannun data hanashin

"Kada ki zama marowaciya mana......i need these soft hands" ya furta yana laluban hannayenta ya
matsesu gam cikin nashi.

Babban shop ne da suke saida kowanne irin nau'inkan kaya da suka shafi yara. Kaya masu kyau
da daukan hankali. Sukayi tsaye a bangaren chocolates yana goye da hannayensa bayan ya zame
hannunsa daga nata a nutse
"For the first time daddy da mommy zasuyiwa yaransu siyayya" ya fadi yana kashe mata ido gami da
dage mata gira guda daya. Kanta ta kawar gefe tana jin wani iri,kalmar daddy da mommy din tana mata
girma da yawa. A tausashe yaja hannunta

"Oya.....choisissez la bonne chose pour eux(zabar musu abinda ya dace)" ya fadi yana daukan cart. Dole
ta fara takawa tana duba kayan.

Dab da dab yake da ita,kusan ko cikakken taku daya babu na tazara a tsakaninsu,yana bibiye da
ita. Duk sanda jikinsa ya gogi nata sai taji wani iri,shikam kamar ma ko a jikinsa ko kuma da gayya yakeyi
ne bata sani ba. Duk sai ya nemi sukurkuta nutsuwarta,har ta dinga zaben wasu abubuwan ba dai dai ba

"Huta kawai,suis-moi(biyo ni)" komawa baya tayi tana biye dashi,tana noticing nasa komai zai dauka me
tsada ne,komai nasa me kyau yake zaba hakanan wanda yake bada kala da nutsatstsen nau'i,hakanan
komai ya dauka din sai taji yayi mata dari bisa dari,batasan dalili ba,ko har yanzu wannan chemistry din
dake tsakaninsu yana nan?,don ko a baya kusan zabinsu akan komai daya ne.

A karan kanta taga siyayyar ta fara yawa,amma kuma batason masa magana kan hakan. Sanda
ya fara jidar musu turare saita koma baya kawai ta zubawa sarautar Allah Ido

"Ba abinda yaran suka rasa,wannan abun kamar almubazzaranci ne ai" cart na uku daya cika ya saki ya
waiwayo,sai suka hada idanu

"Bance kice komai ba,m'as-tu entendu?(kinji ni?" Ya furta da sigar seriousness cikin maganarsa

"Nima shishshigi na" ta fadi can qasan zuciyarta tana dauke kanta. Murmushi kawai ya saki,yasan taji
haushi ne da tsaidatan da yayi,baya jin ko meye zai kashewa yaran zai biya zai kuma sauke haqqinsu
dake kanshi,a dukka tsahon shekarun yana jin kamar ya dawo dasu yayita hidima musu ita dasu din gaba
daya.

Kusan awa guda suka kashe cikin shop din,suka kuma cika bot din motar da siyayya me yawan
gaske.
Sake zubawa sarautar Allah ido ta sakeyi sanda suka dauki hanya,saidai ga mamakinta TV
station Street ya hau. Batace masa uffan ba tana jira taga me zayayi,sannu a hankali sai gasu cikin
harabar gidan,ya samu parking lot ya tsaida motar,ya kasheta ya waiwayo yana dubanta

"Kije ki dauki excuse" maganar yadan bata mamaki. Yadda take kallonsa ya tabbatar masa tana da
buqatar qarin bayani,sai ya dage mata dukka girarsa

"Wannan shine adalcin kawai da zan iyayi miki,kada ki wuce mintuna sha biyar......." Ya fadi yana duba
agogon hannunsa kana ya dauke dubansa daga kanta kaman baiga kallon zallar mamakinsa da take
jifansa dashi ba

"vous perdez votre temps(kina bata lokacinki)" ya fadi still ba tare daya dubeta ba.

Ba sanin jiya ko yau tayi masa ba,hakanan a sanin yau dinma wasu sabbin halaye da kuma
dabi'u yake fitarwa,kulashi din tamkar baiwa kanta horo ne kaman yadda ya alqawarta mata,dole ta
bude murfin motar tana fushi tana kumburi ta fice,saidai kuma itama zata d'ana masa,wannan mulkin
mallakar da yakeyi mata ba zata bari ba.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/9, 8:52 PM] +234 803 546 4710: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 92

Minti goma kacal ta dawo,fuskarta a dan daure,don gaba daya abinda aka tsara zasuyi a yau din
yayi silar rushewarsa,sai uzurin tana da maras lafiya ta basu.

Qofar motar na bude don haka yayi tsammanin shigowarta,maimakon haka sai yaga ta cake
daga bakin qofa. Tana da yaqinin yanzun haka gida zaice zai kaita,ita kuma ba zata taba lamunta a gansu
tare ba kaman yadda aka gansu a nijer,idan aka gansun tare wanne sauran dalili gareta?,me zata cewa
ama ko aba?, infact ma ita batason kowa cikinsu ya ganta dashi.

"Excuse me.......baki gaji da zaman Tv station din bane?" Ya tambayeta cikin zolaya ta window din motar

"Let's go......lokaci yana qurewa.....na tabbatar batoul zasuyi kewanki if kika je musu late"

"A motata zan koma gida tunda a ita na fito" ta fadi tana basarwa. Dan nazarinta yayi na wasu daqiqu,sai
ya amsa da

"Is okay,yayi" yana buda murfin motar ya fito. Wayarsa ya ciro daga aljihu bayan ya haye bayan
motar,yakuma yi magana da bata wuce ta minti daya ba kacal sannan ya kashe ya maida wayar
aljihunsa. Baice mata komai ba ya fidda daya wayar tashi yana latsawa,ba'a cika mintuna ba babban
qofar station din ya bude motarta ta shigo.
Motar tabi da kallo tana mamaki,sam ita ta manta ma da batun motar tunda tsoro ya kamata a
lokacin. A nutse ya sauka daga motar ya doshi farin bafaransen da ya fito daga motar. Key ya karba daga
hannunsa ya miqa masa wani key din,sannan ya juya a nutse ya dubeta

"Bismillah" ya fadi yana bude mata front seat. Idanunsu suka hadu waje daya,ya zuba mata ido yana
sauke mata nannauyan kallo da idanunsa. Zare idanunta tayi daga kansa,lallai sai qafarta qafarsa?,ta
yaya zata musa masa?,bata sani ba,don haka dole ta sauke hannuwanta ta soma takawa a nutse tana
nufar motar.

Da wani sassanyan kallo yake qarewa takunta kallo,komai nata a nutse kamar ba baby
sultanarshi gwanar rawar kai ba,komai nata ya canza,yana hangen tasirin fushi kadan kadan daga can
tsakiyar idanunta,withtime zai wanke komai daga cikin zuciyarta kamar komai bai faru ba,yana sanya ran
hakan in sha Allah.

Maida murfin yayi ya rufe,sannan ya zagaya seat din driver ya shiga,ya kunna motar amma bai
tasheta ba,ta mirror tana iya hangen yadda suke debo kayan suna maidawa boot din tata motar.

Sai da suka kammala sannan yayi bismillah,ya tayar da motar a nutse suka fice daga gurin.

Daga can farkon street din nasu ya gangara gefe a hankali ya ajiye motar,ya juya barin da take
zaune din yana jifanta da wani sassanyan kallo. Cikin jikinta take jin dukka idanun nasa,amma qemene
taqi dubansa,har sai da wayarsa dake ajiye a tsakiyarsu ta kada.

Kaman an fusgi hankalinta ta juyo da dan hanzari,sunan AYANA shi yake yawo kan screen din.
Sai daya gama qarewa sunan kallo sannan ya miqa hannu ya kashe sound din ya maida wayar
silent,sannan a hankali ya maida idanunsa kanta. Sabanin daxun yanxun waje take kalla ta window din
motar. Sai kuma ta sanya hannu ta bude motar tana ficewa daga ciki ba tare data bari yaga fuskarta ba.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*
*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*
09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/9, 9:35 PM] +234 803 066 5772: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 93

Ayana ce,ya saki qaramin murmushi saboda kiran yazo masa a dai dai.

Da muryar nan tasa dake matuqar tafiya da ita yayi mata sallama,ta amsa cikin zumudi da kuma
karadin nan nata

"Yaa maina......ba call ba tex,why na?"

"Munyi wannan dake?" Ya tambayeta a dake,don ya fahimci rawan kanta yayi mugun yawa. Yayi imani
bata sanshi bane a baya da duka batayi irin wannan abun da takeyi yanzu ba

"Nooo...." Ta fada murya a karye tana karyar da wuya


"I think zan samu kulawa tun yanzu,coz next week in sha Allah Ina tahowa nan,zakuyi magana da
daddy,naji kaman yace ba cikin school zan zauna ba"

"Alright..... yayi,karbi nan" yace da suhail yana kallonsa.

"Karbi mana,maza ka tayata hira,she's my sister also" ya fada yana cin serious kaman wani abbansa.
Dariya tasi kama suhail din,sai kawai yasa hannu ya karba wayar,maina din kuma ya juya zai shige ciki.

"Kunyi magana ne da laila?,tacemin cikin satinnan zata shigo Paris,tanason zuwa ta gaidaka......tayi
missing naka,I was surprised da kalamanta,ina ji a jikina anya ba wani abu a boye?" Tsaiwa yayi cak
sannan ya juyo yana duban sardauna,kalaman zuwan ayana da zuwan laila suna masa yawo saman kai

"Did she tell you something?" Ya tambayi sardauna,kai ya girgiza yana tabe baki

"No.....kawai yadda take bawa komai naka muhimmanci ne yasa na saka ayar tambaya" murmushi maina
yayi, sardauna yana da kara da alkunya,amma rashin maganatuwar laila ga kowa tsakanin daddy da
sardauna hakan ya masa,don fadi musun da zatayi tamkar ta masa wani dabaibayi ne

"Kada kayi mata shishshigi to malam ka turata ga abinda ba shine zabinta ba.....wataqila akwai wani a
boye cikin rayuwarta" kai sardauna ya girgiza sai maina yaci gaba da wucewa ciki

"Kada ka jima a wankan nan naka,don akwai gurin da zamuje" sardauna ya fadi

"In sha Allah" ya amsa musu a gajarce.

Sama sama ta dinga jin hayaniya da kuma knocking duka lokaci guda,nauyin baccin da tayi ya
bata mamaki,taja lokaci sosai,amma kuma ba abun mamaki bane saboda ita kanta tasan gajiya ce sosai a
jikinta. Dankwalinta ta dauka ta daura sannan ta sauko daga saman gadon,tasa hannu ta murza key din
ta bude qofar ta jawota baya.

Benazeer ce da batoul sanye da fararen singlet da gajeran pant,da alama shiri ake musu na
birthday din,don gyaran gashin dake kansu kadai ya gaya mata hakan.

Dukkansu ita suke kallo ba wanda yayi magana a cikinsu,tadan fiddo idanu waje tana dubansu

"What's happening?" Tayi maganar da muryar bacci,cikin idanunsu take kalla,sai take ganin idanun nasu
tamkar na maina

"Mommy an kusa a fara fa.....mummy baki shirya ba" benazeer ta fadi a shagwabe

"Bacci nayi yanzun zan fito,shikenan?" Kai suka gyada a tare

"Yes mummy" kasa maida qofar tayi ta rufe har suka wuce,girma yaran sukeyi sosai,idan ka gansu zakayi
tsammanin sun girmi shekarunsu. Da kadan da kadan wasu abubuwan nasu suke juyewa zuwa na
babansu. Shape din idanunsun sak irin nasa lion eyes din data sakawa suna,data kalli qafafunsu kuma
yanzun sai ta sake gani tamkar nashi

"Ya akayi har kika haddace qafarsa?" Wata zuciyar ta tuhumeta,sai taja tsaki tana jin haushin kanta da
kanta,don itama bata san ya akayi hakan ya faru ba,ta maida qofar ta kulle ta taka tana komawa
ciki,sannan tazarce direct zuwa toilet.

Ruwa ta hada me yawa ta hada me yawa tayi wanka,ta gasa jikinta da kyau da ruwa me dumi
sosai,sai taji dama dama,gabbanta suka saki ciwon da take danji ya ragu.

A nutse ta zauna ta soma shiryawa gaban madubi,haka kawai yau din taji tana sha'awar shiga
party din yaran wanda tsahon shekarun da aka dauka ana celebrating birthday din nasu bata taba wani
daukan abun da muhimmanci ba. Kafin ta kammala sun mata knocking ya kusa sau uku.
Atamfa taji tana sha'awar sanyawa,wanda ta jima sosai rabonta da ita. Ta bude Wardrobe dinta
ta tsaya tsaf tana qarewa kayan kallo kafin daga bisani ta jawo wata straight gown ta atamfa da aka yiwa
adon shawbrosky tun daga samanta har qasa. Dinkin ya zauna mata das a jikinta,hakanan kalar atamfar
ta haskata ainun,don data gama ta dora dankwalin saman kanta zakayi tsammanin daga maqwafciyar
qasar take. Sosai qirar jikinta ta fita,shape dinta dukka ya gama fita,ita kanta data kalli kanta a mudubi
saida shigar ta qayatar da ita. Duk wani salon ado da sanya atamfa zamanta da ama ya sanya ta iyashi,ba
zata iya qididdige yawan adadin abubuwan data koya wajen ama ba.

Har zata sanya qaramin mayafinta saita fasa,haka kawai taji idan ta saka mayafin kamar ta bata
adonta,yau daya tanason ta sake sosai cikin yaran,tana jin cewa idan batayi da gaske ba tsaf aliyyu zai iya
janye mata yara,yanayin yadda taga suna maqale masa da yadda suke yawaita zancansa har basa
maganarta kamar haka.

Baqanqe plate shoe da suka haskaka fatar qafarta ta saka,ta shafe jikinta da tsadajjen
perfume dinta sannan ta dauki wayarta tana fita zuwa falon da take jiyo 'yan qananun hayaniya da
tashin kida maras qarfi da yawa.

"Wow,ma sha Allah" ta fadi cikin ranta,irin yadda akayi decorating parlor din dole ya burgeka,ba zaka
taba tsammanin cikin parlor din bane. Idanunta akansu benazeer,wani irin ado akayi musu irin na
larabawa,takanas ama ta dauko matar ita ta shiryasu.

Uwa me dadi,duk jama'ar gurin amma haka suka tattare gown din suka nufota,ta durqusa tana
murmushi gami da bude hannayenta tana jiran isowarsu,daidai lokacin stella maqociyarsu 'yar asalin
qasar england ta bude qofar falon da akayi qaraurawa,ya sanyo qafarsa cikin falon sanye da trouser din
da baqar shirt wadda ta fidda ainihin hasken fatarsa me cakude da sirkin jaja jaja.

Ita ya fara hangowa kaman yadda itama nata idanun a kanshi suka fara sauka. Ita ta fara dauke
kai sai shima ya dauke nashi kan tamkar ma a wunin ranar ba qani abu saya sake hadasu baya ga
gaisuwar da sukayi da safiya.

Zamewa sukayi daga jikinta sanda suka hangoshi yana takowa zuwa cikin falon da tsahon nan
nasa dake cakude da murjajjen jiki da ya zamewa tsahon nasa ado sosai. Idan ka kirashi dogon namiji kai
tsaye bakayi kuskure ba,sumarshi ta zauna sosai a kanshi tana ta qyalli. Kai tsaye ya wuce wajen ama
dake zaune guri dayayayin da benazeer da batoul ke rige rigen isowa wajensa don sun ganshi ne a
bazata,basu taba tunanin da gasken zaizo ba kamar yadda uncle goumar ya gaya musu.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank
_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/9, 9:38 PM] +234 803 066 5772: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 94

Sosai ya zauna daidai qafafun ama kamar zai shige cikinta ko kuma qanqanin yaro,irin wannan
zaman a baya yakeyi a gaban ama din,yana kuma matuqar jin kewar yin hakan duk sanda ya tuna.
"Barka da warhaka ama" ya fadi sanda ya zauna daidai, batoul da benazeer kuma suka haye jikinsa suna
masa hayaniya.

"Barka kade,mun yini lafiya?" Ta amsa masa da dan sakewa har abun ya sake sanya zuciyarsa yin fari.

"Alhamdulillah,ya fama da yara?" Ya furta yana kallonsu benazeer daketa cusa masa alawa a hannu da
baki

"Alhamdulillah" ta fada a nutse tana duban fuskarsa,sam sai yaqi yarda ya kalli aman saboda tambayar
tata da yayi shi kansa yasan tana da nauyi,to amma ya quduri aniyar gyaran komai ne shi yasa ya shirya
fara tunkarar gyaran.

Cikin yaran ta shige abinta tana fama dasu,ta fidda wayarta tana musu hotuna da qananun
videos gaban manyan cakes dake dauke da hotunan su benazeer da batoul din. Kallo daya tak zakasan
cake din ya lashi kudi,duk daya hawa shida gareshi.

A zahiri yana fama ne da qiriniyarsu batoul,wanda tunda suka ganshi sukaqi komawa wajen
baqinsu,sun cikashi da tambaye tambaye

"Daddy ashe zakazo...... Daddy mummy ce tayi inviting dinka?,daddy munyi missing dinka......har uncle
goumar ma muka gayawa,yace mana dama zakazo" ya biye musu sosai,duk gift din da suka karbo shi
suke kawowa yana ajjiye musu,saidai kuma fiye da rabin hankalinsa yana kanta.

Duk wani motsi nata idanunsa yana kai,wani shauqi ke fusgar zuciyarsa,duk sanda ta gilmashi
sai yaji kaman ya jawota zuwa jikinsa yayi mata kyakkyawar runguma. Bugun zuciyarsa yana qaruwa
haka idanunsa ke sake qanqancewa......baisan me yakeji me zafi haka tattare da ita ba,baisan wanne irin
maganadisu ne yake janshi a kanta ba,kamar ba dazu dazu suka kasance tare da juna ba,har sai daya fara
tilastawa kanshi qoqarin controlling abinda yakeji game da ita.

Komai tana yine bisa dakiya da dauriya,don batason barin wajen kota sauya abinda tayi niyya
don kada ya dauka saboda shi ne,wannan ya sanya yadda ya bagarar da ita itama sai ta bagarar dashi
kamar bata ganshi ba ko batasan da wanzuwarsa a wajen ba,saidai kuma can qasan ranta batasan me
yasa takejin haushin yadda ya wani basar ba,kamar bai ganta ba,kamar kuma baisan da ita a wajen
ba,kamar ba dazunnan ya gama jagwalgwalata kaman tsohon maye ba?. Amsar da zuciyarta ta bata
raina mata wayon da yayi yana pretending ma duniya kaman ba komai tsakaninsu shine abinda yafi bata
haushin.

"Meye naki don ya nuna haka?,dama haka kikeso ai yaci gaba dayin walau a zahiri ko a badini ko?" Wani
sashe na zuciyarta ya bata amsa,sai taja qaramin tsaki,tana jin ba wannan tunanin ya kamata tayi
ba,tunanin yadda zata fita aikinta gobe hankali kwance ba tare data hadu dashi ba shi ya kamata ya
dameta,ta sake jan wani tsakin still dai sanda take gyara ma wata yarinya 'yar qasan Bangladesh gashinta
da ya kwance daga jikin ribbon saboda santsi.

"Lokaci yayi" maman yarinyar ta furta da yaren France tana kallon ama tana murmushi

"To bismillah,ni 'yar kallo ce ai,na gama nawa aikin" ama ta maidawa matar amsa. Duka duka ayeesha ba
zata haura shekarun haidar ba,amma jininsu ya hadu sosai da ama,kaf neighbor's dinsu su sukafi
mu'amala da juna

"Ku taso birthday girls" ayeesha ta fada tana murmushi gami da kallon su benazeer da suketa dabdalarsu
akan maina.

Gyara daurin igiyar straight gown dinta takeyi tana tsaye daga tsakiyar yaran,eye glasses din
data mannawa idanunta ya qara fidda sirrin kyanta. A hankali ta waiwaya wai taga ko su benazeer din
sun taso,sai idanunsu suka shiga cikin na juna. Cikin wani irin salon ya kafe idanun nata a cikin nasa yana
aike mata da saqo ta nan inda yake zaunen,duk yadda taso ta janye idanun nata ta kasa,har sai daya
tabbatar bugun zuciyarta ya qaru yadda yakeso,sannan ya sake mata wani shu'umin murmushi yana
dauke kallonsa daga kanta.

Dole ta koma baya ta zauna a hankali saboda wata kasala daya sake mata,kanta ta dan dafe
kadan tana ayyana

"Mugu" cikin ranta. Da shigen kallon yake punishing dinsu a gida tun yana yaa maina,dan makaranta,yaa
maina me shekarun da basu rufa talatin ba. Dauke hannun tayi da sauri sanda ta tuna yana dai
falon,batason ya karanci lagonta,saidai still ta sake kamashi yana mata wannan mayen kallon nasa.
Wanann karon bata bari ya riqeta ba ta janye dubanta da sauri, murmushi ya kubce masa wanda
iyakarsa saman labbansa

"Inda kin isa ki tsaya mana kici gaba da kallon nawa ki gani idan ban saki kin magantu a gaban kowa ba"
ya fadi daga can qasar zuciyarsa. Yasan dukkan wani salo ko lago da zai iya kamata red handed ta
kowanne fanni da yake da buqata,to amma kuma yana daga mata qafa ne saboda yanason ya dafata
yadda ya kamata.

A sace take kallon kowa dake falon,ba wanda ya lura da abinda yakeyi din,wannan ya sanya
taja numfashi da kyau ta furta sannan ta miqe tana zare glass din idanunta. Idan ma yazo ne don ya
hanata sakewa itakam ba zata lamunci haka ba,don itama bata shiga rayuwarsa ba na meye xai shiga
tata.

Cikin mintuna gurin ya dauki saiti yadda ya kamata,'yan abubuwan da ayeesha ta tsara saboda
yara a wajen qananun games dukka akayi aka gama,sai aka fara karban gift,sai a sannan ya fidda wayarsa
yayi kira duka duka da baikai na second biyar ba.

Ba jimawa akayi knocking,da kanshi ya miqe ya bude. Ma'aikata ne na wani kamfanin sarrafa
kayan qarau da kayan yara sanye da rigunan wajen aikinsun suka fara shigowa da kwalaye suna jerawa,a
sannu a sannu saiga kwalaye sun kusa guda ashirin suka kammala suka juya suka fice. Ama na daga
zaune tana kallo komai amma batace komai din ba,kuma bata motsa ba,ya juyo suka hada idanu da ita
saita kau da kai,batason yaci gaba da karya mata da kuma tsinka mata zuciya,soyayyar yaran da take
gani cikin idanunsu har kamar ma taso tafi qarfin kalar soyayyar da su suka gwada masa sanda yana
yaro.

"voici un cadeau de papa(ga kyauta daga baba)" ya fadi yana duban yaran. Sai da suka kalli ama sanna
suka kalleshi,kaman hadin baki suka rungumeshi dukka su biyun suna fadin

"Merci papa" tattaresu yayi cikin jikinsa yana sauke boyayyara ajiyar zuciya,bayajin duk duniya akwai me
iya fahimtar yadda yake son yaran.
Tsbaar zumudi sai suka kasa jira,dukka aka tattaru wajen bude kwalayen. Sutturu ne kala kala
daga manyan kamfanin kaya na duniya dake samar da kayan yara designers masu quality da tsada.
Kamfanin da ama din kawai ta gani ya sanya ta jinijina abun,ita din uwace me fahimtar yaren d'a koda
bada harshen dake furta kalma yayi maganar ba. Ita din 'yar kasuwa ce da kusan kowanne kaya ta gani
tasan a wanne aji yake,ko ba tare sukayi siyayyan ba amma ta sani kudade ya kashewa yaran masu ciwo.

Kowanne kwali da abinda ya qunsa,na sutturu takalma kayan kitso agoguna da sauransu
kowanne kwali goma goma benazeer din da batoul.

A nutse ta dan juya idanunta tana satar kallon sultana,a guri daya take zaune sam bata cikin
sahun masu kallon gift din.

"Sultana" ama ta kira sunanta,ta dauke idanunta daga wayarta da take latsawa tana duban ama din

"Na'am ama" gauraya idanunsu sukayi waje daya,haka kawai sultana din taji nauyi yadan kamata

"Ki duba kitchen an kawo order na abinda za'a ci,ki dinga shirya komai yadda za'a iya dauka ayeesha ta
tayaki fitowa dasu,kallon gift dinnan bazaiyiwu a gamashi a lokaci qanqani haka ba"

"Okay" ta amsawa ama din tana qoqarin ajjiye wayarta.

Duk da dukka kalamanta cikin gajerun furuci ne amma hakan bai hanashi hango kyawun
labbanta ba,kwadayinsu ya kamashi har sai daya hadiye yawu a bakinsa a hankali. Ta fara wucewa zuwa
kitchen,yadda tayin yasan hali,zai wuya ta basu gift din daya cika mata bayan mota dashi. Murmushi ya
saki a boye,idan tasan wata batasan wata ba ai.

Duqawa yayi a nutse daidai saitin kunnen benazeer ya gaya mata wani abu,ta daga kai da sauri
tana fidda idanu waje
"Good daddy....." Bata qara minti daya bama ta daga murya duk da slow music din dake falon amma
saida sautinta ya fito saboda zazzaqar murya gareta

"Mummy...... Ina gift namu?" Cak ta tsaya sannan ta waiwayo tana bakin qoqarin hana idanunta kallon
fuskarsa,don tasan saitin bigiren da yake tsaye,ta fidda fararen idanunta waje da kyau tana duban
benazeer yayin da takejin idanunsa na yawo saman fuskarta amma ta share

"wanne gift?" Ta tambayi yarinyar tana kallonsu duka ita da batoul da suka zuba mata idanu,kai ta karyar

"Ki tuna dai mummy.....na dazu fa.....daddy yace kin saya mana da yawa" dole a sanann ta kalleshin ba
don taso ba. Kwata kwata kaman baya wajen ma,don ya maida dukka hankalinsa akan wayarsa ne
kaman baiji me benazeer ma ta fada ba. Kafeshi tayi da kallo waiko zayaji a jikinsa ya daga kanshi,amma
sai taga ma ya sake gyara zamansa yana bawa wayar hankalinsa.

Duk qiftawar idanunta a kanshi yana ji a jikinsa,saidai ya basar din kaman baisan me yake
faruwa ba,saima ya fara sakin qaramin murmushi still fuskarsa nakan wayar.

Haka kawai taji ranta yadan sosu,tayi imani ba yadda za'a yi ta kalleshi jar hakan baiji a jikinsa
ba,yana daya daga cikun abinda ta haddace sanda suna 'ya'yan bibi,tana tashen jin takai matsayin
sultana,yana jin hakai aliyyu haidar dinsa. Yasha cewa saiya tsone mata idanu,don a sannan tana da
dabi'ar tsureshi da kallo a duk sanda tayi laifi

"Dauken wadannan idanun magen naki a gun!" Saboda tsaban yadda yake damunta da fadin hakan sai
da takai duk magen data gani saita tsaya ta qarema idanunta kallo,tanason taga wanne irin idanu ne da
ita haka da yake goranta mata dasu,wannan ya sanya itama ya baida qaimi wajen kiransa da

"Me idanun zakuna" tun baisan tana fadi ba har sunan yazo kunnenshi,a ranar tasha horo sosai,amma
maimakon ta daina saima ta sake maida kai wajen kiranshi da hakan,sunan da duk gidan ita daya ke
fadinsa.

"Laila" sunan ya fado mata a rai,taja qaramin tsaki zuciyarta na raya mata qilan dasu yake chart
"Sai me?" Ta tambayi kanta,shi yaga zaya iya

"Amma yana cikin yaranshi suna hidima me muhimmanci a wajensu?" Wani sashe na zuciyarta ya furta.
Ranta ta sakejin ya quntata da taga yana gyara Bluetooth din kunnensa da alama kiran waya ne ya shigo
masa

"Ta yiwu ayana ko laila ce" can wani bangare na zuciyarta ya sake fadi

"Sai meye ne?" Ta sake gayawa kanta a tsawacen da sai da taja numfashi ta daidaita kanta.

"Bansan suna ciki ba.....idan na gama abinda nakeyi na baku key kuje ku dauka" ta fada tana juyawa
ranta na mata wani zafin da batasan dalili ba tana wucewa hanyar kitchen din.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800
UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/10, 10:18 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*


*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 95

Boyayyan murmushi ya saki yana satan kallonta ta qasan idanunsa,salon kallon da duk qwqwarka
ba zaka taba zaton ita din yake kalla ba,yadan cije lips dinsa na qasa sannan ya buda muryarsa cikin
qasaitar nan tasa data jima bata jita ba ya kira sunanta

"Sulthana" har inda take sautin ya isketa,ya riski kunnenta da wani irin amo daya sanya tsigar jikinta
tashi,duk yadda taso ta qaryata kunnuwanta dake jin zaqin sunan a bakinsa amma hakan ya kasa gamsar
da zuciyarta.

Kamar kada ta tsaya ko kuma kada ta juyo,to amma cikin jikinta tana ji ama tana ankare da
komai,don haka ya tsaya sannan ta juyo tana dauke fararen idanunta daga kanshi

"take the keys and bring them the gifts" ya fadi da muryar bada umarni nakai tsaye muryarsa a dake da
wani irin deepness me tsayawa a zuciyar wanda ake bawa saqo.

Idanunta dake da yalwar eyelash ta lumshe sannan kuma ta budesu,abinda yayi matuqar yi
masa kyau,sai suka zama tamkar wani ado na musamman saman fuskarta,ya janye dubansa daga gareta
yana sake hade rai,hade ran daya fidda ainihin miskilancinsa da ta sanshi dashi na asali. Juyawa tayi tana
guna guni cikin ranta ta nufi dakinta. Saman bedside drawer ta dauko key din,har ta isa qofa ta fasa,ta
dawo da baya saboda tuna wani abu da tayi,ta bude Wardrobe dinta ta fidda mayafi medium dake da
kauri ta lulluba saman kanta. Sosai mayafin ya sake qara mata kwarjini,ya kuma cikasa kwalliyata,ta fita
sosai da kamanninta.

Tana takowa waje tana wara maqullan tana laluba na motar,har yanzun mita takeyi qasan
ranta. A saman idanunsa ta fito daga dakin,ya saki wata siririyar ajiyar zuciya,mayafin data sanya din ya
masa dadi sosai,bai tsammaci zata saka din ba,sai gashi ta rufe jikinta yadda ya kamata.
Ratasu tayi a nutse har ta fice daga falon,ta maida qofar ta sakayata. Numfashi ya kuma
ajewa,sai kuma yayi saurin daidaita kansa don ya tuna a inda yake,ya dan juya sashen ama,basu hada
idanu ba amma kuma yaga sanda take maida dubanta wani guri na daban. Haka kawai jikinsa ya bashi
duk abinda yakeyi din ta ganshi,sai ya danji nauyi ya kamashi,don haka ya miqe,idan ya fita waje tamkar
ya bita ne,don haka kawai sau ya wuce kitchen yana cewa

"Bari na samo ruwa" batace masa komai ba don nunawa tayi ma kaman bata ganshi ba,ya miqe zuwa
kitchen din yana dan shafa sumarsa kunya na tabashi.

Tana tsaka da mitarta sanda take bude motar taji muryarsa. Goumar ne,ta juya tana kallonsa,da
alama a gurguje yake saboda yadda yake tafiyan da sassarfa

"Mommyn twins me za'a dauko mana ne?" Ya furta cikin tsokana. Harara ta watsa masa sannan ta juya
tana jefa masa key

"Sarkin bin qwaqwqwafi......ka bude boot ka tayani mu kwashe kayan ciki"

"Angama matar babban yaaya" ya kirata da sunan daya jima bai kirata din ba. Tayi tsammanin zataji
zafin nan da takeji cikin zuciyarta a baya idan ya kirata da wannan sunan,ta dauka zataji qunci a zuciyarta
kaman yadda takeji a wancan lokacin,sabanin hakan bataji wannan ba,saidai taji kaman furucinsa ya
taba zuciyarta,ta jefa masa harara tana cewa

"Wallahi yaa goumar ka bini a hankali,idan ba haka ba har najma ka shafa mata wallahi"

"Tuba mukeyi kar a hadamu da babban yaaya" ya fadi yana qyalqyalewa da dariya.

Shine ya taimaka mata tana fiddo kayan yana kwashewa har suka kammala tas. Kafin ta isa
falon benazeer da batoul sun cikashi da karadin murna. Yau mummynsu ta basu gifts din da bata taba
basu irinsu ba. Da gudu suka qaraso sanda take shigowa,suka rungumeta da kyau kaman yadda suka
yiwa maina
"Mommy mun gode,thank you,thank you" yadda suka rungumeta din suna murna sai taji wani abu me
sanyi yana sauka qasan zuciyarta,ta miqa hannunta ta dora a hankali saman sassalkan gashinsu da yasha
gyara

"Allah yayi muku albarka" ta samu kanta da furtawa zuciyarta tana motsawa.

Ajiyar zuciya ama ta sauke tana jin wani alfahari da iyalan nata yana kamata,tayi qas da kanta
tana yawaita addu'a cikin zuciyarta a kansu gaba daya

"Mummyn twins ina tunanin saidai ki fiddo abincin nan,idan nabar yaran nan a wajen nan barna zasuyi
mana" ayeesha dake tsakiyar yaran ta fadi. Juyawa sultana tayi,sai tadan saki murmushi tana gyadawa
ayeesha kai ta wuce zuwa kitchen din.

Yana saman freezer dake daga bakin qofa,duk me shigowa babu lallai ya lura dashi, musamman
idan hankalinsa bai wajen. Apple ce a hannunsa yake gutsira a hankali yana jefa qafafunsa tamkar
qaramin yaro, nishadi yakeji sosai har cikin ransa. Fes ya ganta lokacin data shigo din,amma sai yayi biris
ya kuma sake rage motsinsa don kada ta ankara dashi a wajen.

Idanunshi a kanta sanda ta zare mayafinta ta ajjiye, murmushi ya kufce masa jin tana qananun
mitoci

"Yanzu zanyi maganinta" ya fadi cikin ransa yana ajjiye apple din a gefen freezer din sannan ya sauka
daga saman nashi a hankali ba tare da sautin takun sawayensa ya fita ba saboda socks ne a qafarsa.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*
*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107
*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/10, 10:18 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 96

Cikin nutsuwa ya tsaya dab da bayanta,ya zura hannunsa saman ruwan cikinta ya jawota jikinsa
sosai ya adanata tsakiyar qirjinsa,don dukka tsahonta bata wuce tsakiyar qirjin nasa ba,wannan ya bata
damar samun kyakkyawan masauki cikin jikinsa.

A ba zata abun yazo mata,saidai kafin takai ga cewa komai ya Sanya hannu ya juyo da fuskarta
gefensa yana fadin

"Yarinyar nan har yanzu na fahimci sai a hankali,akwai sauran ladabtarwata......."

"Wai baka da wani punishment sai ta haka?" Ta fadi da sauri tana katsar numfashinsa,muryarta na nuna
zallar tsorota da tayi. Dole siririyar dariya ta kubce masa,a karon farko tsoro ya bayyana muraran cikin
muryarta,wannan shine abinda yakeson gani,wannan shine abinda yakeson fahimta dama tattare da ita
"Ashe da gaske horo na yana isa inda ya kamata yaje kenan" ya furta hakan yana dora hannunsa saman
dogon dokin wuyanta,sai ya fara neman hanya yana zarcewa qirjinta. Numfashinta yaso daukewa jin har
ya fara isa samansu,tayi caraf ta saka hannu ta riqe hannayen nasa tana cewa

"Ni ba tsoron......"

"Ba tsoron abun kikeyi ba?" Ya qarashe mata yana sanya hannunsa ya juyo da ita gaba daya suka koma
suna fuskantar juna.

Musayar numfashi suka shiga yi,idanunsu sarqe dana juna,ya sanya hannu yana jawota qugunta
cikin jikinsa sosai yana cewa

"Tunda ke jaruma ce a sake gwadawa mana........" Kai ta fara girgizawa tana dunqule hannunta saman
qirjinsa

"Ni......niwai......" Ta fara magana cikin in ina,don maganar Allah ta sani,shi din ba kanwar lasa bane,duk
da zuwa yanzun tana jin wani irin sauyi itama,saidai ba zata iya bari ya fahimta komai daga gareta
ba,don babu babban abun kunyar da yafi wannan.

Sanda hankalinta yake neman yin wani gefen yayi amfani da wannan damar ya zame hannun
nasa,bata ankara ba ta tsinci lallausan tafin hannun nasa a tsakiyar dukiyar fulanin nata. Abun yazo mata
a bazata don haka ta dan zabura,bata kuma shirya ba ta fada jikinsa gaba daya tana qanqameshi sosai
wai ko zata samu ya saketa. Ajiyar zuciya ta kubce masa,shi hakan data masa ya masa dadi sosai,sai
kawai ya tayata qanqamewa cikin faffadan qirjinnasa dake fidda sassanyan qamshin turare da wani irin
dumi da nutsuwa ta musamman.

"Na maimaita miki ko mutuwa tana tsoron idon mahaifi......ki sassauta min ko don ama....ko kina zaton
bata sona ne?" Ya jefa mata tambayar yana yamutsata da kyau. Ba tare data shirya ba ta saki wani
zazzafan hucin da siririyar qara,abinda ya qara masa shauqi kenan,ya saki murmushi qasan ransa yana
fadin
"Daya kenan"

"Ka sakeni please,kada wani ya shigo kasan dai gurine na jama'a"

"If not fa?"

"Zan kwarara maka ihu" ta fadi

"Ihu?,wow......abinda sai bada citta..... bismillah mana,kinga daga nan kin ragemin nauyin wahalar yiwa
mutane bayanin ina qaunar matata......ina sha'awarta...... inason kasancewa da ita.......ina buqatar........"

"Enough please....." Ta fada da wani irin tune saboda bala'in da yake kunna mata cikin jikinta,ga kuma
qarin kalamansa da suke matuqar mata nauyi.

"noooo please"shima ya fadi da narkakkiyar murya cikin salon kwaikwayon muryarta yana sake matsata
da kyau sake da sanyata cikin jikinta kamar me tsoron wani zai qwaceta daga gareshi.

Kansa ya soma qoqarin cusawa a tsakanin dukiyar fulanin nata,ba shiri ta riqe kanshi da
kyau,tanason roqonsa amma labbanta dake rawa sunqi bata wannan hadin kan.

Motsin tahowar da akeyi zuwa cikin kitchen din shine ya ceceta,ya saketa da hanzari yayi taku
biyu baya yana qoqarin daidaita mode dinsa,yayin da itama ta taka gaban sink tana qoqarin daidaita
numfashinta gami da gyara zaman rigar jikinta.

Dai dai sannnan ama ta qarasa shigowa kitchen din tana fadin

"Anya sultana?,meye ya tsaidaki haka?" Tayi maganar idanunta akan sultana dake qoqarin bude famfo
jikin sink din. Dan tsaiwa ama tayi tana kallonta,yadda hannayenta suke rawa sai abun ya bata mamaki.
A hankali kuma ta waiwaya bangaren hannun damanta saboda qamshin turarensa data shaqa. Suna
hada idanu sai ya juya yana yana shafa sumar kanshi a hankali,sai kuma ya taka a hankali yabi ta gefen
ama din yana fita daga kitchen din. Batace komai ba ko bayan ya fita din,saita dubi Sultanan

"Kiyi qoqari ki fiddo abincin don lokacin tashi ya kusa"

"Tohm" ta amsa muryarta a shaqe ba tare data yarda ta juya sun hada ido da ama din ba,itama saita
dauki ruwa kawai tana fita daga kitchen din ba tare da tabi ba'asin komai, jikinta dai ya bata akwai wata
a qasa.

Da qyar ta samu ta saita kanta ta fara fita da abincin,saidai duk fitar da zatayi bata taba yadda
su hada ido da ama,hasalima ko maina rin taqi duban sashen da yake,tasan dai kawai zai ja Mata zargine
a zuciyar aman,duk abubuwa da yakeyi din a waje basu isheshi ba,a cikin gida ma sai ya biyota yayi?.
Qwafa taja kadan, cikin ranta tana raya cewa zata yiwa tufkar hanci.

A matuqar gajiye ta isa dakinta don fiye da rabin gift da suka samu sai da suka budesu,don
qememe suka hanata tafiya ta kwanta abinda taso tayi kenan,don tana sanya ran tashi da wuri ta fece
wajen aiki kafin yakai ga iskota. Tun ba'a tashi daga party din ba ta nemeshi ta rasa shi da goumar,
batasan Ina sukaje ba,hakanan sai tayi dabarar qin xama a falon a bude gifts din gudun kada yaje ya
dawo ya taras da ita,so batasan ya dawo ba ko bai dawo ba.

Ruwa me zafi ta hada tayi wanka kawai,ta hada kayan da zata fita dasu goben waje daya sannan
ta isa bakin qofa,key din jikin qofar da tunda tazo gidan bata taba amfani dashi ba ta murza ta rufe
qofan,wannan shi daya zai bata nutsuwa,tunda dai batasan ta yadda yake shigowa dakin ba,to ta
tabbatar kodai aljanine shi bazai iya buda qofan ba,hankalinta kwance ta kashe wutar dakin tabi lafiyar
gado tana karanto addu'o'in bacci.

A nutse ta gama ta hura saman tafin hannunta tabi kowanne sashe na jikinta da ita,taja duvet
ta shige ciki tana lumshe fararen idanunta.

A hankali komai da ya faru wunin yau ya soma dawo mata kwanya,duk kuwa da cewa muradin
bacci take dashi amma sai taji idanunta suna neman qeqashewa. A hankali komai komai daya wakana
cikin office din ya fara dawo mata sabo,ta qanqame jikinta duk a yunqurin hanawa kanta jin abinda take
ji din.
"Wai meye hakan?" Ta tambayi kanta da kanta,bata taba sanin wannan abun zai taba dadata da qasa ko
da sau daya ba a duniya,duba da irin wahalar data gamu da ita a karo na farko na faruwar abun cikin
rayuwarta.

Bude idanunta tayi da sauri waiko zata daina ganin abinda take gani din cikin duhuwar
idanunta,nan ma dai baby wani sauqi sai a wajen Allah,ta kira sunan Allah zuciyarta tana karyewa,kada
dai ace ya goga mata cutar addiction da abinda tasan temporary ne,tana dan da daukan mataki akan
hakan?.

Daidai lokacin da yake tsaye cikin balcony din gidan nasa dake facing gidan ama. Idanunsa tar
akan gidan,yana tuna tunda yazo qasar bai bari aba yasan da zamansa a cikinta ba bare maqotakar dake
tsakaninsu,kuma ya tabbatar zaiyi wuya ace ama ya gaya masa.

Idanunsa ya sake kaiwa kan wayarsa daketa burari kira wani yana bin wani,sai ya dauke kansa
daga kan wayar yana maidawa kan mug din hannunsa ya zuqe ragowar madarar dake ciki yana shimfide
idanunsa akan window din dakinta.

Yanayin rashin wadataccen haske daga window din dake da alaqa da dakin ya tabbatar masa ta
kwanta koma ta jima da yin bacci,cikin kowanne gaba na jikinsa yakejin kewarta,yana jin shauqi izuwa
gareta, xayaso yaje yayi mata kyakkyawan good night,amma koda ya duba agogo sai yaga ya kamata ya
barta ta huta,ya tabbatar yau din ta sha zirga zirga,dole ya danne zuciyarsa,ya saki ajiyar zuciya ya sanya
hannunsa yana debe wayoyinsa tare da kashesu gaba daya,don ya gaji da jarabar kiran yaran su
biyun,kowacce cikinsu akwai albarkacin da take ci yake dage mata qafa.

*********Da qyar ta tashi tayi sallar asuba saboda yadda takejin gajiya a sassan jikinta da kuma rashin
samun wadataccen baccin da batayi ba a daren jiya,a daddafe tayi sallar asuba,bacci yanason dibanta
amma ta gana hakan faruwa saboda plan din d atake dashi na kubce masa da kuma hanashi yi mata
karantsaye a aikinta,ta hada ruwa me dumi sosai ta deba kayan wankanta ta wuce toilet.

Karfe bakwai ta gama shiryawa cikin dubai abaya dake da zip yun daga samanta har qasa,da iya
mayafin abayar kawai amfani tayi rolling bayan ta nade gashinta dukka ta cikin dankwalin da ribbon me
fadi,da hand bag dinta da takalminta me dan tsinin dunduniya dukka na kamfanin gucci ne masu asalin
tsada da tsari,yau kam tayi amfani da sun glasses daya sake maidata balarabiya sak,bata tsaya saka
tarkacen kayan qawa da yawa ba banda dan earrings me wani irin dutse mai daukan idanu da kuma
agogon data daurawa tsintsiyar hannunta na kamfanin Rolex.

Dimple dressing tayi amma kuma yayi matuqar karbarta,ta fito da wani irin sassanyan kyau. A
nutse take taku har ta fito falon,ga mamakinta sai ta samu benazeer da batoul da kuma tanja suna ci
gaba da qarasa aikin jiya

"Tanja biye musu kikayi?,ke din da kika sha hanya ba zasu barki ki kwanta ki huta ba?" Murmushi tanja
ta saki

"Aikinsu ai shine nawa,har kin fito haka yau da wirwuri?,gashi ko karin safe ban gama ba"

"Ba komai tanja,idan ama ta farka kice mata na wuce,zanyi break a office" ta bawa tanja sallahu tana
amsa gaisuwar yaran sannan kai tsaye ta wuce zuwa waje

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400
BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂


[7/12, 9:33 PM] +234 703 962 9900: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 97

Akan qofar gidan idanunta suka fara sauka,saita dauke kai tana dan tabe baki,yau kam taga ta
yadda zaiyi mata karan tsaye,ta riga ta kufce masa,zuwa aiki kam babu fashi.

Sanda motar ta saitu saman hanya saita saki ajiyar zuciya,tana jin cewa lallai tayi escaping.
Hannu ta miqa ta kunna gidan radion qasa dake paris,tana da sha'awar sauran labaran duniya
sosai,wannan yana daya daga cikin abinda ya motsa mata sha'awar aikin jarida a baya.

Cikin qwarewa sa tataccen harshen faransanci aka soma watso labaran,tana biye dasu yayin
data raba hankalinta akan titi,har zuwa sanda ta sanya signal ta fada saman doguwar hanyar.

Tana sake nisa cikin hanyar tana tuna abinda ya faru jiyan. Murmushi ys qwace mata sanda tazo
dai dai inda abun ya faru. Can wani saqo na zuciyarta yana cika da mamaki,duk sanda yayi wani abu saita
dinga jin kamar ba ya maina ba,ya maina dai wanda ko dariyarsa ke musu wahalar gani,me azabar bada
punishment dinnan wanda bashi da sasaauci ko sauqi ko kadan,wacce KADDARA CE ta gauraya
rayuwarsu haka waje daya?. A yau din karon farko kawai taji tana yiwa kanta wannan tambayar.

Kawar da zancan tayi daga ranta,tana sake maida hankalinta ga titi sanda take dab da fadawa
Street na tv station din.

A nutse ta ajjiye motarta,ta zagayo tana daukan jakanta. Harabar maaikatar tasu babu wadatar
zirga zirgar jama'a sosai saboda zuwan wurin da tayi,ita kanta yau tasan tayi sammako,ta kalli agogonta
sanda take tafiya cikin nutsatstsen takunta dinnan ga hanyar da zata sadata da floor din da office dinta
yake. Kafin ta qarasa ta hadu da ma'aikatan da sukayi shigowar wuri irinta,dole ta dorawa fuskarta
murmushi kaman yadda ama tayi mata
Elevator ne ya ajjiyeta,ta fito tana takawa a nutse hadi da qoqarin fidda wayarta. Yasmine
ce,ta saki siririn murmushi,itakam ko kudin da ake janye mata na kira sam bata ji,koda yake yanzun ta
zama 'yar kasuwa sosai yanzun. Sanda ta daga da muryar bibi taci karo,murmushinta ya sake qaruwa,har
yanzu tana son bibinta,tana ji da ita,bata kuma taba manta gatan data gwada mata,duk da ya zame mata
matsala,ya kuma so ya zama silar samun tasgaro ga rayuwarta,amma da yake tayi komai ne da
kyakkyawan nufi bawai don rayuwartata ta samu damuwa ba sai gashi komai yazo cikin sauqi.

Tana tafiya a lobby din zuwa office din nata tana waya da bibi,jifa jifa suna gaisawa sa staff's din
da suke cin karo dasu,har takai bakin office din,ta fidda card na bude qofan ya karashi jikin qofar,ya bada
sauti na alamun tsaro ya bude kansa,ta murza handle din tana tura qofar gami da fadin

"Karki bata bibi,sai na zauna sosai cikin office na zama comfortable sannan zan kirata"

"To ya rage ya naku,ungo ni" bibi ta fadi tana miqawa Yasmine wayar,jin hakan ya sanya sultana qit ta
kashe kiran tana dariya,don ta san qarshen zancan,qorafi ne kawai yasmine din zata cikata da shi.

Tsaf murmushin dake saman fuskarta ya dauke saboda abinda idanunta suka gani. Maina
ne,aliyyu haidar,yana zaune tsaf abinsa saman kujerarta ta office,yayi relax sosai abinsa,ya zare eye
glasses dinsa key da wayarsa duka suna saman table din,daga gefe kuma madaidaicin tray ne dauke da
wasu qananun bowls da butar shayi.

Yayi wani masifaffen kyau cikin tsadaddar suit din jikinsa da aka saqata da zare da auduga me
daraja. A nutse kuma tsaf ya watsa mata lion eyes dinnan nasa da ayau ta gansu sun rusuna qwarai fiye
da kullum

"Come in" ya furta calmly yana tsareta da idanunshi da suke shigar mata da wani magnet me qarfi cikin
jikinta. Tayi tsaye ne kawai cike da mamaki,ita bata shiga ba kuma ita bata fita ba. Wai ta yaya yake
samun access da komai nata?,bayan tayi imanin bashi da wani mabudi nata?,yaushe ya shigo?,yaushe
ma ya taho gaba daya?,ya akayi yasan da wannan plan din nata bayan duk duniya daga ita sai zuciyarta
suka yanke wannan shawarar?.
Bataga tahowarsa ba sai isowarsa bakin qofar,dav da ita ya tsaya idanunsa cikin nata,hancinta
ya shaqi qamshinsa da kyau daya ratsa ta qwaqwalwarta ya sauka a zuciyarta. Tamkar zai gogo jikinta ya
fidda hannunsa guda daya daga aljihun wandonsa ya maida qofar ya rufe still dai bai zare idanunsa daga
nata ba.

Sosai ya tsaya a gabanta,irin tsaiwar da idan yayi kyakkyawan motsi zai iya hade tazarar dake
tsakaninsu. Tsaiwarsa a gabanta ya qara masa mugun kwarjini cikin idanunta,irin kwarjinin data jima
bataji irinsa ba,ya tokare mata ko ina da tsahonnan nasa, hakanan ya hana qwayar idanunta sukuni ko
motsin kirki kwata kwata

"Kina mamaki ne?" Ya jefa mata tambayar kai tsaye da muryarsan nan me ratsa kunnuwa

"Kin manta wannan din uncle maina ne?,wanda ya raineki da wadannan hannayen....." Yayi furucin yana
daga mata hannunsa qwaya daya bayan ya zaroshi daga aljihunsa.

"........yadda maina ya sanki yasan halinki bana tunanin kin san kanki haka,yasan me zaki aikata da abinda
ha zaki aikata ba..... fuskanki kawai tana iya bani labarin abinda yake cikin qirjinki da zuciyarki......" Ya
furta yana hade gap din dake tsakaninsu.

"Kada ki tsorata.......ba wani abu zaki bani ba......bacci kawai nazo ki tayani......jiya ban samu isashen
bacci ba" ya furta yana sabule jakar kafadarta ya ajeta a gefe. Sake miqa hannu yayi ya zare pin din data
maqale rolling din kanta dashi,a hankali mayafin ya soma ware kanshi da kanshi,ya riqe hannayenta cikin
nasa wannan ya sanya bata da damar tsaidashi har ya gama ware kansa ya zame ya fadi qasa.

Baqar lallausar sumarta da tasha mayuka da gyara ta bayyana,kyakkyawar fuskarta ta fito


tarwai,sai ya sakar mata hannu daya ya miqa hannun masa guda dayan ya soma zuge zip din gaban
abayar tata.

Hannu dayan da ya sakar mata ta saka ta riqe hannunsa tsam adan razane,muddin yaci gaba da
zuge zip din to ba makawa komai nata zai bayyana ne, don bata sanya vest ba ganin rigar me kauri ce,
underwear ne kawai a jikinta.
Da idanunta da suka qara laushi ya kalleta, muryarsa a dan sarqe yace

"No" yana girgiza mata kai,sai ya shammaceta ya zuge zip din gar zuwa gwiwarta.

Dukka numfashinsa yaso yayi qaura,farar bra din jikinta zuwa farin underwear dinta sun sauka
sun xauna kuma dai dai saman farar lallausar fatarta da a kullum take cikin gyara da kulawa. Albarkatun
qirjinta dukka suka tsone masa idanu,ya kasa janye dubansa daga kansu,cikin wani irin zafin nama ya
jawota zuwa jikin nasa numfashinsa yana kai komo.

Kyakkyawar runguma yayi mata,ya miqa hannu yana ware band din kanta,hakan ya bawa
sumar kanta damar bajewa saman kansu shi da ita gaba daya. Cusa kansa yayi tsakanin wuyanta,da
muryar rada yace mata

"Karkiyimin gardama please,i want a peace please,am sleepy" daga haka bai barta ta qara sukuni ba ya
dauketa cak ya nufi sofa da ita rigar da mayafin da takalminta dukka suka zame a wajen.

Sosai ya kwanta saman cinyarta hankalinsa kwance bayan ya cire suit din jikinsa sai fara qal din
vest dake jikinsa dake fidda lallausan qamshi,gaba daya yayi mata kane kane saman cinya tamkar yaro
yaso rigima saman cinyar mamansa.

Hankalinta gaba daya a rarrabe yake,yanzun idan akayi mata knocking fa?,wanne amsa zata
basu?. Idan kuma tsautsayi yasa akayi tsammanin shurun da za'a ji bana lafiya bane akayi attempting
shigowa fa?.

"Don Allah...... nan din fa ba gida bane wajen aiki ne"

"Ban gaya miki stay at home ba?,na baki izinin fitowa?......duk wanda ya miki knocking ki gaya masa kina
tare da mijinki" yayi lafazin yana yin wani irin juyi,ya koma rub da ciki yana gyara kwanciyar kansa saman
cinyarta tare da miqa hannunsa ya zagaye qugunta ta baya. Idanu ta sake fiddawa tana mamakin qarfin
hali irin nasa,saidai kuma tana tsoron cewa wani abu,don gwara wanann punishment din nasa akan me
gaba dayan. Bata gama wanann tunanin ba taji ya kamo hannunta ya dora tafin hannun nata saman
tattausar sumarsa yana cewa

"Bacci......bacci nakeyi mummyn twins" ya qarashe fada yana lumshe idanunsa yana jin yayi comfortable
yadda ya kamata.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya


Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/12, 9:33 PM] +234 703 962 9900: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 98
Yadda yayi ruf da ciki saman cinyarta ya sanya take iya jin bugun zuciyarsa sosai. Bugawa takeyi
fiye da kima,sai hakan ya zama tamkar wani Aiken saqo ne zuwa ga gangar jikikta gaba daya.

Sannu a hankali taji bugun zuciyar tasa yana dai daita zuwa matakin da kowacce zuciya ke
bugawa,a hankali taji numfashinsa yana fita a hankali,ya soma sauke numfashi da wani irin
nutsuwa,saidai lokaci lokaci yana sauke ajiyar zuciya tamkar wanda yayi tsaren gudu,ga kuma qanqame
qugunta da yayi sosai kamar zata bace masa.

Nauyi da nutsuwar daya qara yi saman cinyoyinta ya tabbatar mata bacci ya


daukeshi,hannuwanta dake saman tattausar sumarsa ta kalla,ta kasa janyesu,sai kallon yatsunta da suka
nutse cikin sumar tasa takeyi. A hankali ta soma motsa yatsun nata suna sake nutsewa cikin sumar
tasa,wani irin taushi da santsi take dashi. Sannu sannu yadda hannunta ke shigewa cikin sumar sai ya
tuna mata da wasu shekaru can baya da suka shude,lokacin da yake daukanta saman wuyansa,ta riqe
gashinsa da kyau tana dariya,duk da tasan akwai zafi amma baya nuna mata hakan,lokacin da yake
kwanciya saman pillow tayita jagwalgwalata da sunan kitso zatayi masa,wani lokaci ta hanashi bacci har
sai ya tashi,wani lokaci kuma yayi baccin dole da bai shirya ba.

Wata ajiyar zuciya ce ta kufce mata,sai ta dauke hannuwan nata a hankali tana maida kanta
saman makarin kujerar,duk jikinta ya mutu murus,babu wani sauran laka a jikinta itama,ya gama saukar
mata da kasala me yawan gaske,gefe guda ga sammakon da tayi itama bayan kuma bata samu yin
isashen bacci ba a daren jiya.

Idanunta a lumshe taji vibration na wayarsa dake ajjiye dab da cinyarta kusa da kanshi. Bude
idanun nata tayi a nutse tana kallon wayar.......sunan laila ne ya fito radau saman wayar. Batasan me
yasa ba sai taji an motsa zuciyarta,ta zubawa sunan ido yanata yawo saman wayar,tanason ta dauke kai
da idanunta amma ta kasa,wai wacece wannan laila din?,tanason sanin wacece,haka kawai takeso ta
sani din,tanason taji muryarta koma wacece ita.

Zuciyarta na gargadarta akan ta dauke kanta daga wayarsa amma ta kasa,haka ta miqa hannu
ta dauki wayar daketa fidda qamshin tsumammen turarensa daya kama jikin komai da yake tu'ammali
dashi. Tayi shipping ta daga kiran sannan ta sanya wayar a kunne, zuciyarta haka kurum na wani irin
luguden duka
"Helloooo dear...... good morning,ina hanya in sha Allah,bazan wuce awa daya ko biyu ba zan iso
paris......amma champs elysees din ko zaka sa azo a daukeni please ko ka qaraso da kanka?" Ta qarasa
maganar a shagwabe da kuma karyar da murya da alama tanason karya taurin kansa ne

"Bacci yakeyi saman cinyata" ta samu kanta da fadi zuciyarta na mata zafi,ranta kuma yana raya mata
abubuwa da dama. Dif laila tayi daga daya bangaren,dukka wutarta ta dauke daga bayyanar sautin
muryar sultana dake bayyana zallar kamun kai da ajin dame muryar ta mallaka. Qarfin hali tayi ta tattara
dukka dauriyarta gabanta yana faduwa tare da mamakin wacece wannan da zatace yaa haidar yana
bacci saman cinyarta?,ba zata tana mummunan tunani a kansa ba,don ita kadai shaida ce akan tsarkin
zuciyarsa,tsahon zamansu da shekarun da sukayi tare dashi ko kallon banza bai taba yi mata ba bare akai
ga batun wani maganar banza

"Ke din wacece?" Laila ta jefawa sultana tambayar. Tambayar saita zowa sultana da salon rainin
hankali,ita din zata kalla tace wacece?

"Idan ya tashi kina iya tambayarsa" ta amsa mata a taqaice,sannan ta saki siririn tsaki tana katse wayar?.
Kasa aje wayar tayi ta dinga kallon number din,sai taji tana da sha'awar duba cikin wayar,to amma kuma
ta riga ta shiga security wayan. To wacace wannan laila din?,zata iso paris nan da awa daya ko biyu?,it
means kenan akwai wani boyayyar alaqa a tsakaninsu?,me zatazo tayi masa tana baligar mace yana
baligin namiji tun daga wani waje?,a gidansa zai sauketa?. Tambayoyin dukka taji sun mata girma da
yawa,ranta yana sake baci,ta motsa kadan tana leqa fuskarsa.

Fayau take dauke da wani irin kwantaccen kyau,komai na fuskarshi na aje cikin tsari da baiwar
iya halitta ta ubangiji. Mix take gani na kamannin batoul da benazeer saman fuskarsa,abinda duk tsahon
shekarun bata taba gani ba sai yanzun. Kamar jira suke ya dawo rayuwansu dama,suna ta juyewa zuwa
kamanninsa.

"Ki rage fada please" taji ya fada qasa qasa kaman me mayen bacci

"Ki maida wayan silent,ki kuma daina picking mini call" ya sake fada yana gyara kwanciyarsa sosai
hankali kwance.
Mamaki yadan kamata,kada dai ace yana sauraren abinda duk take fadi?,bai bata dama ta biyu
ba ya saka hannu ya jawo hannunta sai gata gaba daya ta kifo saman kansa tayi masa rumfa

"Sleep please......na sani kema baki samu cikakken bacci ba" ya hanata motsawa ya hanata sakat,haka
taci gaba da yi masa rumfar,tun tana qananun tunanuka har idanunta suka soma mata nauyi,sannu a
hankali bacci yayi awan gaba da ita.

A haka suka shafe awa guda da rabi,gaba dayansu jikkunansu da numfashinsu sun gama
gauraya da juna. Shine ya fara farkawa,ya bude idanunsa a hankali yana dubanta. Kyakkyawar fuskar
rigimammiyar qanwarsan nan baby sultana,yau din ta zama madam sultana,duk wani sirrin kyau nata ya
bayyana,irin kyawun da bai taba gani ba tsahon zamansa da ita. Hannu ya miqa saman lips dinta,yana da
muradin taba bakin tsiwa.

Cikin jikinta taji yanayin da take ciki ya sauya sosai,ta bude idanunta a hankali,sai kuma ta
qarasa budesu da sauri,a lokaci guda kuma tayi wani irin hantsilawa a tsorace sai gata ta zauna sosai
sama sofa din. Idanu take bubbudewa cike da mamaki,ita dake a zaune kanshi a saman cinyarta ya akayi
ta koma a kwance,ta matse sosai cikin jikinsa saman doguwar sofa guda daya,wanda koda da yaro ka
kwanta sai jikkunanku sun matsi na juna?.

Yadda ya zauna calmly yana qarewa santala santalan hannayenta da dogon wuyanta
kallo,yadda baqar sumarta me tsaho da santsi ta baje a sassan jikinta ta sake zama ado a tattare da ita ya
tuna mata jikinta ba kaya,ba komai sai bra da underwear.

Da azama ta cure waje daya tana kifa kanta saman cinyarta,itakam wannan wanne irin abun
zub da mutunci yake jawo mata?. Siririn murmushi ya saki yana kada kai,duk da bai gaji da kallonta ba
bazai kuma gaji din ba,amma dazun kafin ta farka daga bacci ya morewa idanunsa kallonta yadda ya
kamata,ta kuma tayar masa da feelings dinsa qwarai,to amma bayason ya cika zaqe mata ko matsarta da
yawa dashen da yake da niyyar yi cikin zuciyarta ya rasa kyakkyawan gurbi da muhallin da yake fata.

Tsam ya miqe yana fadin


"Tashi ki bani abinci......am starving" yayi maganar yana dosar toilet dinta. Ta tsakanin gashin kanta da ya
lullubeta take satar kallonsa har ya shige toilet din,ta miqe da mugun hanzarin ta doshi bakin qofa ta
rarumi abayanta ta maida,saita soma laluben key din office din bayan ta dauki handbag dinta.

Sama da qasa ta rasa maqullin,sai a sannan zuciyarta ta soma raya mata ya boye ne,cak ta
tsaya,tabbas xai aikata,tunda har yana iya gane komai saman fuskarta data shirya,kaman yadda yasan
tsaf meye zata aikata da wanda ba zata iya yi ba.

Dole ta koma saman kujerar ta zauna tana furzar da iska,saita daga kanta a nutse tana duban
agogo

_nan da awa daya ko biyu zan iso paris.....ko zaka qaraso da kanka ka daukeni please_ muryar laila ta
fado mata a rai. Agogon ta jefawa harara ta janye idanunta tana jan tsaki.

"Rashin kamun kan yayi yawa" ta fadi qasan ranta tana kuma jan qwafa,ta maida dubanta ga wayarsa
kamar me jiran shigowar wani kiran. Can qasan zuciyarta kuma sai takejin babu me laifi sai shi,don
meye?,don meye ya fito daga family na mutunci zai dinga jaye jaye?. Lumshe ido tayi abun yana tsaye
mata a rai,yanason bata musu sunan family kenan?

"Sunan family ko sunan 'ya'yanku?" Ta jiyo sautin tambayar data sanyata bude idanunta gaba daya tana
neman amsarta.

Sosai ya hakimce mata saman sofa din,ta dinga zirga zirgan debo abincin dake shirye cikin tray
wanda batasan ma ya akayi ya samu shigowa office din ba,harda kuma wai abincin da ta tabbatar daga
kitchen na station dinnasu aka kawo mishi. Ta qasan idanu yake qare mata kallo,bata da abun cewa sam
bakinta ya kullu,to meye ma zata ce masa?,ya riga ya gama kulle mata baki,itakam zuwa yanzun ma
tsoro yake bata,ta yadda duk yadda tayi qoqarin kaucema qaddarar haduwa dashi hakan bashi samuwa.
Lallabawa takeyi ya fice gurin lafiya lau ba tare daya daura mata jinyar ciwon jiki ba(nace
gulmammiya,anaso ana kaiwa kasuwa).
"Koma ki zauna" ya fadi sanda ta ajjiye abincin a gabansa,yana zaune sosai saman dan center carpet dan
madaidaici da aka qawata office din dashi. Dubansa tayi kaman zata saki kuka,to amma yadda yake
dubanta ya sanyata zamewa ta zauna sosai a a gabansa.

"Oya.....saka hannunki....", Ya bata umarni yana tattare dogon hannun shirt din suit dinsa,ya sanya nasa
hannun cikin abincin ya fara kaiwa baki a nutse. Kasa motsawa tayi,cin abinci tare dashi cikin kwano
daya wani tsohon al'ada ne data manta rabonta dashi,batajin zata iya sam,don haka taci gaba da duban
kwanon sanda yake kai abincin cikinsa hankali kwance. Wani mugun nishadi ne ma yake saukar
masa,duk sanda zasu kasance qarqashin inuwa daya kaman hakan,yakanji kaman ya tsaida lokaci ya
hanashi motsi,abinda ya kasa bawa kansa amsa har yanzu shine,wai dama can wannan matsanancin son
yakewa sultana?,ko kuma bayan faruwar wancan abun a wancan lokacinne mahaukaciyar soyayyarta ke
yagalgalashi?.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200
_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/13, 6:38 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 99

"idan kika bari na rigaki gama cin abincin nan.......dura zanyi miki" ya fadi yana kada yatsansa dan
manuni. Itakam a yanzun ko meye yace zaiyi zai aikata ta sani,don haka ta rufawa kanta asiri ta matso,ta
sanya hannu ta dauki spoon. Hannunsa ya miqa ya karbe yana fadin

"Um um......yau da hannu zamuci,mu samu albarkaci junanmu" cikin ranta ta tabe baki

"Wanne albarka mutumin da yake da side chics dinsa?" Ta fadi qasan ranta

"Me kika ce?" Ya jefa mata tambayar yana tsareta da idanu

"Ba komai" ta fadi qasa qasa tana tura baki gaba. Murmushi ya saki,lallai da gasken tsoro ya sanya ta
fara gyara wasu abubuwan,ya sani akwai abinda tace,amma shakkar tasa ya saka ta kasa fadi masa a
sarari,wanda inda ada ne ya tabbatar zata fadi mashi ne,ko meye zaiyi saidai yayi.

Koda ya gama sai ya koma da baya yayi relaxing yana kallon taunarta,idanunsa can qasa,ba zaka
taba kawowa ita din yake kallo ba. Wayarsa ya jawo sanda ta fara ringing,ya saki murmushi ganin sunan
goumar,yana dagawa muryar benazeer da batoul ne ya soma masa sallama.

A handsfree ya sanya wayar yana fitar da murmushi,muryarsu fes cike da doki da zumudin
mahaifinsu. Hira suke masa sosai hayaniya hadi da shirmensu,ya sakankance sosai ya biye musu

"Daddy munyi missing naka,uncle goumar yace mu tambaya zai kawo mu office dinka?" Tsaiwa tayi da
hadiyar lomar tana kallonsa qirjinta nadan bugawa,ko kusa ko alama batasan kowa yasan suna
tare,kowa dinma irin goumar?,ta tabbatar daga ranar ta kade daga ita har ganyenta,kai wala'alla ma
bakinsa bazaiyi shuru ba saiya gayawa ama, itakam ai da ta kade,da wanne ido zata kalleta?.
Shima din ita yake kalla,kuma salon kallon da yakeyi mata tamkar yana jefa mata tambayar na
basu izinin zuwa?ne a fakaice.

Rau rau tayi da idanunta tana tsame hannunta daga abincin,sai ya zame idanunsa yana cewa

"No kuyi zamanku,nayi alqawari anjima kadan zamu kasance tare" ihun murna suka saki,yanata sakin
lallausan murmushinnan nasa kafin daga bisani yace su bawa goumar wayar.

Magana sukayi kadan sannan ya kashe wayar,ya miqe ya nufi inda suit dinsa take ya saka,ya
maida takalminsa,yana daura agogonsa ya dubeta

"Zaki wuce gida yanzun......daga yau kuma duk sanda kika sake fita bada izinina ba......" Sai bai qarasa ba
ya maida kansa ga daura agogonsa.

Afakaice ta harareshi,kaman yaji hakan cikin jikinsa sai ya waiwayo,saura kadan su hada idanu
tayi hanzari dauke kanta ta maida ga agogon bangon office din nata.

Lokacin yayi daidai da sanda yarinyar tace zata iso paris,hakanan taji wani abu ya tsaye mata a
wuya.....lokacin tashinsu daga aiki da saura,don meye don zaije ya dauko wata can daban zai matsa mata
tabar office yanzu?, bayan ya hana mata yin duk wani aiki,har yanzu program din da zata next week bata
shirya komai game dashi ba,saboda ya hana mata sakat,ya hanata motsi,ya kuma hanata nutsuwar da
zatayi aikinta.

"Are you with me?" Ya tambayeta yana qoqarin daukan wayarsa. Wani tunani da yazo mata ya sanyata
miqewa ba tare data kalleshi ba

"Zanje na danyi submitting wani abu,bazan wuce minti biyu ba" ta fadi tana jin dacin yadda wai saita
nema excuse a gurinsa kafin tama fita
"Hope ba wajen namiji bane?" Tambayar ta quleta,sai taji kaman kada ta amsa masa,amma tana tsoron
hukunci,don haka ta gyada masa kai kawai.

Sai data tsaya tsaf ta maida komai nata inda yake sannan ya barta ta fita din. Qwafa taja bayan
ta fita tana cewa

"Ai idan kasan wata bakasan wata ba" office na qarshe a lobby din ta shiga,tasamu baturiyar matar cikin
aiki kace kace,amma kasancewar suna girmamata saita tsaida komai ta saurareta.

Dan qaramin hutu ta buqata a kwanakin,ta basu uzurin tanason ta shiryama next program sosai
a gida,don mamanta ita zata taimaka mata da wasu research akan culture din da zasuyi magana akai. Ba
wani damuwa ta tura request akan buqatarta,ta kuma bata dama a take ta rubuta letter ta tura,sukayi
sallama ta fita a office din.

Fes takejin ranta sanda ta baro office din,kome zaiyi daga nan zuwa gida ba zataji haushinsa
ba,don tasan abinda ta shirya din shi daya zai mata maganinsa.

Ko a cikin motar yaga ta saki fuskanta sosai,bata damu kaman yadda take damuwa wancan
lokacin ba idan ya yanke zasu wuce gida tare a motarsa.

Duk da hankalinta ya dauke daga kanshi,amma lokaci lokaci sai ta dinga duba agogon
hannunta,abu daya ranta dai keci gaba da bata zayaje daukota,tanaso tayi tsaki amma tana gudun yinsa
a sarari.

Kama ko yaushe ya tsaya daga farkon street din nasu ya bude ya fito ya zagayo inda take zaune
yana miqa mata key din

"What do you want to me to do to you tonight?" Ya tambayeta yana dage masa girarsa guda daya hadi
da kashe mata ido. Wani abu ya zubawa gangar jikinta,saboda tsananin kusancin dake tsakaninsu yayi
yawa,abinda take gani kuma a idanunsa yana son shallake yadda ta daukeshi
"Ki gayyaceni mana yau dai daya da kanki please madam" ya sake fadi yana sassauta mata murya da
salon dake narka zuciya.

Saura kadan ya dauke mata numfashi da wani irin tsananin kunya da kuma nauyi daya saukar
mata. Ya fahimci ne taji,don haka ya miqe daga durquson da yayi ta jikin window din yana watsa
hannayensa gami da dage girarsa sama

"I don't know what's wrong with me,am so addicted to you.....see you tonight" ya fadi da tataccen
turancinsa tamkar baisan wani abu waishi yaren faransa ba. Takowanne bangare gwanine,Allah ya bashi
baiwar harshe qwarai da kuma salon sarrafa kowanne harshe,idan France yakeyi zaka zaci shine kadai
yaren da ya sani,hakanan idan ya juya English.

"Tonight?" Ta maimaita kalmar bayan ta soma gangara motar sosai cikin layinsu. Kai ta gyada
murmushin mugunta yana qwace mata

"You will see tonight kuwa" ta sake fada qasa qasa.

Hannayensa ya saki yana juyawa zuwa inda matashin ya aje masa motarsa kamar kullum. Daidai
nan wayarsa ta dauki flute ringing me sanyi. Ranshi yadan hade kadan,sai kuma ya daga kiran yana
sanyawa a kunnensa.

"Almost over one hour ina jiranka yaa haidar.......bakasan na iso ba ko?"

"Me yasa kika taho laila?,aunty din tana Paris dinne?" Ya tambayeta don baiga ta inda zai bari tayi masa
masauki cikin gida ba.

Ajiyar zuciya ta saki,har yanxu tana jin dacin maganar da matar data daga wayanshi dazu ta gaya
mata,so amma yanzun ba muhallin da zata tambayeshi bane
"Tacemin yau suna hanya in sha Allah,so ko zakamin alfarmar zama cikin gidanka na wasu awanni kafin
su iso?" A yadda sautin nata ya fito ya nuna kaman wani abu ya sosa zuciyarta. Sardauna da daddy sune
mutanen daya tuna,ya kuma tuna halacci da gudunmawar da suka taka a rayuwarsa

"Ki tsaya a wajen,zanzo nayi picking naki"

"Alright, thank you" ta fadi. Ya sauke wayar tausayinta yana dan kamashi,shi da ita dukka yana tunanin
jirgi daya ne yayi jigilarsu,son maso wani da hausawa ke kira da qoshin wahala,ya juya a nutse ya koma
matar yana tayar da ita idanunsa kan hanyar da sultana ta wuce.

Daure da babban towel da kuma qarami ta fito daga toilet. Haka kawai tunda ta dawo gidan
gaba daya hankalinta yana kansa,duk kuwa da cewa duka duka basu zarce awa biyu da rabuwa ba. Duk
bayan wasu mintuna sai ta tuna da kiran LAILA. Sunan da ma yarinyar gaba daya sun tsaye mata a
rai,tayi masifa tayi fada ita da zuciyarta dama ranta gaba daya kan shiga shirgin da bai shafeta ba amma
abun yaqi barin zuciyarta.

Tanata ture tunanin tana shirya kanta cikin wani sassanqan material,so take tayi keeping kanta
busy yau sosai,tanason ta zauna cikinsu ama da yaran ta basu lokacinta,daga magrib zuwa ishai kuma
tana sanya ran ta qarar dashi wajen binciken al'adun qabila daya cikin tarin qabilun Nigeria wato qabilar
KANURI.

Fes fuskarta ta fita ta tsakiyar turban cap data sanya fara qal,ta matsa jikin bed Side drawer
dinta dake daura da window dinta,haka kawai sai taji sha'awar bude window din.

A nutse ta miqa hannunta ta yaye labulen,ta kuma sake zura hannunta ta janye glass din. Fes ta
cikin window din take hangar gidan,gidan da take da tabbacin cikinsa yake rayuwa. Tana qoqarin sakin
labulen motarsa ta tsaya qofar gidan,sai ta samu kanta da gaza sauke hannun nata, idanunta tamkar
wadanda aka yiwa majanyi suka bi qofofin motar da kallo,dai dai sanda shi da laila dukka suka fitowa
daga cikin motar, suhail ya bude back seat shima ya fito. Da qasaitaccen takunsa yabar jikin motor din,ya
haura zuwa qofar gidan ya saka key ya bude gidan,ya tura qofar sannan yaja da baya yana bata hanya.
Takowa tayi cikin murmushi, zuciyarta yau din tana mata wani dadi,yau itace ya haidar din da kansa ya
daukota daga airport?,bayan haka ma sai daya biya da ita wajen cin abinci taci abinci ya taho mata da
takeaway wai don kada taji yunwa,zata iya mantawa da wannan ranar kuwa?. Anya ba nasara da sa'a
bane ya kawota paris?,kodai da gaske hasashen da Sara tayi mata zai tabbata?,zata jarraba......tana fatan
dacewa.

Sanda ta saka kai gidan ya mara mata baya labulen ya subuce daga hannunta,tayi qas da kanta
tana son gayawa kanta da kanta da sabganta bane,ba abinda ya dameta bane,ta soma qoqarin buda
kwalin turaren amma sai ta fahimci hannuwanta rawa sukeyi,taja wani dogon tsaki a matuqar fusace,ta
miqa hannu tana maida window din ta kullesu gam ba tare data sake bari idanunta sun kalli gidan ba

"Bazan sake budeshi ba har mubar Paris" ta gayawa kanta da kanta a fusace tamkar wani ne yayi mata.

Gagara bude turaren tayi don hannuwanta sai tajisu kamar an bugesu,cilli tayi da turaren saman
gadon,saita koma saman madubinta ta fesa wanda ya samu kawai,ta dauki wayarta tana fita a dakin can
qasan ranta tana qoqarin controlling kanta da kanta,don bataga abun damuwa ba a abinda ta gani,meye
sha'aninta a ciki?.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800
UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/15, 10:08 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*


*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 100

Fitowarta ta musu dadi sosai,suka sanyata a tsakiya da karadinsu da basa gajiya. Duk da shuru
shurun batoul amma benazeer tanason koya mata surutu.

Jinsu kawai takeyi,amma sai takejin hankalinta da tunaninta baya tare dasu.

"Mummy yau kiyi mana kwalliya.......daddy yace zaizo mu fita dashi......me zamu siyo miki?" Batoul ta
tambayi sultana tana kallon fuskarta.

Dan kallon yarinyar tayi fuskarta tana tuna mata da tashi fuskar,yadda yayi bacci saman
cinyoyinta dazu lakadan kaman bashi ba......amma kuma yanzun sai gashi yana shiga da wata macen
cikin gidansa shi da wani.

"Ba komai batoul" ta fadi tana shafa kan yarinyar zuciyarta tana karyewa.

"Mummy to ki shirya muje tare dake mana?,.......ama don Allah ta bimu?" Ta maida tambayar ga ama
dake a zaune waje daya,tana karantar sultana din a fakaice,cikin kwanakin tana fuskantar canje canje
daga gareta,saidai har yanzun batakai gacin gano sauyin na menene ba

"Na gaji ni bazan iya sake wani fita ba...... infact ma ina da aiki da zanyi na program dina......saikun
dawo,tanja zata shiryaku" ta basu amsa tana miqewa don dab ake da shiga lokacin sallar.
Dukansu suka bita da kallo,fuskokin yaran tayi rau rau da alama basuji dadin hakan ba,ama ta
kira sunansu tana yafitosu da hannu,suka taso dukansu suka zauna gabanta,saita riqe hannayensu tana
dubansu

"Idan mummynku tace ba zatayi wani abu ba ku daina tursasata kunji?,tana fita aiki,kuma tana dawowa
a gajiye,kunaso tayita ciwon jiki?" Kai suka girgiza a tare

"Yauwa......yanzun ku yiwa uncle goumar waya ya dawo da wuri sai kuje tare" hakan data fada sai ya
saka suka saki ransu,suka suri wayarta suna qoqarin gano lambarsa su kirashi din.

Duk abinda ama din ta fada ma yaran akan kunnenta ne,don tsaye tayi jikin bakin qofarta.
Gwiwoyinta sukayi sanyi,tausayinsu taji yanason kamata,ta daga qafafunta da qyar tana wucewa
ciki,idanunta akan agogo.

Tanaji a jikinta babu ma lallai ya tuna da yaran tunda wancan laila din tazo,duk zumudin fita
dashi din da zasuyi tasan ba lallai ya tuna dasu ba. Ta sake maida idanunta tana kallon window din kamar
zata iya hango cikin gidan,saidai kuma zuciyarta ta gargadarta kada ta soma budewa,don haka ta juya
tana wucewa toilet don dauro alwala.

Sanda ta fito sai tayi deciding ta kira yaran wajenta suyi sallah da azkar tare,wani sashen na
zuciyarta yana gaya mata

"Kinaso kiga baban nasu zaya fita dasu ne?,ko kina son gasgara zarginki?" Tsaki taja tana qaryata wannan
hasashen na zuciyarta,sai ma ta fasa fita,ta dauki wayarta ta kira tanja tana tambayar yaran

"Gasunan suna alwala zasu wajen ama suyi sallah"

"Turomin su"
"Tom" tanja ta amsa mata. Fasa shimfida qaramin abun sallarta tayi,ta sanya musu wadatacciyar
dadduma,ta sanya ustazah dinta da ya fidda kyan fuskarta ta fuskanci gabas,daidai sannan suka shigo
suma kowa sanye da wadataccen hijabi. Fuskokinsu kawai sun sanya zuciyarta yin sanyi,ta lumshe
idanunta ta kuma budesu,ta qarasa saman dressing table dinta ta dauko tutarenta,ta matsa dab dasu ta
feffesa musu duk kuwa da cewa ko yaushe cikin qamshin suke,don suna da personal turarensu. Hakan ya
musu dadi,kuma ya nuna har saman fuskarsu.

"Oya assalaat" ta furta tana maida turaren,duk sai suka matso suka hau saman abun sallar.

Gefen hannun damanta ta tsaidasu suka tada sallar cikin nutsuwa. Kusan a shekarunsu sun iya
komai na sallah,koda akwai gyara bazai wuce wasu qananun abubuwa ba,da haka suka kammala
sallar,suka daga hannu yadda sukaga tayi sukayi addu'a tare suka shafa.

Agogo ta sake kalla, lokacin dai yanata tafiya,zuciyarta taji ta sake matsewa,sai tayi qoqarin
saita kanta ta maida dubanta kansu

"Yaudai karatun islamiyyan kowa zanji" da zumudinsu suka gyara zama,cikin dabara da hilata ta dauke
musu hankali da karatun,duk da hakan tanayi tana duba lokaci,har sannan bataji wani motsinsa ba,bata
kuma ji ance su fito su tafi daddynsu yazo ba.

Tunda suka shiga gidan ya wuce bedroom dinsa ya barta da suhail a falo suna hira,wadda kusan
indai suhail ne sun saba da irin wannan doguwar hirar shida laila din,don ba baqin juna bane. Har kafin
ma a fahimcesu ana zaton soyayya sukeyi,saidai daga bisani sai aka fahimci haduwar jini ne kawai ba wai
soyayya ba.

A dakin ya kashe dukka awannin saman system,sanda magariba tayi ya leqo yayi musu
magana,suhail ya wuce daura alwala don su hada jam'i,ita kuma ta gyara zamanta tana fadin

"Ina fashin salla ne yaa maina" kanshi ya dauke kaman baiji ba,baisan me yasa takeson bayyana masa
komai ba,akwai abubuwan da yasha jin basu dace ta gaya masa ba amma haka kai tsaye take gaya masa.
Tana nan zaune har suka kammala sallar,yayi zaman azkar dinsa har isha'i tayi suka sake jam'i
suka idar. Tun yana sallar yake zuba idanu yaji ta jira aunty din tata,amma sai baiji ba,don haka bayan ya
kammala azkar dinsa a nutse ya shafa,ya miqe yana nade carpet din da sukayi sallar.

"Dare yanayi......call them mana kiji idan sun iso,ya kamata ki wuce tun yanzun" ya fadi da sarautar nan
tasa da takan motsa masa time to time,wadda me masifar qara masa kwarjini ainun da haiba.

Dan kame kame ta farayi,abinda ya sanyashi zama saman one sitter sofa din dake falon ya hade
qafafunsa daya saman daya yana kallon idanunta

"Banjin fa sun iso......amma dai, lemme call" ta furta da sauri sauri tana zuge jakarta ta fiddo wayarta.

Cikin motsinta da idanunta ya gano qaryarta,taso tahowa ne kawai taqi jiran lokacin da zasu
dawo saboda ta matsu ta ganshi shi yasa tayi qaryar yau din zasu dawo

"Sakata a handsfree" ya bata umarni nakai tsaye yana ajjiye carbin hannunsa a side table.

"Okay" ta amsa qasa qasa,wayar ta fara ringing,

muryar aunty din ta fito tarwai.

Tun daga yanayin yadda suka gaisa ya tabbatar masa basu da masaniyar tahowarta ma

"Yaushe xaku iso aunty?" Tayi qarfin halin tambaya,don ko ba'a gaya mata ba koda bata kalleshi ba ta
sani jifanta yakeyi da kallo da wannan fitinannun idanun nasa

"Next week by now in sha Allah muna gida"

"Alright.....saikun iso"
"Yauwa.....byee,ki gaida nenne(mamarta)" sauke wayar tayi daga kunnuwanta amma sam taqi yarda ta
kalleshi,shi dinma yasan ba zata iya hada idanu dashi ba,don ba abinda yafi qin jini irin qarya.

"Ina da alqawarin fita dasu BB suhail,can u please help me?,ka dauketa ka sama mata daki for one
week?" Da sauri ta dago idanunta ba tare data shirya ba, muryarta a raunane tace

"Amma yaa haidar..... nan din fa akwai spare din daki,meye laifi don an barni cikin guda daya?tunda dai
daddy da nenne dukkansu sun yarda dakai?" Kafeta yayi da wani irin kallo,ya yadda duk iya zamansa
dasu yarinyar bata gama sanin halinsa ba tabbas

"es-tu dans ton sens ?(kina da hankali?)" Ya tambayeta da harshen faransanci saboda ranshi da ya fara
baci. Qasa tayi da kanta,ya jima yana dubanta kafin ya janye idanunsa daga kanta

"Wannan ba tarbiyyarki bace kema kuma kin sani,ba zaki kuma fara yanzu ba,pack your stuff za'a kama
miki masauki......" Ya fadi mata yana daukan counter dinsa. Daidai nan wayarsa ta dauki tsuwwa. Daddy
ne yake kira sai ya koma ya zauna yana daga kiran

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/15, 10:08 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 101

Cikin girmamawa da mutuntawa ya gaidashi,bawan Allahn yana daya daga cikin mutanen da
yake ganin girmansu qwarai.

"Lafiya alhamdulillah aliyyu,kaga baquwa ko?,sardauna nata fadan me yasa aka barta ta taho,mamana
rigimammiya ce,kuma na yarda dakai,na tabbatar she's safe a wajenka" dan murmushi kadan ya fidda
yana cewa

"In sha Allah daddy"

"To ma sha Allah,kada ta wuce ona week,tacemin gidan aunty surayya zata sauka ko?" Kallonta yayi,sai
ta marairaice masa alamun kada ya fada ya rufa mata asiri

"Eh haka tace" ya bawa daddyn amsa,don bazai taba iya mara mata baya tayi qarya ba,don qaryar tana
cikin dabi'un da bai iya ba,hasalima abune da idan kanason ganin tsananin bacin ransa kayi mata ita,idan
ya gane shikenan,idan bai gane ba Allah ya taimaketa

"Tow yayi,kada ka barta ta wuce one week kaji haidar?"

"In sha Allah daddy"


"Allah yayi muku albarka......ya aikin?" Ya sauka daga kan wancan maganar ya koma masa hirar wajen
aiki. Sun dan tattauna da daddy din a taqaice sannan sukayi sallama,ya ajjiye wayar yana dubanta ransa
na sake baci da kalar qaryarta

"Kina so ki xama maqaryaciya ko?" Kai ta girgiza da sauri,don ta sanshi farin sani akan yin qarya,duk
yadda kake dashi yanzu yanzu zaku bata,yanzu za'a ji kanku akan qarya

(Don Allah,don Allah iyaye mu kula,mu tsaya tsayin daka game da tarbiyyar yaranmu,wallahi wallahi
qarya masifa ce,itace silar rugujewar komai da kuma dukkan wahalhalun rayuwa da mukesha,wasu
qarairayin kuma daga wajenmu yayanmu suke koya,kiyi qaramar qarya kina ganin batakai ta kawo ba
wallahi tana affecting tunanin yaro sosai,misali ungo nan,zo ka ka karba,jeka dauko takalminka mu tafi
sai ya dawo ya tarar kin gudu kin barshi,duk da irin haka suke farawa,zasuga au ashe idan na fadi
magana kaza ba daidai yadda abu kaza yake ba ashe akwai wani abu da ake cimmawa,ko babansu ya
dawo ki karkace ki shirga masa qarya don ki Kare kanki bayan duk suna kallo,da haka saimu wayi gari
muga mun cika al'umma da maqaryata,muyita mamaki ina suka samo wannan dabi'a,bayan ba daga ko
ina bane daga wajejenmu ne,Allah ya bamu ikon gyarawa ameen).

Siririn tsaki yaja yana kauda kanshi gefe,sai kuma yayi wami gajeran tunani,daddyn ya riga ya
damqa amanarta a hannunsa,dole ya kula ma dashi kansa hotel din da zaya sauketa,kafin gobe ya laluba
mata inda zata zauna cikin gidajen abokan aiki,don bayason xaman hotel ga mace baliga babu
muharrami,don haka ya miqe tsaye yana kallonta,yama fasa suhail din ya kaita,gwara ya kaita da
kanshi,fatansa su rabu 'yar mutane ta koma gidansu lafiya

"Wuce muje" ya fadi a dake. Dakewarsa bata dameta ba saboda kaita din da zaiyi da kansa ya mata
dadi,hakanma daraja ce,sai yayi gaba yana barwa suhail din sallahun ya jirashi yanzun zai dawo.

Yana fitowa idanunsa suna kan gidan,daidai saitin window din nata, hankalinsa yana kan
yaran,bayason ya musu alqawari ya gaza cikawa,don yanason su tashi da dabi'ar cika alqawari.

Seat din driver ya shiga ya tayar da motar. Full light din da ya yiwa motar yana kunnawa sau biyu
yana kashewa sai taji tamkar da ita ake sanda take tsakiyar yaran tana qoqarin su qara assignment dinsu.
A nutse ta daga kanta ta kalli window din gabanta yana dan tsinkewa, zuciyarta ta bata ko shine zaya
dauki yaran?,amma kuma zai kunna mota tun yanzun bayan da qafa zai shigo?. Wannan tunanin ya
sanyata kauda kai ta sadda kanta qasa. Duk yadda akayi zai fita ne da wancan yarinyar, that's why bazai
iya zuwa ya kwashi yaran ba,iya wannan tunanin ya saukar mata da qunci a zuciyarta.

Kaman goumar yasan tambayar da taketa yiwa kanta kenan saiga muryarsa yana baiwa ama
saqo

"Yanzun naga ya maina zasu fita da laila......yacemin zai zo ya dauki su benazeer"

"Sai ya iso" ama ta amsa,don bai boye mata wacece laila ba ta riga ta Santa.

Sosai ranta ya qara baci,ta dinga jin koda yazo ma ba zata bari yaran suje ba,tunda laila gaba
take da 'ya'yansa,saita sake karkata hankalinta akan yaran,daidai sanda akayi knocking qofar dakin nata.

"Goumar ne" ya fadi tun bata tambaya ba,daya daga cikin dabi'unsa masu kyau baya taba shiga waje ko
inane ba tare daya nema izini ba

"Baqin buzu?" Ta tambaya yau daya tana jin sha'awar tsokanarsa

"Ban sani ba mummyn twins" qaramin murmushi ya qwacewa kyakkyawan fuskarta,inda yasan yanzun
sunan baya bata haushi,dadi ma yakeyi mata da bai dinga fadi da zummar ya tsokaneta ba

"Indai ka yarda da baqin buzu sunanka ka shigo,idan baka yarda da sunan ba ka koma"

"Indai kin yarda da matar babban yaaya,matar maina MAYAK'I kike to tabbas zan shigo" dif wuta ta
dauke mata,ta xubawa qofan idanu kafin kuma ta sauke idanun nata akan yaran. Kamar suma suna
fahimtar abinda yake fada din dalla dalla,dukkansu sun gwalalo mata fararen idanun nan nasu masu
wani irin kala irin na ubansu
"Kallon kuma na meye?" Ta jefa musu tambayar tana kallonsu,dariya duka suka saki sai suka maida
kansu ga rubutun nasu, daidai nan goumar ya tura qofar ya shigo.

Kamar ko yaushe suka miqe suka maqaleshi ya daukesu sannan suka koma suka zauna.
Yawancin lokuta idan ya musu hakan saita tuna sanda maina yake yaya kuma uba a wajenta,fiye da
wannan kusancin ne a tsakaninsu.

Daga qarshe dai komawa tayi 'yar kallo,suka gama assignment suka shiga shirmensu su da
goumar din,wanda dukansu basa gajiya dashi,sannan tanja ta shigo musu da abinci sukaci,a hankali
kuma bacci ya kwashesu suka zube a wajen.

Da murmushi yake dubansu sannan yace

"Yara kun looser......yau ba fita da daddy kenan". Maganar goumar saita zame mata tamkar fami cikin
zuciyarta,ta daga idanunta ta kallesu,saita maida kanta ga tattara karikicen karatunsu.

Yadan saci kallonta sai ya fahimci maganar da zaiyi ma kamar ba zata samu gurbin zama a
wajenta ba,don haka ya miqe,ya dauki yaran da daya da daya ya fita dasu zuwa dakinsu. Sanda ya dawo
tana bakin qofa yana shirin kulle dakin,ya dubeta yasan saki murmushi. Tunda taga yayi murmushin ta
tabbatar tsokana ce ta dawo dashi,sai ta dan tsuke gira tana cewa

"Sai kuma me?"

"A'ah,gulman mijinki nazo gaya miki,sai kuma na ganshi da wata bafulatana mazauniyar France zasu fita
yawon shaqatawa ke kina cikin gida a zaune" harara ta balla masa, goumar din duk yadda zai bata takaici
ya iya

"To sai me?,su wuce the great wall ma,sukai qarshenta su dawwama a can" saita ja qofarta tana rufewa.
Tana jiyo dariyarsa daga bakin qofar harda durqusawa,sai ta kasa barin qofa,lokacin yadan daga murya
yana cewa
"Kinci bashi wallahi......amma dai ina gaya miki,tabbas mijinki rububinsa ake,abu daya da Allah ya rufa
miki asiri shine bame fuskar da za'a tareshi bane,nima kuma ki godemin,don na tsare miki kishiyoyi da
yawa" tanason yaba masa baqar magana amma kuma batason yasan ma taji abinda yake fada,saita juya
zuwa ciki taja jan tsaki kamar zata tsinke harshenta.

Haka kawai taji komai ya quntace mata,daga bisani ta dinga masifa ita daya da ranta kaman an
mata wani abu. Ta gama shirin kwanciyarta kaf,ta matsa bakin qofar dakin ta murza key ta barshi a
jiki,don haka kawai jikinta yake bata zaya shigo.

**Daure da towel a qugunsa ya fito daga wanka,faffadan qirjin nan nasa me cike da gargasa sun kwanta
luf sunbi jikinsa sosai,sai suka sake fidda qirarsa ta qaqqarfan namiji ma'abocin motsa jiki da daga qarfe.

Agogo ya kalla,sai yaja siririn tsaki,sosai yarinyar ta bata masa lokaci yau,kwata kwata yayi niyyar
kama mata wajen kwana ne kawai,amma ta dinga amfani da damarta don tasan matsayin daddy da
sardauna a wajensa har sai data tsaya taci abinci,ta saka order din wasu kayan amfanin,wannan ya bata
masa lokaci har sukayi dare haka.

Cikin lallausan pyjamas ya shirya kansa,ya wuce kitchen riqe da wayarsa,ya kunna coffee Maker
ya hada coffee me zafi sosai saboda iska da take dan kadawa me dadi a daren,iskar data haifar masa da
kasala da kewarta me yawa.

Koda ya juye a cup sai ya fita zuwa balcony dinsa,inda zai samu daman kallon gidan sosai. Yana
kurba jifa jifa yana duba wayarsa,rabin hankalinsa kuma yana kan gidan dake dauke da halittu mafi
soyuwa a wajensa a duk fadin duniya.

Ya kusa minti goma sha biyar kafin ya shanye din,ya ajjiye mug din yana jin kewarta tana
qaruwa cikin ransa,gaba daya zuciyarsa da ruhinsa yafi karkata ga yaje yaji duminta,koda na awa daya ko
biyu ne,ya tabbatar muddin baije din ba,babu shi babu bacci me dadi,bama lallai ya samu baccin,don
haka ya miqe ya ajjiye wayoyinsa gaba daya,ya zura slippers dinsa dake ajjiye a gefe ya fito cikin nutsuwa
yana saka hannayensa cikin aljihun pyjamas dinsa.
Batasan adadin sau nawa taji juyi ba daga kwanciyarta zuwa wannan lokacin,wani irin qunci
takeji cikin qirjinta sosai wanda ita kanta batasan meye dalilin hakan ba.

Jin da gaske baccin yaqi zuwa saita miqe tana maida cap dinta ta bacci,ta zuro qafafunta qasan
gadon tana shirin yunqurawa sai taji ana taba qofar dakin. Da farko ta tsorata sosai,amma daga bisani
hancinta ya fara dauko mata qamshinsa yana aiko mata dashi. Zuqar qamshin tayi da kyau,sai taji wani
kaso na qullewar da qirjinta yayi yana sassautawa,sai kuma murmushi ya subuce mata,tadan cije lips
dinta,hasashenta yayi daidai kenan,dama tasan zaiyi wahala baizo ba,kawai sai ta koma saman gadon
abinta ta nannade cikin duvet tana fidda murmushi tana kuma jiyo motsinsa sama sama.

Bayan wasu mintuna taga wayarta tana haske,koda ta duba sai sunan da yayi mata saving dashi
ya bayyana,maida wayar tayi ta ajjiye tana murmushin,har tayi iya yinta ta katse.

Iska me dumi ya furzar daga hunhunsa yana maida wayarsa da dole ta sanyashi fita ya daukota
cikin aljihunsa,bayason ya matsanta kan sai ya shiga,duk da idan yaso zai shiga din,to amma bayason
tada kowa cikin gidan. Kwata kwata issue din laila ya sanyashi baiyi wani dogon nazari akanta ba,inda a
nutse yake tabbas zai gano zata aikata hakan,ya watsa hannayensa yana daga kafadarsa,lallai bazai
qyaleta ba,wannan abun da ta ciwa kanta bashi ne.

Murmushi me dan qaramin sauti ta saki sanda taji shuru,ta tabbatar ya gaji ya wuce,ko iya yau
kadai ta dan rama kadan daga cusa matan da yakeyi ya kuma hanata katabus,da wannan murmushin
saman fuskarta bacci ya dauketa.

********Cikin kwanaki biyar din data dauki hutu ko qofar gida bata fita,tana daki zuwa parlor tana hada
ayyukanta. Da zarar anyi knocking Bell zata tattara komai ta wuce daki kafin a shigo,wannan ya sanya
tsahon kwana uku basu hadu ba,har sai rana ta hudu,ranar da benazeer ta tashi da zazzabi.

Da yammaci ne dukkansu suna zaune a falon, benazeer din an rakwarkwabe jikin ama anata
zuba shagwaba,dama yaya lafiyar kura bare tayi hauka,sultana na zaune da system saman cinyarta,gefe
kuma kayan sawa na asalin qabilar KANURI,ta gama shirinta tsaf, gobe kawai idan Allah ya kaimu take
jira.
Door bell aka kada,sai ta daga kanta daga aikin da takeyi ta maida ga qofar,yau din bata da
sauran option dole itace me budewa, benazeer na cinyar ama, batoul tsahonta baya kaiwa,dom haka ta
tattare tarkacen dake saman cinyarta ta miqe tana gyara top din jikinta hadi da gyara daurin scarf dinta
da santsinsa yasa ya kusa faduwa ta nufi qofar.

Adan darare ta bude,don jikinta yana bata shine. Kaman yadda ta zata din kuwa shine,yana
tsaye qyam daga bakin qofar,sanye da baqin trouser da baqar shirt short sleeve data fidda qirar
damtsensa sosai. Ya sakaye idanunsa cikin baqin glasses daya fitar da tsananin kyawun
fuskarsa,hannayensa dukka cikin aljihun trouser dinsa,wannan ya sanya ya sake cika qofar gaba daya.

Wani mugun kwarjini taji yayi mata,gabanta ya yanke y fadi. Ga mamakinta sai taga tamkar bai
ganta ba,ya dauke kansa yana shigowa cikin falon kamar bata wanzu a wajen ba.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200
_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/16, 9:16 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*
BOOK 02 PAGE 102

Dukka hankalinsa yana kan yarinyar,wadda itama tana ganinsa ta sake narkewa jikin ama. Cikin
nutsuwa da kuma girmamawa ya qaraso gaban kujerar da ama din ke zaune akai ya zauna sosai a qasa
yana miqawa benazeer din hannu. Nata hannun ta miqa masa sai ya jata cikin jikinsa yana jin yadda nata
jikin yayi dumi sosai

"Barka da warhaka ama" ya gaidata cikin girmamawa. Ajiyar Zuciya ta saki tana gyara zamanta,ita daya
tasan me take tunawa

"Barka kadai"

"Ya gida yame jikin?"

"Alhamdulillah da sauqi,ta karba magunguna ai,amma da yammar nan za'a maidata su sake gwada
jininta" shuru yayi hannunsa saman sumar yarinyar yana shafawa,tausayinta sosai yakeji haka kawai
yana ratsashi

"Akwai inda yake miki ciwo yanzun?" Ya tambayeta cikin nuna kulawa,kai ta gyada masa tana nuna masa
kanta,kan ya kama a nutse ya karanta mata addu'o'i,sannan ya zare idanunsa ya maida ga ama

"Wanne asibiti ne?,yanzun lokacin zuwa ganin likitan yayi?" Ya tambayi ama din

"Mamarsu ta sani.….." ta furta tana dan duban sultana,wadda tunda ta bude qofan ta zauna a hannun
kujerar dake daura da qofar. Haka kawai takejin jikinta dukka a mace,batason kuma wucewa daki don
kada ama taji ba dadi game da hakan da zatayin
"Alright" ya amsawa ama a taqaice. Miqewa yayi yana daukanta saman kafadarsa yace da ama

"Tanja tana kusa?,ta fiddo mata takalminta" ya amsa yana yin hanyar waje.

"Ki dauki takalminta cikin shoe rack,kisa mayafinki kuje" ama ta bata dukka umarnin lokaci guda tana
miqewa daga zaman da tayi don dauke batoul da bacci ya dauketa a wajen.

Kawai take dari dari dashi da kuma tsoro tsoro,kaman ta dojewa ama din amma kuma sam ba
zata iya ba,ala dole tayi yadda ama dij tace,ta fito sanye da wani mini hijab data dora saman doguwar
rigar jikinta.

A seat din kusa dashi ya zaunar da benazeer din,tanata zuba tabararta,yau aiki ya samu shi
kuma yana biye mata,tasa hannu ta bude seat din baya ta shige ba tare da tace komai ba,shima din bai
tanka ba ya kunna motar ya soma motsata suna barin layin.

Dukka dakiyarta da dauriyarta ta tattaro sannan ta hada kalaman

"Ina yini" lion eyes dinsan nan ya daga,ya kalleta ta cikin glass din gaban motar. Kamar idanuwanta
sunsan ita yake kalla itama takai nata duban ga mirror din,take idanunsu suka hadu waje guda. Shi ya
fara janye kallonsa daga kanta yana amsa mata murya ciki ciki

"Lafiya" yadda ya amsa mata din sai ya tsaye mata a rai,yayi mata kama da lokuttan baya ko tace
shekarun baya s nijer,sanda yake mata ire iren wadannan abubuwan a duk sanda sarautar tashi ta
motsa. Daga haka bai sake cewa da ita komai ba,itama bata sake fada din ba,to me zatace bayan ma
tasan bata da abun fada din.

Yana driving yana hira da yarinyarshi,sam kaman ma bata cikin motar,duk da benazeer na
zazzabi amma baki bai mutu ba,surutu kuma ba'a daina ba,a haka suka isa asibitin. Kaman dazu yanzun
ma daukarta yayi sukayi gaba,tana biye dasu a baya har suka isa reception. Shi ya gabatar da abinda
zasuyi da tattacen faransancinsa,suka bashi number ya tafi daga gaban office din yana jiran number su
ya nuna.
Sanda number ya fito wayarsa tayi ringing,ya katse kiran suka shiga office din likitan. Yar
asalin qasar faransa,me yawan fara'a da kirki da kuma son yara,tana ta jan benazeer da wasa,saita daga
kai tana murmushi ta dubesu

"beau couple,vous êtes parfaits l'un pour l'autre(kyakkyawan ahali,kun dace da juna)" ta qarasa fada
tana kallon fuskar sultana. Dan qaramin murmushi ta saki tana satar kallonshi ta gefan idanunsa,sai taga
shi duka hankalinsa ma yana kan wayarshi. Haka kawai taji ranta ya quntatar mata,wataqila wannan
yarinyar fa yake magana da ita?. Bata qarasa wannan tunanin ba taji yana cewa

"Je suis désolé, quand ils auront fini, ils me trouveront dehors, je lancerai un appel d'urgence au
téléphone(Yi hakuri, idan sun gama za su same ni a waje, zan yi kiran gaggawa a waya)" murmushi tayi

"aucun problème monsieur(babu matsala yallabai)". Matsawa yayi ya shafa sumar benazeer yana cewa

"Il n'y a pas de contestation(banda taurin kai),ba zasuyi miki allura ba kinji my angel?,see you soon" ya
qarasa fada yana dan jan kumatunta. Murmushi tayi tana bashi peck a bayan hannunsa.

Juyawa yayi ya fice a nutse yana sanya wayar a kunnensa.

Idanunta ta lumshe tana jan numfashi da kyau saboda wani motsuwa da ranta yayi,ta zaci uzurin
lalurar benazeer din tafi dukkan wayar da zai daga din muhimmanci?. Kiran sunanta da likitar tayi shi ya
dawo da hankalinta,ta sauka daga kujerar da take kai ta koma saman wadda ta tashi tunda tafi kusa da
likitan,tayi qoqarin tattara hankalinta don suyi abinda ya kawosu su gama.

Cikin minti ashirin da biyar suka gama komai,ta karba dukkan sauran magungunan da zataci
gaba da amfani dasu.

Sun fara fitowa zuwa haraban asibitin benazeer taja tunga ta tsaya. Ta juya tana kallonta,sai
babbata fuska takeyi
"Lafiya kuma?"

"Mummy ni ki daukeni" idanu sultana ta fiddo waje tana kallonta

"Dauka benazeer?,bakiga kinyi nauyi ba?, infact ma kin girma fa" narke mata tayi tana shirin sakar mata
kuka

"Mummy amma bani da lafiya fa,bakiga daddy dauka yakeyi ba?" Sak ta tsaya tana dubanta,wayo ya fara
sangartasu kenan?,to ita din ba zata lamunta ba,don haka ta hade rai tsam tana dubanta

"Ba zan daukeki ba don kin fara wayau ai,ki wuce mu tafi ko kuma ki jira daddy din naki yazo ya daukeki"
qafa ta soma bugawa zata tabare mata,wannan din ya fusatatata ta daka mata tsawa sosai.

Har inda yake tsawan ya taddashi,sai ya leqo da kanshi daga seat din driver da yake zaune
qafafunsa a waje yana amsa waya ta handsfree. A kansu idanunsa ya sauka,sai ya dauke kallonsa ya
maida kan diyarshi.

Hawaye takeyi sosai tana share fuskanta da bayan hannunta,suna hada ido ta tako da gudu ta
qaraso wajensa ta fada jikinsa.

"Daddy mummy ce...... " Benazeer din ta fada cikin shesheqar kuka. Cikin jikinsa ya sanyata sosai yana
fadin

"Am sorry,cool down B" ta samu abinda takeso saita lafe tana goge hawayen.

Fuska a hade tana sake kama kanta ta bude back seat kaman yadda sukazo ta shiga,tana shirin
maida murfin ta rufe muryar data dade da haddace ta waye taji ta cika motar,da alama waya yakeyi,ya
kuma jona wayar da speaker din motar
"Halan waye ya taba B?" Laila ta fada tana fidda murmushi me sauti. Ware idanu benazeer tayi wadda
itama batasan waya akeyi ba,ta kalli maina sannan ta kalli speaker din

"Mummy ce"

"Rabu da mummy,sai an zaneta ko?" Laila da batasan alaqarsa da benazeer ba ta fadi. Murmushi
benazeer ta saki tana leqen sultana dake baya. Ba benazeer ba,ko maina bai isheta kallo ba. Saidai wani
abu da yazo ya tsaye mata a wuyanta me matuqar tauri da zafi.

Dama da yace zai amsa kiran gaggawa wayo zaizo yi cikin motar da wannan yarinyar?,ashe su ya
rainawa.hankali,kenan ciwon bai dadashi da qasa ba?,kawai sai taji idanunta sun fara mata yaji
yaji,alamun suna neman dalilin da zasu fidda qwalla,saidai kuma cikin tsananin dakiya sa jarumtarta ta
girgiza kai alamun a'ah,akan meye zatayi qwalla?,shi din waye da zatayi masa qwalla

"Am on my way"

"Saika qaraso dear........" Ta fadi tana katse kiran da sauri kaman wadda tasan tayi laifi.

Sallamarta ta qarshe sai ta dinga mata amsa kuwwa cikin kunne,tana ji ya tayar da motar suka
fara fita daga asibitin,batace komai ba,bata motsa ba kuma bata bude idanunta ba.

Tana jin hirarsu daya bayan daya,wanda duk kalamansa a nan zallar qauna kulawa da soyayyar
da yakema yaran suke nuna kansu. Batasan me yasa shariyarsa take mata ciwo a zuciya ba,bayan irin
wannan abun ta jima tana buqatar ya dinga yi mata,a yanzun data samu kuma batasan me yasa ta kasa
jin hakan dai dai bane.

"Bari naga wata" maina din ya fada yana rage gudun motar tashi,sannan kuma a hankali ya soma
gangarawa gefen titi kusa da wasu shops yana neman area din da ake parking
"Alhamdulillah" ya fadi bayan ya tsaida motar,ya kasheta yana bude side dinsa ya zura qafafunsa waje.

Kamar a mafarki cikin rufaffun idanunta taji muryar yarinyar dab dasu,gabanta yayi wani
mummunar faduwa,hakanan ba tare data shirya ba ta soma ware idanun nata sanda muryarta me karadi
ke tashi

"Na gode sosai da ka bani damar ganin B......B.....how far?,ya jikin?" Ta fadi da murmushi sosai saman
fuskarta tana yunqurin xagayawa side din kujerar benazeer.

Sisiririyar bafulatana sanye da gown na chiffon da bata sauka idanun sawunta ba,ta sanya
qaramin scarf ta manne idanunta da baqin sun glasses,qafafunta saye da takalmi sneakers daya dace da
material din.

A shekaru zata iya bata shekara uku,a kyawun sura kuwa tabbas koda wasa ba zatayi gigin shiga
sahun da sultana take ciki ba, ba'a maganar diri da structure na jiki,amma a idanun sultana sai taga gaba
daya ta kowanne fanni ma kamar ta kere mata.

Sanda ta bude side din benazeer din ta sako kanta tana bawa benazeer hannu tare da
tambayarta jikinta duk dai taji kaman iskan wajen yana neman yi mata kadan.

A nutse ta dauki wayarta da qaramar jakarta,ta sanya hannu ta bude murfin motar ta sanyo
santala santalan fararen qafafunta waje tana fita a motar,wannan motsin ya sanya laila ta ankara da
zaman mutum a seat din bayan.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*
*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107
*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/16, 9:16 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 103

Qamshinta da motsinta yaja hankalin laila,ta daga kanta tana bin bayanta da kallo. Bataga
fuskarta ba amma gabanta yayi wani mugun faduwa

"Mummy karki tafi ki barni" benazeer da taga fitan sultana ta fadi. Sosai tayi qoqarin daidaita mode na
fuskarta sannan ta waiwayo,sai a lokacin laila da take binta da kallo ta samu daman ganin fuskarta da
kyau.

New TV show presenter Sultana mohmoud,ta shaida fuskarta,tun a ranar data fara program
din,a ranar aka fara ganinsa da ita,a ranar kuma taji tayi matuqar burgeta,har ta dinga jin tamkar itama
ta sauya hannu ta koma aikin jarida. Qwarewarta kawai zai sanya kayi tunanin ta dade a harkar,kyanta
ya burge laila qwarai ya kuma bugar da ita,to amma kuma me takeyi a mota tare da maina?. Saurin
kauda tunanin daya darsu a zuciyarta tayi,muddin ya kasance wata alaqa ce data danganci soyayya
tsakaninsu to tayi imanin kashinta ya bushe,don ita kanta da take mace tahi imanin wanda yake da
sultana babu abinda zaiyi da ita.
"Zan shiga in sha coffee" ta bawa benazeer amsa tana shiga shagon coffee dake daura dasu.

Jakarta kawai ta daura saman table din,ta kuma order din coffee din,yanata zuba tururi da
qamshi a gabanta amma batasan meye zatayi dashi ba,haka kawai zuciyarta dukka taqe a quntace,
idanunta nakan qofan Glass din da ta yiwa wajen qawanya,wadda bata hana wanda ke ciki hango kai
kawon jama'ar waje.

Agogonta ta duba,a qalla mintuna goma da shigowarta wajen kenan,sanda zata daga kai daga
agogon benazeer ta shigo

"Mummy kizo wai mu tafi, za'a ajjiye aunty laila a hanya"

"Aunty laila?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar tana duban idanun benazeer. Kai ta gyada tana kallon
sultana din. Numfashi ta ajiye tana qoqarin controlling kanta

"Ku wuce zan biyo ku a baya" ta bata amsa tana jawo cup din takai bakinta wai ko hakan zai rage mata
abinda takeji.

Kaman ba zata motsa ba yarinyar sai kuma ta juya tana fita a wajen a sanyaye.

Yana jingine da jikin motar yayi crossing qafafunsa ya kuma goye hannayensa a qirji yaga
fitowarta ita kadai,idanunshi a kanta har ta qaraso

"Daddy tace wai mu wuce zata taho".idonsa ya lumshe gami da budesu duka lokaci daya

"Me kikace mata?" Ya tambayeta


"Da waye kikace mata zamu tafi?" Ya sake gyara tambayar yadda zata fahimta

"Da aunty laila....."idanu yadan zaro sai kuma ya saki murmushi. Ya samarwa laila taxi kuma har ta
wuce,don shima bawai yanason yadda take rabarsa bane,kawaidai yana tuna karamcin daddy da
mutuncin sardauna,tanacin darajar mutum biyu.

Mota ya budewa benazeer ya kwnatar mata da kujera sannan yace

"Zauna,karki fito har sai na dawo,ki zauna kiyi game ko ki kwanta" ya fadi yana fiddo mata wata mini
game wadda dama ya ajeta cikin motar ne sabodasu. Baki ta washe tana karba da sauri,ta kwanta abinta
kuwa tana maida hankalinta ga game din.

Hannun rigarsa ya gyara sannan ya fara takawa zuwa cikin coffee bar din.

Tunda ta kurba sau daya bata qara ba,ta ajjiyeshi a gabanta tana juya tea din da spoon,tayi nisa
a duniyar tunanin da batasan ina ta tafi bama,sai inuwarsa ta gani saman kanta.

Yayi qyam a gabanta da wanna tsahon nasa da dakiyarsa,fuskar nan ta fito a asalin sunansa na
aliyyu haidar,ya motsa bakinsa cikin wata ginshira da izza data jima rabon data ganta tattare dashi

"Kin shiya tafiya da qafafunki ko kuma ni kike jira na daukeki?" Ya mata kwarjini sosai ta yadda ba zata
iya kallon cikin idanunsa ba,amma duk da haka tayi namijin qoqarin kauda fuskarta gefe

"Idan kika qara minti daya zaune a wajen nan da hannayena xan daukeki,kuma kinsan hukuncinki basai
na gaya miki ba......and benazeer ba zata hana aiwatar da komai ba" yayi maganar yana gyara hannun
rigarsa. Ba shiri ta suri handbag dinta tana miqewa tsaye. Hannu ya miqa mata yana tsareta da idanu,ta
fahimci abinda yake nufi,don haka ba musu ta miqa masa hand bag din,ya sakata a gaba suka fice daga
wajen bayan yaje ya biya kudin abinda ta karba din.
Da kansa ya bude mata gidan gaba yana basarwa,tadan dubi benazeer da tayi kwanciyarta a
baya,ta shiga a hankali ta rufe,ya daidaita zamansa ya tayar da motar.

Bai ajesu gida ba sai daya gama yawon yima yaransa siyayya kaf,kaman ta sanya hannu aka ta
saki ihu,don sam zaman cikin motar ya gama gallabarta,shi da benazeer kawai suke sabgarsu,yaqi sakata
ma a cikin hirarsu gaba daya.

Koda ya ajesun ma bai shiga gidan ba ya juya abinsa bayan ya raka benazeer da sayayyarsu har
bakin qofa,ya tsugunna yayi kissing nata ya wuce.

Itama dauke kai tayi ta wuce ciki,saidai kuma can qasan ranta tana jin wani qunci yana saukar
mata. Ba abinda idanunta ke nuna mata sai yadda yake hira sosai da wancan yarinyar tashi,wai wacece
ita?,meye ne alqarsa da ita?.

"To ke menene sha'aninki da ita?,suje su qarata mana" wani sashe na zuciyarta ya gaya mata,saita ja
tsaki tana qoqarin fincike komai daga ranta, tsakin da ya sanya ama waiwayowa ta kalleta,tayi sauri ta
dake ta dauki jakarta tana wucewa ciki.

Duk yadda taso fidda abun daga ranta tayi amma a banxa,don sanda ta kwanta saman
gadonta,sanda garin ya sake daukan shuru,dare ya fara nisa sai komai yake neman kwance mata,ta dinga
laluba murmushi guda daya tak da yayi mata a yau din ta rasa,magana tsakaninta dashi bata iya tuna
guda daya ba,hirarsa kaf da yarinyarsa sukayi suka gama har suka rabu.

A daren yau din saita samu kanta da sauraren bakin qofarta wai ko zataji kusurkusur ko
motsinsa,ta dinga juyi saman gadon ita daya,daga hannun dama zuwa hagu. Bacci taketa buri da fatan
tayi amma yaqi zuwa mata,gefe guda ga wani muguwar kasala da mutuwar jiki data saukar mata,sai kace
wadda aka yiwa dukan tsiya,ko ina na jikinta ta dinga ji yana mata ciwo,duk burin da taci nayin bacci
isashe don ta samu gabatar da program dinta a gobe cikin karsashi da fara'a dukka ya zagwanye. Bata
taba ji jikinta na mata ciwo irin haka ba,ba kuma wai bata da lafiya bane,batasan meye dalili ba. Wannan
abu biyun su suka taru sukayi mata rubdugu suka nakasa baccinta,don ba itace bacci ya dauka ba sai da
biyu na dare ya raba.
Da sassafe taso fita a washegari wai ta shammaceshi kaman wancan karon,to saidai yanayin da
takeji jikinta na kasala ya sakata shiryawarta dama komai nata ya zama a sanyaye. Koda ta buda break
din da tanja ta hada mata sai taji cikinta ya cushe ta kasa ci,don haka taja tissue kawai ta goge
hannunta,ta dauki key dinta da hand bag tayi hanyar fita,daidai sannan ta kalli agogo. Duk saurintama ya
tashi a banza,don a irin wannan lokacin yake shigowa gidan. Amma kuma sam bataga alamun gidan a
bude ba ko kuma da mutum a ciki.

Tana shirin tashin motar kiran bibi ya shigo,ta zauna daga gaban motar tana amsa wayar, jifa
jifa idanunta nakan qofar gidan,tamkar wadda ke tsammanin fitowar wani ko wata,saidai qasan
zuciyarta ta tabbatarwa kanta babu wanda take tsimaye. Sukayi sallama da bibi,ta ajjiye wayar a gefanta
tana sake kallon qofar gidan,sai taja siririn tsaki ta tayar da motar a kasalance tana barin layin nasu.

Sanda ta isa tv station din ta samu ma'aikata sosai,don yau batayi sammakon da tayi jiya
ba,duk inda ta gifta saita gaisa da mutane,batasan da wanne irin farinjini ta shigo tv station din ba,qauna
suke nuna mata sosai,duk kuwa da cewa ba ita daya bace 'yar Africa a wajen.

Bugun zuciyarta ne ya dinga qaruwa sanda take lalubar key tana qoqarin bude office din,sai
takeji har cikin zuciyarta kaman zata taras da wani a cikin office din,kamar wancan lokacin......kamar
waccar ranar.....

"Maina?" Wata zuciyar ta tambayeta

"Ban sani ba" tayi saurin amsawa kanta da kanta rana murguda baki kaman ita da wani ne.

Sanda qofar ta bata sautin ta budu daita aza hannunta saman qofar tana jin yadda bugun
zuciyarta yake qaruwa,sai data kulle idanun nata taja numfashi da kyau sannan ta tura qofar a hankali ta
sanya qafafunta.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*
*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*
09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/17, 10:03 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 104

Dukka idanun ta wara sanda ta shiga office din, zuciyarta na bada sautin bugun da har ya take
iya jinsa ga kunnenta. Office din fetal yake,babu kowa babu ma alamun an shigo tun bayan gama gyara
mata shi da akayi. Sosai ta wara hancinta wai ko zata jiyo wani baqon qamshi daban,ba qamshin komai
saina freshner da ake mata using nata cikin office din. Jinta tayi kaman an buge mata gwiwarta,haka
kawai taji ta sare,qwarin gwiwarta ya sake raguwa,dannkarsashin data samu daga qasa zuwa
hawowanta sama dukka babu ya zagwanye.

Jikinta a sanyaye ta isa cikin office din,ta ajjiye tarkacen hannunta taja kujera ta zauna tana
maida numfashi. Ta sake bude idanunta,sai suka sauka saman kujerar,inda ya zame duk kayan jikinta da
inda ya zaunar da ita,tsigar jikinta tayi wani irin tashi,ta runtse idanunta tana kiran sunan Allah hadi da
lullube fuskarta da tafin hannunta. Sosai takejin zafi cikin zuciyarta,tayi imani yarinyar ce ta tareshi,qilan
ma yanzun haka suna tare,ai hakan bai taba faruwa ba sai yanzu,sai yanzu da tazo qasar.
"Idan yazo meye zaiyi miki?,ina ruwanki dashi?" Ta yiwa kanta da kanta tambayar

"Aifa" ta sake bawa kanta amsa. Knocking din da akeyi ya sanyata miqewa tana nufar qofar,gabanta
nadan faduwa tana tunanin ganin wani abu da zai wanke mata wannan kai kawon da zuciyarta keyi.
Saidai kuma sanda ta bude din da

Dioura ce da fuskar nan tata ma'abociyar fara'a. Qoqari tayi ta tattaro dukka fara'ar dake kan
fuskarta dama qasan zuciyarta tana mata sannu da zuwa cikin harshen abzinanci. Ta amsa mata itama ta
bata waje ta shigo.

Shigowar dioura ya debe mata kewa sosai,qarasa tattaunawa da kuma tsara daukan program
din suka qarasa yi.

Ita daya cikin dakin sauya tufafin na musamman da aka tanadar mata a cikin office dinta,tayi
wani fitinannen kyau cikin laffayar me azabar kyau da tsada,idan ka ganta a sannan zakayi tsammani
shuwa ce,duk suturan data sanya yana karbarta ainun haka jikinta yake.

Fuskarta take kalla,tanason bawa kanta qwarin gwiwar shiga studio din. Ta jima tana zumudin
randa zata gabatar da al'adun kanuri saboda yadda abubuwansu suke burgeta,yau ranar yazo,amma kaf
ta rasa duk wani walwala da nishadi da take da buqata. Ga kasalar da take sake saukar mata,tana jin
kanta da idanunta tamkar wadda ta tara bacci na shekaru aru aru a kanta.

Siririn tsaki taja sanda akayi knocking qofar dakin,sannan kuma tace

"Ina fitowa" ta sake juyawa tana gyara fuskarta,tana ambaton sunan Allah a hankali a hankali wai ko zata
samu sassauci daga dukkan abinda takeji din.

"Wow......bansan wanne shiga bane yafiyi miki kyau,na last week ne ko na wannan satin?" Dioura ta fadi
da kwantaccen murmushi da gurbatacciyar hausarta tana kallon sultana. Dan murmushi da yafi kama da
na yaqe ta saki tana maida abubuwan hannunta data cire cikin jaka.
Har sun soma ficewa ita da dioura saita tsaya,tana buqatar wani abu da zai dawo mata da
karsashinta cikin jikinta,idan ta fita a haka tabbas ba zata taba bada abinda program din yake buqata ba.
A nutse ta koma ta zauna,ta fidda wayarta ta soma kiran layin ama.

Dab da zata katse ta daga da sallama a bakinta

"Good morning ama"

"Morning sultana,ban tashi da wuri ba yau din,tanja tacemin har kin wuce"

"Eh ama......"

"To ma sha Allah.....ina fatan komai lafiya?" Ta tambayeta saboda yanayi muryarta daya bata kaman
akwai wani abu

"Lafiya alhamdulillah,zan shiga program.......ina buqatar addu'a" ta qarasa fada muryarta na danson yin
rawa. Tausayinta sai ya saukarwa ama,ta dinga ji a ranta inda mahaifiyarta tana raye tabbas ita zata kira
ta nema addu'a kaman haka,maraici ba dadi komai gatan da zaka samu,gatan uwa daban yake,mahaifiya
kuma ba madadinta.

Sai muryar ama da jikinta dukka sukayi sanyi,cikin nuna kulawa tace

"Allah ya bada sa'a,yasa a gama lafiya.......zaki magana dasu batoul ne?"

"Eh ama" ta fadi qasa qasa cikin dan jin nauyi

"Gasu" ta fadi tana miqawa yaran wayar.


Da zumudinsu suka soma magana da ita don yau basuje school ba saboda jikin benazeer,koda
batoul taje ita daya ba lallai ta zauna,shi yasa ama tace a barsu duka,ta dinga murmushi tana biye
musu,a qalla sun kusa mintuna goma da ita tana biye dasu kafin tace su bawa ama wayar sukayi sallama.

Iska ta furzar daga bakinta tana kallon fuskar wayar,ta samu relief kaso hamsin cikin dari,amma
ta rasa gane dalilin da ya sanya wannan gurbin ya gaza cikewa,ta rasa me yasa ta kasa samun satisfaction
dari bisa dari?. Idanunta ta rufe tana karanto addu'o'i,tana jin zatayi managing da 50% din data
samu,don haka ta miqe tana fita daga office din.

Ita kadai tasan yadda tayi forcing kanta tayi program din,a fuska ne kawai take da karsashi da
kuma kuzari,amma cikin zuciyarta da gangar jikinta wani irin emptiness take ji.

Ita daya ta koma office ta zare dukka kayan data gabatar da program din dasu duk da cewa sun
zama mallakinta. Haka kawai taji bata da buqatar barinsu a jikinta,ta maida kayanta data taho dasu ta
koma saman sofa tana maida numfashi. Kanta ta juya tana kallon agogon wayarta,ta gama abinda ya
shigo da ita gidan don haka tana tunanin komawa zatayi gida,don kasalar dake jikinta koda ta zauna ba
zata barta tayi komai ba. Komai nata ta tattare tayi sign-in ta wuce parking lot,ta zuba duka tarkacenta
cikin motar ta shiga ta tayar da ita ta fice daga gidan.

^^^^Motsa jiki yayi a safiyar na tsahon mintuna talatin da biyar,sosai yake jin kanshi fresh a safiyar,don
jiya ya samu yayi bacci isashe ba laifi. Direct ya wuce toilet yayi wanka,ya dawo ya shirya kansa cikin
long sleeve shirt da dogon trouser. Yayi wani fresh sosai kaman yadda zuciyarsa yake jinta da sauqin
damuwa a ciki. Ta falo ya dawo yana duba abubuwan da suhail yayi kafin ya fita a gidan,bai jima ba
yaron dake musu share share ya qaraso,sai ya matsa bakin window ya bashi space don ya gyara gidan.

Idanunsa saman gidan,yana kallon abun hawa aba,abinda yake tabbatar masa da aba bai fita ba
kenan. Yanason shiga yaga batoul da benazeer,ya kuma gaida ama,amma bayason aba din yasan da
wanzuwarsa a unguwar,har yanzu wannan lokacin baiyi ba, yafison yayi nesa dashi,ya tabbatar hakan zai
sanyata yaci gaba da jin kewarsa.

Idanunsa ya mayar side din window dinta,idan ya rantse bazaiyi kaffara ba ya tabbatar ta wuce
wajen aiki ne,barin hali sai mutuwa,sai kuma yanzun da ya tasamma sauyata. Murmushi ya kubce masa
sanda ya tuna yanayinta a jiyan,indai har da gaske ne abinda yake gani cikin idanunta kishi ne hakan
yana nufin akwai soyayyarshi koda bame yawa bace a zuciyarta?. Ajiyar zuciya ya saki,yana jin kewarta
sosai cikin kowacce jijiya dake dauke da alhakin zagayawar jini a jikinta,to amma yanajin dole yadanyi
step down kadan don yayi taste akan irin nata soyayyar a kanshi.

Matsawa yayi daga jikin window din sanda wayarsa ta dauki tsuwwa,ya juya a hankali yana
nufar wajen wayar,a yadda ya tsara din yau gaba daya bazai fita ba saboda shirye shiryen tafiyar da
zasuyi shida suhail na sati uku. Haka kawai bayason yin tafiyar,don bayason yayi nesa da ama da twins
dinshi,to amma kuma hakan ya zama dole,don daddy ya nema alfarma a wajensu su wakilceshi,daddyn
kuma yafi qarfin kowacce kalar alfarma a wajensu.

Tunda ya fita ya dawo ma bai duba wayar ba sai yanzun,tarin miscals ya samu,ciki harda na
ayana wanda ya kusa guda goma. Yadan tsuke gira kadan,yana shirin yayi deleting na miscals din wani
kiran na ayana ya sake shigowa.

Hakanan ya daga ba don ranshi yana so ba,surutunta har hawan masa kai yakeyi,baisan inda ta
gaji surutu ba,tunda dai shi yasan uncle tahir ba haka yake ba.

Da dakakkiyar muryar nan tashi yayi sallama,sallamar data sanya ayana shiga taitayinta,murya
ce me ratsa zuciya da qwaqwalwar wanda ake magana dashi

"Good morning yaa haidar"

"Morning,kina lafiya?"

"Lafiya Lau nake,na kira ne na gaya maka yanzu haka ina airport,yau ne taho wana,transit daya zamuyi
kuma,ina saka ran nan da wajen dare anan paris in sha Allah ina Paris"

"Yayi kyau,Allah ya tsare hanya....."


"Amma ya haidar......baka manta dai da alfarman da daddy ya nema min ba ko?"

"Name?" Ya tamabayeta don shi bilhaqqi ya manta

"Habba ya haidar........daddy fa ya gaya maka,kaine wakili na......ya wakiltaka akan al'amurana a cikin
Paris"

"Oh......,karki damu,muna tare da ama,kuma nasan She will do her best to take care of you.......ina da
harkoki da yawa,ba komai ne zan iya concentrating akai ba" shuru ta danyi jikinta yana sanyaya,anya
abinda take gani me sauqi ne zayazo da sauqin kuwa?.

"I know yaa haidar....but kulan mace da namiji ba daya bane......"

"She's the one who raised me......so that tana iya kula da 'ya'ya dari ma" ya datsi numfashinta. Yanajin
yadda ta aje numfashi,sannan muryar qasa qasa tace

"It's okay,saina qaraso"

"Safe flight"

"Thank you" ta amsashi tana jin dadin fatansa na qarshe a gareta.

Iska ya furzar,ya soma gajiya da wadannan abubuwan,ga laila sai kuma ga ayana ta
taho......ayana me sauqi ce a gareshi,laila dince yake komai da takatsantsan a kanta,ta yadda komai idan
ya tashi qarewa tsakaninsu za'a yishi cikin girma da mutunci. Wayarsa ya mayar aljihu,ya koma bakin
window din ya duba,ba motar aba,hakan kuma yana alamta mishi ya fita kenan,don haka ya koma ya
zura lallausan fluffy dinsa yana fitowa daga gidan,yana buqatar ganin ama.
_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261
*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/17, 10:03 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 105

Ya samu qofan a bude,don haka ya turata kawai ya shiga da sallama. Suna saman carfet sanye
da wasu pink loungwear,an raba musu sumarsu me tsaho gida biyu,kowacce an kameta da pink din
ribbon da ya dace da kayan jikinsu,sun yiwa building blocks baja baja a falon sunata qoqarin hadawa.
Ama na zaune saman kujera,gabanta dan madaidaicin table ne da system akai,da alama wannan lissafe
lissafen nata da ya santa dashi shekara da shekaru takeyi,akwai madaidaicin tray daga gefanta,da alama
late breakfast zatayi ko kuma takeyi din.

Building blocks din dake saman cinyarsu suka watsar sunata qoqarin tararsa. Tsaiwa yayi yana
kallonsu murmushi ya subuce masa,kafin su iso sai ya goce,sannan kuma ya miqa hannu ya dauki
benazeer. Baya batoul tayi tana kyabe baki alamar zata saki kuka
"Daddy nifa?"

"Benazeer ce bata da lafiya,baki gani ba har wadannan kumatun sun zazzage?....." Ya fada yana jan
kumatunta wadanda da gaske sundan ragu,sai kuma ya dora da cewa

"Kin manta kuma ke din babbace,qanwarki ce ita fa" hakan daya fada sai ya faranta mata ta fara tsalle,ya
saku murmushi ya duqa yana miqa mata hannunsa,saita riqe ta tattakashi itama ta haye kafadarsa suka
nufo ama,wadda a haka zaka dauka batasan me yake faruwa ba,saidai tana karance dasu. Duk sanda irin
hakan zata faru ita kadai tasan farincikin da takeji, addu'a daya takeyi Allah ya sanyaya zuciyar
sultana,tana da matuqar buqatar tarin jikoki,musamman da bata haihu da yawa ba,takanji kamar ta yiwa
almu da saddi aure,saidai sunyi qanqanta sosai,amma tana ji a jikinta ko shekarun maina ba zasukai ba
zata aurar dasu da ikon Allah.

Da qyar suka bari ya gaisa da ama,suja tattaro masa blocks din sukace lallai shima ya hada nasa
aga waye zaiyi abu me kyau. Yanata murmushi ya fara diban nasa,yana sane ya dinga hada shirme
sunata masa ihu,sai ya narke fuska shima kaman qaramin yaro ya dubi ama

"Ama kinga abinda sukema danki ko?" Tun bata kulasu har dole ta dinga sanya baki a ciki,ita ta dinga
raba maki ba yadda ta iya. A daidai lokacin qararrawar qofa ta buga,tanja ta baro kitchen zata bude yace
ta koma taci gaba da aikinta,ya tashi yana gyara hannun rigarsa daya tattare ya nufi qofar.

Bata kawo komai ba sanda ta danna bell,don haka tana tsaye sosai tana jira a bude mata,duk
ta qagauta ta qarasa cikin gidan,kwanciya kawai take da buqatar yi ko zata samu mode dinta da abinda
takeji a jikinta ya koma daidai.

Shi da ita duka basu tsammaci ganin juna ba,idanunsu suka sarqe waje guda,kowannensu sai
ya kasa janye nashi idon,kamar masu kallon quda na wani sakanni,sai yayi hanzari janye idanunsa yana
juya ciki jikinsa a mace.

Duk wani feeling nashi da yake qoqarin dannewa yana controlling nasa tasa kakkaifar qwayar
idanunta cikin qasa da second sittin ta rusashi,gaba daya ta saukar masa da kasala,ta tayar masa da wani
irin abu cikin sassan jikinsa,amma duk da haka da yake namijinne da gaske, sai ya yaqi hakan saman
fuskarsa,ya koma cikin yaran ya zauna sosai abinsa kamar dazu.

Da qyar ta daga qafanta ta sanyo kai cikin falon tana yin sallama,kallo daya ama tayi mata ta
karanci ba cikin daidai dinta take ba

"Sannu da gida ama" ta furta tana qoqarin qaqalo murmushi,don ita kanta taji idanunsa har cikin
tsakiyar jikinta,wani kakkaifan kallo daya tayar da kowacce tsiga ta jikinta,ya aike mata da wani irin saqo
me nauyi,saqon da taji inama ace zaya shimfida mata kyakkyawan qirjinsa ta samu masauki a ciki,tana ji
tana kuma tsammani a nan ne kawai zata samu sassaucin abinda takeji,a nan ne kawai zata samu
nutsuwar da take da buqata.

"Yauwa sultana......lafiya kuwa?" Ta tambayeta tana tattara hankalinta a kanta sanda ta matso kusa da
ama din tana kwashe mata takardunta da suka zube a qasa

"Laf.....fiya ama,na gama abinda najeyi ne" amsar data bawa ama din sai data sanyashi lumshe
kyawawan idanunsa. Yanzu haka a wannan safiyar miliyoyin maza nawa ne suka kalle masa
fuskarta?,anya zai qyaleta a haka kuwa?,zai iya ci gaba da yi mata wannan zurun?.

"Gajiya ce kenan?" Ta sake tambayarta,saita gyada kai kawai ba tare da tace komai ba

"Saiki shiga ciki ki kwanta ai ki huta sosai,may be idan kika samu bacci zakiji kin ware"

"To ama" ta amsata tana riqe kayanta da kyau. Sai sannan benazeer da batoul da hankalinsu yayi nisa a
wasa da daddynsu sukayi mata sannu da zuwa. Tadan saci kallonsa na abinda yayi qasa da second biyu
sannan ta watsa musu harara

"Sai yanzu kuka ganni?,banason sannu da zuwan" murmushi ya qwacewa ama,har sai data dora
hannunta saman bakinta kadan ta maida jikinta bayan kujera tana lumshe ido
"Yaro man kaza" ama din ta fada qasan ranta. Tanajin yaran suna fadin

"Am sorry mommy.....am sorry mommy".

"Naji" ta fadi,cikin dakewar da takeson nuna tsananin kamun kanta tace

"Barka da rana" saidai tayi maganar ne tana kallon gabanta. Kamar baijita ba haka yayi mata,yasan daya
daga cikin abinda bataso kenan.

"Ina wuni" ta sake maimaitawa wani abu yana tsaya mata a wuya

"Maina bakai ake gaidawa ba?" Ama tayi saurin kawo qarshen drama din

"Oh.....sorry ban ganta ba,kina lafiya?" Ya amsa yana duba letter A cikin tarkacen building blocks din.
Kasa amsa masa tayi,don tayi imanin idan ta bude baki kuka zata sake masa,sai kawai ta qara wuta ta
wuce dakinta.

Tana maida qofar suka hada idanu da ama,har tayi kaman ta jefa masa harara sai kuma ta dauke
kai saboda wani tunani da tayi,bata harareshi ba amma ya fahimci harara taso jefa masan,sai ya qunshe
dariyarsa yana dauke kai,ya maida kai ga yaransa.

Tana ajjiye jakarta saman gado taji damshin hawaye ta eyelashes dinta,takai hannu ta tabosu,ta
dawo da dubanta kan yatsun nata

"Kuka kuma?,na me?" Ta tambayi kanta cikin qarfin hali,duk kuwa dacewa sosai takeji wani abu yana
damunta a zuciya

"No" ta fadi tana girgiza kai,tana gayawa kanta kada tayi kukan,tayi qoqarin hadiye komai,sai kuma taji
zuciyarta tana bala'in tashi.
Gefan gadon ta samu ta zauna,ta dinga jan numfashi me zurfi tana kuma fesar da wani,dukka a
qoqarinta na daidaita damuwarta. Ta kusa kashe minti ashirin a haka sannan ta danji dama dama,sai ta
tashi ta cire kayan jikinta,ta nemo riga da skirt free size masu taushi ta saka.

Idan zata iya tunawa wunin yau babu abinda ta sanyawa cikinta,bata kuma jin yunwar kwata
kwata,a cushe takejin cikinta,to amma kuma koma meye bai kamata takai har irin wannan lokacin ba
tare da taci komai ba,don haka ta sanya baby hijab saman kayan ta fito kitchen ko zata samu wani abu
taci.

Qin yarda tayi kwata kwata ta kalli sashen da suke,ta maida dubanta ga qofar kitchen din da take
tunkara,saidai duk da haka hakan bai hanata jiyoshi yana gayawa ama saqo ba

"Zuwa dare idan Allah ya kaimu ayana zata iso,nace bari na gaya miki,zanje daukota around 8,don munyi
magana da uncle tahir ya bani ita........" Bata bari ta gama jin sauran abinda yake fada ba ta shige kitchen
din da sassarfa,ayana.....tasan ayana sosai,kusan mate ne ita da ayana din,duk a sannan ayana din ta
bawa sultana shekara daya. Ama nason ayana don 'yar yayanta ne uwa daya uba daya,sannan a baya
tasha jin uncle tahir yana tsokanar maina zai bashi ayana.....tun maina din yana dan makaranta.

A birkice ta dauko fresh milk,ta bude da zummar tasha ko zata wuce da abinda ya tsaya mata a
maqoshi,amma data sanya baki sai taji ba zata iya ba,don haka ta dauki qaramar tukunya ta juyeta a
ciki,ta jefa citta da kanunfari da cardamom da kuma mint fresh mint leaves da basa rabo dashi,ta rage
wutar can qasa,ta goye hannayenta a qirji ta zubawa tukunyar idanu tunaninta kuma yana lulawa wata
duniyar ta daban.

Sanda ama ta tashi tana shiga dakinta dauko wasu files ya samu ya miqe yana miqawa batoul
gidan daya hada mata

"Ina zuwa,bari na samo ruwa" ya fadi yana gyara bottom na rigarshi,ya soma takawa zuwa kitchen din.
Tunda ta wuce hankalinsa yayi can,yadda ya karanci sultana yayi imani koda mahaifiyarta a yanzu da
zata dawo duniya ba zatayi mata karatun da yayi mata ba,ya tabbatar daga jikinta har zuciyarta bata jin
dadinsu,to amma wannan hanyar daya biyo ita daya ce sassauqar hanyar da zata kawo musu qarshen
komai,don dukka wata jarrabawa da zaiyi game da ita ya gama yinta,ya kuma gama fahimtar inda ta
dosa gaba dayanta.

Tun kafin ya qaraso yaga madarar ta cika tukunyar tana kuma zubewa,yayi mamakin ganin tana
tsaye a wajen amma bata lura da hakan ba,yadan qara sauri kadan ya isa bakin gas din ya kashe.

Gilmawarsa ta sanyata ankara da shigowarsa amma saita gaza motsawa daga wajen,tana
kallonsa ya dauki rariya da cup ya tace madarar,ya dawo kusa da kitchen cabinet inda take tsaye,ya bude
ya dauko zuma ya zuba ya sanya spoon ya barta a wajen. Ya qarasa bakin freezer dake daya side din ya
fiddo ruwa mara sanyi cancan sannan ya juya yana barin kitchen din.

Samun kanta tayi da binsa da kallo,yana qarasa ficewa sai taji hawaye ya silalo mata,ta shafo
hawayen tana kallonsu

"Again?" Ta tambayi kanta muryarta tana rawa,kawai saiga wasu hawayen sabbi suna sake fitowa.

"No.....no" ta fadi sau biyu a jere tana girgiza kanta,saita matsa gaban fanfo dake kafe a sink ta kunna,ta
fara tarar ruwan tana wanke fuskarta dashi. A qalla ta kusa mintuna biyar a haka kafin ta samu nasarar
tsaida hawayen,saidai abinda takeji a cikin zuciyarta bai sauya ba.

Da kadan kadan take kurbar madarar,sai taji tana zauna mata sosai,a hankali ta shanye,wanda
tun kafin takai ga ajjiye kofin jikinta ya sakeyin weak,wani kasala ya sake sauko mata,saita ajjiye cup din
a daddafe ta fice a kitchen din. Yaga fitarta,ya rakata da idanu har ta shige dakinta saiya fidda ajiyar
zuciya a sirrance yana dauke kanshi.

Sosai ta duqunqune cikin duvet tana jin sanyi cikin qashinta kamar wadda zazzabin cikin qashi
yake neman kamawa,ta lumshe idonta tana fidda numfashi,ita kanta zuwa yanzu ta tabbatar ba lafiya
lau take ba,ta dinga karanto addu'o'i cikin ranta,cikin ikon Allah sannu sannu wani irin mahaukacin bacci
yazo yayi awon gaba da ita.
Batasan tsahon lokacin data dauka ba,itadai ta farka ta jiyo maganganu sama sama daga
falo,da alama baqi ke dasu a gidan. Ta kalli agogo,saita miqe da dan hanzarinta zata wuce toilet,mararta
taji ta murda,tadan dafeta tana yamutsa fuska,a hankali kuma saita saki,ta miqe ta wuce bandaki don
daura alwala ta biya bashin sallar da yake kanta.

Koda ta idar bandakin ta koma,tayi wanka da ruwa me dumi sosai sannan ta shirya cikin wata
doguwar rigan kayan bacci me taushi. Ta taje gashinta da kyau ta dameshi cikin band,saita tsaya tana
kallon fuskarta. Skin dinta ya sake fresh sosai,hakanan idanunta ma kaman sun qara girma da haske.
Yunwa taji tana dan ji,hakan kuma ya mata dadi,don tanaso taci abincin sha'awar cinne bata jinsa.
Juyawa tayi ta dauki wayarta ba tare data daura dankwali ba ta nufi falon,sam ta manta da batun zuwan
ayana,hakan wannan lokacin tasan lokacine da daga su saisu a gidan.

Sai data bude qofan ta soma isa falon sannan tunaninta na daxun ya fara dawo mata.
Benazeer da batoul da kuma maina suna zaune saman carfet,sun sake sosai sun kuma yiwa wajen abinda
suke so,sun batashi da abinci,ayana na duqe a gabansu tana qara musu miya da lettuce. Muryarta da
tasu benazeer kadai ke tashi,alamun da zai bayyana maka lallai ita din ba baya bace wajen surutu da
karadi. Yayin da hannun maina na hagu ke riqe da waya yana daddanawa tamkar hankalinsa baya kansu.

Idanunta dukka ta zube akan ayana din, shirt ce a jikinta inner da top me budadden gaba,sai
palazzo madadin kayan,wata irin hula ce kawai saman kanta,wannan ya sanya sumar da ta danyi
gadonta ta fito ta qasan hular. Tayi kusanci da yawa da maina,ko luma bata sani ba idanunta ne suka
nuna mata hakan?,koma mene sai taji ci gaba da kallonsu bashi da wani alfanu face wani abu me zafi da
yake saukar mata saman zuciyarta. Tana zare idanunta daga kansu yana dago kansa suka hada idanu,tun
fitowarta fitinannen qamshinta ya ziyarci.hancinsa.

Kanta ta dauke,daidai sanda ayana itama ke qoqarin dauke kanta daga kan fuskar sultana, fuskar
data rudar da ita da kwantaccen zallar sassanyan kyau. Tun sultana batakai haka ba tasan ita din me
kyau ce,don kaf iyalin MAYAK'I ba wanda ya kamo qafarta, mutum daya ne suke gogayya,ya haidar
din,aliyyu maina,to amma a yanzun zallar kyau aji da kuma nutsuwa me cakude da kwarjini da take gani
tattare da ita yaso firgita zuciyarta.

*_tofa,wanne ne ba wanne ba?,ga sultanar ama?,ga AYANA da take matsayin diya a wajen ama,wacce
AMA da MAINA zasu zaba?_*
*_tayi masauki cikin gidansu,kuma kusa da gidan MAINANTA,ya zata kaya?_*

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_


09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/20, 9:16 AM] +234 803 066 5772: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 106

Daga ayana har shi ta bawa banza ajiyarsu,taci gaba da takawa da nutsuwarta har ta isa dining
area sannan ta dubi batoul cikin muryartan nan dake saurin janye hankalin me sauraro
"Ina ama?"

"Ta shiga wanka" benazeer sarkin karadi ta baiwa sultana amsa. Kai kawai ta gyada,saita maida idanunta
ga kayan abincin dake saman dining din tana nazarinsu,daidai lokacin tanja ta fito daga kitchen dauke da
nata kwanaon abincin.

"Uwar daki kin tashi kenan" wani qaramin murmushi da baikai zuci ba sultana tayi tana dan shafa
kwantaccen gashinta,murmushin da ya kusa sanya maina kasa controlling kanshi,don tunda ta fito ta
wafci hankalinsa da tunaninsa,kowacce gaba dake jikinsa tana amsa kallon da yayi mata sau daya tak

"Wallahi tanja......yunwa nakeji,kuma na rasa meye zanci a ciki" tayi maganar tana taba warmer din da
tafi kusa da ita.

"Ba zaki rasa ba kam,bari na bude miki ki gani"

"Na gode tanja" sultana ta fadi cikin girmamawa da qauna. Matar ta jima tana hidima wa rayuwarta,ta
dade tana nunawa rayuwarta kulawa da soyayya.

Dukka abincin ta bude,ta zuba musu ido tana ci gaba da nazari kafin tace

"Inajin pepper soup din catfish dincan zanci"

"Yauwa nasan ba zaki rasa ba" tanja ta fada tana daukan plate ta soma zuba mata tana bata labarin
program dinta na yau data kalla. Murmushi kawai takema tanja din,don sai taji haka kawai batason
dogon magana,duk da taci gaba da surutanta da yaran,amma jikin sultana yana bata daga ita har maina
din hankalinsu yana kanta,wanda ko sau daya bata waiwaya sashensu bama bare ta basu damar tunanin
tasan sunayi.

"Da kin zauna ai" sultana tace da tanja wadda ke nufin sauka tabar wajen
"To ai sai na tayaki hirar" tanja din ta fada tana jan kujera ta zauna. A hankali da kuma kadan da kadan
take diban pepper soup din tana sawa a bakinta suna hira da tanja. Duk da bakinta babu dadi amma sai
taji ta samu appetit sosai,kafin wani lokaci sai gashi ta cinye tas

"Yayi dadi tanja,xan samu qari?"

"Me zai hana?" Ta amsata tana murmushi,sai tana plate din ta sake qara mata harma yafi na farko yawa

"Zan iya cinyewa kuwa?"

"Mummy zanci......"

"Nima mummy zanci" muryoyin benazeer da batoul suka bata amsa. Baki tadan bude tana dubansu ba
tare data bari ta hada idanu da wani tsakanin maina da ayana ba. Kafin ma tace komai har sun iso saman
dining din,suka sanya hannu suka fara ci,sai batace komai ba ta maida kai tana cin tana musu qananun
mitoci

"Idan kika cinyemin ban qoshi ba tam,ni daku ne" tanja na zaune tana dariya,gami da mamakin cin kifin
sultana,don ba abune data fiya damuwa dashi ba,dashi da nama duka basu wani dameta ba da zatayi
musu cin qoshi.

Nannauyan ajiyar zuciya ayana ta saki a boye,ita kadao tasan me takeji cikin qirjinta. Duk
yadda takeso kada ta saci kallon sultana koda a boye ne amma ta kasa,ta kalleta ta kalleta har ta dinga
jin ta raina kanta da kanta,a yanxun da take xaune tsakiyar yaran nata suna cin kifin saita dinga jin inama
ace itace?,inama ace yaranta ne ita da maina?. Babu wanda zai kalleta yace itace mamarsu,haihuwace
irin ta quruciya,quruciyarma iya quruciya ko ciwon kai ba'a gama sani ba bare ayi maganar girma. Tana
jin kamar zata sare da maina din amma wata zuciyar tana bata qwarin gwiwa,abu daya ne da bata sani
ba......har yanxun yana nan a matsayin mijinta,tana nan a matsayin matarsa ko kuwa?,bata da
amsa,batasan kuma waye zata tambaya ba ta samu hasken da zai haska mata kalan takun da zatayi.
Maida hankalinta tayi ga maina tanason janshi da fira,saidai kuma hausawa sukace miskili kafi
mahaukaci ban haushi,gaba daya attention din da take buqata daga garesa ta gaza samunsa,wayarsa ya
bawa kusan dukka a hankalinsa a idanunta,amma kuma ta wani gefen sultana ke daukan hankalinsa. Ya
qware qwarai wajen iya satar kallo,wannan ya sanya ba lallai ka fahimci ita yake kalla din ba.

"Alhamdulillah,ku matsa ku bani waje na wuce" sultana ta fada tana miqewa daga saman dining din
bayan ta kammala cin kifin.

"Idan ama ta fito kice mata na koma daki,zan duba program na next week in sha Allah"

"To ba laifi" tanja ta fada tana matsa mata hanya.

Tana sauka daga dining area din ama na fitowa,cikin shigar BOUBOU na wani material
sassauqa ruwan bula wanda ya zauna mata sosai,ya kuma boye shekarunta,tamkar ba itace ta haifi
maina ba,daya daga cikin dabi'un ama din dake burgeta qwarai wato ado da kwalliya,ta kuma tasirantu
sosai dasu a iya tsahon zamanta da ita

"Ama zan wuce daki,sai da safe" sulta tayi saurin fada sanda taga ama din tana kallonta

"Zan duba wasu ayyuka" ta sake bawa ama uzuri don batason tace mata ma ta zauna a falon

"To Allah ya taimaka.......ayana......ga yayarki kun gaisa kuwa?" Ama dake shirin zama saman kujera ta
fadi.

"Sultana ga ayana" aman ta kuma maimaitawa ganin sultana kamar bataji ba tana nufin wucewa ciki.
Tsaiwa tayi da tafiyar ta juyo,idanunsu suka gauraya waje guda karon farko tun shigowarta falon. Zubin
halittar idanun sultanar na dabanne,suna da wani irin kyau da koke mace kika kallesu sai sun burgeki,sun
kuma bar miki kishi me yawa a zuci muddin akwai abinda ya hada tarayyarku ta fannin kishin

"Barka da dare kina lafiya?" Ayana ta fadi tana qaqalo murmushin dole
"Sannu ya kike?,ya garin?" Sultana din ta fada itama tana qoqarin arowa fuskarta sakewa.

"Lafiya qalau,ya paris?" Ayana ta sake tambaya

"Paris normal alhamdulillah.......kema gaki a cikinta"

"Yes....... gaskiya ne,Allah dai yasa tana da dadi" ta sake fadi tana kuma karantar duk wani motsi na
sultana. Qaramin murmushi ta saki mata,ta gaji da wannan tambayoyin marasa fa'ida da bataga
ma'anarsu ba illa kawai bata mata lokaci da sukeyi,so take ta wuce daki gaba daya kifin da taci ma
kaman yazo mata wuya ya zauns ne,bugu da qari wani abu daban kuma yaja hana numfashinta fita
yadda ya kamata

"Me na gaggawar tamabaya?,gaki a cikinta?,nan da sati daya ma qilan ke xaki bawa wasu labari" ta
qarashe da wani murmushin. Idanu ta kada tana duban maina

"Allah yasa haka......amma ya maina saika kawo taimako......tunda dai bansan ko ina ba ka
sani.......sultana ki sanya baki ki tayani roqarshi kada yace a'ah" ta qarashe fadi a shagwabe.

Har tsakiyar ranta taji abun,amma kuma har yanzun tana yaudarar kanta da ba wata alaqa
tsakaninta da maina din

"Sultana bare ce fa......kunfi kusa gaki gashi,ina da abinyi a ciki,lokaci kinsan yanzun sauri yakeyi,ko kai ka
yankeshi ko kuma shi ya yankeka,goodnight, enjoy ur new home" ta fadi tana juyawa tayi ciki abinta.

Da kallo ya bita ta qasan idanu har ta wuce ciki,qaramin boyayyen murmushin gefen baki ya
saki,dole yau yayi rarrashi koda indirect ne,ya hangi abubuwa masu kaifi cikin idanunta da batasan tana
fiddasu ba,uwa uba kuma fushi dake lasar zuciyarta. Ayana ba damuwarsa bace,shi yasan
maganinta,hakama laila,amma zuwansu sai yake neman zame masa alkhairi,kaman sun pushing nata ne
wajen matso abinda batasan yana ajjiye cikun zuciyarta ba,abinda taketa qoqarin yima kanta qaryar
babu shi sam tattare da ita.
Ta kusa minti biyar tanason controlling kanta da zuciyarta,ta zuqi numfashi ta fesar har
batasan adadi ba amma abinda takeji yaqi ya sauka,gaba daya abincin da taci a wuyanta take jinsa,daga
qarshe ta gasgata tabbas idan ba amayar dashi tayi ba ba zata samu sassauci ba,don haka ta wuce toilet
kai tsaye,ta sanya brush a bakinta,zunguri daya kuma ta soma kelayashi kaman zata fidda 'yan hanjinta
gaba daya a waje.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya


Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/20, 9:16 AM] +234 803 066 5772: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 107


Ta dade dafe da sink tana maida numfashi kafin fa samu numfashin nata ya daidaita,ta daga
idanu tana kallon fuskarta da tayi jazur a mudubi. Wasu siraran hawaye ne suka gangaro mata,tasa
hannu ta share,ta ware famfon ta tara hannuwanta tana wanke fuskarta gami da daura alwala.

Gefan gadon ta zauna tana lumshe idanunta,tasa qaramin towel ta share fuskarta tana sauke
ajiyar zuciya kaman jaririn da ya kwana yana kuka yake kuma buqatar lallashi.

Saman gadon ta koma ta kwanta rigingine,ta rungume pillow tsam a qirjinta,idanunta a rufe
amma batasan me take tunawa ba,tun tana a matsayin fakare har bacci yayi awon gaba da ita cike da
wata irin kasala.

Ficewarta daga falon sai yaji gaba daya zaman falon ya gundureshi,ya duba agogo a hankali
sannan ya maida hankalinsa yana duban batoul da benazeer

"Daddy zai gudu.....kuxo muyi sallama" ya fada yana miqa musu hannu.

"Naga dare kaman baiyi ba ya haidar......tun yanzun?" Ayana ta fada tana kallon agogon hannunta itama

"Ina da busy gobe in sha Allah" ya bata amsa yana miqewa tsaye,ya saka wayarsa a aljihun wandonsa
hannunsa guda daya cikin hannun batoul da benazeer.

Durqusawa yayi yayi kissing hannayensu,ya dago yana duban ama

"Ama zan wuce...." Ya fadi yana duban idanunta

"Allah ya bada sa'a ya kiyaye,Allah ya bamu alkhairi" ama din ta fada,daga tsakiyar idanunsa ta karanci
addu'a yakeso,kawai yana mata kawaicin magana a kai ne.

"Ameen ya hayyu ya qayyumu" ya fadi yana juyawa


"Bari na rakaka......ya haidar baka gayyaceni naga gidan ba" ta furta a shagwabe tana karya wuya

"No,na yafe dare yayi...... goodnight" ya fadi yana nufar waje.

Jikinta a mace ta koma ta zauna tana kallon hanyar da ya wuce din.

"Ya kamata ki kwanta ki huta ayana......goben sai kiji dadin shiga school da wuri ko?" Ama ta fadi tana
tarkata kan su benazeer da suka zube sunason fara bacci a gurin.

^^^^^Cikin farare qal din pyjamas yake takowa zuwa cikin dakin,hannayensa dukka biyun zube a aljihun
wandonsa. Jikinsa na fidda sassanyan qamshin turarensa.

A nutse ya maida qofar ya rufe yana jin wani shauqi yana ratsashi,yana jin kamar ana fusgarshi
zuwa gareta. Duk da dim light dakin yake dashi amma hakan bai hanashi hangota ba. Tana kwance miqe
saman sofa da matsakaicin tsahon nan nata,ta rungume pillow tsam a qirjinta. Idanunshi fes a kanta har
ya isa dab da ita,saitin kanta ya tsugunna yana kallon fuskarta,kallo daya yayi mata ya fahimci tunda ta
shigo dakin a dazu bacci yayi awon gaba da ita. Gashinta dukka ya barbaxu saman pillow din kujerar da
ta dora kanta. Dan qaramin bakin nan nata me labba masu sulbi ta turoshi gaba kadan,kana kallonta
kasan cikin fushi tayi baccin.

Murmushi ya saki yana tuna quruciyarta,wannan kwanciyar irinta takeyi masa shi ko bibi idan
tana fushi,ba kuma me shawo kanta sai shi ko bibi din ko madararta,madarar da baisan har yanzu me ya
rabata da ita ba,tasha gaya masa

"Uncle......ko nayi aure ai zaka siyamin motar madara na tafi da ita ko?,kuma kaima tare xamu tafi ba zan
tafi ni kadai ba kaman yadda aka yiwa su aunty chamsiyya" tayi tambayar ne a sannan cike da
quruciya,tayi tambayar ne a lokacin ba tare da sanin me ma aure yake nufi ba,ashe shine mijin.......shine
abokin rayuwarm.....Mallakinsa ce". Wannan tunanin da yayi ya haifar da raurawar zuciyarsa da kuma
haihuwar wani abu me nauyi cikin qirjinsa da zuciyarsa,ya miqa hannu a hankali yana matsar mata da
gashin da yake son rufe mata hancinta. Zama yayi sosai gabanta yana morewa kallonta,kallo irin me
haifar da kusanci qwarai tsakanin zukata. Bayan wucewar kowacce daqiqa soyayyarta ke sake
haukacewa cikin zuciyarsa,feeling sosai kallonta ke tayar masa,shi kansa yasan yayi mugun haqurin
rashinta a kusa dashi, abinda bai taba kawowa zai iya ba.

Cikin baccinta ta dinga jin qamshin nan nasa yana isa har cikin kwanyarta,ta dinga motsa idanu a
hankali,hankalinta da yayi nesa da gangar jikinta ya fara dawowa. Shuru tayi bata nuna ta farka din ba,ta
nutsu sosai wai ko xataji wani motsi daya danganceshi?. Cikin ranta ta dinga fatan jin motsin ko yaya
ne,duk da har yanxu batasan meye silar da yasa takeson taji motsin nasa ba

"Bs kowa,ke kadai ce dai" zuciyarta ta gaya mata. Qasan ranta taja tsaki,ta motsa tana son gyara
kwanciyarta,saidai kuma batakai ga aikata hakan ba taji tattausan hannunsa ya lullube kafadunta.

Har cikin ranta taji saukar tafukan hannayen nasa,da mugun sauri ta ware fararen idanunta da
suka sauya launi kadan saboda bacci ta watsasu a kanshi. Tabbas shine,farin qaqqarfan ba'abzinen nan
daya qaurace mata tsahon kwanaki,qauracewar da tayi awon gaba da dukka nutsuwarta...... qauracewar
da batasan dalilin da ya sanya ta dameta ba har ya wuce iyaka.

Da sauri tayi niyyar miqewa amma sai ya nuna mata mazantaka ya maidata kwancen,ya maye
gurbin pillow din da take rungume dashi bayan ya zareshi ya aza mata nauyinsa.

Kallon tsakiyar idanu yakeyi mata wanda shi ya kassarata,ya kuma zare mata duk wata laka daga
jikinta,bai daina duban tsakiyar qwayar idanunta ba kamar kuma yadda bai dagata ba,numfashinsa da
nata sukaci gaba da gauraya waje daya,hakan ya haifar musu da wani irin yanayi me matuqar nauyi cikin
gangar jiki da zukatansu.

Cikin qarfin hali ta soma yunqurin tureshi,amma sai yayi mata wani mahaukacin riqo,muryarsa
da numfashinsa yana rarrabewa ya soma magana da ita cikin muryar can qasa

"ita yake sharewa amma shike amsar hukuncin fiye da ita.....Allah ne kadai yasan yadda ya wuce dararen
nan.......awanni da sa'o'i masu tsaho da suka zame masa tamkar shekarun da suke wanzuwa rayuwar
dan adam cikin tsanani.......kekam wai babu zuciya ne a qirjinki......ko sau daya mana ki gayamin cewa
MAINA NAYI MISSING DINKA YADDA KAYI KEWATA NIMA" ya qarasa fada da wata iri murya yana kuma
hade fuskokinsu guri guda,hancinsa yana gugar nata.
Idanunta kawai ta mayar ta rufe saboda abubuwan daya aike ma jikinta ita kanta tasan bata isa
ta kauce musu ba. Hakan yake nema dama daga gareta,ya kuma fahimci aikinsa na farko ya fara isar
masa da saqon yadda yakeso,don haka ya zura hannunsa ta gefen kunnenta ya shafo wuyanta da wani
irin salo da ya sanya ajiyar zuciyar da bata shirya fitarta ba kubce mata

"Ke bakya kewar mijinki?" Ya sake jefa mata tambayar yana lalubar bakinta. Batasan amsar da zata bashi
ba,baima kuma bata daman yin hakan ba ya bame bakinta cikin nasa.

Wani irin zazzafan saqo ya shiga aike mata,wanda girmansa ya Sanya sofa din da suke kai ta
gagara daukarsu shi da ita,suka zame a hankali zuwa qasan carfet din,jikinsa gaba daya rawa
yakeyi,kaman yadda nata jikin ya dauki kakkarwa,tanata yunqurin janye hannunsa amma ina bai bata
wannan damar ba,sake shigewa jikinta yakeyi yana kuma sake boye fuskarshi sosai cikin jikinta a duk
inda yaga yayi masa,a kuma wajen da duk yake da muradin hakan.

Bata tayashi da komai ba,amma kuma ya samu cikakken hadin kan da bai taba samu daga
gareta ba,ko a guri daya bata yi yunqurin hanashi ko dakatar dashi ba daga abinda ya nufa. Ita a karan
kanta batajin zata iya hanashin,jikinta ya sauka daga dukkan wani tsari data dorashi akai,tahau wani
bigire da ita kanta batasan yaushe ta soma hawa wannan layin ba,saqonsa ya isketa fiye da yadda ta
saba jinsa.

Kuka ta sake masa tana juya baya bayan komai ya kammala. Dariya ce taso qwace masa,ya
cusa kansa a tsakiyar bayanta tana fidda qaramin sauti gami da janye bargon data duqunqune a ciki.

"zo kiji mummy twins" ya furta yana qoqarin birkitota. Jikinta ta hade guri guda taqi bashi
wannan damar,da gaske rigima takeyi masa,don ya gama sanyata ta kunyata iya kunyata,ita kanta tasan
ta saki layi fiye da yadda ya dace,batasan da wanne ido zata kalleshi,ya sakata shallake iyakoki sosai. Har
yanxu dariyar ke cinsa,ya sani shi da kansa yasan yau din baibi mata ta sauqi ba,ya sani duk
dauriyarta......duk kafiyarta......koda wani irin mahaukacin qiyayya take masa a yau din layin da ya dorata
akai dole tabi.

"Ba wani kunya mummyn twins......ba wanda yasan fa me ya faru.......daga ni saike fa.....kome kikayi lada
za'a rubuta miki......kuma kome kika fada na miki uzuri nasan cikin yanayi kik......."
"Me kuma nace?" Ta tambayeshi da sauri,sai ya saki dariya har yana cusa kansa a pillow. Dariyar tasa ta
sanyata ta tsargu,itakam yau ta shiga uku,ba zata iya tuna da meye da meye ta fada ba bare tayi
gyara,Allah ne kadai yasan irin baran baramar da tayi kenan,sai kawai ta sake fashewa da kuka tana cusa
kanta a qafafunta.

Har tsakiyar zuciyarsa yakejin sautin kukanta,ya lumshe idanu yana dakewa sosai

"Tashi muyi magana......"

"Banaso......ka barmin dakina" ta fadi tana kuka da gasken gaske

"Bazan fita ba indai baki tsaya munyi magana ba.....hasalima a nan din zan kwana kinji na rantse" yana
kaiwa nan ya hantsilo daga gadon, cikin nishadi da kuma jin kansa da yakeyi fresh ya shige bandakinta.

Kasaqe tayi tana sauraren saukar ruwansa a bayi. Abinda bai taba yi ba kenan,ga qoshi ga
kwanan yunwa,tasanshi farin sani,kuma ita zata fada bada labari a kansa,baya rantsuwa bai cika ba,da
gasken idan bata saurareshi din ba xai kwana a dakin nata?,baya tsoron ama ko aba su ganshi?,baya
tsoro ko kunyar idanun kowa?. Wadannan tambayoyin suka tsaye mata a rai,ta rasa wanne zata zaba,ta
murje kunyarta ta saurari abinda zaice ko kuma ta barshi taga iya gudun ruwanshin,da gaske zai iya
kwana din?,to meye ma wai zaya gaya mata bayan ya gama sanyata ta barar da mutuncinta?.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*
_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*

LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*
09033181070

*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

[7/20, 9:46 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 108

Tana jin motsin fitowarsa ta maida idanunta ta kulle,ita batajin zata iya sake hada idanu dashi. Ta
cure waje daya tana neman gurin cusa kanta taji anyi cak da ita

"Leave me please......ka sakeni......banaso" birkitota yayi ya lullubeta tsakiyar qirjinsa yana cewa

"Da alama baki biya bashin nan da kyau ba,shi yasa bakinki yake iya magana har haka" ya qarasa
maganar yana laluben bakinta. Bam ta bameshi ta cusa dukka labbanta cikin bakinta. Qaramar dariya ya
saki,yayi maganin mitarta hankali kwance.

Duk ta firgice kada yace shi zaya wanketa yadda yakeyi mata,itakam yanxun ma gaba daya
lamuransa tsoro suke bata,nema yake ita kanta ya sauyata,so yakeyi yayi mata dole ya kuma shiga
rayuwarta ta qarfin gaske. Sai daya gama hada mata komai,hatta towel da zata buqata idan ta gama
sannan ya soma ficewa daga toilet din da baya da baya yana cewa

"Karki dade a ciki.....idan ki gama ki kirani" ya hada hannayensa biyu ya mata sign na heart sannan ya
juya yana ficewa.
Wata doguwar ajiyar zuciya taja tamkar zata tsinke jijiyoyin zuciyar dake jikinta,ta sauke
numfashi tana bude idanunta taba duban hanyar daya fice din. Batasan me yakeson sauyata ba kwata
kwata,da gaske yake rikita mata tunani bayan ita a yanzun bata shirya faruwar hakan ba.

Tana wankan qwaqwalwarta ta dawo mata da komai daya faru tsakaninta dashi mintunan da
suka shude,ita daya a toilet din ta dinga jin wani mugun nauyi da kunyar kanta da kanta,komai na jikinta
a yanzun ta tabbatar babu abinda baisan gwajin yawansa tudunsa zurfinsa da kuma fadinsa ba.

"Innalillahi" ta fadi tana tara ruwan hawaye,me yasa ta barshi tun sanda ya fara abun batakaj qararsa
ba?.

"Wajen wa?" Ta samu kanta da tambayar kanta da kanta

"Ama ko aba?" Ta sake tambayar kanta. Kai ta girgiza,abunma sam baiyi ma'ana ba,takai qararsa tace
me?,yana shigowa gidan?,yana kuma shigowa dakinta?,idan ya shiga to meye yayi mata daya cancanci
takai qarar?.

"Tace gana k....."

"Subhanallahi" ta fadi a ranta da sauri,ba zata iya gayawa ama da aba wannan maganar ba,kenan koda
zatakai qarar ma yana da hujjar musa mata?,yana da kuma hujjar kare kanshi tunda ita din dai bata da
wata qwaqwqwarar hujja.

Wankan ta farayi amma har a sannan bata haqura ba,so takeyi lallai ta samo hanyar da zata
yakiceshi,tana tunanin kamar zata iya din,kaman yin nesa dashi din ba komai bane a wajenta,batasan ya
riga yayi mata dashen da rayuwarta ma ta soma dogara da fitar numfashinsa ba.

Tana yi tana zancan zuci ita kadai,tana wassafa yadda zata fita daga toilet din
"Wai ta yaya ma zaki iya kai qararshi wajen ama?.....shin kin manta cewa ita din uwa ce?" Tambayar data
sanyata tsaiwa cak daga goge sumarta da takeyi da towel. Gabanta ya fadi tana maimaita kalmar
uwa,saita koma da baya ta zauna kawai a toilet seat. Dukka zamannan sam sam ta manta da batun ama
ba ita ta haifa ba MAINA ta haifa. Ta manta da zancan cewa ba zata taba qin maina ba saboda
ita,wannan yana nufin duk abinda takewa maina kenan ama tana jun haushin hakan?,to amma me
yasa?,me yasa ama din bata taba nuna mata ba ko a fuska?,wacce irin jarumar uwa ce ita dake iya
shanye qiyayyar da ake nunawa dan cikinta?. Ta dade xaune a haka tana son tuno wanne iri da wanne
irin rashin kyautawa ta yiwa maina a gaban ama tsahon zamansu,to amma abun da yawa, lokacin da
tsaho ba zata iya riqewa gaba daya ba,dole ta gaji ta miqe tana daure bathrobe din jikinta sosai da nufin
idan ta koma daki ta sauya kaya.

Idanu ta fidda sosai ganinsa kwance dai dai abinsa saman gadonta,da alama ma ya fara bacci
ne abinsa. Tsoro sosai ya kamata,ta kalli agogo,uku saura na dare,ta yaya zaiyi mata bacci a daki?,bata
tsoron asuba ta riskeshi suje suyi kacibus da wani cikin gidan?. Cikin sanda ta dinga takowa har ta iso
gefan gadon ta zauna. Idanunta suka sauka saman kyakkyawar fuskar nan tasa dake da wani irin
kwarjini,ta qura mishi idanu tana kallon fuskokin su benazeer cikin tashi,wani lokaci kuma sai ta dinga
hangen tata fuskar kadan kadan. A baya sanda yake matsayin uncle mafi soyuwa a gareta tafi kowa jin
dadi idan akace suna kama,amma daga baya sai ya zamana muddin zaka ce suna kama da yaa maina to
ka tarowa kanka masifa,ranan babu me rabata da kai sai Allah,ta dingi mita har sai bibi tayi kaman ta
bugeta,amma sai gashi a yau din da idanunta tana hangen gaskiyar maganar quru quru.

Idanun ta janye daga kallonsa,tayi masa kallon da bazata iya tuna lokaci na qarshe data yi masa
shi ba,idanunsa na ganin kyawunsa zuciyarta nata avoiding,zuciyar kuma na karbar wani saqo da batasan
daga wanne guri ya taso ba.......amma taurin kanta da jin cewa ba komai game da ita daya shafeshi ya
hanata yarda da hakan.

Maida dubanta ta sakeyi,da gaske lokaci yana tafiya,kuma awanni kadan suka rage lokacin
sallar asubahi yayi,tayi imani kuma muddin ama ta samu maina a dakinta a yau dai ba ita ba kwanan
paris,tana kyautata zaton saidai ta kwana a nijer.

Hannu takai zata tasheshi sai kuma ta janye zuciyarta na gargadarta da kuskuren tabashi,ta
dunqule hannun nata tana wassafa yadda zata tasheshin,bata da wata mafita don haka ta sake kai
hannu,saidai yanzun ma kuma janye hannun nata tayi kamar me tsoron taba wuta. Sake kallon agogon
tayi, tafiyarsa yakeyi bai fasa rage tsahon mitunan da suka rage musu ba,sai ta sakejin hankalinta ya
kuma tashi.
Motsi ta jiyo daga bakin qofarta kaman ana shirin mata knocking,ai batasan sanda ta sake kai
hannu da zummar tashin nasa ba. Tattausan hannunsa da yayi wani dumi ya miqa ya jawo hannun nata
da sauri ya aza saman kuncinsa sannan ya lullube bayan hannun nata da tafukan hannayensa. Da sauri ta
dauke kanta daga kallon qofa da ta tafi yi ta dawo dashi kansa,saita samu zagayayyun lion eyes dinshin
nan fes saman fuskarta yana kallonta da narkakkun idanun nan nasa da a yanzun suke matuqar bata
tsoro. Kallon kallo suka yiwa juna na wasu sakanni,yana lumshe idanunsa yana kuma budesu dukka
lokaci guda,shi daya yasan me yakeji a kanta,bai taba tsammanin watarana zai jarabtu da soyayyar
'yarshi ba,koda kuwa a wasa ne.....wancan lokacin..... wancan ranar da komai ya afku ya zame masa
alkhairi. Kalmar FYADE shikam zai iya cewa alkhairi ce a tattare dashi,banda furtatan da tayi yayi imani
da tuni a yanzun ita din ta zama mallakin wani.

"Kinason kallona amma gulma ya hanaki ko?......am aliyyu maina,not yaa maina da kika sani shekarun
baya.....ni naki ne yanzun.......ba maina yayanki kuma uncle dinki da kika sani ba" sosai kalamanshi suka
sauka a zuciyarta,amma kuma tana cikin tsoron da bata da nutsuwa

"Don Allah...... please na roqeka,ka tashi ka tafi tunda ka gama abinda ya kawoka..... inajin motsi kada
wani ya shigo ya sameka a nan" ta fada a mugun narke sannan kuma a karye tana daga hannunta guda
daya da bai samu ya riqe ba alamun roqo.

Sanda taga ya motsa ta zaci tashi zaiyi ya tafi,sai taga ma ashe dogara gwiwar hannunsa yayi
saman gadon,ya kuma tallafe kumatunsa yana sake qare mata kallo. Yadda tayi masa shagwabar nan ta
sake tsumashi sosai,ta kuma sake tuna mashi da little sultanarshi,wani shauqinta yakeji kamar ya
dauketa ya boyeta a inda idanuwa basu isa sukai wajen ba

"Pleeeeassseee ya mai......"

"Uhmmm.......say it.....i missed the way you are calling me YAA MAINA" Ya fada yana lumshe idanunsa
dake kafe har yanzu a kanta yana fidda murmushi. Kanta ta kawar, calmly yake magananshi kaman
baisan wanzuwarsa a wajen bai dace ba,ta fahimci abinda ma take hange shikam bashi yake hange ba

"Please" ta sake fada a mugun karye ba tare data kalleshi ba. Hannunta dake cikin nashi ya matsa
"I love it......inaso naji kina begging dina......but ba'a irin wannan yanayin ba,ba kuma a irin wannan
muhallin ba.........inason wata rana tazo da zaki dinga begging dina kaman haka akan kinaso na kasance
dake......,mu raye wani dare......." Wani zabura tayi a gigice kaman wadda aka watsawa kunama,abinda
ya sanya zancansa yankewa ba tare daya shirya ba saboda dariyan da yaso kamashi,waishi baya jin
nauyin fadin maganganu har haka?,yana mantawa ita din wacece?,qaramar sultanar nan daya
raineta?,yana mantawa ne wai?.

"Already na gaya miki af first,idan baki saurareni ba a nan zan kwana ai ko, right?" Da sauri ta juyo a
hargitse da firigitattun idanun nan nata tana dubansa

"Na saurareka,tell me please" tsareta yayi da idanu kafin ya saki wani tattausan murmushi

"It's too late madam sultana......baki saurareni ba saboda rad'in kanki,kin saurareni ne don tsoron kada
azo a ganki da kwartonki ko me miki fyade kullum?" Ya furta da wani qaramin murmushin,saboda xuwa
yanzun kalmar ta zame masa wani abu na daban cikin rayuwarsa.

"No....." Ta fadi cikin nuna karaya

"Oya.....zo muyi bacci.....bazan iya gaya miki komai ba yanzun don bacci nakeji,kin gajiyar dani" ya furta
duka lokaci daya yana birkitota cikin jikinsa.

Wani kyakkyawan boyo yayi mata cikin qirjinsa,ya bata skin to skin contact me kyau wanda ya
sanyaya mata kowacce gaba ta jikinta,tsoron kada ya zamana wani ne a bakin qofar dakinta ya sanya
bata ko motsa ba tayi luf,saidai kuma qirjinta bai fasa bugawa ba da tunanin ta yaya zai kwana mata a
daki kuma ya fice daga gidan salin alin ba tare da kowa ya ganshi ba?,ta sanshi shi din fada da cikawa
ne,tunda ya dauki aniyar kwana tayi imanin bata isa ta sauya masa ra'ayi ba,sai kawai ta maida idanunta
ta rufe tana ambaton

"Rabbi sallim sallim" cikin qasar zuciyarta,tana jinsa sanda ya saki wata wawiyar ajiyar zuciya yana furta
"Thanks" da tausasashen sauti,yana tsammanin tayi shuru ne don ta bashi hadin kan samun nutsuwa da
bacci me kyau,baisan meke yawo cikin zuciyarta ba,hanyar da zai fita daga gidan ba tare da ya kunyatata
ya tona musu asiri ba. *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 109

Tun kafin a kira sallar asuba ta tashi,ta daura alwala ta zauna tana raba idanu,amma a zahiri ta
nuna kaman tana jiran ayi kiran sallar assalatu ne,a qasan zuciyarta kuwa tana fata ya tashi ne yayi
alwala ya fice,ita koda baiyi alwala bama din indai zaibar mata daki buqatarta ya biya.

Yayi likimo kaman baisan meke faruwa ba amma yana sane din,ya danne dariyarshi kawai
yana mamakin yadda tsabar rigimarta ta hana mishi barci itama kuma ta hana kanta,tanayin abune
kamar wadda ta kawo kwarto. Yana sane ya sake miqewa sosai cikin duvet,bai kuma tashi ba sai da aka
kira assalatu.

Hankalinshi kwance ya wuce toilet dinta,bai jima can can ba ya fito daure da alwala,ta bishi da
kallo tana addu'ar ya fita amma sai taji yana bata umarnin ta shimfida musu darduma ya jasu jam'i. Da
hanzarinta tayi komai tana zaton zai tafi idan sun idar,amma da suka idar din sai taga yayi zaman yin
azkar din safiya. Nutsuwarta ta fara yin qaura daga gangar jikinta sanda taga alfijir yana neman
ketowa,ta kasa azkar dinma gaba daya,sai idanu da take fama binsa dashi tana satar kallonshi.

"Ki nutsu kiyi azkar dinki,nima nan din gidanmu nefa,bawai baqo bane" ya bata amsa da dakiyar nan tasa
yana kallon qibla ba tare daya dubeta ba. Duk yadda taso ta nutsu din ta kasa,saita soma sarewa sanda
taji wucewar tanja har sau biyu zuwa kitchen. Dukka dauriyarta ta qare sanda taga ga kammala azkar
din,ya miqe yana sake wucewa zuwa gadonta. Muryarta ta dauki rawa ta dubeshi
"Amma...... amma fa safiya yayi.....baka kalli agogo ba?" Girarsa ya dage mata dukka biyun sanda ya
jingina da fuskar gadon

"Wannan ce gaisuwan barka da safiyan?" Nauyinsa kuma taji ya kamata,abinda ya kamata ace tayi ne
batayi ba,sai tayi qasa da kanta don yadda ya tsareta da idanun ya mata nauyi

"Barka da safiya,ina kwana?" Murmushi ya sake kadan,yanajin inama zasu tabbata a haka ita dashi,sai ya
miqa mata hannuwansa daga nan inda yake yana cewa

"Gaisuwan nesan nan bana sonta,zo kiji" ya furta yana lumshe idanunsa,feelings da yake samu a duk
lokaci irin wannan yana motsa masa. Maslaha take nema,so take ta lallabashi ya fita tun aba da ama
idanunsu baikai kai ba,don haka ta miqe a sanyaye tana takawa gareshi.

Da idanu yake bin kowanne taku nata,kowanne sashe na jikinta yana motsawa cikin wani salo
kamar wanda ake bawa umarni,idanunsa suka qara qanqancewa,kishinta ya wani cikashi har ya dinga jin
kamar zuciyarsa na matsewa. A hijab yaga dukka kyakkyawan surarta,ina ga sanda take cikin veil ko
scarf?,ina ga sanda ta sanya abaya ko gown,anya kuwa zai iya ci gaba da xuba idanu?,xai kuwa iya tausa
zuciyarsa yadda yaso yayi daga baya akan ya qyaleta ta mori karatunta?,aikin gidan tv fa?,abune da yake
international ba iya state daya ba ba jaha daya ba na qasa baki daya.

Hannunsa ya sanya ya riqe dogayen siraran yatsunta yana kallonta,muryarsa tayi laushi sosai da
wani irin duka da kishi yayi masa

"Please......ko menene,ko yaya ne sultana.....ki taimakeni,ki rufamin asiri ki killacemin kanki.....i swear
bazan iya dauka ba,zuciyata me rauni ce a kanki,bazan iya jurewa ba naga wani ko wasu suna kallemin
ke......" Bata yarda abinda yake fadi da gaske bane dai da yaja hannunta saitin qirjinsa,da gaske zuciyarsa
bugawa takeyi,har abun ya bata tsoro ta janye hannunta da sauri tana kallon fuskarsa. Raunannen
murmushi ya sakar mata yana kallon cikin idanunta

"Har yanzu maina shine nada,ba abinda yake sanyashi sauya magana.....so that kada ki damu da zamana
dakinki don sai na qarasa hutawa.....karki damu ya waye zai ganni?,yaushe zan fita?,duk kada ki
damu,ina da ragowar lokaci kafin na fita,zaki iya joining dina kafin lokacin walaha,karkiyi stressing kanki
too much da tunani..... please" ya qarasa fada yana hade hannayensa waje guda alamun roqo.
Eh tabbas yaa maina na baya shine yanzun,wasu dalilai yasa take gani kamar ya canza amma bai
canza ba din da gaske,ta saki baki tana kallonsa sanda ya shige duvet yana sake qudunduna da
kyau,muryarsa can qasa ya sake cewa

"Join me please mummy twins" ji tayi kaman da gayya ma yake roqonta, saita dauke kai tana zamewa a
wajen ta zauna sosai kaman me gadinsa,itadai tasan ya gama da ita,lallai yau da alama ranar shan kunyar
su ne daga ita har shi ya kama,to amma zata iya cewa ita daya din,tunda shi koma meye zai faru shi ya
jawo,kuma tunda yayi hakan tasan akwai abinsa ya taka.

Duk wucewar mituna tana irge dashi,rana na sake fitowa fargabarta yana qaruwa,ta dora kanta
saman gadon a hankali tana kiran sunan Allah,fatanta daya ya tashi ya fice salin alin.

Knocking akayi wanda ya sanya 'yan hanjinta hautsinewa,tayi qoqari da qyar ta gyara muryarta
qasa qasa,ta kalli inda yake kwance baima san anyi knocking din ba,ta sake maida dubanta ga qofar
sanda ake qwanqwasawa Karo na biyu

"Waye?" Ta tambaya adan tsorace

"Mummy mune.....BB"

"Get out ko CC ne,da safen nan?,to ban tashi ba"

"Mummy ki bude mana don Allah,yau Halloween party ki duba mana kayan nan"

"Benazeer.......sa'arki ce ni?,zaku bacen a wajen ko sai na fito na bubbugeku?" Ta fadi a harzuqe tamkar
su suka sanya daddynsu yayi kwance kwance a dakinta😂.
Tana jinsu suka juya jiki a sanyaye,ta zuqi iskar ta fesar tana ware idanunta,cikin ranta tana
addu'ar Allah yasa kada yaran su matsa da yawa,kuma kada Allah ya kawo wani. Sau biyu taji sun sake
wucewa da tanja zuwa kitchen,saidai ko motsi me qarfi taqiyi bare suyi tunanin idanunta biyu.

Awa guda ba kadan aka sake buga qofan,yanzunma dai a hasale ta soma magana

"Batoul ku fita a ido na fa?"

" Da sukayi me?" Taji muryar ama tana tambayarta daga bakin qofar. Wani gumi taji ya karyo mata

"Innalillahi" ta fadi da muryar rad'a tana ware idanu

"Tashina sukeson yi ama.... Kuma....."

"..... Kuma me?,yau baki da aiki ne?"

"Na dauki hutu ama sai next week ana gobe zan sake program" ta fada tana hadiye wani yawu me kauri
a maqoshinta

"To yayi,kizo aba dinku yana kiranki......but kada ki wuce minti talatin don fita zaiyi"

"Gani nan ama" ta fada da sauri. Yadda take amsawar ya bawa ama mamaki,tadan tsaya jim

"Are you okay?" Ta tambayeta tana kallon qofar dakin

"Yes am....ama"
"Budemin qofar dai" ta fada tana jin bata gamsu da yadda muryarta ke fita ba kaman a tsorace.

Maida dubanta tayi ga maina a tsorace,hankalinsa kwance,hasken safiyar ya haske fuskarshi ta


wani sake fresh.

"Sultana" ama ta sake kiran sunanta

"Gani nan ama ina saukowa daga gado ne....."

"Alright.....daga baccin kika tashi ashe.....karki zauna kizo kiran aba dinku" sai taji ama din ta juya tana
barin wajen.

Ido ta lumshe tana yada kanta gefe hadi da sakin ajiyar zuciya

"Matsoraciya" taji ya fada da muryar bacci. Da sauri ta daga kai cikin mamakin dama duk abinda akeyi
yana jinsu?. Tun bugun dasu benazeer sukayi suka katse masa baccinsa,sai baccin ya zama ba wani me
nauyi ba,yanajin komai amma kwanciyar ta masa dadi shi yasa yaqi tashi. Idanunsa ya bude sai idanunta
cikin nasa,ya ture duvet din ya miqe yana zama sosai saman gadon.

"Am starving......me zan samu?" Ya fadi yana lumshe idanunsa. Gaba daya zuciyarta ta karye,ya qarasa
gigitata,sai kawai ta sakar masa hawaye. Ta yaya zaice zaici wani abu?,salon ta fita dauko masa wani ya
shigo?.

Tsaiwa yayi yana kallonta,kaman bazaiyi magana ba sai ya rusunar da idanunsa yana cewa

"Banason kuka.......tashi ki shirya kije kiran aba"

"Ni a shirye nake" ta tari numfashinsa,sai kuma hankalinta ya dawo jikinta sanda taga yana bin jikinta da
kallo. Tabbas yamutsewarta da yamutsewar jikinta kadai zai sanya ka saka mata ayar tambaya. Baice
komai ba ya sauko ya a nutse daga gadon yana wucewa toilet,sai tayi amfani da wannan damar ta wuce
wardrobe dinta tana laluba abinda zata sauya din.

Allah ya taimaketa ta shirya cikin sauri, doguwar riga ta saka daga ciki sannan ta dora babban
hijab har qasa. Tana gyara madaurin fuskar hijab din ya fito daga toilet din,ta gefan ido ta saci kallonsa
sai akaci sa'a shima ita yake kalla din,ta masa kyau qwarai,hijab din ya wani qara mata kwarjini sosai,ta
dauke idonta tana qoqarin gyara igiyar,sai yayi taku hudu ya qaraso gareta. Hannunsa ya sanya saman
nata,dumin hannunsa ya ratsata,sai ta zame hannunta da sauri,hakan ya bashi daman gyara igiyar ya
daura mata ita saman tulin gashinta data nannade ya zamana kamar ribbon ta sanya.

Ta saman kafadunta ya zura kanshi yana kallon kyawawan idanunta ta cikin madubi

"Zaki tafi baki sake tambaya na me nakeson gaya miki ba.......well,na cinye abuna nima......yanzun ace
aba ya tambayeki idan kinje......me ya kawo aliyyu dakinki yake kwana wanne amsa zaki bashi?" Ji tayi
kaman a gaske aba dinne yayi mata tambayar,saita juyo a rude suka hada idanu,ta dauke kanta kuma da
sauri tana jin tana dirircewa.

Murmushin gefan baki ya saki, yayi taku biyu da baya da baya

"If kuma ya tambayeki kinason maina?,zaki koma dakin mijinki?,wanne amsa zaki bashi?" Ya jefa mata
tambayar yana kallon reaction nata ta cikin madubi. Qin daga idanunta tayi bare ya samu damar kallon
qwayar idanunta,abu daya taji har cikin jininta ya jefeta da wata magana me girma. Ta qarasa ta zira
slippers dinta ta soma takawa a hankali shi kuma idanunsa yana biye da ita,ta tsaya cak sanda ta isa
bakin qofa,ba kuma tare data waiwayo ta dubeshi ba tace

"Zan gaya masa bana sonshi......ban kuma taba sonshi ba,bazan kuma koma ba.....idan zaka fita daga
dakinnan kayi qoqari kada wani ya ganka please" daga hakan kamar wadda ke tsoron za'a kamata ta
taka da sauri tana fita a dakin.

Qas yayi da kansa yana jin maganarta na shiga ranshi,baiga fuskarta ba bare ya karanceta ta cikin
idanunta,saboda haka bashi da tabbas din abinnan da take gaya masa gaskiya ce ko qarya
tsagwaronta,koma meye take fada yaji saukar furucinta sosai,wani qaramin murmushi da baisan a
wanne gida ya ajeshi ba ya qwace masa
"Saina sanyaki kin qaryata kanki da kanki da bakinki......wallah.....indai na haifu jinin aba......saikin
qaryata kanki cikin mutane sababin yadda kika fadi maganarki a sirrance" ya fadi a fili murya a qasa. Ya
fahimci abu na qarshe da bataso shine asan yana cikin gidan cikin dakin,kanshi tsaye hannayensa zube a
aljihun wandonsa ya fara dosar fita daga dakin gaba gadi,kanshi kuma tsaye,duk da yana jiyo muryar
ama benazeer da batoul daga falon.

[7/20, 10:00 PM] +234 706 859 6814: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 109

Tun kafin a kira sallar asuba ta tashi,ta daura alwala ta zauna tana raba idanu,amma a zahiri ta
nuna kaman tana jiran ayi kiran sallar assalatu ne,a qasan zuciyarta kuwa tana fata ya tashi ne yayi
alwala ya fice,ita koda baiyi alwala bama din indai zaibar mata daki buqatarta ya biya.

Yayi likimo kaman baisan meke faruwa ba amma yana sane din,ya danne dariyarshi kawai
yana mamakin yadda tsabar rigimarta ta hana mishi barci itama kuma ta hana kanta,tanayin abune
kamar wadda ta kawo kwarto. Yana sane ya sake miqewa sosai cikin duvet,bai kuma tashi ba sai da aka
kira assalatu.

Hankalinshi kwance ya wuce toilet dinta,bai jima can can ba ya fito daure da alwala,ta bishi da
kallo tana addu'ar ya fita amma sai taji yana bata umarnin ta shimfida musu darduma ya jasu jam'i. Da
hanzarinta tayi komai tana zaton zai tafi idan sun idar,amma da suka idar din sai taga yayi zaman yin
azkar din safiya. Nutsuwarta ta fara yin qaura daga gangar jikinta sanda taga alfijir yana neman
ketowa,ta kasa azkar dinma gaba daya,sai idanu da take fama binsa dashi tana satar kallonshi.

"Ki nutsu kiyi azkar dinki,nima nan din gidanmu nefa,bawai baqo bane" ya bata amsa da dakiyar nan tasa
yana kallon qibla ba tare daya dubeta ba. Duk yadda taso ta nutsu din ta kasa,saita soma sarewa sanda
taji wucewar tanja har sau biyu zuwa kitchen. Dukka dauriyarta ta qare sanda taga ga kammala azkar
din,ya miqe yana sake wucewa zuwa gadonta. Muryarta ta dauki rawa ta dubeshi

"Amma...... amma fa safiya yayi.....baka kalli agogo ba?" Girarsa ya dage mata dukka biyun sanda ya
jingina da fuskar gadon

"Wannan ce gaisuwan barka da safiyan?" Nauyinsa kuma taji ya kamata,abinda ya kamata ace tayi ne
batayi ba,sai tayi qasa da kanta don yadda ya tsareta da idanun ya mata nauyi

"Barka da safiya,ina kwana?" Murmushi ya sake kadan,yanajin inama zasu tabbata a haka ita dashi,sai ya
miqa mata hannuwansa daga nan inda yake yana cewa

"Gaisuwan nesan nan bana sonta,zo kiji" ya furta yana lumshe idanunsa,feelings da yake samu a duk
lokaci irin wannan yana motsa masa. Maslaha take nema,so take ta lallabashi ya fita tun aba da ama
idanunsu baikai kai ba,don haka ta miqe a sanyaye tana takawa gareshi.

Da idanu yake bin kowanne taku nata,kowanne sashe na jikinta yana motsawa cikin wani salo
kamar wanda ake bawa umarni,idanunsa suka qara qanqancewa,kishinta ya wani cikashi har ya dinga jin
kamar zuciyarsa na matsewa. A hijab yaga dukka kyakkyawan surarta,ina ga sanda take cikin veil ko
scarf?,ina ga sanda ta sanya abaya ko gown,anya kuwa zai iya ci gaba da xuba idanu?,xai kuwa iya tausa
zuciyarsa yadda yaso yayi daga baya akan ya qyaleta ta mori karatunta?,aikin gidan tv fa?,abune da yake
international ba iya state daya ba ba jaha daya ba na qasa baki daya.

Hannunsa ya sanya ya riqe dogayen siraran yatsunta yana kallonta,muryarsa tayi laushi sosai da
wani irin duka da kishi yayi masa

"Please......ko menene,ko yaya ne sultana.....ki taimakeni,ki rufamin asiri ki killacemin kanki.....i swear
bazan iya dauka ba,zuciyata me rauni ce a kanki,bazan iya jurewa ba naga wani ko wasu suna kallemin
ke......" Bata yarda abinda yake fadi da gaske bane dai da yaja hannunta saitin qirjinsa,da gaske zuciyarsa
bugawa takeyi,har abun ya bata tsoro ta janye hannunta da sauri tana kallon fuskarsa. Raunannen
murmushi ya sakar mata yana kallon cikin idanunta
"Har yanzu maina shine nada,ba abinda yake sanyashi sauya magana.....so that kada ki damu da zamana
dakinki don sai na qarasa hutawa.....karki damu ya waye zai ganni?,yaushe zan fita?,duk kada ki
damu,ina da ragowar lokaci kafin na fita,zaki iya joining dina kafin lokacin walaha,karkiyi stressing kanki
too much da tunani..... please" ya qarasa fada yana hade hannayensa waje guda alamun roqo.

Eh tabbas yaa maina na baya shine yanzun,wasu dalilai yasa take gani kamar ya canza amma bai
canza ba din da gaske,ta saki baki tana kallonsa sanda ya shige duvet yana sake qudunduna da
kyau,muryarsa can qasa ya sake cewa

"Join me please mummy twins" ji tayi kaman da gayya ma yake roqonta, saita dauke kai tana zamewa a
wajen ta zauna sosai kaman me gadinsa,itadai tasan ya gama da ita,lallai yau da alama ranar shan kunyar
su ne daga ita har shi ya kama,to amma zata iya cewa ita daya din,tunda shi koma meye zai faru shi ya
jawo,kuma tunda yayi hakan tasan akwai abinsa ya taka.

Duk wucewar mituna tana irge dashi,rana na sake fitowa fargabarta yana qaruwa,ta dora kanta
saman gadon a hankali tana kiran sunan Allah,fatanta daya ya tashi ya fice salin alin.

Knocking akayi wanda ya sanya 'yan hanjinta hautsinewa,tayi qoqari da qyar ta gyara muryarta
qasa qasa,ta kalli inda yake kwance baima san anyi knocking din ba,ta sake maida dubanta ga qofar
sanda ake qwanqwasawa Karo na biyu

"Waye?" Ta tambaya adan tsorace

"Mummy mune.....BB"

"Get out ko CC ne,da safen nan?,to ban tashi ba"

"Mummy ki bude mana don Allah,yau Halloween party ki duba mana kayan nan"
"Benazeer.......sa'arki ce ni?,zaku bacen a wajen ko sai na fito na bubbugeku?" Ta fadi a harzuqe tamkar
su suka sanya daddynsu yayi kwance kwance a dakinta😂.

Tana jinsu suka juya jiki a sanyaye,ta zuqi iskar ta fesar tana ware idanunta,cikin ranta tana
addu'ar Allah yasa kada yaran su matsa da yawa,kuma kada Allah ya kawo wani. Sau biyu taji sun sake
wucewa da tanja zuwa kitchen,saidai ko motsi me qarfi taqiyi bare suyi tunanin idanunta biyu.

Awa guda ba kadan aka sake buga qofan,yanzunma dai a hasale ta soma magana

"Batoul ku fita a ido na fa?"

" Da sukayi me?" Taji muryar ama tana tambayarta daga bakin qofar. Wani gumi taji ya karyo mata

"Innalillahi" ta fadi da muryar rad'a tana ware idanu

"Tashina sukeson yi ama.... Kuma....."

"..... Kuma me?,yau baki da aiki ne?"

"Na dauki hutu ama sai next week ana gobe zan sake program" ta fada tana hadiye wani yawu me kauri
a maqoshinta

"To yayi,kizo aba dinku yana kiranki......but kada ki wuce minti talatin don fita zaiyi"

"Gani nan ama" ta fada da sauri. Yadda take amsawar ya bawa ama mamaki,tadan tsaya jim

"Are you okay?" Ta tambayeta tana kallon qofar dakin


"Yes am....ama"

"Budemin qofar dai" ta fada tana jin bata gamsu da yadda muryarta ke fita ba kaman a tsorace.

Maida dubanta tayi ga maina a tsorace,hankalinsa kwance,hasken safiyar ya haske fuskarshi ta


wani sake fresh.

"Sultana" ama ta sake kiran sunanta

"Gani nan ama ina saukowa daga gado ne....."

"Alright.....daga baccin kika tashi ashe.....karki zauna kizo kiran aba dinku" sai taji ama din ta juya tana
barin wajen.

Ido ta lumshe tana yada kanta gefe hadi da sakin ajiyar zuciya

"Matsoraciya" taji ya fada da muryar bacci. Da sauri ta daga kai cikin mamakin dama duk abinda akeyi
yana jinsu?. Tun bugun dasu benazeer sukayi suka katse masa baccinsa,sai baccin ya zama ba wani me
nauyi ba,yanajin komai amma kwanciyar ta masa dadi shi yasa yaqi tashi. Idanunsa ya bude sai idanunta
cikin nasa,ya ture duvet din ya miqe yana zama sosai saman gadon.

"Am starving......me zan samu?" Ya fadi yana lumshe idanunsa. Gaba daya zuciyarta ta karye,ya qarasa
gigitata,sai kawai ta sakar masa hawaye. Ta yaya zaice zaici wani abu?,salon ta fita dauko masa wani ya
shigo?.

Tsaiwa yayi yana kallonta,kaman bazaiyi magana ba sai ya rusunar da idanunsa yana cewa
"Banason kuka.......tashi ki shirya kije kiran aba"

"Ni a shirye nake" ta tari numfashinsa,sai kuma hankalinta ya dawo jikinta sanda taga yana bin jikinta da
kallo. Tabbas yamutsewarta da yamutsewar jikinta kadai zai sanya ka saka mata ayar tambaya. Baice
komai ba ya sauko ya a nutse daga gadon yana wucewa toilet,sai tayi amfani da wannan damar ta wuce
wardrobe dinta tana laluba abinda zata sauya din.

Allah ya taimaketa ta shirya cikin sauri, doguwar riga ta saka daga ciki sannan ta dora babban
hijab har qasa. Tana gyara madaurin fuskar hijab din ya fito daga toilet din,ta gefan ido ta saci kallonsa
sai akaci sa'a shima ita yake kalla din,ta masa kyau qwarai,hijab din ya wani qara mata kwarjini sosai,ta
dauke idonta tana qoqarin gyara igiyar,sai yayi taku hudu ya qaraso gareta. Hannunsa ya sanya saman
nata,dumin hannunsa ya ratsata,sai ta zame hannunta da sauri,hakan ya bashi daman gyara igiyar ya
daura mata ita saman tulin gashinta data nannade ya zamana kamar ribbon ta sanya.

Ta saman kafadunta ya zura kanshi yana kallon kyawawan idanunta ta cikin madubi

"Zaki tafi baki sake tambaya na me nakeson gaya miki ba.......well,na cinye abuna nima......yanzun ace
aba ya tambayeki idan kinje......me ya kawo aliyyu dakinki yake kwana wanne amsa zaki bashi?" Ji tayi
kaman a gaske aba dinne yayi mata tambayar,saita juyo a rude suka hada idanu,ta dauke kanta kuma da
sauri tana jin tana dirircewa.

Murmushin gefan baki ya saki, yayi taku biyu da baya da baya

"If kuma ya tambayeki kinason maina?,zaki koma dakin mijinki?,wanne amsa zaki bashi?" Ya jefa mata
tambayar yana kallon reaction nata ta cikin madubi. Qin daga idanunta tayi bare ya samu damar kallon
qwayar idanunta,abu daya taji har cikin jininta ya jefeta da wata magana me girma. Ta qarasa ta zira
slippers dinta ta soma takawa a hankali shi kuma idanunsa yana biye da ita,ta tsaya cak sanda ta isa
bakin qofa,ba kuma tare data waiwayo ta dubeshi ba tace

"Zan gaya masa bana sonshi......ban kuma taba sonshi ba,bazan kuma koma ba.....idan zaka fita daga
dakinnan kayi qoqari kada wani ya ganka please" daga hakan kamar wadda ke tsoron za'a kamata ta
taka da sauri tana fita a dakin.
Qas yayi da kansa yana jin maganarta na shiga ranshi,baiga fuskarta ba bare ya karanceta ta cikin
idanunta,saboda haka bashi da tabbas din abinnan da take gaya masa gaskiya ce ko qarya
tsagwaronta,koma meye take fada yaji saukar furucinta sosai,wani qaramin murmushi da baisan a
wanne gida ya ajeshi ba ya qwace masa

"Saina sanyaki kin qaryata kanki da kanki da bakinki......wallah.....indai na haifu jinin aba......saikin
qaryata kanki cikin mutane sababin yadda kika fadi maganarki a sirrance" ya fadi a fili murya a qasa. Ya
fahimci abu na qarshe da bataso shine asan yana cikin gidan cikin dakin,kanshi tsaye hannayensa zube a
aljihun wandonsa ya fara dosar fita daga dakin gaba gadi,kanshi kuma tsaye,duk da yana jiyo muryar
ama benazeer da batoul daga falon.

[7/22, 10:23 PM] +234 810 016 0470: *_GUDUN ƘADDARA_*

*H U G U M A*

BOOK 02 PAGE 110

Cikin nutsuwar data roqa Allah ya bata kada wani cikin gidan ya gano komai tattare da ita take
fitowa a dakin. Ayana itace ta farko da suka fara kacibus,tana tsaye tana kurbar wani abu cikin
mug,jikinta sanye da pajamas masu dogon hannu da dogon wando,kanta sanye da qaramar hula. Sultana
ce ta fara dauke idanunta daga kan ayana din. Haka kawai batason wannan kallon da take tsireta
dashi,kuma sam tana jin jininta dana ayana bai hadu ba kwata kwata,tana da zaqewa hali guda daya da
sultana taqi jininsa kenan.

Ci gaba tayi da fitowa cikin falon,ta gota ayana din ba tare data waiwayeta ba. Wani abu me
tauri ayana ta hadiya hade da madarar da takesha,ita kadai tasan yadda takejin matsanancin kishin
sultana cikin ranta,bayan kishi tana kishin yadda ta fita da komai,duk kuma yadda taso gano makusar
sultana ko aibunta ta gaza ganowa,hasalima duk wani move nata sai yakeson ya dinga burgeta,kama
daga yanayin takunta,salon yadda take magana da kums kallo,komai bisa aji da wani irin tsari.
"Good morning" ayana tace da sultanar sanda take giftata, saboda tayi imani ama zatace ta gaida matar
yayanta ne,sunan matar da ama ke bawa ayana yana sanyata a nazari,da auren ko babu?,idan da auren
bataga alamar wani good relationship tsakaninsu ba.

Adan dake sultana ta juya tana qoqarin dora murmushin dole kan fuskarta

"Kin tashi lpy baquwar Paris?"

"Alhamdulillah" ayana ta amsa tana lumshe ido jin yadda sunan PARIS din ya fita a bakin sultana tarwai
kaman don ita aka sanyama garin sunan. Daga haka sultanan bata qara ba tayi gaba wajen yaran da ama.

Tana riqe da hannun benazeer da batoul suna gaidata,amsa musu takeyi amma kaf hankalinta
ba'a kansu yake ba. Gani takeyi kaman zai fito yabar dakin,tasan halinsa komai ma zai iyayi,bashi da
tsoro,hakanan ba abinda yake canza masa maganarsa.

Waiwayawa tayi suka hada idanu da ama,saita samu kanta da sulalewa har qasa tana
gaidata,duk da saita rusuna sosai din take gaidata kullum kwanan duniya,amma gaisuwar yau din ta
banbanta da ta kullum.

"Lafiya alhamdulillah" ama din ta amsa mata tana dauke kanta daga gareta

"Batoul riqewa aba wannan muje" ama ta fadi tana miqawa batoul wasu qananun cups biyu

"Ni ba za'a bani na riqe masa ba?" Benazer ta fada tana karya wuya gami da maqale kafada

"Batoul yace a bawa,next time sai a baki kema" ama ta amsata tana daukan warmer ta soma yin gaba.

'Yar qaramar sautin da qofofin dakunan ke bayarwa a duk sanda aka budesu yaja hankalin ayana
dake zaune cikin falon tana satar kallon sultana da yaranta cike da kishi. Mutuwar zaune tayi ganin
wanda ke fitowa daga dakin sanye da kayan bacci da suke bada tabbacin ko a nan ya kwana,ko kuma ya
shigo da asuba yayi bacci cikin dakin,don yanayin fuskarsa ta nuna lallai daga baccin ya tashi. Kasa motsi
tayi,sai idanu data zuba masa,qwaqwalwarta ta kasa tuna ko tantance komai. Ya haidar ne ya fito daga
dakin sultana, dakin da tana a tsaye itama sultanar ta fito daga ciki?. Wani irin abu taji yana mata yawo
dukka sassan jikinta,ta kasa controlling yadda zuciyarta ke mata zafi,saita dinga qoqarin dauke kanta
daga sashen da yake don tana gudun abinda zuciyarta zata iya ci gaba da raya mata a kansu.

Sam baima lura da wanzuwarta a wajen ba,dukka hankalinsa yana kansu,yana jingine jikin qofar
dakin yana murmushi gami da kallon dukka drama din da akeyi tsakanin ama dasu din hannayensa nade
a qirjinsa. Dama haka akeji duk safiya sanda ka wayi gari cikin familynka?. Baya benazeer taja alamun
taji haushi,sultana da takeson kowa da kowa yabar falon koda zai fito ta juya tana zare mata idanu

"Ba za'a gaya miki magana ki haqura ba?,oya wuce muje" baki ta kyabe kaman zata saki kuka sannan tayi
gaban,sultana ta bita da kallo ta soma takawa tana bin bayansu itama. Bakin qofar ya bari shima yana
nufar hanyar fita,saidai kuma kafin takai ga bacewa cikin jikinta ta dinga jin kaman ana kallonta,wannan
ya sanyata waiwayo babu shiri.

Mutum biyu ta gani a falon,tanja dake fitowa a kitchen da kuma maina din dake qare mata kallo
tamkar yau ya fara ganinta,sai ayana da itama ke kallonsu kamar idanunta zasu fado d wani mahaukacin
kishi. Wani gumi ya yanko mata,ta firgice gaba daya tana fidda fararen idanunta

"Barka da safiya" tanja ta fada tana dan rusunar da kanta

"Ina kwana tanja,mun tashi lafiya"

"Lpy alhamdulillah" ta amsa masa tana wucewa dining area da dan sauri sauri da alama tanason aje
abun hannunta ne ta wuce tabar musu falon,hakan ke alamta kenan ta fahimci daga inda ya fito?,
sultana ta tambayi kanta da kanta. Ga ayana da tayi imanin taga fitowarsa,don ta karanceta da alama
zatayi qwaqwafi da sanya idanu akan lamuran da basu shafeta ba.

Kallonta ta maida kan tanja,amma sai taga tanja din fuskarta bata nuna komai ba,bata gamsu
ba,tunda tasan tanja farin sani,daga ita har maina din tanja ta haddace halin kowa,tunda ba wai yau ko
jiya take tare dasu ba,tun tale tale da quruciya cikin jikkunansu. Ganin tanja ta soma barin wajen ya
sanya itama ta qara sauri da zummar barin wajen,sai kuma muryar benazeer tayi mata birki

"Laaa.......daddy a nan ka kwana?" Faf ta buge bakin benazeer ba tare data shirya ba,ta kuma juyata da
sauri tana saita mata hanya. Tayi imani idan ta bari wannan akun ta isa wajenshi to ba wanda ya isa ya
rufa asirinsu sai Allah.

Idanunsa ya runtse har cikin zuciyarsa yana jin zafin bugun da ta yiwa benazeer din,ta riga da
tabar wajen,koda yayi magana ta bacewa ganinsa bazaiji ba. Ya kusa minti biyu tsaye a wajen sannan ya
juya yana ficewa daga gidan,amma ranshi yana masa susa har yanxun na dukan yarinyar da tayi. Ji yayi
ya kasa jurewa,har ya isa bakin qofar gidanshi suhail ya bude masa sai yace

"Ina zuwa" ya juya yana komawa cikin gidan,duk da yaci alwashi bayason aba yasan da zamansa cikin
paris ko zuwansa cikin gidan,amma yau yana jin bazai bar gidan ba sai ya mata gargadi na gaske,tafiya
zaiyi na sati uku,haka zai tafi tana dukan masa yara?. Da qyar ayana taja numfashi takai hunhunta,ji tayi
babu sauran space da zata iya zama cikin falon tana kallonsu,bayan ba abinda take ganowa cikin
idanuwansu illa zallar soyayya me masifar zafi da akan jarabci zukata da ita,saidai kuma qasan zuciyar
akwai wani abu da yakeson lallai saiya murqushe soyayyar ya hanata bayyana kanta. Duk kuwa da
idanuwa suna qaryata hakan,ta cikin idanunsu kawai zaka iya karantar kome,saita miqe da sauri saurinta
tana wucewa daki tun kafin ta rasa ragowar numfashin da zata shaqa,zuciyarta tana karyewa,tana jin
kamar tana dab da rasa dukka damarta ne.

Tunga taja ta tsaya a hanya tana tsare batoul da ido,ta tabbatar sukaje wajen aba a haka tana
kuka zai tambayi ba'asi,kuma lallai indai benazeer ce me bakin bada labari ba zata kasa gaya masa ba,
musamman ita din,tatabbatar indai ta fadi aba zaya lallasheta ne,yakuma hadata da chocolate ko sweet

"Bana hanaki surutu akan duk abinda kika gani ba?,ban hanaki bada labarin abu koda tambayarki akayi
ba bare ba'a tambayeki ba?" Ta fadi tana tsare yarinyar da idanu fuskarta a daure.

"Kinaso na daina kulaki kwata kwata?" Da sauri benazeer ta girgiza kai kukanta yana tsayawa tana duban
sultana a tsorace

"To daga yau indai baki bar wannan halin ba ruwana dake"
"Na daina mummy" ta fada tana qwalla

"Naji......goge hawayen" ta fadi mata tana dubanta. Da kanta ta saka gefan hijabinta ta goge mata
fuskar,ta tabbatar ta koma normal sannan suka wuce.

Ta samu aba tuni ya fara breakfast shi da batoul, benazeer tayi joining dinsu,ita kuma ta zauna
suna hira kadan kadan da aba din tana tattare duk inda su batoul suka bata har suka kammala.

Aikenta yayi saman study table dinsa ta dauko wasu takardu,ya budesu ya miqa mata

"Wadannan fa aba?" Ta tambayeshi idanunta a waje

"Nakine sultana, mohmoud baya raye,duk abinda na raya a raina inda yana raye zanyi masa to ke ya
cancanta na yiwa" jikinta gaba daya yayi sanyi,ta kasa cewa komai sai ama datake kalla kamar tana jira ta
bata umarnin yin magana

"Kinga ama" ta fadi tana dorawa ama takardun a cinya. Murmushi ama ta saki,duk duniya batasan me
zasuyiwa jinin mohmoud su saka masa ba,alkhairi keta bibiyarsu ta sanadin sadaukarwarsa da kuma
jininsa daya bari a duniya,ita ko da benazeer da batoul ta tsira daga jinin mohmoud bata da abun cewa

"Na gani sultana,aba muna godiya Allah ya qara budi da arziqi" tayima aba godiya don ta bawa sultana
qwarin gwiwa. Qwalla taji ta cika mata idanu,batasan adadin dukiyar data mallaka ba daga hannun
aba,komai ya rarumo sai ya rubuta mallaka da sunanta,tamkar baisan ciwon kudin ba. Muryarta na rawa
take masa godiya,yayi murmushi yana janta da tsokana,bari barta ta tashi a wajen ba sai data sake.

Ita ta fara fitowa ta barsu,don muddin aba yayi irin wannan zaman benazeer da batoul na
gefansa to tashinsa a wajen ba yanzu ba. Dam bata lura dashi ba,don hankalinta yana kan takardun
hannunta tana sake shiryasu,saidai kuma abinka da aikin jini,tana qarasa fitowa falon dukka jikinta ya
dauka,saita dan rage saurin tafiyarta tana maida hankalinta gabanta.
Ya nutse sosai cikin kujera yana fuskantar tv,a haka idan ka kalleshi zakayi tsammanin bacci
yake,amma kuma ba baccin yakeyi ba,yana kallon komai fes,yana kuma ankare da kowa. Fitowarta ya
sanyashi dan qarawa idanunsa girma,wannan ne ya bata daman sake tantance idanunsa biyu.

Yunqurawa yayi ya zauna sosai,daidai sanda ama ke fitowa daga wajen aba din. Fuskarshi a
matuqar daure,daurewar data haifar mata da tsoronsa,irin tsohon tsoron nan da take masa a
baya,sanda yake tamkar wani mai gadin motsin kowa na gidan,ya zamewa gidan katanga,idanunsa akan
tarbiyya da shige da ficen kowa.

"Daga yau......kada ki sake gangancin dukarmin yarinya a fuska ko a baki,idan ba haka ba zakisha mamaki
na wallahi" ya fadi mata yana bude dukka idanunsa. Saida gabanta yayi mummunan faduwa,don ta jima
bataga fuskarshi da idanunsa cikin irin wannan yanayin ba. Kanta ta kawar da sauri, zuciyarta na raya
mata kodai maganar daxun itace ta tunzurashi?,banda haka dukan data yima benazeer baici ace ya dagi
hankalinsa ko ya bata masa rai har haka ba.

Sum sum ta wuce zuwa ciki,sai a sannan yaga ama dake tsaye a bayanta. Idanunsa ya lumshe
sanda suka hada idanu da ama din,yanajin bacin rai sosai cikin zuciyarsa

"Ina kwana ama?" Ya fadi cikin rusunawa da girmamawa

"Lafiya qalau" ta amsa masa tana nazarin fuskarsa. Zuwa yanzun tana jin zuciyarta tana quntata da
yawa,haqurinta yana shirin gazawa,ta fahimci daga maina sultana har aba zuru da zuba idanu ba zatayi
musu aiki ba,wacce irin rayuwa ce suke shirin tanadarwa gobensu?.

"Ka gaida aba?" Tayi masa tambayar tana zama saman kujera tana kuma qureshi da kallon nan da yake
sanyashi jin shi din tsantsar me laifi ne

"Zanje ama,kiyimin afuwa sai na dawo daga tafiya,ina buqatar adduarki,yau zan wuce los Angeles,sati
uku kawai zanyi in sha Allah,idan na dawo komai zai daidaita......na miki alqawari,amma da taimakon
adduarki" shuru ta danyi tana karatu akan muryarsa, muryarsa tayi rauni da yawa,ta tabbatar akwai
damuwa sosai cikin zuciyarsa
"Allah yasa,Allah ya tsare ya bada sa'a"

"Ameen ya Allah na gode" ya fadi yana tashi,hanyar waje ya kama,kamar tace ya tsaya yayi breakfast
dasu amma ta sani ba lallai ya iya ci din,ranshi a bace yake,kuma muddin yana cikin bacin rai irin haka
baya iya cin komai.

"Aliyyu" ta kirashi da sunansa,sai ya dakata ya waiwayo

"Ka dinga qoqarin rage bacin ranka akan sultana......karka manta har yanzun rainonka ce ita,kafi kowa
sanin yadda zaka tafi da ita" karon farko ta sanya baki akan abinda ya shafeshi shi da ita,sai yaji cikin
tsakiyar zuciyarsa kaman an cire wani dutse an maida gurbin wajen da dutsen qanqara,har ajiyar zuciya
tana subuce masa. Wato har yanzun dai sultana nada wannan matsayin cikin rayuwa da zukatansu,har
yanxun basa ganin laifinta cancan,harda ita kanta ama din ma,bata taba yaba ma juriyarsa da kawaicinsa
ba,amma ya yiwa diyarta fada sau daya ta kasa haquri?. Murmushi ya subuce masa yadan girgiza kai

"In sha Allah ama,na gode" ya qarasa fada yana ficewa da sassarfa.

_KWANKWASON JIMINA_*

*_TSUTSAR NAMA_*

*_AMEENATOU_*

*_GUDUN KADDARA_*

_DUKKA AYARIN LITATTAFAN KUDINSU YA KAMA KAMAR HAKA_*


LITTAFI DAYA_400

BIYU_800

UKU_900

HUDU_1200

_IDAN TA BANKI NE ZAKI SANYA KUDINKI A WANNAN ASUSUN_

6019473875

Musaa Abdullahi safiya

Keystone bank

_ANTAYA SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA WANNAN NUMBER_

09166221261

*Masu tura katin waya ko vtu kuma kai tsaye wannan number zaku tuntuba*

09134848107

*Maqotanmu kuma al'ummar qasar nijer zaku tuntubi wannan number dinne kai tsaye don biyan naku
kudin*

09033181070
*ZAFAFA FAMILY na maraba daku*🫂🫂🫂🫂🫂

You might also like