0% found this document useful (0 votes)
312 views210 pages

Attachment

The document is a fictional narrative centered around Captain Ahmad Junaid, detailing his daily life, interactions with family, and a dramatic incident involving a distressed woman and a child. The story highlights themes of compassion, family dynamics, and the challenges faced by the protagonist. It includes elements of Hausa culture and language, showcasing the character's relationships and experiences in a vivid manner.

Uploaded by

Zaynerb Eerderm
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as TXT, PDF, TXT or read online on Scribd
0% found this document useful (0 votes)
312 views210 pages

Attachment

The document is a fictional narrative centered around Captain Ahmad Junaid, detailing his daily life, interactions with family, and a dramatic incident involving a distressed woman and a child. The story highlights themes of compassion, family dynamics, and the challenges faced by the protagonist. It includes elements of Hausa culture and language, showcasing the character's relationships and experiences in a vivid manner.

Uploaded by

Zaynerb Eerderm
Copyright
© © All Rights Reserved
We take content rights seriously. If you suspect this is your content, claim it here.
Available Formats
Download as TXT, PDF, TXT or read online on Scribd
You are on page 1/ 210

COMPILED BY ESHATT SMILER

HOME OF HAUSA N ENGLISH NOVLS DOCUMNTS


WASPP 08066360176 FOR MORE

CAPTAIN_AHMAD JUNAID
_By Khaleesat Haiydar_
*Dedicated to......*
*Ya Allah! Ya Allah! Ya Allah, Ya ubangiji kamar yanda ka bani ikon fara littafin
nan ka bani ikon kare shi cikin aminci da yardar ka, Ya Allah ka min katanga irin
ta China da duk wani soul da xai daga min hankali a Media ya Allah ka rabani da
sharrin mahassada da duk 'Yan uwana musulmai baki daya, ya Allah ka kara hada
kawunan musulmai a duniya ka tsare mu a duk inda muke, Ya Allah ya ubangiji kasa mu
gama da iyayen mu lafiya, kasa mu cika da imani da tsoron ka a xuciya don son
ma'aiki S.A.W*
Uhnm! my greetings goes to my die hard fans nd frnds dat are alwayz their for me
My Phatiemarkh
Habibah Marafa
Hafsat (Ummu Ilham)
My Humainah bala Abkr
Eeshatullah Goni
My Maryam Aliyu
Rukky Usman
Saknah Ibrahim
Sallynah
Ummu Lailah(AY)
My Salmah
Maman Shakur
Fiddo s dangi
Waow to mention but a few, Khaleesat heart you all. Shout out to my lovely fans.
Allah bar min ku.
1.....
Ya jima xaune kan darduman bayan ya kai Ayan karshe a Surah At-tawbah, ganin har
shidda da rabi ya sa shi mikewa a hankali ya rufe qur'anin ya ajiye a bedside
drawer, jallabiyan jikinsa ya cire ya nufi bathroom, ya dau lkci yana wanka sabulai
masu dadin kamshi da shower gel duk ya cika dakin, sanye da bathrobe ya fito yana
goge lallausan bakin gashin kansa da karamin towel, gaban mirror ya nufa ya dauko
lotions dinsa daga tsaye nn ya shafa, yana gamawa ya jawo mayyukan gashinsa ya
shafa ya shiga combing gashin nasa, closet dinsa ya bude ya fiddo well ironed wear
din da xae sa dake jikin hanger, farar singlet ya fara sawa, cikin mintuna bakwae
kacal ya gama shiryawa, ya dauki silver wrist watch dinsa kirar Emporio Armani ya
sa, shoe rack dinsa ya nufa ya dauki bakar cover shoe kirar Haggioti ya koma gefen
makeken gadonsa ya xauna ya sa bakar safarsa na kafa snn ya sa shoe din, duk wnn
abinda yake kwata kwata bae da walwala, mikewa yyi ya shiga tucking din farar
uniform din jikinsa kafin ya dauki belt ya sa, wayarsa ya dauka da hularsa ya koma
gaban mirror ya feshe jikinsa da turarruka ya nufi kofa ya fita, Captain Ahmad
Junaid kenan, A Certified seafarer (Merchant Navy) Kmr bae son taka kasa yake
tafiya a makeken compound din, sai yake ga kamar yayi shekara rabonsa da gidan
nasu, Where as sati biyar kawai yayi a Egypt, kai tsaye part din Hajiyarsa ya nufa,
bbu kowa falon se kamshi me ddi dake tashi da ya hade da kamshin soye soyen da ake
a kitchen, falonta ya nufa da sallama cikin sanyayyan muryarsa, fitowarta daga
bedroom knn ta amsa sallamarsa, xama yyi kan kujera yana kallonta yace "Gud morning
Mumy" ta dan yi murmushi tana kallon agogo tace "Baka makara ba, dubi har bakwae ya
gota ko duk gajiyar ce haka" Shafa lallausan gashin kansa yyi yace "Jiya da
headache na kwana Mumy duk na gaji" tace "Ba na baka magani ba? Baka sha bne" a
hnkli yace "Na sha" tace "Toh taso mu je kayi break, sae ka kuma sha, kar ka
makara" mikewa yyi ya bi bayanta suka koma falo yace "Ina su Fatima?" Tace "Sun
tafi makaranta" da kanta ta jera masa breakfast kan dinning, ta hada masa tea me
kauri, snn ta koma falonta dauko masa magani, ko kan ta dawo ya shanye tean, don ba
da xafi ta hada masa ba sanin bae shan abu me xafi, tana tsaye kansa ya kora
maganin snn ya mike yace "Mumy bari in tafi am almost late" tace "OK, amma ka shiga
ka gaida 'yan gidan, tun da ka dawo baka shiga ba" bude dara daran idanuwansa yyi
bae ce komae ba ya kafa hularsa sai dai da gani kasan ransa bai so ba, ta rakasa
har bakin kofa don ta tabbatar ya shiga gaida mutan gidan, part din Hajiya Fati ya
nufa, ya tura kofar da sallama, xaune ya sameta tana karyawa a babban falo, xaunawa
yyi yace "Ina kwana Hajiya" ta dan kallesa tace "lfya lau mutan misra, an ga daman
shigowa gaida mu kenan" shiru yayi bai ce komai ba sai kuma ya mike yace "Na tafi
aiki" daga haka ya fice daga falon, ta bi sa da kallo ba dae ka iya gane ma'anar
expression din fuskarta, ta dan yi murmushi ta ci gaba da cin kwan gabanta, Part
din Hajiya Bilki ya shiga, ita kuma ya sameta tana kunduma ma 'yan aikinta xagi kmr
xata dokesu, 'yar ta Sadiya na kwance tana danna waya, daga bakin kofa ya tsaya ya
dan duka ya gaisheta, harara ta 6alla masa tace "Ehh lallai Ahmad a 6akin kofa ka
gaida Uwarka yau d'an rainin wayo, sai yanxu kasan da mu a gidan?" Hade rae yyi
wanda hkn ya kara fito da ainahin kyansa na dan fillo, tsaki tayi ta ci gaba da
6abatun ta ma 'yan aikin ya juya yyi ficewarsa, parkin lot ya nufa ya dauki motar
da xae dauka ya bar compound din bayan masu gadi sun bude masa gate, today at work
was so stressful for Captain Junaid don duk a gajiye yake from yesterday's journey.
Karfe biyar da 'yan mintuna ya isa gida, ya jima xaune cikin mota yana latsa waya,
ganin motar da ya shigo compound din ya sa shi kashe motarsa ya fito ya rufe ya
nufi bangarensa, tuni itama ta fito daga motar tare da step sis dinsa Sadiya, bin
bayansa tayi tana kallonsa cikin sanyayyan murya tace "Ya Junaid Ashe ka dawo!"
Juyawa yyi har lkcn bae tsaya ba ya kalleta snn ya dauke kai yana ci gaba da
tafiyarsa yace "Eh!" D'aga hka ya shiga balcony din bangarensa, dariya ta ji daga
sama ta d'aga kai taga Muhibba dake xaune balcony macbook dinta a gabanta tana
taunar cingam ta tabe baki tace "Cusa kai ba kwarjini" Suhaima ta dauke kanta
xuciyarta na tafarfasa ta nufi bangarensu kmr xata tashi sama, Sadiya tayi 'yar
dariya ta rufe motar ta bi bayanta. Shi kam dakin sa ya nufa ya cire uniform din
jikinsa ya shiga bayi, wanka yyi ya fito ya shirya cikin kananun kaya, jeans baki
da polo blue duk hankalinsa na gun Mum dinsa, wayarsa ya dauka ya nufi bangaren ta,
xaune ya sameta falo ita da kanninsa Fatima da Aysha, gefenta ya xauna yyi mata
side hug ya kwanta jikinta cikin murya me shige da ta shagwaba yace "Momyna am
back" Fatima ta kalli Aisha suka tabe baki a tare, Mumy kam murmushi tayi ta dauke
fuskarta tace "Welcm! ga abincin ka can dinning, ga dai kannin ka suna kallon ka"
yayi 'yar dariya yace "Toh ina ruwana da su" gaishesa suka yi a tare, Fatima tace
"Ya A.jay ina tsarabar mu" mikewa yyi ya nufi dinning yace "Aiki na tafi ba holiday
ba ai" abinci kusan kala uku ya tarar dining din, farfesun naman rago ya soma diba
yana ci. Ko da ya gama bai bar dining din ba yana ta danna waya ganin shidda ya
kusa ya mike ya dawo parlor yace ma momy xae je gun abokinsa El-Ameen, tace
"Maimakon ka huta kai da kake ciwon kai Ahmad!" Girgixa kai yyi yace "Mum ni ba
ddewa xan yi ba" tace "toh shikenan Allah ya tsare!" Bangarensa ya koma ya canxa
kaya xuwa farar shirt da blue jeans ya dauki makullin motarsa bayan ya feshe
jikinsa da turare ya fito ya nufi parkin lot ya dau motarsa ya bar gidan. A hankali
ya rage gudun da yake ganin d'andaxon jama'ar da ke gefen titi a tsaye, da yawan
motoci ma sun tsatsaya gefen titi masu shi duk sun fiffito ko wanne na son ganin
abinda ya janyo taron, a hnkli ya gangara gefen titi don a tunaninsa hatsari ne
kuma bae ga alamar taimako mutanen dake tsatstsaye suke badawa ba yasan kallo kawae
suka tsaya yi, bude motarsa yyi ya fito ya nufi cikin taron jama'ar ya kutsa kai,
sae a snn ya dinga jin ihun da wasu ke yi, wata ya gani xaune tsakiyar taron
hannunta rike da wani yaro da baxae wuce shekaru goma ba sae dukansa take iya
karfinta, ga jini na xuba goshinta ba kadan ba, duk tayi dukun da daud'a cikin wata
yagaggiyar doguwar riga, wasu samari biyu ne ke kokarin kwace yaron dake kurma ihu
hannunta amma sbda irin rikon da tayi ma yaron suka kasa, da ganinta ka ga
mahaukaciya, karasawa Junaid yyi da sauri inda suke ganin xata ma yaron lahani ya
fixgo gashin kanta da yyi wani dukun dukun da datti, ta saki kara don ba rikon wasa
yyi ma gashin ba, amma duk da hka ta ki sake yaron, kara damke gashin yyi da karfi
ae ba shiri ta sake yaron tare da kwala wani k'aran, samarin biyu suka dauke yaron
da ya rage kiris ya suma don wahala, ta yunkura xata cakume Junaid, ae da sauri ya
hade hannayenta da karfi ya murda su xuwa bayanta, ta dinga ihu tana shure shure,
kallon samarin gun yyi yace a samo masa igiya, ae da sauri suka juya xuwa neman
igiyan, wata 'yar dattijuwa dake cikin taron ne tace "Baiwar Allahn nn ta kusa
shekara unguwan nn bata taba kama d'an mutum tayi masa haka ba sae wannan karan,
kuma wllh yaran ne suka addabeta da tsokana shi yasa tayi hkn" wata mata ta karbe
tace "Yo dama idan ba tsokanarta suka yi ba me suka mata, dubi goshinta dutse suka
jefa mata, yara basa ji sae daukan magana da tsokana, ni ko kadan ban ga laifin
Baiwar Allahn ba, sae ma tausayin da ta ban, haba jama'a" nan dae aka dinga
jajantawa, ko wa na fadin albarkacin bakinsa, shi dae yana rike da hannunta ta
baya, ta sunkuyar da kai, duk farin shirt din jikinsa ya bace da datti, samarin ne
suka dawo da igiya babba, da taimakonsu ya shiga daure mata hannu da kafa, ba
karamin kokuwa suka sha da ita ba yyi mamakin karfinta hka, Suna gama daureta ya
koma baya yana kallonta don ganin ko xata iya kuncewa, hawaye ne ke sakkowa daga
idonta, jikinsa ne yyi sanyi yana kallonta, lkci daya tausayinta ya ratsa sa, a
hnkli ya shiga kakkabe hannunsa, idonsa ya kai kan goshinta da har ya gaji da fidda
jinin da yake ya daskare, ya girgixa kai yana kallon samarin yace "Ku taimaka a sa
min ita a mota in kai ta a duba goshinta" 'yar dattijuwar daxu tayi wani k'ara tace
"Wani asibitin yaro? Ynda Duniyar nn ta dawo ba gskya ynxu, kai waye? Kuma d'aga
wani anguwa kake?" Nan jama'a suka fara cece kuce a wajen ana kallonsa, shiru yyi
bae ce komae ba, can ya sauke ajiyar xuciya ya juya ya nufi motarsa cikin rashin
kuxari, nn aka bi sa da kallo ana cewa "Kun ga rashin gskyar knn, don da yana da
ita da dole xae tsaya ya amsa tambayoyin da aka yi masa, kaiii Allah ya raba mu da
sharrin mutum" shi kam motarsa ya shiga ya ja ya bar wajen, nan aka fara watsewa
kowa na fadin albarkacin bakin sa, wani tsoho ne ya karasa ya kunce mata daurin
yana d'an ja da baya kadda ta cafkesa har ya gama ya bar wajen bata d'ago ba bare
ta kallesa.
*Haske Writers Association*
[16/10, 19:05] Hassan Atk: *Captain Ahmad Junaid*
_By Khaleesat Haiydar_
6.....
El-Ameen ya juya yana kallon Junaid ganin ya ki karasowa da karfi yace "baxa ka xo
ka ga abinda mahaukaciyar da ka sa na kawo gidana tayi ba, ya Salam!" Junaid na jin
hka ya karaso da sauri yana leka parlon, kwalalo ido yyi yana kare ma palon kallo,
palon komawa yyi kamar wanda aka yi karamin yaki, don duk ta tarwatse plasman palon
da frames gaba daya, lafiyayyen centre table din ma bata raga masa ba, ko ta ina
kwalabe ne a falo, duk ta tuttuge labulaye da karafunansu, kujeru kam upside down
ta juyasu dukka, Junaid bae san lkcn da ya fashe da dariya ba har da rike ciki, El-
Ameen ya bude baki yana kallonsa idon nan nasa ya kada, fixgosa yyi yana huci yace
"Yhu see wat you've caused koh Ahmad, gud! this mad woman is adding not a minute
more in my house" yana fadin hka ya turasa ya shiga palon, da sauri junaid ya
hadiye dariyarsa ya rikosa yace "Haba frnd, Chill plss ka mance mahaukaciya ce ita
kamar yanda kake kiranta, I promise wllh duk xan siya maka abubuwan da tayi damage,
that's a promise frnd!" marairaice masa Junaid yyi yace "Plss!" El-Ameen yyi kwafa
yace "Yanxu naji bayani, kuma ga motata ma can a gida bbu kyan gani, kasan yanda xa
kayi da shi, I need it the way it was before, nd don't forget it's my favourite
car" Junaid yyi murmushi yace "Kar ka damu xa a gyara" El-Ameen yace "Gud! Kuma
ynxu idan mu ka shiga naga tayi fitsari ko otherwise wllh kai xaka gyara min waje"
Junaid ya d'aga kafada yace "Na yarda" Nan El-Ameen ya sa kai ya shiga falon yana
bin ko ina da kallo, sae a lkcn ya kula da jinin da yayi littering din falon alamar
duk ta ji ciwo, kamar ance ya kalli bayan kofar falon ya ganta durkushe wajen duk
jini jikinta, suna hada ido ta mike da sauri xata yi waje ya yamutse fuska ya
fixgota da karfi, kokuwa ta shiga yi da shi ya mata wani lafiyayyen rankwashi ae
sae ga hawaye a idonta tana kallonsa, Junaid da yyi shiru yana kallonsu a hankali
yace "Haba El-ameen rankwashi kuma?" Ko kallonsa El-Ameen bae yi ba, ya ja ta suka
koma sama xuwa dakin da aka ajiyeta, bude baki yyi ganin duk ta fasa glass din
windunan dakin ma, ita nan duk neman hanyar fita take, kwalo ma Junaid kira yyi da
karfi, Junaid ya nufi stairs da sauri ya haura ya shiga dakin, El-Ameen na huci
yace "Ohh my God! Dubi windows dina Captain" Junaid ya langwabar da kai yace "Duk
xan gyara maka as soon as possible" El-Ameen yyi kwafa yace "Allah kar ya wuce
kwana biyu, kuma ni ka xo ka ajiye mata abincin my frnd, I have important things
doing a office" karasowa Junaid yyi ya ajiye abincin ya bude yana kallon yanda ya
rike hannunta gam sai mutsu mutsu take, El-Ameen ya kai ta k'asa ya nuna ta da
yatsa yace "Wllh Kika sake min barna a gidana sae na gaggalla maki mari, wawiya
kawai" ita dae kanta na k'asa, tsaki yayi ya mike yana kallon Junaid yace "Mu je
plss malam gashi ka kawo mata abincin hankalinka ya kwanta" Junaid yace "But ya
kamata mu samo 'yar dattijuwa yanxu koh?" Wani kallo El-ameen yayi masa yace "Ya
kamata dai ka samo" daga haka ya fice daga dakin, Junaid ya bi sa da kallo sannan
ya kalleta, har lokacin bata d'ago ba, abincin ya matsar mata gabanta a hankali
yace "Ki ci abinci kin ji, we are only helping yhu Baiwar Allah" ita dae kanta na
kasa sai d'ada takurewa waje daya take, kwala masa kira El-Ameen yyi ya fito da
sauri, El-Ameen ya sa ma dakin key yace "barnan ya tsaya iya dakin" shi dae Junaid
bae ce komae ba har suka fito, El-Ameen ya tafi gun tap din dake compound din gidan
ya wanke hannunsa yana tsaki ya nufi gate Junaid na bin bayansa, a cikin mota El-
Ameen ya ciro waya ya shiga neman nmbr, yana dialing ya sa hands free, sallama aka
yi masa ya amsa yace "Jibril kana ji na," d'aga daya bangaren aka ce ehh oga, yace
"Gud mai gadi nake son ka samo min nan da 'yan awanni don Allah, wanda ka sani
kasan halinsa fa" D'aga daya bangaren aka ce "Toh oga, in'sha Allah xa ayi hkn"
katse wayar El-Ameen yyi, Junaid ya tada motar suka bar layin, sae da ya fara ajiye
El-Ameen clinic bbu wanda yace ma kowa komae, yana fice masa a mota ya ja motar ya
nufi office shima, El-Ameen yyi murmushi yace "Ina xaune xa ka dawo ka same ni ne
ae"
Karfe hudu da rabi Junaid ya koma gida daga gun aiki, tunaninsa daya karyar da xae
ma Mumy ta bar shi ya fita, don ryt from time shi ba mae xuwa ko ina bane daga gun
aiki sae gida sai in kuma yaje kallon kwallo shi ma ba ko da yaushe ba don yafi son
kallon a gida, ko da yaushe yana manne da ita shi dai, yawanci ma El-Ameen ne ke
xuwa gidansu shi bae fiye xuwa can ba sosae, yana xaune bangaren Mumy bayan ya gama
lunch, ita kadae ke hiranta sai fatima dake ta shirin islamiyya, shi kam duk
hankalinsa baya tare da shi kawae ya kafa ma tv ido ne kmr me kallo, agogo ya duba
ya ga har biyar, ya fiddo waya ya kira lambar driver yace ya xo ya samesa bangaren
Mumy, ba a dau lkci ba drivern ya xo, Junaid ya ciro dubu goma ya mika masa yace
"Gashi wannan ka siyo fruits din dare kamar ynda kake siyowa ka kai ma kowa nasa"
Drivern ya risina ya karba yace "Toh yallabai," Junaid ya ciro Atm dinsa yace "ka
d'an biya Atm Machine ka ciro min dubu talatin" Drivern ya karba yace "In'sha Allah
yallabai" yana fita Mumy tace "Me xaka yi da dubu talatin Junaid" Junaid yace "Su
Umma xan ba ko suna bukatar abu kafin Abba ya dawo jibi" Mumy tace "Ohk Hakan yyi"
yana xaune sae kallon agogo yake a kai a kai har Ishaq ya dawo da ledoji hudu dauke
da fruits kala kala, ya ajiye ma Mumy nata snn ya ciro 30k ya mika ma Junaid,
Junaid yace "Yauwa ka raba dubu sha biyar biyar ka kai ma Hajiya daya Umma daya"
Mumy tace "A'a kai ya kamata ka kai masu" bae yi musu ba ya karbi kudin hannun
Ishaq, Mumy tace "Ajiye naku fruits din ka fara kai masu nasu" Ishaq ya ajiye leda
daya ya fita da biyu don kai ma Umma da Hajiya, ba a dau lkci ba ya dawo ya dauki
nasu ledan na masu gadi da masu wanki da share sharen gidan ya fita don xuwa su
raba bayan yyi godiya. Junaid ya kalli Mumy yace "Mumy xan je gidansu El-Ameen!"
Mumy tace "Gidansu El-Ameen kuma, wae wnn sintirin xuwa gidansu El-Ameen da kke
kwana biyun nn kalau kuwa Ahmad? Ko dae gun budurwa kake xuwa?" Ta kare maganan
tana murmushi, Dariya yyi ya shafa kansa yace "Kai Mumy budurwa kuma, shi dae nake
rakawa fa" Mumy na murmushi har lkcn tace "uhn uhn kai dae fadi gskya Ahmad" ya
shagwabe mata yace "Mumy ni da gske wllh ba gun budurwa nake xuwa ba, El-Ameen nake
raka wa" Mumy tace "In ma gun ta kake xuwa ae ba laifi bne Ahmad, it's high time
yhu start planning of settling down with a wife yanxu son" murmushi yyi ya mike
yace "Allah ya kawo lkci mumyna" tayi murmushi tace "Toh Ameen" yace "Bari in kai
ma su Umma kudin Mumy, daga can xan wuce" Mumy tace "Toh Allah ya tsare kar dae ka
yi dare plss Ahmad" yace "In'sha Allah mum" daukan wayarsa yyi ya fita daga falon,
gun Umma ya fara shiga ya samu Muhibba ce da wata kawarta a falon, ya wani hade rae
ba tare da ya damu da amsa gaisuwar da suka yi masa ba ya mika mata 15k din yace
"Gashi ki ba ma Umma" juyawa yyi ya fice daga falon, Kawar Muhibba me suna Salima
tace "Kai amma wllh kina bada mata Muhibba, har wannan dan karamin alhakin ne xaki
dinga barin yana walakanta ki don yana da kyau, ubansa kuma na da dukiya, sae kace
ba gogaggiyar 'yar jami'a ba?" Muhibba tayi murmushi tace "Baki san Ahmad bane
Salim, ya fice tunanin ki wllh...." Salima ta katse ta tana kalle kalle tace
"Da'alla banxa tsaya ki saurareni, mu je daki in baki wani plan ki ga ko baxae yi
aiki ba" mikewa Muhibba tayi suka yi daki da kawar tata cike da xumudin jin plan
din. Junaid na fita bangaren Hajiya ya nufa ita ma ya bata kudin, tana jujjuya
kudin tace "Duk kudin da Alhaji ya bari Ahmad ka rasa abinda xaka kawo min sae wani
shegen dubu sha biyar, wato sauran kuma ka ba uwar ka koh, toh wallahi ka ji tsoron
Allah don hakkinmu baxai bar ka ba" Junaid ya daga kafada yace "Ni Abba bae bar min
kudi ba, kawae gani nayi hakan ya dace shi yasa na kawo maki na kai ma Umma don ko
mahaifiyata ban ba kudi ba gidan nn, gobe ko jibi ae Abban xae dawo, in kina da
wani bukatar da ya wuce na wannan idan ya dawo sae ki tambayesa" yana kai wa nn ya
fice mata daga palo, ta bi sa da kallo baki bude, idonta ya kankance don bacin rai,
rufe bakin tayi tana gyada kai tace "yaro yaro ne" kwafa tayi ta juya ta koma don
ci gaba da abinda take tana wani murmushi. Karfe shidda saura Junaid ya isa gidansu
El-Ameen sanin ya baro clinic yanxu, Mum din sa ya samu falo, bayan sun gaisa yace
"Ummi El-Ameen ya dawo koh?" Hajiya Maryam da ake kira da Ummi tace "Ehh ya dawo
daxu amma ya fita yanxun nan, ka kira sa kaji inda yake don nasan baya asibiti"
Junaid yace "Toh shknn Ummi xan kirasa, ni xan koma" Ummi tace "Toh ko ruwa baxa ka
sha ba Ahmad?" Yyi murmushi yace "Alhmdllh Ummi" Ummi tayi murmushi tace "Toh ka
gaida min Hajiya Amina" yace "Xata ji Ummi" fita yyi daga falon yana tunanin inda
El-Ameen ya tafi, sae da ya shiga mota snn ya kirasa, bugu daya ya d'aga Junaid
yace "Kana ina ne?" El-Ameen yace "Au! ai nayi xaton xuciya kayi ka bar ni da
mahaukaciyar taka" Junaid yyi tsaki yace "Kana ina nace?" Dariya El-Ameen yyi yace
"Kai dae duk abun ka baxa ka iya xuciya da ni ba wllh, come over ina gidana, na
samo mai gadi, ya kuma min hanya an samu wata dattijuwa, we are ol there 2gether
ynxu, mind yhu duk wata xaka dinga biyan mai gadin dubu 30, ita kuma warce xata
tsaya da mahaukaciyar xa'a bata dubu 50 monthly, coz its not an easy job, ga kuma
risk din dake tattare da job din, and yhu make sure ka shiga kasuwa ka siyo mata
kayayyakin da xata dinga sawa including inner wears" Junaid yace "Ni ban san inda
ake sai da kayan mata ba" El-Ameen yace "So? Ba sae ka ce a raka ka ba, ko ka shiga
kasuwar kayi tambaya" tabe baki Junaid yyi ya katse wayar ya kama hanyar gidan. A
waje yyi parking ya shiga, sabon mai gadin da ke xaune compound din ya gaishesa da
ladabi, Junaid ya amsa ya nufi kofar shiga palo, daga bakin kofar ya tsaya yana
kare ma palon kallo, duk an share barnar daxu ko ina yyi fess, kallon El-Ameen dake
xaune kan daya daga kujerun falon yana danna waya yyi snn ya karasa shiga falon,
El-Ameen ya kallesa yace "Kayan fa, ni fa I can't put her under medication da
suturan jikinta, it's very irritating, na dae yi mata alluran barci daxu don ban ga
alaman tana yi ba" Junaid ya xauna gefensa yace "Toh don Allah ka raka ni mu siyo
kayan mana, serious ban san ina xan samu women wears ba" El-Ameen yace "Nace idan
ka shiga kasuwar kayi tambaya mana sae kace ba wayayye ba" shiru Junaid yyi yana
kallonsa, wata yar dattijuwa ce da baxata haura sittin ba ta fito daga kitchen da
alama ita ce ta yi gyaran gidan gaba daya, gaishe da Junaid tayi, yyi murmushi yace
"Sannu da aiki mama" mikewa El-Ameen yyi ya haura sama ba a dau lkci ba ya sakko
rike da sabulan wanka tsadaddu da sponge, sae toothbrush da toothpaste yana kallon
dattijuwar yace "Mama ga wannan, wanka xa ki taimaka kafin mu dawo, xae kai maki
ita bayin yanxu," Matar tayi shiru tana kallonsa sae dae da ganinta kasan a tsorace
take, El-Ameen yyi dariya yace "Babu abinda xata maki wllh mama, bacci ae take kuma
baxa ta tashi ba yanxu, mu je ki ga" bin bayansa tayi suka haura sama, Junaid ya bi
su da kallo kafin ya shafa kansa, El-Ameen ne ya fara shiga dakin snn ita ma ta
shiga, tana nan kwance yanda ya bar ta bayan yyi mata allura, idanuwanta duk a
rufe, kallon dattijuwar yyi yace "Kinga bacci take ko mama, kuma na gaya maki baxa
ta tashi ba sae bayan awanni takwas," kai kawae ta gyada masa, bayi ya nufa ya hada
ruwan dumi da yawa snn ya fito dakin ya dauketa ya nufi bayin da ita ya kwantar da
ita kasan neat bathroom din ya fito yana kallon tsohuwar da ya sa ma Mama yace
"Gata can na kai maki bayin, don Allah ki wanke mata wannan gashin da kyau mama,
nasan baxa kiyi wahalan fito da ita ba idan kin gama don bata da nauyi, xan fito
maki da bargo kawae ki lulluba mata har mu dawo da kaya" tace "Toh yaro" juyawa yyi
ya fita ta nufi cikin bayin. Siyayya ba kadan ba Junaid yyi ma Mahaukaciyar, tun
daga kan normal English wears wato dogayen riguna, xuwa mayyukan shafawa,
turarruka, da inner wears da jallabiyoyi, har man gyaran gashi da combs duk sae da
ya siya da takalma sae huluna da 'yan kunnaye, shi dae El-Ameen bin sa kawae yake
yana dariya, ganin har xa ayi magrib yasa El-Ameen yace "Kai koh kayan lefe kake
hadawa fa sae haka Junaid, for God's own sake kayan nan sun isa haka it's time for
magrib" Junaid ya kallesa yace "Ohk" Karfe bakwae da rabi suka isa gida, shi ma don
sun tsaya hanya sun shiga masallaci sun yi sllh snn sun tsaya eatry siyan abinci,
xaune suka samu dattijuwar a falo kan dankwalinta alamar sllh ta idar, tayi masu
sannu da xuwa, Junaid ya ajiye kayayyakin hannunsa, El-Ameen ya bude wani leda ya
fiddo doguwar riga da man shafawa da na kai sae inner wears da turare ya mika ma
matar yace "Gashi mama ki taimaka ki sa mata" ta mike tace "Toh" sannan ta karbi
kayan ta haura sama, durkusawa tayi gabanta ta yaye bargon da ta rufe ta da shi ta
bude tsadadden man da aka bata ta shiga shafa mata jikinta, cikin mintuna da basu
fi goma ba ta gama shiryata, ta debi hair cream me yawa ta shafa mata a dogon
gashinta sannan ta shiga taje gashin a hnkli saboda tsantsin sa, tana yin haka
hawaye na xuba idonta kmr daxu da take mata wanka, rayuwa kenan duk yanayin da ka
tsinci kan ka ka gode Allah, Coz he knows best, shi kadae yasan dalilin barin
wannan Baiwar Allah haka, ba wae kuma don baya sonta ya bar ta a hakan ba, har ta
gama tufke mata dogon gashinta da ya kusa bayanta hawayenta bae tsaya ba, gyara
mata kwanciya tayi ta rufa mata bargon ta fito tana kallonsu El-Ameen tace "Na
gama" El-Ameen ya mike yace "Kin sa mata komae dae koh mama" tace "Na sa mata" yana
'yar dariya yace "Kin tabbata mama" murmushi tayi tace "Na sa mata komai yaro"
kallon Junaid yyi sannan ya nufi stairs, Junaid ya mike ya bi bayansa, El-Ameen na
shiga dakin ya karasa gabanta ya durkusa ya yaye bargon dake jikinta a hankali,
rike breath dinsa yayi yana kallonta ko kiftawa bae yi har Junaid ya shigo ya same
sa a hka, shima ya durkusa a hankali nan gabanta yana kallonta.
*Haske Writers Association*
[16/10, 19:05] Hassan Atk: *CAPTAIN AHMAD JUNAID
_By Khaleesat Haiydar_
2....
Junaid na isa gidan su El-Ameen yyi parking daga waje ya shiga, Sumayya kanwar El-
Ameen ya samu xaune falo da kawayenta biyu, ya karasa cikin falon cikin tafiyarsa
ta k'asaita, yi tayi kmr bata gansa ba ta ci gaba da ba kawayenta labarin da take,
gaida shi kawayen nata suka yi suna kallonsa, don Capt Junaid ko namiji bae masa
kallo daya, ya amsa gaisuwar su ba tare da ya dube su ba yana kallon Sumayyar yace
"Ke yayanki na gida?" Ba tare da ta kallesa ba tana yatsine fuska tace "Nima bn
sani ba" wayarsa ya ciro aljihunsa ya shiga kiransa, Kawayen nata biyu duk suka
xuba masa ido, El-Ameen na d'agawa Junaid yace "are yhu at home?" El-Ameen yace
"Yea are you coming?" Wani kallo ya watsa ma Sumayya ya katse wayar ya nufi dakin
El-Ameen, Husnah ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Kai Sumayya waye shi, ya hadu
wllh, don Allah ni dae ki hada ni da shi, yyi min ni dae plss" Sumayya tayi dariyar
rainin hnkli tace "Uhm Kinga gayen nn irin mace masa da nake a da, na so shi kmr
raina amma he looked into my face nd told me baya sona, I cried my life dat day,
gashi i downgraded my sef telling him I love him" bude baki duk suka yi suna
kallonta, Fiddausi tace "Tabdi! Toh meye hadin ku da shi? D'an uwanku ne?" Tsaki
Sumayya ta ja ta dauki lemon gabanta ta shiga sa. Xaune ya samu El-Ameen kan laptop
da siririn farin glass a idonsa yana danne danne, El-Ameen ya kallesa yace "Uhnn!
Our great Capt Ahmad Junaid Murnai, kaga yanda ka kara kyau ka koma kamar wani
Egyptian kuwa" Junaid ya tabe baki ya xauna gefen makeken gadon dakin yace "You
will neva change" El-Ameen yyi murmushi ya tura laptop din gabansa ya juya yana
fuskantarsa yace "I missed you a lot frnd, am glad you are back" Junaid ya shafa
kansa yace "Sai kace gaske," El-Ameen ya kura ma farin shirt din jikinsa ido yace
"Wait! Ciwo ka ji Captain" Junaid ya kalli shirt dinsa da sauri ya ga jini daga
gefen shirt din, El-Ameen ya mike yace "What's dat? The shirt looks dirty ma"
girgixa kai Junaid yayi ya shiga unbuttoning din shirt din yace "Wata mahaukaciya
ce wllh" El-Ameen ya kwalalo ido yace "Mahaukaciya kuma" Junaid yace "Yea!" Nan ya
ba El-Ameen lbrin abinda ya faru a hanyarsa ta xuwa, El-Ameen yace "Eyya! Poor her,
but kai me ya kai ka rike mahaukaciya ma banda abun ka" Junaid bae ce komae ba ya
mike ya nufi bathroom, wanka yyi ya fito sanye da Bathrobe din El-Ameen ya goge
jikinsa ya bude wardrobe ya fiddo wasu kayan abokin nasa ya sa. Bayan Magrib yace
ma El-Ameen xae koma gida, El-Ameen yace "Haba frnd baxa ka raka ni gun Iman ba
plss, wllh ban san me xan ce ba idan na je, gashi Mami fushi take da ni, escort me
plss, dama jira nake sai ka dawo sai mu je" Junaid yyi d'an murmushi yace "Ohk buh
bari in kira mumy kar taji shiru har ynxu" Bayan isha suka bar gidan bayan Capt
Junaid yyi ma Ummin El-Ameen sallama, A motar Junaid suka tafi El-Ameen na tukin,
El-Ameen ya lura da yanda Junaid ya kafa ma tagar motar ta inda yake xaune ido yana
kallon waje, El-Ameen xae yi magana ya ji Junaid yace "Dr d'an tsaya nn don Allah
in ga ko an kwance mata igiyar, it's gud ace anyi hkn" El-Ameen ya kafa masa ido
sae kuma ya tabe baki ya daga shoulder ya gangara gefen titi yyi parking, Junaid ya
bude motar ya fita, tana nn xaune kan bolan, rike da wani bakin Leda a hannunta,
rungume hannayensa yyi yana kallonta, El-Ameen ya dafa sa yace "let move on Capt,
they've freed her" juyawa Capt Junaid yyi suka koma motar suka bar wajen, suna isa
gidan El-Ameen ya kira Iman da nmbr da Ummi ta basa, kanwar ta ce ta fito tayi masu
iso har falo ta cika su da drink, mahaifiyarta ta fito suka gaisa ta bar palon, ba
a dau lkci ba Iman ta fito sanye da wata doguwar riga me adon stone blue da gold,
tayi rolling kanta da plane blue mayafin kayan, kyakkyawa ce ba kadan ba, ta karaso
falon kamshin turarenta ya cika ko ina ta xauna, kallon Junaid El-Ameen yyi, Junaid
ma ya kallesa, suka shiga kallan kallo, ganin El-ameen yaki cewa komai Junaid ya
d'an yi gyaran murya yana kallonta yace "Ina yini Hajiya" amsawa tayi ba tare da ta
kallesu ba, Junaid ya d'an taba El-ameen alamar yyi magana mans, a hnkli El-Ameen
ya matso kusa da shi murya can kasa yace "Me xan ce mata plss" ae Junaid bae san
lkcn da ya fashe da dariya ba, El-Ameen ya tsaya kallonsa sai shi ma ya saka
dariyar, nan suka dinga dariya kamar tababbu suka yi me isan su suka yi shiru,
Junaid ya shafa kai yana kallonta yana murmushi yace "Ehm dama Ummi ce tace in rako
El-Ameen wajen ki.... Shine muka xo" El-Ameen yace "Eh Ummi ce tace in xo gurin ki
shine ya rako ni" kala bata ce masu ba, Junaid ya mike yace "Toh shknn mu xa mu
koma sai mun sake dawowa" El-Ameen ma ya mike yace "Eh xa mu koma, sae wani lkcn,
mun gode kwarai" mikewa tayi tace "Allah ya kiyaye" daga haka ta haura sama ta bar
su tsaye parlon, dariya suka dinga yi cikin motar barin Junaid, El-ameen ya ja
motar suka bar anguwar daga karshe, sae da El-ameen ya kai kansa gida sannan ya
fita suka yi sallama Junaid ya koma driver seat ya ja motar ya bar layin, yana isa
inda mahaukaciyar take yyi parkin yana kalle kallen inda xae ganta daga cikin
motar, sae bae bae ganta ba ya ja motar ya nufi gida. Yana jiran masu gadi su bude
masa gate kiran mum dinsa ya shigo wayarsa, jan motar yyi ya shiga compound din ya
nufi parkin lot yyi parking snn ya fito, ganin motar Abba yasa shi kallon agogon
wrist dinsa ya ga har goma ya kusa, bangaren mumy ya nufa, tsaye ya sameta palo
tana rike da wayarta ta rungume hannu, yyi murmushi yace "Ga ni na dawo Mum," ta
hade rai tace "Daga ina kake hka Ahmad?" Ya shafa kansa yace "na gaya maki Gidansu
El-Ameen na tafi mum, na raka sa xance ne" yana murmushi ya k'are maganar, mumy
tace "Zance! Lallai ba ayi abun arxiki ba kenan" dariya yyi lkci daya ya hade rai
yace "Allah mum mun yi magana me ma'ana, infact ni ne ma nayi don shi shiru yyi wai
kunya" Mumy tayi dariya tace "Au, kace ka kora masa budurwar knn in har kai kayi
magana, tab!" Dariya shi ma yyi ya mata side hug yace "Kai Mumyna ni din ne ban iya
magana ba" murmushi tayi tace "Kaje gun Abba yana neman ka" ya saketa yace "Ohk
Mum" kofar da xae sada sa da part din dad dinsa ya nufa, xaune ya samesa babban
falonsa yana kallon news lkci daya yana shan fruit salad din dake kan d'an table
gabansa, Hajiya Fatee na xaune gefensa, sae step sisters dinsa su uku gaba daya
suna palon, xaunawa yyi kasan lallausan rug din yana kallon Abbansa yace "Barka da
dawowa Abba" Abba yace "Yauwa daga ina kake naga baka duty ae" yace "Naje gidansu
El-Ameen ne Abba," kallon Hajiya Fatee yyi yace "Ina yini Hajiya?" Tayi murmushin
da bai kai ciki ba tace "Lfya lau, ya aikin" yace "Alhmdllh" Muhibbah ce ta shigo
falon da sallama rike da bowl din kankana da akayi slicin, ta duka ta ajiye gefen
Abba, xama tayi tana kallon junaid da ya maida hankalinsa kan Tv tace "Ina yini
yaya" amsawa yyi ba tare da ya kalleta ba, Hajiya Fatee sae kallonsa ta gefen ido
take, mikewa Junaid yyi yace "Sae da safe Abba" Abba yace "Yauwa ka ba Muhibbah
dubu ashirin xa tayi amfani da su a makaranta gobe wae," yace "toh Abba" daga nn
yyi ma Hajiya Fatee sae da safe, kanninsa ma suka yi masa sai da safe ya fice daga
falon rai a bace, mikewa Muhibba tayi ta bi bayansa, bae tarda mumy a palo ba, hka
yasa ya nufi bedroom dinta ya sameta har ta kwanta, xauna wa yyi daga gefenta yace
"Kin kwanta mum?" Tace "Har ka fito?" Yace "Eh mum" peck din goshinta yyi yace
"Gudnyt mum, xan tafi in kwanta" tace "Toh Allah tashe mu lfya, make sure kayi
alwala kayi addu'a kafin ka kwanta" yace "In'sha Allah mum" mikewa yyi ya kashe
mata wutan dakin ya rufe mata kofa ya fita, dakin da kanninsa suke ya bude, Aisha
ce ke waya ita ko Fatima tayi bacci, ya rufe kofar ya fito parlor, xaune ya tarda
Muhibbah tana jiransa, yyi mamakin rashin ganin Hijab a jikinta don da hijab ta
shigo palon Abba, kauda kai yyi ya fita daga parlon ta mike ta bi bayansa, yana isa
part dinsa ya bude ya shiga ya juya yana kallonta ganin tana kokrin shigowa yace
"Ki jira ni a nn malama" rufe kofar yyi, ta hade rae ssae tana kallon kofar, tsaki
tayi ta bude ta shiga, ganin bae palon ta nufi bedroom dinsa, ya dauko kudin zae
fito suka kusa cin karo, wani tsawa ya daka mata yace "Are yhu insane xa ki biyo ni
daki" kallonsa ta tsaya yi, yyi tsaki ya bangajeta ya fice a fusace, bin bayansa
tayi ba tare da ta ji haushi ko kadan ba, a palo ya jefar da kudin ya nufi kofa ya
bude yace "Leave yanxu!" D'an tsaki tayi ta duka ta dauki kudin ta fice, ya kulle
kofarsa ya sa key don wani mugun haushinta yake ji a gidan. K'asa bacci yyi daren
ranan, duk juyin da xae yi sae mahaukaciyar nn ta fado masa, hankalinsa ne ya tashi
don shi dae bae mata komae ba illah taimakon yaron da yyi, mikewa yayi daga karshe
ya nufi bayi ya dauro alwala ya fito ya shimfida pray mat ya shiga nafila, sae
kusan Karfe uku da rabi bacci ya daukesa. Da asuba ruwan sama ya sakko kamar da
bakin kwarya, kmr jiya yau ma bae fita mosque sllhn asubahin ba sbda ruwa, ruwan
dumi ssae ya hada yyi wanka don ko kadan bae son sanyi shi, ya shirya cikin uniform
dinsa ya dauki babban kadigan na uniform me kalan Navy blue ya sa snn ya fito falo
rike da rain coat dinsa, sae da ya tabbatar wayoyinsa na aljihun wandon uniform din
jikinsa snn ya fito balcony ya saka rain coat din da hulansa ya nufi bangaren Mumy,
a balcony ya cire rain coat din ya bude kofa ya shiga, tana kitchen da mai aikinta
sai fatima suna hada breakfast, ya shiga kitchen din ya gaisheta ta amsa da cewa
"Ka tashi lfya, ya ruwa?" Yace "Alhmdllh mumy" Fatima ta kallesa tace "Gud morning
ya Ahmad" yace "Morning" ya fita kitchen din, tea kawae ya sha da kwae shi ma sae
da mum ta takura sa wae ya makara xuwa aiki, har balcony ta rakosa tace "Baxa ka
shiga gaida 'yan gidan da Abba ba kenan" ya dan tsuke fuska yace "Am late mum,"
tace "Toh Allah ya tsare" rain coat dinsa ya sa yace "Ameen" snn ya nufi parkin
space, kusan a tare suka jero da Suhaima dake rike da lema tayi shirin makaranta,
ko kallonta bae yi ba ya
bude motarsa ya shige ta nufi tata motar tana kallonsa, jan motar yyi ya danna
horn aka bude masa gate ya fice. A hnkli ya ke driving din har ya iso inda
mahaukaciyar jiya take, samun kansa yyi da parking gefen titi yana kalle kallen
inda xae ganta idonsa ya sauka kanta, xaune take cikin ruwan ta hade kai da gwiwa,
duk ta jike da alama tun da ruwan ya sauko bata bar wajen ba, Junaid ya jinginar da
kansa jikin kujera yana ci gaba da kallonta, duk jikinsa yyi sanyi, da kyar ya iya
jan motarsa ya bar wajen ganin yana bata lkci, shi mutum ne me tausayi da raunin
xuciya kamar mace, har ya isa office bae da sukuni, colleagues dinsa duk suka lura
da shi suka kuma tambayesa ko Lfya yace bai jin ddi ne, Karfe biyar saura ya bar
gun aikin, driving kawae yake cikin rashin kuxari, bae bi hanyar da xae ga
mahaukaciyar ba ya canxa hanya, ko parking din arxiki bae yi ba ya bude motar ya
nufi part din mumyn sa, kwanciya yyi kan dogon kujera ya rufe idonsa gam, Mumy ce
ta fito daga kitchen ganinsa a kwance tace "Lfya Ahmad" jin bae ce komae ba yasa ta
karasa kusa da shi tace "Ahmad!" Bude idonsa da ya kada yyi ya mike xaune ya dafe
kansa, taba jikinsa ta shiga yi da damuwa tace "baka da Lfya ne?" Lumshe ido yyi ya
kwanta jikinta ta rungume sa tace "Talk to me mana son, me ya faru?" A hnkli yace
"Kai ne ke man ciwo Mumy" tace "Ci abinci mu tafi asibiti" da sauri yace "No mum,
xan sha magani" hade rai tayi tace "Wani maganin xa ka sha, sau nawa kke sha bae
maka aiki ba, so kake ka dauko min magana gun Abba koh" shiru yyi ta mike ta nufi
dinning ta dawo rike da kulan abinci da plate da spoon, fried rice din ta dibar
masa ta ajiye snn ta koma kitchen ta hado masa tea, bae son mum din tasa ta daga
hankalinta shi yasa ya daure ya dinga cin abincin don kwata kwata bae da appetite.
Mikewa yyi da ya gama Mumy tace "Ka tafi ka canxa kawae mu tafi clinic" yace "Toh"
snn ya fita xuwa bangarensa, wanka yyi ya canxa uniform din jikinsa xuwa kananun
kaya, ya d'an kwanta yana tunanin karyar da xae ma Mumy ta hakura da xuwan su
asibiti, dubara ce ta fado masa ya mike da sauri ya dauki wayarsa ta fita, xaune ya
sameta palo ta shirya tana jiransa, murmushi yyi yace "Mumy ynxu El-Ameen ya kira
ni, I told him m nt ok, shine yace I shud cum over ya duba ni" hararansa Mumy tayi
tace "Yhu should come over dai kuyi hira, my frnd mu wuce clinic" marairaice mata
yyi ya mata side hug yace "Haba mum, ga ni da amini likita kice mu je clinic, kinga
baxae ji ddi idan ban je ba plss"
*Haske Writers Association*
[16/10, 19:05] Hassan Atk: *Captain Ahmad Junaid*
_By Khaleesat Haiydar_
5.....
Falo El-Ameen ya sakko ya samu Junaid tsaye bayan kujera yana kallon mahaukaciyar,
El-Ameen yace "Toh ae sae ka dauketa ka kaita spare room ka ajiye ta ka kunce rope
din" karasawa falon Junaid yyi, yyi yanda El-Ameen yace masa, yana kunce igiyar a
daki ya fice da sauri ya ja kofar, kulle kofar palon El-Ameen yyi bayan sun fito,
har lkcn ruwan da ake bae tsaya ba, El-Ameen ya d'an yi tsaki ya sa kai ya shiga
ruwan ya nufi gate, bin sa Junaid yyi a baya ba tare da ya damu da hakan ba, sae a
snn ya dinga jin sanyi na shigar sa ba kadan ba, El-Ameen ya kulle gate din daga
waje bayan sun fito suka shiga mota, suna hawa kan titi El-Ameen yyi murmushi ganin
yanda Junaid yake rawan dari, yyi kwafa yace "Ai baka fara rawan sanyi ba tukun
malam, sai randa 'Yan gidan ku suka samu labarin mahaukaciyar nan I assure you oven
ma yyi kadan yasa ka daina rawan sanyi" Sharesa junaid yyi, El-ameen yyi dariya
yana kallonsa yace "Mu je can gidanmu, idan ya so da asuba sae ka koma gida, don
kana komawa gida ynxu Mumy ta kama ka har duka na tabbata xata iya maka, ni kam na
girma bbu abinda Ummina xata ce min" yana maganar ne yana kyalkyala dariya, shi dae
Junaid bae tanka sa ba don sanyin da yake ji ma kadae ya ishe shi, kuma yasan gskya
ya fadi yana komawa gida ynxu Mumy xata daga hnkli baxa kuma ta barsa ba sae ya
fadi daga inda yake cikin ruwan nn. El-Ameen na gama parkin a parking lot din
gidansu ya juya yana kallon Junaid yace "Let move in frnd" bude motar Junaid yyi ya
fito ya nufi cikin gidan da sauri don ba karamin sanyi yake ji ba, bbu kowa palon
ya nufi dakin El-Ameen, bathroom ya shiga ya hada ruwa me dumi sosae yyi wanka, ko
da ya fito El-Ameen na xaune yana shan tea, ya fiddo rigan sanyi babba a closet
bayan ya goge jikinsa ya sa, wayarsa ya dauka yana dubawa ko bae jike ba snn ya
ajiye gaban mirror ya dawo yyi kwanciyarsa ya ja bargo ba tare da ya kalli El-Ameen
ba, El-Ameen yace "Baxa ka sha tea'n ba?" Share sa Junaid yyi, El-Ameen yyi
murmushi sanin baxae kulasa ba yace "Toh fa gwara ka tashi ka sha magani kar ka
k'asa tashi gobe, ana kuma tambayata ba'asi xan tona wllh" Dariya El-Ameen ya dinga
yi jin Junaid bae tanka sa ba still, ya mike ya dauko paracetamol ya dawo da Goran
ruwa ya xauna gefensa yace "Look frnd, tashi ka sha drug kafin ka kwanta kar ka
tashi da mura gobe, yhu knw I may be annoying a times" yana murmushi ya kare
maganar, mikewa Junaid yyi ya karbi maganin da ruwa ya kora ya koma ya kwanta don
shi kansa yasan without dat baxae tashi lfya ba gobe. Washegari da asuba kafin ayi
sllh Junaid yace xae tafi bayan ya daura alwala yyi Raka'atainil fajr, bae yarda ya
dau motar El-Ameen ba don yasan hkn na iya tona masa asiri, ko mum din El-Ameen
bata san yana gidan ba, El-Ameen ya rakasa bakin titi ya tsayar masa da a dai daita
don ca yyi bae iya ba. Ana kokarin tada sllh ya iso anguwarsu na Government reserve
area, masallaci kawae ya shiga, ana idarwa ya dde xaune yana Azkar har ya ga fitan
Abbansa snn ya mike ya bi bayansa, part dinsa ya nufa ya gaishesa ya amsa masa snn
yace "Kana mura ne Ahmad?" Junaid ya girgixa kai yace "Ya ma yi sauki Abba, ina
shan magani" Abba yace "Gud! Babu damuwa ko?" Junaid ya shafa kai yace "Ehh Abba!"
Abba yace "To Allah maka albarka" Junaid yace "Ameen Abba," Abba yace "Gobe xan
fita xuwa Germany, tafiyar ya xo min da gaggawa ne, as usual am handing the family
over to yhu son" Junaid yace "Toh Allah kai mu Abba, journey mercy dad, in'sha
Allah" Abba ya shafa kansa yace "Ameen dear son" mikewa Junaid yyi yace "It's
almost daybreak Abba, bari in je in shirya xuwa aiki" Abba yace "Its ohk, stay
blessed" fita yyi ya nufi bangarensa, cikin mintunan da basu fice ashirin ba ya
shirya cikin uniform dinsa na dark navy blue trouser da light blue shirt, kadigan
yasa navy blue bayan ya feshe jikinsa da turare ya rike hularsa a hannu, waow yyi
kyau har ya gaji lips din nan nasa kamar ya shafa jan baki, ya bude manyan
idanuwansa sanin bae shafa komae ba ya daga kafada ya fita xuwa side din mum dinsa,
fatima dake shara a balcony ta gaida shi, ya amsa ya shiga parlon, Mumy na jera
masa breakfast dinsa a dinning ya sameta, ya nufi dinning din ya mata side hug ya
kwanta jikinta a hankali yace "Sabahul khair Ummu na" Mumy tayi murmushi tace "How
are yhu, baka rufe windows bne jiya naji kmr mura na neman kama ka" shagwabe mata
yyi yace "Na rufe mana Mumy," ta hararesa tace "Toh ka bar Ac a kunne ko" ya
girgixa kai yace "Not at all mum, kinsan ynxu lkcn ruwa ne kuma tun da na dawo ciki
nake fita aiki shi yasa kmr muran ke son kama ni" tace "Toh I will get yhu an
umbrella don ban ga amfanin Raincoat din da kake sa wa ba" yace "A'a ni nafi son
raincoat dina, umbrella sae kace mace mumy" tace "Toh idan na baka kar kayi amfani
da shi" langwabar da kai yyi ya xauna yana kallon ynda take hada masa tea, plate
din potatoe'n da ta xuba masa ya jawo ya shiga ci yace "Aisha ta koma ne Mumy?"
Mumy tace "Tun jiya" daga haka ta bar dining din ta shiga daki, a hnkli junaid ya
ajiye fork din hannunsa tunawa da mahaukaciyar da suka dauko jiya da yyi, har Mumy
ta fito bai kuma cin komai ba, ta kalli agogo ta kallesa tace "Kana kallon agogo
dai koh" yyi yake ya ci gaba da cin potatoe'n, tutturawa kawae ya dinga yi don
neman appetite yyi ya rasa, ya mike yana goge bakinsa da tissue yace "Allah amfana
momy, thnks a lot" tace "Welcm, but make sure ka shiga ka gaida mutan gidan yau"
d'an hade rae yyi amma da yake baya mata musu cewa yyi "Toh mumy" ta rakasa har
balcony, yyi side din stepmums din nasa, bangaren Hajiya Fatee ya fara shiga tana
xaune da Muhibba a palo da Rabi'a dake gugan Hijab, ya xauna kan kujera hannunsa
rike da hularsa me kaman face cap me dauke da symbol din captainship a jiki, yyi
k'asa da kai yace "Ina kwana Hajiya" a dakile tace "Lfya lau d'an gwal" hade rae
yyi yana jujjuya hular hannunsa, Rabi'a tace "ina kwana ya Ahmad?" Yace "Lfya lau
ya sch?" Tace "Alhmdllh" Muhibbah dake ta kallonsa ko kiftawa bata yi ganin ko
kallon inda take bae yi ba cikin wani siririn murya tace "Ina kwana ya A.jay" ba
tare da ya kalleta ba yace "Lfya lau" sae kuma ya mike ya nufi kofa yace "Na tafi
aiki Hajiya," bata tanka sa ba har ya fita, Muhibba ta kalli Hajiya tace "Hajiya
kinga ko amsa gaisuwata bai son yi ma" Hajiya Fatee tayi wani murmushi mai wuyar
fassara ba tare da tace komae ba, Rabi'a tayi 'yar dariya tana guganta tace "Aiki"
harara uwar ta wurga mata, ko sanin tana yi bata yi ba, part din Hajiya Bilki
Junaid ya nufa, bbu kowa palon ya nemi gu ya xauna yana kallon agogon wrist dinsa,
daga kitchen khadija ta fito ta d'an wara ido tace "Lah ya Ahmad ashe kana nan, Gud
morning" yayi murmushi yace "Morning lil sis, ya sch?" Ta karaso kusa da shi ta
shagwabe murya tace "Lfya lau, plss yaya ka d'an min transfer din 5k frnd dita na
birthday gobe xan siya mata perfume" yace "Kije ki samu Abba mana ae bai tafi ba"
ta d'an bata rai tace "Shekaranjiya fa ya canxa min phone" yace "Ohk ltr" Hajiya
bilki ce ta shigo palon, kallo daya tayi masa ta dauke kai, tana kallon Khadija
tace "Ke don uwar ki me ya hada ki da Suhaima kike mata fitsara?" Khadija ta hade
rai ta juya ta koma kitchen, junaid yyi k'asa da kai yace "ina kwana Umma" ba tare
da ta kallesa ba tace "lfya lau" Suhaimah ce ta shigo palon da alamar muryarsa
taji, tace "Ina kwana ya Ahmad" mikewa yyi yace "Lfya lau" daga hka yace "Na tafi
aiki Umma" bae jira cewarta ba ya fice, ta bi sa da harara, Suhaimah ta samu waje
ta xauna ta xabga tagumi tana kallon Umman. Junaid na xuwa gun aiki ya dauki
permission Karfe sha daya ya fito, driving yyi xuwa clinic din dad din El-Ameen,
Yana rike da hularsa ya haura sama xuwa office din El-Ameen, Nurses din suka bi sa
da kallo ko kiftawa bbu, yana attending to patient ya same sa, ba tare da ya
kallesu ba ya shige bedroom, xama yyi yana addu'ar Allah yasa baxae dau lkci da
patient din nasa ba, ko minti biyar ba'ayi ba sae ga El-Ameen ya shigo yana
kallonsa yace "Ya? Duty din naka ya kuma shifting xuwa yamma ne?" Junaid yace "No
of course, yarinyar da muka bari kulle a gida fa?" El-Ameen ya hade rai ya galla
masa harara yace "Kaga xaka fara daga ma mutum hankali da sassafen nn koh, Toh me
xa ayi mata ynxun? Ba sae xuwa yamma in mun gama aiki ba" Junaid ya girgixa kai
yace "Yanxu fisabilillah da xaka fito baka yi breakfast ba Dr? Ita ba mutum bace da
xa a bar ta ba ruwa ba abinci har xuwa yamma?" El-Ameen yyi masa wani kallo yace
"Toh wai wa ya hana ka xuwa kai mata abincin ynxu, iyaka ka xo kace in baka
makullin gida in baka, pls let me be Captain, am getting sick of you," Junaid ya
lumshe ido ya rike kansa don walakancin El-Ameen ya fara isan sa, mikewa yyi ba
tare da ya kallesa ba yace "Ohk! Bani keyn" El-Ameen ya d'an shafa kai yace "Alryt
am sorry, haka ne kuma fa ya kamata a kai mata abinci, tun da ita ma mutum ce kamar
Junaid" ficewa Junaid yyi ya bar masa dakin, El-Ameen yyi dariya ya bi bayansa,
makullin gidan dake table dinsa ya dauka ganin Junaid ya bar office din shi ma ya
fita, kusan a tare suka iso gun motar junaid, El-Ameen ya bude gaba ya shiga,
junaid ma ya shiga ba tare da ya kallesa ba yace "Kaga hand me dat key ka fice min
a mota" El-Ameen ya gyara xama yace "Toh fitar da ni mu ga" Junaid ya fi minti
biyar bae tada motar ba, El-Ameen kuma yaki fita, sanin ba fitan zae yi ba kawae ya
tada motar ya ja suka bar asibitin, wani eatry ya fara biyawa ya siyo abinci da
ruwa sae hollandia drink, El-Ameen ya rike kai ya dinga dariya da ya ga hollandian,
shi dae Junaid bae tanka sa ba, sae da suka dau hanyar gidan yace "kaga malam da ka
rufa ma kanka asiri ka bude hollandian nn mu shanye kawae, dama am thirsty, banda
haka a ina ta san wani hollandia in ba neman magana irin naka ba" driving kawae
Junaid yake bae tanka sa ba, El-Ameen yyi dariyarsa me isarsa yana mamakin Junaid,
a waje suka yi Parkin motar, El-Ameen ya bude gidan suka shiga, kallon Junaid yyi
da ya tsaya yace "A'a Toh ka shiga gaba mana goga" murmushi Junaid
yyi bae ce komae ba yana shafa kai don shi har ga Allah tsoro yake, El-Ameen ya
dinga kyalkyala dariya har suka isa kofa Junaid na biye da shi a baya, El-Ameen na
bude kofar ya koma baya da saurinsa ya fiffito da ido, Junaid na ganin hka kan kace
me sae gashi a tsakiyar compound cikin 'yan sakwanni, El-Ameen ya rike kai yace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya nanata hakan ya kusa sau goma, Junaid na
daga tsakiyar compound sae tambayar me ya faru yake, cikin tsawa yace "Junaiddd xo
ka ga abinda ka jawo min"
*Haske Writers Association*
[16/10, 19:05] Hassan Atk: *Captain Ahmad Junaid*
_By Khaleesat Haiydar_
4.....
Washegari Karfe hudu da wani abu Junaid ya baro office, tun safe dama ya kira
agents din Abbansa yace su sama masa apartment ko me dakuna biyu ne but kar su yrda
Abba ya sani, driving yake yana kokarin kiran daya daga agents din yaji ko an gama
komae, mutumin na d'agawa ya gaishesa snn yace "Yallabai an samu, amma xaka iya
xuwa ka ga ko ya maka" Junaid yace "Alryt! Ohk, na gode" katse wayar yyi ya nufi
asibiti gun El-Ameen sanin yana clinic, xaune ya samesa yana attending to wata
patient, Junaid ya nufi bedroom dinsa da ke office din ya kwanta, bayan minti
talatin El-Ameen ya shigo ya cire farin lab coat din jikinsa yace "Uhnn! Ko uniform
baka cire ba tsabar xumudin taimakon mahaukaciya kenan" Junaid ya mike xaune ya
hade rai yace "Yea daga office nake, na kuma samu apartment" El-Ameen yyi murmushi
yace "Ohh dats gud for yhu" Junaid yace "But yau da nyt xa mu dauko ta ko" wani
kallo El-Ameen yyi masa yace "Xa dae ka dauko ta malam, kai da wa xa ku dauko ta"
shiru Junaid yyi yana kallonsa, ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh naji xan dauko ta"
mikewa yyi yace "i will be on my way, but ina son ka min favour daya, plss motar ka
xaka bar min a layin ku sae ka bar min key din karkashin motar ko in btwn flowers
dake kusa da motar, I will then cum over to take it sbda Mumy baxata bar ni in fito
so late ba" El-Ameen ya bude ido yace "What? A motar tawa xa a saka mahaukaciya,
kuma tsabar walakanci sae in bar motar at risk da makulli a waje, you are dreaming"
Junaid ya girgixa kai yace "Ka dae san ba sonka Allah ya fi yi a kanta ba da ya
barka da hankalinka ita ya gusar mata da nata koh?" El-Ameen yace "Toh preacher,
amma ni baxan bada motata ba period!" Junaid bae ce komae ba ya fice daga dakin,
tunanin wa enda xa su taimaka masa ya dauko mahaukaciyar ya dinga yi, sae da ya
biya ya duba apartment din da aka samar masa ya ga ba laifi snn ya nufi gida. Da
daddare yana xaune palon Mumy yana cin tuwon shinkafa da lafiyayyen miyar vegetable
da tayi masa, sae dae duk bae da appetite turawa kawae yake, ya kalli Fatima dake
kwance parlon yace "Xo dauke abincin nan" ta mike tace "Baxa ka ci bane yaya?" Bai
ce komai ba hakan yasa ta kwashe tray din tayi kitchen da shi, takwas da rabi ya
mike ya shiga bedroom din Mumy don mata sae da safe, tace "Yau ba hiran kenan" yayi
yake yace "Bacci nake ji momma" tace "To Allah ya tashe mu lfya, make sure yhu
ablute nd pray b4 going to bed, kuma ka rufe windows ka ga hadari" yace "In'sha
Allah mum" fita yyi daga bangaren nata rike da wayarsa. Bedroom dinsa ya shiga ya
canxa kaya cikin hanxari snn ya fito, gate ya nufa yana yi yana waige waige har ya
fice, da kafa ya karasa titi iska na kadawa sosai ga walkiya alamar ko da yaushe
ruwa xae iya sakkowa, yana tsaye yana jiran abun hawa abinda bae taba yi ba duk
tsawon rayuwarsa a iya saninsa, bae ma san ta ynda xae tsaida adai daitan ba sae
kalle kalle yake gashi kuma sae wucewa suke, yayyafi aka fara yi sosae, ya lumshe
ido ya bude yana kallon motocin dake wucewa, wata farar lafiyayyen mota ce tayi
parking gefensa, wata kyakkyawan yarinya ta fito sanye da hijab tana kallonsa tace
"Bawan Allah shigo in rage maka anya if its ok by yhu, ka ga its raining kuma ruwan
xae iya karfi at anytime, na wuce daxu xanje pharmacy na ganka kuma na dawo na kuma
ganin ka" kallon motar yyi snn ya kalleta, yarinyar baxata wuce 18 ba, ta d'an bude
ido tace "Noo! Am just being helpful" daga hka ta juya xata koma motar ta, sanin
bashi da wani alternative yasa ya bude gaban motar ya shiga, dai dai lkcn da ita ma
ta shiga maxaunin driver, ta kallesa ta ja motar suka bar wajen, tana tuki tace
"Ina ka nufa?" Ba tare da ya kalleta ba ya gaya mata, tace "Ohk" wayarsa ce ta fara
ring ya ciro a aljihunsa ya ga El-Ameen ne, da kmr baxae daga ba sae kuma ya d'aga
ya kara a kunne yyi shiru, El-Ameen yace "Ya ka samu fitowan?" Cikin kaushin murya
yace "Ba Matsalar ka bne wnn" El-Ameen yyi dariya yace "Haba name same, naga baka
xo daukan motar bane har ynxu" Junaid yace "Ehh xan je in karba na Faisal" El-Ameen
yace "Kai na fa fito maka da motar Wllh come over, yhu knw I can be annoying a
times" Junaid yace "Noo dnt wrry ina hanyar gidan ynxu" El-Ameen yace "Look stop
this plss junaid, na fito maka da mota Wllh, just teasing yhu daxu" Junaid yyi
shiru sanin baxae iya fushi da abokin nasa ba, lumshe ido yyi ya bude yace "Ohk"
snn ya katse wayar. Juyawa yyi ya kalli yarinyar ya gaya mata anguwarsu El-Ameen
yace nn xani, tace "Ohk" dai dai bakin gate yasa ta tsaya ya juya yana kallonta
yace "Thanks a lot" tace "Yhu are welcm!" bude motar yyi xae fita duk da ruwan da
ake tsugawa, sae kuma ya juya ya kalleta, wayarsa ya ciro ya mika mata yace "Sa min
digit din ki so I can thank yhu some other time" tace "Do yhu need to? Its ohk ba
sae ka kuma gode min ba, it payz to be kind" murmushi yayi ya mayar da wayar
aljihunsa yace "Ohk Allah saka da khairan" juyawa tayi bayan motar ta dauko
raincoat ta mika masa tace "Hope yhu will cope with this" karba yyi ya kuma mata
godiya ya fita daga motar, ta ja motar ta bar wajen. Bin motar yyi da kallo dai dai
lkcn da aka dallara masa wutan fitilar mota, juyawa yyi yaga motar El-Ameen ce,
karasawa yyi da sauri yana rike da raincoat ya bude front seat ya shiga, El-Ameen
yace "Wani mota ce wannan?" Junaid yace "A good Samaritan" El-Ameen ya tabe baki
yace "Ynxu ka mana adalci kenan Junaid, ko wani mahaluki na cikin bargo cikin ruwan
nn kasa muna tsaye a titi?" Junaid yace "Look! Ni ae bn ce ka fito ba xaka iya
komawa abun ka" El-Ameen ya hararesa yace "Ehh In koma ka ji haushi na koh" Junaid
yace "No Baxan ji ba" tsaki El-Ameen yyi ya tada motar suka bar layin, sae da suka
hau kan titi snn yace "Ynxu ina xa mu bi?" Junaid ya gaya masa suka kama hanyar
inda mahaukaciyar take, banda tsaki bbu abinda El-Ameen yake, shi dae Junaid bae ce
komae ba har suka iso, Junaid ya fara kalle kallen inda xae hangota, bae ganta
wajen ba hankalinsa ne ya tashi, shi dae El-Ameen kallonsa kawae yake, ya juya ya
kalli El-Ameen yace "Frnd bn ganta wajen ba kuma" El-Ameen yace "Toh me xan yi ni
kuma, haka kawae ka shiga hakki na ka hanani kwanciya cikin sanyin nn" bude motar
Junaid yyi ya fita cikin ruwan, ya fara nemanta, lkci daya ya jike jagab, can ya
hangota rabe jikin bango kusa da wani kiosk duk ta jike jagab ta takure waje daya,
wani tausayinta ne ya rufe sa jikinsa yyi sanyi sosai, ya kusa minti biyar tsaye
cikin ruwan yana kallonta snn ya juya ya koma gun motar ya bude yana kallon El-
Ameen cikin sanyin murya yace "I've seen her" El-Ameen yace "Gud for you, sai ka
bude baya ka dauki igiya ka daureta ka dauko ta ai" shiru Junaid yyi yana tsaye
cikin ruwan yana kallonsa, can yace "Ka xo ka taimaka min toh" El-Ameen yace "What!
cikin ruwan nn xan taimaka maka, Noo" Junaid bai kuma cewa komai ba ya bude bayan
motar ya dauki igiyan da ke nan ya rufe ya koma inda mahaukaciyar take, k'asa
karasawa yyi don gabansa sae faduwa yake, da kyar yyi shahada ya isa gabanta,
kallonsa take tana kara takurewa waje daya, sae a snn ya lura da rawan sanyin da
take, a hnkli yace "Kiyi hkuri baiwar Allah, am only trying to help" kamar ta ji me
yace ta yunkura ta mike xata bar wajen da gudu, fixgota yyi ya rike ta gam, ta
shiga kokuwa da shi tana ihu, El-Ameen na daga mota yana lekansu, ban da dariya bbu
abinda yake har da kyakyatawa, ba karamin wahala ta ba Junaid ba don da kyar ya kai
ta k'asa ya daure hannunta shima din ba wae dauri sosae ba don taki tsayawa ga wani
karfi dake gareta, bude mota El-Ameen yyi ya fito cikin ruwan ya karasa inda suke
da sauri, karban sauran igiyar yyi junaid na rike da ita ya daure ta gam, ihu ta
dinga masu tana shure shure, El-Ameen ya mike yace "Ae sae ka dauketa Mr Do good"
bbu musu Junaid ya dauketa, ko kadan bata da nauyi ya nufi motar da ita El-Ameen na
biye da shi a baya yana 'yar dariya, ya bude baya ya saka ta ciki ya rufe, yatsine
yatsine El-Ameen ya shiga yi ya nufi driver seat, muryoyi suka ji daga bayansu duk
suka juya, wasu matasa suka gani tsaye da gora da adda a hannayensu, da ka gansu ka
ga masu gadi, cikin tsawa suka ce "Maxa ku fito da ita ynxun nn" kallon Junaid El-
Ameen yyi, El-ameen ma haka, ae kan kace me sae ga Junaid cikin mota ya rufe, El-
Ameen na ganin hka shi ma ya shige motar ya tada da sauri, samarin suka taho da
gudu, cikin hanxari El-Ameen ya ja motar suka bar wajen, bin motar samarin suka yi
da guda suna buga ma motar gora da karfi, El-Ameen ya dinga cewa "ya Salam! ya
salam! ya salam!" har suka bar anguwar abinda yake maimaitawa kenan, juyawa yyi
yana kallon Junaid dake ta kallon mahaukaciyar dake fixge fixge tana son freeing
kanta, a fusace ? yace "Kai ka ji irin ynda suka tarwatsa min bayan mota kuwa
Junaid" Junaid ya sauke ajiyar xuciya yace "Xan gyara maka motar ka idan Allah ya
yarda" kwafa El-Ameen yyi yace "Better, kuma ka dinga lura da ita kar ta cafko ni
mu shiga uku, ynxu ina muka nufa?" Junaid ya gaya masa ya kama hanyar anguwar,
cikin minti goma suka iso, har lkcn ruwa ake, parking El-Ameen yyi yana kallon
Junaid ya bude motar ya fito, fitowa yyi shi ma suka shiga gidan a tare, gidan
babba ne ba laifi, junaid har yasa anyi furnishing gidan kar ya tsaya empty, El-
Ameen yyi tsaki yace "Lallai! A wannan gidan xa a ajiye mahaukaciya? ba sae ta
balla windunan nn mara karfi ba ta yi ficewarta, bugu daya idan tayi ma kofar nn
ficewa xae yi wllh" Junaid ya shafa kansa a hankali yace "Toh shi suka samo min ya
xa ayi" El-Ameen yace "Oho, amma idan ta gudu wallahil Azim ba da ni xaka je nemota
ba" da damuwa Junaid yace "Toh hw are we going to do it ynxu ga shi mun dauko ta"
El-Ameen yace "Oho it's left to yhu" xama Junaid yyi ya rike kansa, can yace "Ohk,
let bring her in I will stay nd guard her till 2morrow kafin nn sae a samo mata
wani gidan." El-Ameen ya shiga hararansa can ya ja tsaki yana kallon agogo yaga har
goma ya wuce, yace "Kaga mu je can gida na, don ni na gaji sanyi nake ji kar in yi
ma kai na illa haka kawai" daga hka
ya fice daga palon, junaid ya bi bayansa ya fita ya kulle gidan. Har suka isa
gidan El-Ameen bbu wanda yace komai sae Junaid dake juyawa lkci lkci yana kallon
mahaukaciyar, El-Ameen ya dauko makulin gidan dake motarsa ya fita ya bude gate don
bbu kowa gidan, dawowa yyi cikin motar ya shiga compound din da motar, yana gama
parking ya juya yana kallon Junaid yace 'Ohhw ni! yanxu mahaukaciya ce mace ta
farko da xata fara shigar min gida bayan mahaifiyata maimakon matata" Junaid bae
tanka sa ba, El-Ameen yyi tsaki yana girgixa kai ya fito daga motar ya nufi cikin
gidan, Junaid ya fito ya bi bayansa, a balcony ya tsaya ya canxa change over din
gidan don akwae wuta, ya juya yana kallon Junaid yace "Toh ni xan fito maka da
mahaukaciyar?" Junaid ya girgixa kai ya juya ya koma gun motar, bae sha wahalan
daukota ba don sosae El-Ameen ya daureta kuma duk tayi laushi, ihu take tana shure
shure har suka shigo falon ya direta k'asa yana kallonta, El-Ameen ya rike haba
yana kallonta yace "Ikon Allah, muna xaman xaman mu Junaid ya ja mana!" Juyawa
Junaid yyi yana kallonsa, El-Ameen yyi tsaki ya nufi stairs, Junaid ya lumshe ido
ya bude ya bi bayansa, daki ya samesa ya bude drawern kayansa da alamar kaya xae
canxa, Junaid yace "It's late ynxu, muyi freeing dinta sae mu wuce koh" El-Ameen
yace "wait tukun! Wae kai xaga dinga tsayawa da ita a gidan?" Junaid ya d'an yi
shiru yana kallonsa, sae kuma ya sauke ajiyar xuciya yace "No, xan sa a samo min
yar dattijuwa dat will be staying, nd I will hire a gate man" El-Ameen ya kyabe
baki ya cire jikakken shirt din jikinsa da wando ya fiddo wasu kayansa ya sa, sae a
snn ya juya ya kalli Junaid da ke xaune gefen gadon dakin yana kallonsa yace "Kai
baxa ka canxa kaya ba?" Mikewa Junaid yyi ba tare da ya kallesa ba ya fice daga
dakin, dariya El-Ameen yyi sanin haushin sa kawae Junaid ke ji.
*Sai dai da aka rushe katangar Chinan dai, ko wani katanga xan kuma cewa Allah yayi
min da su*
*Haske Writers Association*
[16/10, 19:05] Hassan Atk: *Captain Ahmad Junaid*
_By Khaleesat Haiydar_
3.....
Wani kallo Mumy tayi masa tace "Kaga ka kiyaye ni Ahmad, baxa ka gun El-Ameen din
ba asibiti xa mu" shiru yyi yana kallonta sanin baxae taba convincing dinta ba, a
hankali yace "Toh kiyi hkuri mumyna mu tafi asibitin" jakarta ta dauka tace "Sake
ni mu tafi" saketa yyi dai dai lkcn da wayarsa ya fara ring, fiddowa yyi a aljihu
yana kallon me kiran nasa ya ga El-Ameen ne, ya juya ya kalli Mumy ya ga kallon
wayar take, d'agawa yyi ya kai kunne daga daya bangaren El-Ameen yace "ya ne
captain, kana gida yau?" Junaid ya d'an saci kallon Mumy ya ga kallonsa take, yace
"Noo! Don't worry frnd Mumy tace mu tafi clinic kawae ba sai na xo ba" El-Ameen
yace "What are yhu talking about guy?" Junaid yace "No ba komae wllh, kawae dae
tace mu tafi asibiti ne" tsaki El-Ameen yyi yace "HeyJunaid are you ohk, wat are
yhu sayin?" Junaid yace "Ohk Tnx for ur care frnd!" D'aga hka ya katse wayar ya
kashe gaba daya ya mayar aljihunsa yana sinne kai, Mumy tace "Don me xaka ce Mumy
tace, maimakon kace Abban ka ne yace kaje clinic" Junaid yyi shiru yana kallonta,
komawa tayi ta xauna ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh shknn, ka tafi can ya duba
ka, amma yana prescribing maka magunguna ka dawo Ahmad, I repeat my self ka dawo"
farin ciki ya lullubesa sae dae yyi kkrin boye hakan yace "Toh Mumy I promise" har
bakin motarsa ta rakasa tace "Drive carefully" yace "Sure mum" tana tsaye har ya
bar gidan snn ta juya xata koma bangarenta, xaune ta ga Hajiya Fatee da Hajiya
Bilkee a balconyn Hajiya fateen suna kallonsu, Mumy ta karasa tayi masu sannu da
xama, Hajiya Bilki kadae ta amsa da yauwa a dakile, juyawa Mumy tayi xata bar wajen
Hajiya Fatee tace "Ynxu an ma hana d'an gwal din xuwa gaida mu tsabar mulki" juyawa
Mumy tayi tana kallonsu tace "Ayya Bashi da lfya ne, ynxun ma gun likita xa shi"
bbu wanda ya tanka ta cikinsu, ta nufi bangarenta ba tare da ta sa ma kanta
damuwarsu ba. Junaid na isa ya tarda El-Ameen na clinic, bae so hkn ba amma bbu
ynda ya iya hka ya nufi Babban asibitin Dad din El-Ameen din, don shima kwararren
likita ne da yyi fice a Nigeria, da yake Nurses din sun san tsakanin Junaid da El-
Ameen, bbu wanda ya dakatar da shi xuwa office din El-Ameen din, murda kofar yyi ya
shiga babban office din, El-Ameen dake xaune yana dube duben files sanye da farin
glass a idonsa ya dago yana kallon Junaid, ajiye pen din hannunsa yyi ya rike ha6a
yace "Kan ka daya kuwa captain?" Dariya junaid yyi ya xauna kan table din office
din yace "Kai da ban yi hka ba da Mumy bata bari na xo ba yanxu ai" El-Ameen ya
girgixa kai yace "Mummy's boy, na ga randa xaka girma ka samu freedom din kanka"
murmushi yyi yana shafa kansa yace "Uhm am 30 ynxu kace ban girma ba, ae kila har
in mutu baxan samu wannan freedom din gun momma na ba" El-Ameen yyi dariya yace
"Idan kayi aure xa ka samu" murmushi Junaid yyi yace "Aure kuma" kallonsa El-Ameen
yyi ya cire glass din idonsa yace "Amma ba ka jin ddi koh, you look weary?" Junaid
ya lumshe ido ya bude da damuwa yace "Kinda frnd! Am just disturb, bani da
kwanciyar hankali kwana biyun nn, M just nt my self..." Rike kai yyi ya kasa ci
gaba, El-Ameen ya dafa sa yace "What's wrong frnd, tell me ur problem, 'Yan gidan
ku ko?" Junaid ya d'aga kai yana kallonsa cike da damuwa yace "No! Wnn mahaukaciyar
ban san ko laifi nayi da na kwace yaron nan a hannunta ba, duk na kwanta ita nake
tunawa nake gani, k'asa bacci nake yanxu duk bani da sukuni" El-Ameen ya ja tsaki
ya mayar da glass din idonsa ya jawo files din gabansa yana ci gaba da dubawa yace
"Thought it to be something better ma, wai mahaukaciya" wani tsakin ya kuma ja,
Junaid ya runtse ido ya watsar da files din yace "Haba Dr in ce maka bana iya bacci
kace min yhu thought it was somethin better," El-Ameen ya rike chin dinsa yana masa
wani irin kallo da mamaki yace "Wae halan kana da dangantaka da mad woman din nn ne
junaid" a fusace Junaid yace "Wa ya sani" wani dogon tsaki El-Ameen ya kuma ja yace
"Kaga ka rabu da ni, I have meaningful things doing ynxu, aikin gaba na ma ya ishe
ni stop bothering me plss da wata mahaukaciya can." Kallonsa junaid ya tsaya yi na
kusan minti biyu kafin ya sauka daga kan table din da yake ya dauki wayarsa da
makullin mota ya juya ya nufi kofa, bin sa da kallo El-Ameen yyi kafin ya birkita
lallausan gashin kansa a xuciyarsa yace "What's wrong with Junaid da xae damu kansa
ya damu wani da wata gagarumar mahaukaciya can" mikewa yyi da sauri tun kan ya fita
ya kulle kofar office din yace "Look Captain, to ynxu me kake son ayi da rashin
baccin naka, ko kuma dai kawai mu je ka ba mahaukaciyar hakuri?" Junaid ya kallesa
yace "bude min kofa" El-Ameen na 'yar dariya yace "Of course No baxan bude maka ba
sae ka gaya min dalilin ka na xuwa gu na, which help do yhu want me to render yhu,
mu je ka nemi gafararta mad woman din ne" tuni idon Junaid ya sauya kala, still
behaving gently yace "Bude min kofa nace" El-Ameen yace "Noo!" Wani kara yyi ya
cakumo sa yana huci yace "Bude min kofa Ahmad!" Murmushi El-Ameen yyi yace "Naki!
ka xama Zaki a nn in ga" turasa da karfi Junaid yyi ya koma kan dogon kujera ya
xauna ya rike kai, El-Ameen yyi dariya ya koma kan office chair dinsa ya xauna, sae
bayan kusan minti goma Junaid ya dago kansa, ya kalli El-Ameen dake ta aikinsa, El-
Ameen yace "Har iskokan sun sake ka kenan" Junaid bae ce komae ba ya kauda kai,
mikewa El-Ameen yyi ya dawo gefensa ya xauna yace "Now tell me, ya kake son ayi?"
Junaid ya sauke ajiyar xuciya cikin sanyi ya fara magana, "Frnd! May be tana son in
taimake ta ne, shi yasa take bi na, she want me to help her" El-Ameen ya kwalalo
manyan idanuwansa yace "Kayi me?" Shiru Junaid yyi yana kallonsa, El-Ameen ya
girgixa kai yace "Yhu must be crazy Junaid, meye hadin ka da wata mahaukaciya can
har kake tunanin taimakon ta, kai ka daura mata haukan, ko kasan me ya haukatar da
ita? Wait! which help ma xaka iya rendering dinta tukun, taking her to psychiatry
nd staying with her there ko yaya?" Junaid ya tabe baki yace "Ae dan Mumy da Abba
baxa su yrda bne da nayi hkn wllh" El-Ameen yyi dariya sosai yace "Ehh lallai
Junaid ka ja ma kanka" Junaid yyi kasa da murya yace "Listen to me plss Dr, ban da
kai akwae wanda xan kai ma damuwar da na k'asa gaya ma mahaifiyata duk kusanci na
da ita, why kake min hka frnd?" El-Ameen ya sauke ajiyar xuciya yace "Noo ba hka ba
Junaid, ynxu tell me ya kake son ayi, hw did yhu want me to help in here?" Cikin
kwantar da murya junaid yace "yhu are a Neurologist as well as a qualified MD, I
knw yhu can cure her by the grace of Allah idan ka sa kanka, yhu neva can tell
where one's reward Lie's" wani matsiyacin kallo El-Ameen ke yi masa kafin ya mike
yace "Gaskiya ka janyo ma kanka fitina ka ja mana muma da muke tare da kai Ahmad,
dama ban da abun ka me ya kai ka kama mahaukaciya kai da kake tuki a mota, Ohh My
God! ga irinta nn ka tabo aljana, don Wllh yhu are not on ur right senses" Mikewa
Junaid yyi shi ma yace "Stop this El-Ameen, meye illar taimakon Baiwar Allah da xa
mu yi? Haba idan wani yace min xaka yi hka I won't believe wllh," El-Ameen yyi
shiru yana kallonsa baki bude, cike da mamakin aminin nasa, Junaid ya juya ya nufi
kofa rai bace, girgixa kai El-ameen yayi yace "listen Captain" ko sauraransa Junaid
bae yi ba ya fice daga office din, ya birkita kansa ya bi bayansa da sauri, a tare
suka isa inda motar Junaid yake, El-Ameen yace "Haba frnd listen to me, ynxu mu
koma ka min bayani sosai yanda zan gane abinda kake nufi don wllh am confuse"
hararansa Junaid ya shiga yi yace "Ka dae san ba kai kadai bane abokina likita ba
koh?" El-Ameen ya d'an yi murmushi yace "I know" hannunsa ya rike suka koma
asibitin dae dae lkcn da wayar Junaid ya shiga ringing, fiddo wayar yyi yaga Mumy
ce ke kiransa, El-Ameen yace "Mummy's boy" d'agawa Junaid yyi daga daya bangaren
Mumy tace "Ka kyauta Ahmad" Junaid ya marairaice yace "Ohh Ummata, drip karami yake
kara min ne fa, nd am feeling much beta ynxu har na ci abinci kuma" Murmushi Junaid
yyi bayan ya gama sauraranta yace "in sha Allah mum" daga hka ya katse wayar suka
nufi office din El-Ameen.
El-Ameen ya tallabi chin dinsa da hannu biyu yana kallon Junaid yace "ina jin ka,
Allah sa ka dawo senses dinka yanxu, ya kake son ayi kace?" Junaid ya lumshe ido ya
bude yace "Wae da cure dinta nake son kayi ko nawa ka bukata xan biya ka" El-Ameen
yyi murmushi yace "Ohh i see, A can kan bola xan dinga tafiya ina samun ta kenan"
Junaid ya ce "Noo of course, dauko ta xa mu yi" El-Ameen ya bude ido yace "Mu kai
ta ina? Gidan ku?" Hararansa Junaid yyi yace "Plss frnd be serious, a gidan ka xa
mu ajiye ta, ni idan nace xan ajiyeta a nawa gidan dole sae su Mumy sun sani, barin
ma ni da nake da 'Yan sa ido, kai kam bbu me sa maka ido" El-Ameen ya buga table
din gabansa yace "Wnn ne kuma baka isa ba Malam, I can't keep a mad woman in my
house, the house that's meant for my wife!" junaid yyi shiru yana kallonsa, a hnkli
yace "Ohk let me rent an apartment" Tsaki El-Ameen yyi yana Mamakin Matsalar
Junaid, anya kuwa kansa daya, Junaid yyi murmushi yace "I knw u are thinking if am
alryt at all, tausayi ne ba wani abu ba frnd, naga yarinyar is too young ace hakan
ya sameta duk da ba a ja da ikon Allah, baka san inda rayuwa xae yi da kai ba
wataran frnd, it really pays to be kind, and you neva can tell where one's reward
lies! ni xuciyata daya nake son taimakonta saboda Allah, I will pay yhu wat ever
amount yhu require for the bill, ni dae fatana ta samu lfya ta nemi 'yan uwanta"
wani dariya El-Ameen yyi yana tafe hannu yace "Toh governor Ahmad Junaid, don this
is the government's job not urz" mikewa Junaid yyi yace "What ever, ynxu dae let me
start lookin for an apartment" El-Ameen ya daga kafadarsa yace "Left to yhu, amma
ina guje maka reaction din yan gidanku idan suka ji shirmen da kake shirin
aikatawa" Junaid yyi tsaki yace "Ni dae nemo plaster ka sa min a hannu am leaving,
gobe I might come back idan na sami apartment" El-Ameen ya mike ya dauko plaster ya
mika masa yana kallonsa cike da mamakinsa, a tare suka fito, El-Ameen yace "Yi
Dropping dina a gida kawae, na mance key a office" a hanya El-Ameen ya kwashe da
dariya yace "Tabdi wa ya ga Capt Junaid da taimakon mahaukaciya, but idan taimako
kake son yi Why not kaje orphanage home kayi ne" share sa Junaid yyi, yana parking
kofar gidansu ya juya yana kallonsa fuskarsa daure yace "Sae da safe" El-Ameen yyi
dariya ya bude motar ya fita sanin har ya ji haushi ne.
*Haske Writers Association*
[16/10, 19:05] Hassan Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

8....

Bude kofar kitchen da El-Ameen yayi yasa Junaid ya mike da sauri ya koma baya, El-
Ameen ya tsaya daga bakin kofar yana mata wani irin kallo yace "Wato ni ta raina
xata kwale koh?" Junaid yayi murmushi yace "Kai fa ka tsokaneta gashi ka sa ta
xubda hawaye, haba Dr!" El-Ameen ya karaso palon yana kallonta kanta a sunkuye yace
"Xa tayi me dalili ne ma ae, ba dae ni xata kwala ma Karfe ba" mikewa tayi tana
kallon kofa, Junaid ya karasa da sauri ya sa key, kallonsa ta tsaya yi, El-Ameen ya
xaga ta baya ba tare da ya bari ta lura ba, ya cafke hannayenta ta baya, ta kwala
wani ihu, ya kai mata rankwashi yace "Shut up!" Hade rae Junaid yayi sae dae bae ce
komae ba, El-Ameen ya ja ta ya nufi stairs da ita, kokuwan kwace kanta kawai take,
ya dauketa cak ya haura sama da ita, Junaid ya lumshe ido ya bude ya karasa cikin
palon ya xauna, da kyar El-Ameen ya daure mata hannu, snn ya samu yayi mata
allurori guda uku, ta gama fixge fixgenta da ihu ta sulale wajen sae bacci, mikewa
yayi daga durkushen da yake yana kallonta, ya karasa inda take ya kunce mata daurin
da yayi ma hannunta ya dauketa ya kwantar kan gado, tsayawa yayi yana kallonta
ganin yanda dogon gashinta ya hargitse, ribbon din da ya gani kasan dakin ya dauka
ya karasa gadon ya xauna gefenta ya dago kanta a hankali ya shiga packing din dogon
gashin, da kyar ya daure mata sannan ya mike ya gyara mata kwanciya ya fita, palo
ya sauko yana kallon Junaid yace "Ina tsohuwar nan?" Junaid bae tanka sa ba, El-
Ameen ya tabe baki ya fita waje, xaune ya sameta can gurin wani flower tayi tagumi,
ta basa dariya sosae ya karasa inda take yace "Mama nan kika dawo, ae bata komae
mama kawae tsokanarta nayi shi yasa tayi hakan" Mama tace "Uhn" dariya yayi sosae
yace "Allah kuwa mama, ta ma yi bacci yanxu" Mama tace "Allah sarki" El-Ameen yace
"Amma bata cin abinci ko mama?" Tace "Toh gskya ni ban sani ba don xubarwa take"
yace "A'a bata ci gaskiya, xan taho da maganin cin abinci gobe, mu shiga ciki to
mama" ba musu ta mike ta bi bayansa suka koma palon, mikewa Junaid yayi bayan sun
shigo yana kallon El-Ameen yace "Xan tafi ni" El-Ameen yace "Eh nima tafiya xan yi"
kallon mama El-Ameen yayi ganin har lkcn dari dari take yace "Na rufe kofar dakin
mama, kuma baxa ma ta tashi yanxu ba sae can dare" tace "Toh Allah dae ya bata
lfya" yace "Ameen" a tare suka fita da Junaid, ko wannensu ya shiga motarsa ya
wuce. Junaid na isa gida bayan yayi wanka ya canxa kaya ya nufi part din mumyn sa,
xama yayi gefenta ya kwantar da kansa kan shoulder dinta yace "Gud evenin mum" tace
"Evenin dear ya aiki? Yhu are kinda late yau" yace "Yea mum, yau Abba xae dawo
koh?" Tace "He said tomorrow da muka yi waya daxu" tace "Kasan Hajja ta xo kuwa"
mikewa xaune yayi da sauri yace "haba Mumy, When?" Mumy tace "Kana tafiya aiki daxu
da safe" yayi murmushi yace "Amma bata san Abba baya nan ba koh?" Mumy tace "Ta
sani mana yanxu dae ka ci abinci ka tafi ka gaida ta tun daxu take shigowa tana
tambayar ko ka dawo har ca tayi a kai ta gun aikin naka" dariya sosae Junaid yayi
yace "Ta hakura ta dawo nan din kenan" Mumy tayi murmushi tace "Nima haka nace,
tace inaa kwana biyu kawae xata yi ta koma" Junaid yace "Lallai Hajja" mikewa yyi
ya nufi dinning, cikin 'yan mintuna ya sakko yace ya koshi, Mumy tace "A'a wannan
baka ci komae ba junaid" Da sauri ya nufi kofa yana cewa "Allah Mumy na koshi" bin
sa da kallo tayi kafin ta tabe baki, yana fita ya nufi part din grandmum dinsa, ya
tura kofa da sallama ya shiga palon, tana xaune sanye da glass din ido tana dama
fura, cire glass din tayi tana kallonsa, yayi dariya ganin irin kallon da take masa
ya dauke furan gabanta ya rungume ta yayi pecking goshinta yace "Oyoyo granny" ta
tsuke fuska tace "Ni dae daga ni Amadidi" saketa yayi ya daure fuska yana kallonta
yace "Wai baxa ki bar kirana da wannan sunan ba Hajja" tace "Toh toh Junaidu,
shikenan?" bude baki yayi yace "Xan fa sa asa min ke a guard room in jefa ki cikin
ruwa ko don baki ganni da uniform din ba" washe hakora tayi tace "To yi hakuri
soja" dariya yayi yace "Ya mutan Daura Hajja?" Tace "Wannan kuma sae ka shirya ku
je kai da ubanka" Junaid ya tabe baki yace "Toh ni dae yi ki dama furar ki debar
min nawa" hararansa tayi tace "A'a wannan na ni da jikata ne" yace "Wace haka"
Hajjo ta juya tana kallon kofar daki tace "ke fito ki gaida yayanki 'yar nan kina
jin ya shigo kin yi mukus a daki" Junaid yace "Wacece?" Kwalo mata kira Hajjo tayi
kusan sau uku sae ga ta ta fito ta karaso cikin palon ta xauna kasa jikin kujera ta
hade rai tace "Na'am" kallonta kawae Junaid yake ganin ynda take rurrufe fuska da
hijab yace "Wacece wannan kuma Hajjo" Hajjo ta washe baki tace "ehh baka santa ba
gaskiya" sae kuma ta hade rae tace "barin ma kai da ba shiga yan uwa kake ba, ga ka
kai daya namiji gun Muhammad kmr tsiya, maimakon ka dinga shiga yan uwanka ku saba,
ko da yake tana karama ka santa, 'yar uwar ka ce Humainah, 'yar wajen kawun ka,
kuma matar da na xaba maka" fashewa da kuka yarinyar tayi ta mike tana kallon Hajjo
tace "Ni bana son haka fa Hajjo" daki ta nufa da sauri tana kuka, Hajjo tace "Au!
Ji shirme" Junaid ya tabe baki yace "Ni dae ki dama fura ki sammin inyi tafiya ta"
Hajjo tace "kai ba fa xancen wasa ba, ita na xaba maka matsayin mata tunda ka ki
fito da matar aure godai godai da kai" yace "Toh bana so!" daga can cikin daki
yarinyar tace "Ni ma bana so!" Hajjo ta fashe da dariya tace "Au, naga ko in ku
kuka haife kan ku, xumunci ne dae sae na hada" tsaki Junaid yayi ya mike ya fice
daga palon tana kiransa ko waiwayowa bae yi ba, Hajjo tace "Ahaf abinda ma a gidan
xan bar ta ta kare secondary ayi auren kawae" yarinyar ta kuma rushewa da kuka tace
"Wallahi baxan tsaya ba Hajjo ni ki maida ni gida kawae" Hajjo ta tabe baki tana ci
gaba da dama furar ta tace "Kwa yi ku kare" Junaid na komawa part din Mumy ta bi sa
da kallo ganin mood dinsa, tace "Ya aka yi Ahmad?" Cikin bacin rae yace "Wae kina
jin Hajjo ta kawo wata yarinya wae xata ce a hadani da ita" dariya Mumy tayi tace
"Kai kanwarka Humainah ce fa, 'yar gidan kawu Bala" Junaid ya xaro ido yace "Au ita
ce ta girma haka mumy?" Mumy tayi dariya tace "Ita ce mana" ya d'an tabe baki yace
"Mumy wani colleague dinmu bae da lfya, xan je duba sa" Mumy tace "Ayya, toh Allah
basa lfya, my regardz" mikewa yayi yace "Ameen Mumy sae na dawo" fita yayi rike da
makullin motarsa, kallo daya yyi ma Suhaima dake xaune balcony mac book a gabanta,
ya shiga motarsa ya tada ya fice daga gidan bayan mai gadi ya bude masa gate, kafin
ya isa main road ya kira layin El-Ameen, bugu biyu El-Ameen dake xaune kasa gaban
mahaifiyarsa ya d'aga bayan ya nemi ixinin yin haka, Junaid yace "Kana clinic koh
gida?" El-Ameen yace "Ina gida" katse wayar Junaid yayi, El-Ameen ya kalli Mum
dinsa da ta wani hade rae, sannan yayi kasa da kai, tace "Yauwa, in kuma ban isa da
kai bane sae ka sanar da ni in ji" marairaice mata yayi yace "Wllh Ummi ranan mun
je, tare da Junaid ma muka je, ae yanxu xae xo sae ki tambayesa ki ji" Ummi ta
watsa masa harara tace "Ku ka je ina, ba duk jirgi daya ya kwaso ku kai da Junaid
din ba, kuma ni bance ae baka je ba, Ca tayi dariya kuka dinga yi mata kai da
Junaid din" xaro ido yayi ya bude baki yace "Dariya kuma Ummi, wllh fa mun mata
magana" ta galla masa harara tace "Da'alla rufe min baki malam, da ban san ka da
sakarci bane, sannan ka kuma tafiya da d'an uwanka sakarai kamar ka" Murmushi El-
Ameen yayi yana shafa lallausan gashin kansa, Ummi tace "Kuma Dad dinku yace baka
xuwa clinic da safe kwana biyun nan, sannan baka ma xaman clinic din during day
time, nan kuma da sassafe kke barin mana gida, ina kake xuwa Ahmad" shiru yayi na
wani lokaci kafin ya hade rae yace "Nurses din ne suka gaya masa haka koh?" Ummi
tace "Dake shi makaho ne ba" shiru El-Ameen yayi bae ce komae ba, dae dae lokacin
da Junaid ya shigo palon, ganin El-Ameen xaune kamar me neman gafara yasa yayi kasa
da kai yyi hanyar stairs sanin sanin sai Ummi ta iya hadawa da shi kai kace shi
yayi laifin, Ummi ta bi sa da harara tace "Dawo nan ina xa ka? ka wani yi kasa da
kai kmr munafuki" dariya Junaid yayi yana shafa kai, ya dawo cikin palon yace
"Laifi ya maki ko Ummi?" Ummi tace "Xauna nan!" Ba musu ya xauna gefen El-Ameen,
Ummi tace "Ranan da ku ka je gidansu iman sa ta gaba kuka yi wae kuna ta dariya
koh?" Junaid ya xaro ido yace "Dariya kuma Ummi, ae ko mun yi magana me ma'ana,
nine ma nayi maganan don shiru El-Ameen yayi" Ummi bata san lkcn da tayi murmushi
tana kallonsu ba, ta girgixa kai tace "Ahaf ai magana ta lalace tunda kai kayi!
Wato ku baxa ku yi ma kanku fada ba ko, babu me ba wani shawara cikin ku kan ya
kamata ku ajiye iyali yanxu," Junaid yayi kasa da kai yace "Ina yi masa wallahi
Ummi" harara ta xabga masa tace "Common keep quiet my frnd ai har kai" El-Ameen
yayi murmushi shi ma yayi kasa da kai, Ummi tace "Toh gaskiya it's high time ku san
me ku ke, don ku ba yara bane, and yhu guys ain't getting younger, ku yi ma kanku
fada ku fito da mata kuyi aure abun ku, as a mother nake gaya maku haka, in ma baka
son Iman din sae ka nemo wata very soon, kai ma Junaid kayi kokarin yin hakan kafin
wata uku, I want to see my boys getting married soon, in kuma kun ban wuka da nama
sae in nemo maku mata wallahi" a tare kamar sun hada baki suka ce "A'a Ummi" dariya
tayi tana kallonsu, Junaid ya shafa kai yace "In'sha Allah Ummi xa muyi ynda kuke
so" tace "Toh Allah yasa, ya bamu aron ran ganin bikin boys dinmu" dariya suka yi
gaba daya, Ummi tace "Toh ku tashi ku tafi, Allah maku albarka" mikewa suka yi suka
nufi dakin El-Ameen bayan sun amsa da Ameen, xama Junaid yayi gefen gado yana
kallon El-Ameen dake kakrin kunna desktop dinsa yace "Baxa mu je can gidan ba?" Ba
tare da El-Ameen ya kallesa ba yace "Kai ka tafi mana, kaga ni am busy" Junaid bae
ce komai ba sae kallonsa da yake, shi kam sae danne dannensa yake ba tare da ya
damu ba, Junaid ya mike yace "Ohk am off" El-Ameen yace "So early, to ka gaida
Mumy" Junaid
bae tanka sa ba ya fice, El-ameen ya bi sa da harara yace "You think kowa ma bai
da aiki kamar ka sai na mahaukaciya yanxu" Ummi dake Palo har lkcn ta kalli junaid
tace "Har ka fito?" Junaid ya dan yi murmushi yace "Dama sako na xo karba Ummi, sae
gobe" tace "Toh Allah ya kiyaye, ka gayar min da Hajiyar ka" yace "Xata ji." Sannan
ya fita.


*Haske Writers Association*馃挕
[16/10, 19:05] Hassan Atk: *Captain Ahmad Junaid*
_By Khaleesat Haiydar_
7.....
Fara ce sosai ba kadan ba don kamar ka latsa ta jini ya fito, dama ashe wahala ce
ya maida kalanta baki, ko kadan bata da jiki sai tsayi, bakin gashin kanta ya rufe
kusan rabin fuskarta sbda yanda tayi kwanciyar, d'an karamin bakinta me kalan baki
da ja Junaid ya kalla yyi murmushi yace "Uhnn! Kamar me hankali koh? Da xata tashi
ynxu duk sae mun yi bayani ryt?" murmushi El-ameen yyi ya mike yace "Yea! Exactly!"
Juyawa yyi ya fice daga dakin Junaid ya bi sa da kallo sae gashi ya dawo da wasu
alluran har uku, ya dawo gabanta ya durkusa, Junaid na ganin haka ya mike ya fita
daga dakin, ya sakko palo ya dauki ledan abinci daya ya ba Mama, tayi masa godiya
yyi murmushi kawae ya xauna, bayan kusan minti goma El-Ameen ya sakko falon ya
xauna gefen junaid yace "Kana ji na, akwae drugs din da xa'a siya har biyar, kuma
duk pack daya kusan dubu 40 ne kafin ayi diagnosing dinta...." Junaid yace "Ohk xan
maka transfer ltr" El-Ameen ya mike ya dauki ledan abincin da ya rage da ruwa ya
nufi sama, ajiye mata yyi bayan ya bude snn ya fito ya sa ma kofar key, ya dawo
palo yana kallon Junaid yace "Let leave!" Mikewa Junaid yyi, El-Ameen ya kalli
dattijuwar da ke xaune yace "Mama za mu tafi sae gobe, duk buge bugen da xata yi
kar ki bude mata kofar" tace "Toh Allah ya tashe mu lfya, yayi maku albarka," duk
suka amsa da Ameen suka fita palon. A bakin gate El-Ameen ya tsaya yana kallon
Junaid yace "ka ba mai gadi kudi ya siyo ma tsohuwar abinci da safe ya kai mata
ciki don am not coming here da safe" Junaid ya ciro dubu uku aljihunsa ya mika ma
mai gadin snn suka fita, Suna isa gun motocin su El-Ameen yace "Gobe kuma
foodstuffs xaka siya idan xaka xo" Junaid bae ce komae ba ya shige motarsa ya tada
ya bar wajen, El-Ameen ya bi sa da kallo yana murmushi, snn shima ya shiga tasa
motar. Karfe takwas da wani abu Junaid ya isa gida, bangarensa ya nufa yyi wanka
snn ya dauro alwala ya fito yyi isha yana xaune kan darduma ya ji an bude kofar
palonsa, bae motsa daga inda yake ba har aka bude kofar bedroom, ya daga kai don
ganin waye, Mumy ce ta shigo dakin, yayi murmushi ganinta yace "Yanxu fa xan shigo
d'a Mumy" ta xauna gefen gadonsa tace "Sae ynxu kake isha Junaid?" Yace "Mun hadu
da traffic ne sosae a hanya Mumy" ta tabe baki ta mike tace "Toh taso mu je ka ci
abinci" ba musu ya mike ya linke pray mat din ya ajiye ya bi bayanta, Mai aikinta
ce ta dauko abincin nasa daga dinning ta ajiye nan tsakiyar lallausan rug din falon
da ya ke xaune, Mumy ta sakko gefensa ta bude warmern dake dauke da Shinkafa fara
ta dauki plate ta dibar masa iya yanda tasan xae cinye snn ta bude miya ta xuba
masa k'adan a gefe don bae fiye son miya da yawa ba, sae cow meat da ta cika masa a
abincin, spoon ya dauka yace "Thanks sweet mum" snn ya fara cin abincin ita kuma ta
dauki wayarta da ke ring, ganin Abba ne yasa ta nufi daki. K'asa cin abincin Junaid
yyi ya kuma rasa dalilin hakan, ya lumshe ido ya jinginar da kansa jikin kujera, ya
kusa minti goma a hka sanin Mumy na fitowa sae ta sa shi ya cinye abincin yasa ya
kira mai aikinta, yarinyar ta taho daga dakinta da sauri, ya dauki abincin ya mika
mata yace "ina fatima?" Tace "Ta kwanta" yace "Ohk tafi daki ki ci na koshi" ba
musu ta koma dakinta da abincin, juice ya diba ya shiga sha a hankali, a hka Mumy
ta fito ta samesa tace "Har ka cinye?" Yace "Eh Mumy" ya ajiye cup din hannunsa
yana lullumshe ido yace "Nafara jin bacci mumy" tace "Toh Allah ya tashe mu lfya,
kayi alwala kafin ka kwanta, don't forget to pray also" ya mike yace "In'sha Allah
mum" wayarsa ya dauka ya fita ya nufi side dinsa, sae da ya dauro alwala yyi
shafa'i da wutr snn ya kwanta ya ja bargo. Washegari yana office yayi ma El-Ameen
transfer din dubu dari da hamsin, yana barin office dama kasuwa ya shiga ya siyo
food stuffs sannan ya wuce gidan El-Ameen, mai gadi ne ya shiga da kayan abincin
palo, Junaid ya xauna bayan sun gaisa da mama yace "El-Ameen din ya xo ne mama"
tace "Eh ya xo da safe, ya kuma xuwa daxu, bae dde da tafiya ba amma yace xae dawo"
Junaid yace "Ohk, bacci take ne?" Mama tace "A'a gskya, sae dae yace kar a bude
kofar makullin na jiki ma" Junaid yace "Tana cin abinci kuwa?" Girgixa kai tayi
tace "Gskya ban sani ba don kifarwa take duka, bana gane ko ta ci ko bata ci ba"
Shiru yyi bae kuma cewa komae ba, yana son ganinta amma shi gskya tsoro yake, dama
El-Ameen na nan ne, can ya kalli agogo ya ga har biyar yayi, mikewa yyi yace "toh
ni xan tafi mama, bbu matsala dae koh?" Tana murmushi tace "Babu komae wallahi" xae
yi magana aka bude kofa El-Ameen ya shigo, ya d'an kyabe baki ganinsa, shi dae
Junaid bin sa da kallo yayi har ya karaso cikin palon, ledan hannunsa na magunguna
ya ajiye yace "Ba dae har xaka tafi ba, kuma kama duba mahaukaciyar taka kuwa?"
Junaid ya dauke kai bae ce komae ba, El-Ameen yace "Ehh Lallai ma, wato ni xaka yi
ta bari da wahala koh, daxu da safe ma sae da na xo nan kafin in tafi clinic nasan
kai ko tashi kila baka yi ba lokacin" yana kai wa nan ya nufi sama, Junaid ya sauke
ajiyar xuciya ya bi bayansa, El-Ameen ya bude kofar dakin da key ya tura kofar a
hankali, tana xaune ta rakube waje daya bayan ta kuma cire labulayen dakin gaba
daya kamar yanda ta saba, doguwar rigar kanti ne jikinta ja da ya haska farin fatar
ta, duk ta birkita dogon gashinta kmr ba da safe Mama ta kuma daure mata ba tana
bacci, kayan ma da gani ta kasa cire shi ne don duk ta yamutse shi jikinta, El-
Ameen ya balla mata harara yace "Wai ke wace irin mutum ce, wllh kika sake cire min
labule sae na gaura maki mari, baki da aiki sai barna" Junaid dae na d'aga bakin
kofa yana leko dakin, El-Ameen ya kallesa yace "Da'alla matsoraci shigo baxa ta ma
komai ba" kin shigowa junaid yayi yace "Nan ma ya isa" El-Ameen ya hade rae yace
"Ohh wato ni ne ban san ciwon kai na ba da nake shigowa koh, sae in daina shigowa
nima in dinga tsayawa daga bakin kofa in ga ta ynda xa ayi maganin" a hankali
Junaid ya d'aga kafa ya shigo dakin yana kallonta sae shishshigewa jikin bango take
a tsorace, El-Ameen ya kalli Junaid dake tsaye shi ma duk a tsoracen, Junaid bae
ankara ba sae gani yyi El-Ameen ya fixgosa ya tura sa har sae da ya fada kanta, a
tare suka kwala ihu daga shi har ita, El-Ameen ya dinga kyakyata dariya har da rike
ciki, da kyar Junaid ya mike, ita ma ta yunkura ta mike, tsorata junaid yyi ya nufi
bayi da sauri, ita kuma ta wawuri d'aya daga karafunan labulen dakin tayi kan El-
Ameen dake dariya har lokcin, xaro ido yyi ya hadiye dariyarsa ganin haka, ya juya
da sauri xae fita ae da hanxarinta ta bi bayansa, me Junaid xae ban da dariya, ya
dinga kyalkyala dariya ya bi bayansu, har downstairs ta bi El-Ameen, mama na ganin
hka ita ma tayi waje da gudu, El-Ameen ya dinga cewa "Junaid wllh ka xo ka riketa,
junaiddd" Junaid ya durkusa nan stairs ya dinga dariya ganin yanda El-Ameen ya rude
yana xaga palon, ita ko sae binsa take xata buga masa karfen, Hadiye dariyar Junaid
yyi ganin El-Ameen ya shige kitchen ya sa key ya barsu su biyun a palon, ta dade
tsaye bakin kofar kitchen din, kafin ta juyo tana bin ko ina na palon da kallo,
k'asa motsi Junaid yyi daga inda yake xuciyarsa na bugawa, ta jefar da karfen
hannunta ganin kofa a bude ta nufi kofar da sauri, Junaid bae san lkcn da ya nemi
tsoron ya rasa ba ya bi bayanta cikin hanzari ya riga ta isowa kofar ya rufe gam,
juyawa tayi tana kallonsa tana maida numfashi, sae kuma ta fasa wani ihu tayi kansa
ta fixgosa, rungumeta yyi ya riketa gam, ta dinga fixge fixge ya ki saketa, Sosae
suka jigata daga ita har shi, don kin saketa yyi, ita kuma bata fasa kokuwa da shi
ba, daga karshe tayi lamo jikinsa bata sake yunkurin kwatar kanta ba, a hankali ya
saketa ta sulale nan kasan palon, hawaye yaga kwance fuskarta, jikinsa yyi sanyi ya
durkusa gabanta yana kallonta.
*Haske Writers Association*
[16/10, 19:05] Hassan Atk: � *Captain_Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

9.....

Gida Junaid ya nufa, yana gama parkin ya fito ya shiga bangaren Mumy ya gaida ta
sannan ya tafi nasa part din, kwanciya yayi Palo ya lumshe ido, ko minti goma bae
yi da kwanciya ba wayarsa ya soma ringing, daukar wayar yayi yana kallon mai kiran
nasa ya ga abokinsa ne Faisal, d'agawa yayi yace "Yane Faisal!" Faisal yace "Are
yhu at home capt?" Junaid yace "Yea ina gida" Faisal yace "Ohk gani nan shigowa"
daga haka ya katse wayar, bayan minti takwas Faisal ya shigo palon, Junaid ya mike
xaune yana kallonsa yace "Daga ina haka" Faisal ya xauna yace "Gida mana tun da kai
baka neman mutane sae El-Ameen" Junaid yayi dariya yace "Kai haba ko ranan da
daddare ban kira ka ba" Faisal dake kokarin kira a wayarsa yace "Really!" kallonsa
kawae junaid yayi yana murmushi, faisal yace "Hello Muhibba gani gidan ku part din
Captain" daga haka ya katse wayar, Junaid ya hade rae yace "idan gun ta ka xo ba
sae ka je can bangarensu ba xaka wani kira min ita nan" faisal yace "Chill guy sako
xan bata" ko rufe baki faisal bae yi ba sae ga ta ta shigo, murmushi dauke fuskarta
tace "ashe da gaske kake" hade rae sosai Junaid yayi ya jawo waya yana dannawa,
faisal ya ciro waya aljihunsa ya mika mata yace "Gashi nan na bada an gyara maki"
ta wara ido ta karbi wayar tace "Waow am so happy ya faisal, kuma nawa?" yace "No
don't bother" tace "Toh na gode kwarai, ya salima fa?" Yace "Tana gida," kallon
Junaid tayi tace "Sannu ya Ahmad" ba tare da ya kalleta ba yace "Yauwa!" Tayi
niyyan xama palon amma sanin junaid sae ya iya gwaleta yasa ta juya kawae ta fita
tana tunanin yaushe ne wannan ranan da junaid xae fara sonta kamar yanda Hajiya ke
yawan assure dinta. Faisal yace "Fatee fah?" Junaid yace "Oho!" Sae bayan Magrib
faisal ya bar gidan bayan sun shiga ya yi ma Mumy sallama ya kuma shiga part din
Hajja ya gaidata, a tare suka fita bayan Junaid ya ce ma Mumy bari ya rakasa, sai
dai rakiyar iya bakin gate yyi sa, yana ganin tafiyar Faisal ya nufi titi don yasan
in har yace ma Mumy fita xae yi sai ya amsa query, kalle kallen abun hawa ya shiga
yi ya rasa yanda xae ce su tsaya, can dae wani mai adai daita ya tsaya yana
tambayarsa ina xa shi, shiga kawae Junaid yayi yana kallon mai adai daitan yace "Mu
je" sae da suka dan yi nisa kafin ya gaya masa inda xa shi, suna isa junaid ya
sauko ya fara dube duben kudi a aljihu, dubu daya kawae ya gani aljihun nasa, mika
masa yayi a hankali yana kallon mai adai daitan yace "Kayi hakuri malam ban san ban
fito da kudi ba, dubu daya ce a hannu na nagani" dariya mai adai daitan yayi ya
karbi kudin, ko ba a gaya masa ba yasan junaid sabon shiga ne a tricycle, canjin
dari shidda ya mika masa yace "Ga canjin ka bawan Allah" dan xaro ido Junaid yayi
ya karbi kudin yace "Har canji gare ni? Toh na gode" mai adai daitan yayi murmushi
ya ja machine dinsa ya wuce, Junaid yayi mamakin ganin motar El-Ameen a parke waje,
shi da yace baxae xo ba kuma, tabe baki yayi ya shiga gidan, mama ce xaune Palo ita
kadae Junaid ya gaisheta da ladabi, ta amsa tana murmushi ta tambayesa ya aiki,
Junaid yace "Lfya mama, ya kamata a siyo maki tv ya dinga debe maki kewa koh"
dariya tayi tace "lallai kam" Junaid yace "El-Ameen ya xo ne" mama tace "Eh yana
sama" mikewa junaid yayi sae dae duk bae da kuxari ya nufi saman, a hankali ya tura
kofar dakin yana kallon ciki, xaune ya ga El-Ameen gabanta ya tankwashe kafa plate
din abinci a tsakiyarsu hannunsa rike da spoon ga wayar rechargeable dake gefensa,
ita ma xaunen take ya daure mata hannu sae shisshigewa jikin bango take hawaye
kwance fuskarta, duk gashin kanta a birkice yake, Junaid ya rungume hannayensa yana
kallon El-Ameen, El-Ameen yace "Uhnn! yau baka kwanta da wuri ba kenan mumy's boy"
junaid dae bae tanka sa ba ya maida kallonsa kanta ganin yanda take kokuwa da bango
kamar xata shige ciki, yunkura tayi xata mike El-Ameen ya daka mata tsawa ya dauki
wayar rechargeable din gefensa ta koma da sauri ta xauna, shinkafar ya diba ya kai
mata baki, ta dinga kauda kai tana boye fuska, tsawa ya kuma yi mata ya juyo da
kanta ya matse bakinta har sai da ta bude ya xuba mata abincin da sauri, murmushi
Junaid yayi ganin yanda jikinta ke rawa tana hadiye abincin ba tare da ta tauna ba,
da ganinta kasan ba karamar matsoraciya bace, Haka El-Ameen ya dinga mata har sae
da ta ci kusan rabin abincin sannan ya mike yana kallon Junaid yace "Bata cin
abinci shi yasa na mata haka," Junaid ya buda manyan idonsa yace "So yhu do really
care ashe haka?" El-Ameen yayi dariya yace "Darajar ka take ci ae" Junaid bae kuma
cewa komae ba sae kallonta yake duk da ba ganin fuskarta yake ba don dogon gashin
kanta ya rufe fuskar, wasu allurai biyu El-Ameen ya fiddo ya shiga hadawa, ae tana
hango alluran ta mike tayi kofa da gudu, fixgota El-Ameen yayi don shi Junaid hanya
ma ya bata da sauri, El-ameen ya jefa ta kan gado, yana hararan Junaid yace "kaji
d'an iskan hanya ma ya bata" Junaid yayi dariya yana shafa kai, ta fasa wani uban
ihu da ya tsorata Junaid xata mike El-ameen ya hau gadon ya rike ta yana mata wani
mugun kallo yace "Keehh", Ribbon dinta da ke kan gadon ya dauka ya shiga daure mata
gashin kanta, yana kallon fuskarta yace "Kika kuskura kika sake cire ribbon dinnan
sae na gaggaura maki mari" banda rawa babu abinda jikinta yake tana kallonsa,
murmushi yayi ya kwantar da ita a hankali ya kwance daurin hannunta sannan ya juya
yana kallon Junaid yace "Miko min alluran ko shi ma tsoron sa kake" Junaid bae ce
komae ba ya dauki alluran ya mika masa, juyar da ita El-Ameen yayi xae mata alluran
Junaid ya juya ya fita dakin, El-Ameen ya bi sa da kallo sannan ya tabe baki yayi
mata alluran, tsam ya riketa a jikinsa ganin yanda take shure shure da ihu, sun
kusa minti goma a haka har ya ji duk jikinta ya saki, ya dago fuskarta yana
kallonta ya ga bacci tayi, kwantar da ita yayi ya lulluba mata bargo, sannan ya
dauki abincin da ta rage da ruwa ya fita ya kullo dakin, xaune ya samu Junaid a
Palo, ya ajiye abincin nan tsakar palon yace "Mama a xubar da wannan ta d'an ci
kad'an," Mama ta jawo abincin tace "A'a baxa a xubar ba xan ci" El-Ameen bae kuma
cewa komae ba, Junaid ya mike yayi ma Mama sae da safe ba tare da ya kalli El-Ameen
ba ya fice daga falon, bin sa da kallo El-Ameen yayi sae kuma ya tabe baki shi ma
yayi ma mama sae da safe ya fita.

Washegari Junaid ya fito bayan ya shirya cikin khakin sa ya shiga part din mumyn
sa, tana jera masa breakfast as usual ya shigo, bata amsa gaisuwar da yake mata ba
tace "ka shiga gaida Hajja kuwa?" Girgixa Kai yayi yace "Na ma manta tana nan" Mumy
tace "Toh tafi ka gaida ta ka dawo tukun." Ba musu ya fita yayi bangaren kakar
tasa, xaune ya sameta Palo tana shan kunu ga kosai cike kula, dariya yayi yace
"Dama abinda ke kawo ki gidan nan kenan ae Hajja" kallo daya yayi ma Humainah dake
goge goge palon ya dauke kai, ita kam dama ko kallonsa bata yi ba, Hajja ta hade
rae tace "Wae baka ga Humainah bane Junaid?" Ya hade rai shi ma yace "Toh ni xan
gaisheta?" Hajja tace "Toh ba kai ka xo ka sameta ba" bude baki yayi yana kallon
Hajja, ita ko Humainah ta mike ta dauki bucket fuu xata wuce, fixgota yayi ta kusa
faduwa ya turata ta xauna nan kasa, bata fuska tayi xata yi kuka, ya hade rai yace
"ke yaushe kika girma har kika iya fitsara haka?" Kuka ta fashe da tana kallon
Hajja, Hajja ta mike tsaye ta tsuke fuska tace "Kai Amadidi ka fita idona wllh,
walakancin da cin fuska har a gabana, a haka xan baka 'yar kaje kana cutar min da
ita in shiga uku?" Dariya Junaid yayi yace "Tabdi! Allah ya tsare ni, ke in kin ga
matar da xan aura ma wllh kunyar fito min da wannan fitsararriyar xa ki yi"
Humainah ta tabe baki tana hararansa tace "Ni ma in kaga saurayina wllh kunyar
tsayawa gabana xa kayi" Hajja ta fashe da dariya kyal kyal kyal har da kwanciya,
shi ko bude baki yayi yana kallan Humainah da ta wani tabe baki, murmushi yayi ya
saketa ya mike ya fice daga palon, Hajja na dariya tace "A'a da ka tsaya mana
fitsararre" Humainah tayi dariya tace "Ya fa ji tsoro ne Hajja, shi in banda haske
da dogon hanci me garesa xai wani sa uniform da hula ya xo yana d'addaga mana
hanci" Hajja tace "Atoh! Gane min hanya 'yar nan, ko ubansa xai burge Oho!"
Humainah ta fashe da dariya har da rike ciki.

Da yamma Junaid na kwance palon Mumy bayan ya dawo aiki idonsa lumshe kamar me
bacci sae dai ba baccin yake ba, Mumy kuma na kitchen tana ta girke girke don ranan
Abba xae dawo, Bude kofar da aka yi ya sa shi bude ido, El-Ameen ya shigo palon da
sallama, kallonsa kawae Junaid ke yi bae ce komae ba, El-Ameen ya karaso palon yace
"Capt A.jay Murnai!" Da xolaya ya kare kiran nasa, Junaid ya mike xaune yace "Uhm!"
Kitchen El-Ameen ya nufa ya tsaya daga bakin kofa yace "Ina yini Mumyna" juyawa
tayi tana kallonsa tace "A'a Ahmad yaushe ka shigo?" yayi murmushi yace "Yanxun nan
Mumy, ya gida ya aiki" tace "Alhmdllh, ya Hajiyar ka?" El-Ameen ya karasa shiga
kitchen din ya mata side hug yace "Tana lfya Mumy, tace a gaishe ki" Mumy tace "Ina
ta sa rana xan je can gidan ku Allah bae yi ba" El-Ameen ya sa hannu ya dauki daya
daga kajin da take soyawa yace "Bari in d'an d'ana maki ko gishiri ya ji Mumy"
dariya tayi tace "Naga alama" ya wara ido ya fice daga kitchen din yana murmushi,
gefen Junaid ya xauna yana cin kaxar Junaid xae yi magana aka bude kofa, Hajja ce
ta shigo palon da sallama, El-Ameen ya wara ido ya boye fuskarsa bayan Junaid yace
"Kai yaushe Hajja ta xo?" Hajja ta cire glass din idonta tana leken El-Ameen tace
"Wannan ba gantalallen nan me sunan ka bane Amadi?" El-Ameen yayi dariya yace "Ehh
Nine Hajja, ashe kin xo, ae bae gaya min ba" Hajja tace "Toh ko ya gaya maka xuwa
xa ka yi, kar ka manta turare ne fa yayi mani iyaka da kai, daga nace ka siyan
turare na xama makiyiyar ka, toh Allah yayi mana tsari da irin ku" dariya sosae El-
Ameen yayi, Junaid yayi murmushi yana canxa tashan tv, Hajja ta xauna tace "Har
yanxu Muhammad din bae iso bane?" Mumy ta fito daga kitchen tace "Kila sae xuwa
magariba Hajja" mikewa Junaid yayi ya kwashi wayoyinsa yana kallon El-Ameen yace
"Mu je" El-Ameen ya mike, Hajja tace "Au don na shigo shine xa ku watse" Junaid ya
balla mata harara yace "Da'alla! Rikicin tsufa ya maki yawa wllh" El-ameen yace
"Kyalesa kawai Hajja ta so mu je kar ayi ba ke" Junaid yace "Allah kar ta xo min
don rufe kofata xan yi" daga haka ya nufi kofa, El-Ameen ya bi bayansa yana dariya,
ta tsuke fuska ta bi su da kallo tace "Wahalallu ko uwar me xasu ban da Allah bai
ban ba, kuma naga dai gidan d'ana ne yau nace duk ya kora ku wllh ta xauna!" Mumy
tayi murmushi ta koma kitchen. kwanciya El-Ameen yayi a palon Junaid yace "Kana ji
na Capt?" Junaid yace "Ina jin ka." "xa ayi diagnosing din patient din ka don in
san irin neurological disorder dinta da treatment din da ya kamata in mata, nd
dat's money!" Junaid ya dauki remote din hannunsa yayi powering din Tv yace "Aiit!
Nawa ake bukata?" El-Ameen ya mike xaune yace "ka turo dubu dari tukun mu ga"
Junaid yace "Ohk I will transfer it ltr" El-Ameen yace "Gud! Ko gida xan sa a xo
ayi diagnosing din nata, no need of taking her out" kai kawae Junaid ya gyada masa,
"Kaga daga nan sae mu san irin uban kudin da xaka kashe" da xolaya El-Ameen ya kare
maganar, Junaid yayi murmushi bae ce komae ba.


*Haske Writers Association*馃挕
[16/10, 19:05] Hassan Atk: � *Captain_Ahmad Junaid*�
_By Khaleesat Haiydar_

10....

Har Abba ya dawo bayan magrib El-Ameen na gidan, suna gama cin abinci da Junaid
suka tafi palon Abba a tare don yi masa sannu da dawowa, Hajja na xaune palon da
Hajiya da Umma, Humainah da fatima ma na xaune daga gefen Abba dake ta sauraran
xancen da mahaifiyarsa ke masa, khadija da sadiya step sister dinta ma duk suna
xaune palon, junaid da El-Ameen suka samu waje suka xauna, El-Ameen ne ya soma yi
ma Abba sannu da xuwa ya gaishesa, Abba ya amsa murmushi dauke fuskarsa yace "Kana
lfya son? Ya aikin?" El-Ameen yace "Alhmdllh Abba, ya hanya?" Abba yace "Alhmdllh
mun gode Allah, jiya mun yi waya da Alhaji Mahmoud yace xae tafi Germany gobe" El-
Ameen yace "Ehh gobe xae tafi" Abba yace "Maa sha Allah, Allah ya tsare" Junaid ya
kalli Abbansa yace "Barka da dawowa Abba" Abba yace "Yauwa Ahmad, how yhu?" Junaid
ya shafa kansa yace "Alhmdllh Abba, ya hanya?" Hajiya ta d'an tabe baki ta mike,
Umma ma ta mike ta fice daga palon. Hajja ta bi su da kallo sannan tayi tsaki ta
maida dubanta kan Abba tace "Ni dai Muhammadu matan nan naka basa min abun arxiki
wllh, tun da na xo ko ruwan su ban gani ba sai daxu da safe, Amina kadae ce 'yar
arxiki take ta dawainiya da ni" siririn tsaki can kasa Sadiya ta ja tana hararan
Hajja ta gefen ido ta mike ta fice daga palon. Murmushi kawae Abba yayi ya maida
dubansa kan Humainah dake gefensa a kasa yace "ya karatu Humainah? Ss3 xaki yanxu
koh?" Hajja ta karbe tace "Ehh ajin karshe xata, tana gamawa sae a hada aurensu da
Amadidi sai taje can ta kare karatun a gidansa" da sauri Junaid ya kalli Hajja ya
wani hade rae, ita ma Humainah kallon Hajjan ta ke kamar xata yi kuka, El-Ameen ya
fashe da dariya, Abba kam murmushi yayi ya kalli Humainah da har hawaye ya cika
idonta yace "Kyale Hajja dotana, wanda kike so xa a aura maki kin ji, kuma sae kin
fara jami'a ma xaki yi auren," tana goge hawayenta tace "Toh Abba" Junaid ya harari
Hajja da ta sake baki tana kallon Abba ya dauke kai, Abba ya kallesa murmushi dauke
fuskarsa har lkcn yace "Ae ni baxan ma 'ya yana auren dole ba Hajja, duk abinda
suke so shi mu ma xa mu so," murmushi Junaid yayi ya mike yana kallon Hajja da ta
wani hade rai, ya kalli El-Ameen yace "Tashi mu je" El-Ameen ya mike yana dariya
suka yi ma Abba sallama suka fita daga palon, Hajja tayi kwafa tace "Toh zan ga ko
kai ka haifeni kuwa,"
Bakin mota Junaid ya raka El-ameen yace "Gud nyt!" El-Ameen yace "Aitt, saura kar
ka xo can gidan gobe!" junaid yayi murmushi bae ce komai ba, sai da El-Ameen ya ja
motar ya bar wajen snn junaid ya juya ya koma gida. Part din Mumy ya shiga ya tarar
tana bathroom ya fito ya nufi nasa bangaren.

Washegari ya kama Sunday Junaid na gida baya duty, kwance yake palon sa misalin
Karfe goma da rabi na safe Khadija ta shigo palon, kasa ta xauna kusa da kujeran da
yake tace "Gud morning ya A.jay" yace "Morning baki je islamiyya bane" tace "daxu
ae anyi yayyafi shine Abba yace in bari gobe," yace "Keep quiet ba cikin ruwan
fatima da Rabi'a suka tafi ba, ina ga gishiri ce ke koh, continue deceiving ur
self" shiru ta dan yi tana turo baki sae kuma tace "Ae da yamma xan je" bai tanka
ta ba, tayi kasa da murya tace "Yaya dama plss 5k xaka ban xan siya wani takalmi ne
plss" wani uban harara ya watsa mata yace "Tashi ki bar min Palo, ke baki da aiki
sae dae a baki kudi, beside kije ki samu Abba mana, get out my frnd" marairaice
masa tayi tace "Don Allah fa yayana" xae yi magana aka bude kofa Suhaima ta shigo
palon cikin wasu shegun English wears lokaci daya wani shegen kamshi ya bade palon,
mikewa xaune yayi yana kallon Khadija yace "Naji! naji tashi ki tafi" Khadija tayi
murmushi tace "Yauwa ya A.jayy nagode" ta mike ta hade rai tana kallon Suhaima tace
"Toh ae sae mu je koh" wani kallo Suhaima tayi mata tace "Wa kike gaya ma haka"
Khadija ta ja tsaki tace "Duk inda mutum yayi sae ayi ta bin sa da'alla" bata rufe
baki ba Suhaima ta fixgota ta sauke mata mari, Khadija ta dafe kunci tana kallonta,
mikewa Junaid yayi ya karaso ya bude kofar ya fixgo Suhaima ya wulla ta waje cikin
kakkausar murya yace "Kada ki sake taba ta" Umma dake balconyn ta xaune tare da
Hajiya ta mike da sauri ganin abinda ya faru, Hajiya ta bi bayanta da sauri ita ma,
a fusace ta karaso bangaren Junaid tana huci tana kallon Junaid dake tsaye bakin
kofa har lokacin tace "Kai Ahmad uwar me tayi maka xaka jefota haka kamar pillow?"
Suhaima ta fashe da matsanancin kuka, hakan ya kuma harxuka Umma cike da masifa da
bala'i tace "Ba magana nake maka ba" kallonta kawai yake bai ce komai ba, idonta ya
kankance don fitina ta juya tana kallon Suhaima tace "me ya faru, me kika yi masa?"
Suhaima na matsar kwalla ta gaya mata, Umma ta xaro ido tana kallon Khadija dake
tsaye bayan Junaid a tsawace tace "ke har abun farin cikin ki ne bare yayi ma 'yar
uwar ki wannan cin mutuncin Khadija, to don uwar ki fito kar in karya ki palon nan,
Shegiya me halin banxa, fito nace" Hajiya tace "Ke dae sallamammiya ce wllh
khadija, munafuka wawiya kawai" Hajja ce ta leko jin surutai, ganinsu tsatstsaye
part din Junaid ta fito da sauri ta karaso tana tambayar me ya faru, ko kallonta su
Umma basu yi ba, Umma na kallon Khadija tace "baxa ki fito ba sae na maki lahani a
palon nan?" A fusace Hajja tace "Yau na ga bala'i, ta ya xa ki ce ta fito palon
d'an uwanta, ke kin isa ki shiga tsakaninsu?" Hajiya ta tabe baki ta dauke kai,
Hajja ta karasa balconyn tace "Me ya faru khadija?" Khadija tace "Wae fa Hajja
Suhaima ce ta mareni shine ya Junaid ya koreta palon, shine fa take kuka haka"
Hajja ta xaro ido tace "Ta mare ki? Toh Muhammadu ya fito ayi ta ta kare yau, duk
ko wannensu ya kwashe agololinsa a gidan nan don ba gidan ubansu bane nan din,
shima maganinsa knn da auren xawarawa, haka kawae xa a sa mashi 'ya ya a gaba, kuma
bari kiji abinda baki sani ba Bilki, wllh Khadija ta fi kusanci da Ahmadu a kan da
warcan bakar yar taki a gidan nan, don uba daya ba wasa bane" ae sum sum Hajiya
Fatee ta bar wajen, Mumy ce ta fito jin hayaniya ta karaso da sauri tana tambayar
abinda ya faru, Hajja ta shiga mata bayani cikin fada, shiru Mumy tayi tana kallon
Junaid, Umma ta fixgi hannun Suhaima suka bar wajen tana huci, Hajja tace "haka
kawae, xata kawo mana agola a gida ta adaddabe mu, ita ma wancan mai kama da
kutaren ma haka ta kawo nata agolar, duk an cika masa gida da agololi," juyawa tayi
tana kallon Khadija tace "Toh wllh ki rike d'an uwanki, don shine dolen ki kuma kun
fi kusanci da shi akan wancan bakar don uba daya ba wasa bane" tana kai wa nan ta
nufi bangarenta kamar xata tashi sama, Humainah dake tsaye balcony tana kallon film
din sae dariya take, Fitowa Khadija tayi daga palon ta bi bayan Hajja don tasan ko
hauka take baxa ta nufi sashinsu yanxu ba, Mumy ta sauke ajiyar xuciya ta karasa
cikin palon Junaid ya bi bayanta, a hankali ta soma magana tace "Ahmad ina raba ka
da shiga tsabgan mutanen nan baka ji koh, ba sonka suke ba kai kanka ka sani, ina
ruwanka da shiga tsakanin Khadija da 'yar uwarta?" Junaid yace "Marinta fa tayi
Mumy" Mumy tace "koma dai meye ni dae ka kiyaye su bbu ruwanka da su, tsakanin ka
da Khadija daban tsakanin Khadija da Suhaima daban" yace "Toh shknn Mumy kiyi
hakuri," juyawa tayi ta fita daga palon, ya koma ya xauna yana kallon agogo don duk
ya kagu ya fita xuwa gidan El-Ameen. Har bacci ya fara daukansa yaji ana buga
kujerar da yake kwance kai, ya bude ido da sauri ya ga Humainah tsaye kansa, mikewa
xaune yayi, ta rufe bakinta da hannu tana 'yar dariya tace "Dama haka kake bacci
baki bude" shafa kansa yayi yyi saurin fixgota ya xaunar da ita kasa, kara tayi
tana kiran Hajja, ya hade rai yace "me ya shigo da ke Palo na?" A rikice tace "wllh
Abba ne yace in kira ka" yace "A bude kika ga baki na?" Da sauri tace "A'a wasa
nake" daga hannu yayi kamar xae kai mata duka ta boye fuskarta tana kiran Hajja, ya
saketa yace "Ashe fitsarar ta karya kike yi" shiru tayi bata ce komae ba, ya mike
ya nufi kofa, ta bi sa da harara, yana fita ta sa dariya, mikewa tayi tana kare ma
palon kallo ko ina tsaf kamar na mace ga kamshi ya kama palon sosai, bedroom dinsa
ta nufa, nan ma very neat ta rike kugu tana bin ko ina da kallo ganin how over tidy
it is ga kamshi me ddi dake tashi, ta nufi gaban madubi tana kallon turarruka masu
tsadan gaske dake jere gaban mirrorn, daukansu ta shiga yi da daddaya tana fesawa
don jin irin kamshin su, kala biyu ta dauka ta fito daga dakin da sauri ta fita
daga palon ta ja masa kofa, part din Hajja tayi da saurinta. Junaid na xaune kasan
lallausan rug din palon Abbansa yana kallon Abban nasa da mamaki jin abinda yake
cewa, juyawa yayi ya kalli Umma da ke xaune ta sha kunu palon ga Suhaima ma xaune
kasa, Junaid ya lumshe ido don ko kadan bae son a laka masa sharrin abinda bae yi
ba a hada sa da mahaifinsa, cikin fada Abba yace "Kana jina kayi shiru Ahmad?" Bude
ido yayi a hankali yace "Kayi hakuri Abba hakan baxae kuma faruwa ba in'sha Allah"
Abba yace "kasani daga yau matsayin Suhaima daya da na khadija wajen ka, kar in
kuma jin wannan shirmen, ashe baka da hankali ban sani ba" a hankali Junaid yace
"Kayi hakuri Abba" Abba yace "Xancen banxa kake yi, kuma ka bata hakuri yanxun nan"
juyawa yayi yana kallon Suhaima da idonta ke kansa ko kifta wa bata yi yace "Kiyi
hakuri" tayi kasa da kai tace "Ya wuce" Abba yace "Tashi ka ban waje" mikewa Junaid
yayi xuciyarsa na kuna ya fice daga palon. Part dinsa ya nufa yana shiga Palo yasan
an shiga bedroom dinsa, ya karasa bedroom din ya kalli gaban mirror ya ga an dauka
turare, kayan jikinsa ya canxa xuwa blue jeans da farar T shirt ya feshe jikinsa da
turare ya dauki car key da wayoyinsa ya fice daga dakin. Kulle part dinsa yayi da
makulli sannan yayi bangaren Mumy, bedroom dinta ya karasa ganin bata Palo ya
sameta tana gyara kayanta a closet yace "Mumy xan dan fita sae na dawo" Mumy ta
kallesa sannan ta ajiye kayan hannunta ganin mood dinsa tace "Me ya faru son?"
Shiru yayi da farko sae kuma yace "Wae shine xa su samu Abba su ce na doki Suhaima,
meyasa idan basu yi karya ba basu ji ddi ba 'yan gidan nan?" Mumy tace "Ae tun ba
yau ba na sha fada maka ka daina shiga hurumin da ba taka ba, to yanxu gashi sun
hada ka da Abban ka ae" ya fuzar da iska yace "Na tafi Mumy sae na dawo" tace "Ina
xaka?" Yace "Gidansu faisal xan je" Mumy tace "Toh shknn kar ka dde, and drive
carefully" yace "Ohk Mum" har bakin mota ta rakosa, su Umma dake xaune da Hajiya
suka bi su da kallo suna tabe baki, ko kallonsu Mumy bata yi ba har Junaid ya ja
motarsa ya bar gidan, Mumy ta koma part dinta, Hajiya ta sauke wani ajiyar xuciya
tace "Wannan Yaro ya xame mana babban obstacle a gidan nan wllh, komae sae yanda
yace ma ubansa, idan ba ina bakin ciki da numfashin da yake a duniya ba Shegiya
nake" Umma tace "Uhm ke ko ni, da da yanda xanyi da shi da tuni ni dae nayi wllh,
don ko uwarsa bata isheni kamar yanda ya ishe ni a gidan nan ba, na tsane shi wllh
wllh, ko 'ya yan mu fa Hajja bata ji da kamar yanda take ji da shi wae don yana
namiji mu kuma mata gare mu" Hajiya tace "Toh shine kike kokarin ganin yanda xa ki
cusa masa Suhaima ya aura kuma" Umma tace "Toh ae ke ma da xae auri Muhibba so kike
naga" Hajiya tace "Da kenan ba yanxu ba don nasan hakan ma baxae taba yiwuwa ba,
bari mu shiga ciki ki ji shawarar da na yi a kan matakin da xamu dauka kan Ahmad a
gidan nan" Umma tace "Toh me muke a nan, mu shiga kawae ki ban in sha" mikewa suka
yi gaba daya suka yi palon Hajiya. Gidan El-Ameen junaid ya nufa, yana gama parkin
a waje ya shiga ciki, wanki ya tarar mama nayi a compound din na kayansu, ya karasa
inda take suka gaisa sannan yace "El-Ameen ya xo ne mama?" Tace "Eh ya xo daxu da
safe" yace "Ohk, bacci take yi ne?" Ta girgixa masa kai tace "A'a idonta biyu sae
dae ya kulle dakin," cikin gidan ya nufa ya haura sama, sae dae ya kasa bude dakin,
ya kusa minti biyar tsaye sae kuma ya murda key din a hankali, bayan kusan second
talatin ya murda handle din kofar, tsaye ya ganta jikin window tayi baja baja da
gashinta tana sanye da doguwar rigar kanti pink colour da blue nd black flowers
jiki, kallonsa take tana bobboyewa jikin bango, yayi murmushi ya rungume hannayensa
yana kallonta.


*Haske writers association*馃挕
[16/10, 19:09] Hassan Atk: � *Captain_Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

11.....

Sulalewa kasa tayi ta xauna ta takure waje daya tana rufe fuskarta da dogon
gashinta, dakewa yayi ya karaso cikin dakin kamar bai son taka kasa yana kallonta
ya isa gabanta sae dae banda faduwa bbu abinda gabansa yake, bata dago har lkcn ta
kallesa ba sae d'ada takurewa waje daya take, cire tsoro yayi ya durkusa gabanta a
hankali, dago kanta tayi tana kallonsa a tsorace, murmushi yayi murya can kasa yace
"Hello!" Kuri ta kura masa da ido, shi ma hakan yayi ma manyan fararen idonta, can
ya lumshe ido ya bude cikin sanyin murya yace "Allah ya baki lafiya don son ma'aiki
S a w." A hankali ya kai hannunsa kanta ta kuma shigewa jikin bango, murmushi yayi
ya matsa gabanta ya tattare mata gashinta ya mayar baya yace "Ki daina kunce gashin
ki idan an daure maki Kinji" yana magana ne yana kallon fuskarta, ita kuwa wani gun
daban take kallo, ji yayi ana haurowa sama, ya juya yana kallon kofa sae ga El-
Ameen, dauke kai yayi El-Ameen ya shigo yana murmushi yace "Uhnn! Ka daina tsoron
nata kenan yanxu?" Mikewa Junaid yayi bae ce komai ba, El-Ameen yayi dariya yace
"In gaya maka meyasa kaga ta kyale ka?" Junaid ya juya yana kallonsa, sai da ya dau
kusan minti daya sannan yace "akwae alluran da na mata daxu shi yasa ta nutsu, but
ina me tabbatar maka da xaran ya saketa xaka gane kuran ka idan ka tsaya gabanta"
yana murmushi ya kare maganar, Junaid ya tabe baki ya juya ya fice daga dakin ba
tare da ya tanka sa ba, El-Ameen ya bisa da kallo yana dariya sannan ya juyo yana
kallonta, karasawa gabanta yayi ya durkusa ya dago kanta, hade rai yayi yace "Sae
da kika kuma cire ribbon din koh?" Kallonsa kawae take ko kiftawa bata yi, ya hade
rai yace "I will knock yhu idan baki bar kallona haka ba" kamar taji me yace ta
dauke idonta daga nashi, mikewa yayi ya dauko ribbon ya dawo gabanta ya durkusa ya
kama gashinta waje daya ya daure da ribbon din sannan ya dagota suka mike a tare ya
kama hannunta, kin binsa tayi tana tutturjewa yace "Keehh" daga haka ya ja ta suka
fita daga dakin tana bin sal, Palo ya sauko da ita ya xaunar da ita kasan rug, ya
dauko ledan da ya shigo da ya durkusa gabanta ya bude, fried Irish ne da kwae, sae
tomatoe ketchup, ya dauki potatoe daya ya dibi kwae ya kai mata baki, dauke kai
tayi da sauri tana komawa baya, ya tsaya kallonta, kai wa bakinsa yyi ya ci, Junaid
dae sai kallonsu yake yana yi yana danna waya, kara daukar wani chip din El-Ameen
yayi ya dangwali ketchup ya kai bakinta, tsura ma dankalin ido tayi sae kuma ta
matso a hankali ta lashe ketchup din, El-Ameen ya wara ido yana kallonta, sai kuma
ya saka dariya, murmushi junaid yyi yana ci gaba da danna wayarsa, sae tsotsan
ketchup din take a baki, El-Ameen ya kuma dangwala ya kai bakinta ta kuma lashewa,
rike kanta yayi ya tura mata dankalin a baki ta fito dashi ya fadi kasa, ya hade
rai yace "I will slap yhu fah" kallonsa kawae take ko kiftawa babu, ya dauki wani
dankalin ya dangwali ketchup ya kuma kai mata baki, lashewa ta kuma yi ta bar masa
dankalin tana tsotsan bakinta, yayi murmushi yana kallon Junaid yace "this shows
tana son ketchup lkcn da take da hankali" shi dae junaid bae ce komae ba, El-Ameen
ya dinga dangwalan tomatoe din yana kai mata baki tana lasa, exotic drink ya bude
ya juya yana kallon Junaid yace "Get me cup plss a kitchen Captain, kaga dai
patient dinka nake feeding" Junaid bai ce komai ba ya mike ya nufi kitchen ya dauko
cup din ya kawo masa, ya karba ya tsiyaya drink din ya dauka ya kai mata baki,
dauke kai tayi da sauri, ya juyo da ita ya rike kanta ya kai cup din lip dinta,
kadan ta kurba ta cire bakinta tana yamutse fuska, xae kara bata ta sa hannu xata
karbi cup din ya sake mata, ta dade tana kallon cikin cup din kafin ta kifar da
lemon nan tsakiyarsa, El-Ameen ya mike da sauri ya bar wajen cikin tsawa yace
"Kehh!" Tsorata tayi sosae ta dinga shisshigewa jikin kujera, ya karasa kusa da
ita ya duka ya mata knock a kai yace "kika sake min irin haka sae na tsula maki
bulala" Murmushi Junaid yayi yana shafa kansa, El-Ameen ya dago ta ganin drink din
duk ya bata kayan jikinta, tsaye ya bar ta nan wajen ya fita xuwa ya kira Mama, ta
juya tana kallon Junaid dake kallonta, ya sakar mata murmushi ta dauke kai ta
durkusa wajen ta jawo ledan take away din da Irish din ke ciki ta dauki wanda yake
bata ta ajiye gefe, ta bude wanda bae taba ba ta tsura ma dankalin ido, kifarwa
tayi a kasa, Junaid ya mike da sauri yace "Noo! Me yasa kika xubar" kallonsa tayi
kafin ta maida hankalinta kan abinda take, ta dauki take away din da ya fara bata
ta juye cikin na wanda ta xubar a kasa sannan ta mike tsaye, tattare gown din
jikinta tayi ta juye dankalin a rigarta ta jefar da take away din, Junaid ya
langwabar da kai yana kallonta ya ma rasa me xae ce mata, El-Ameen ne ya shigo Mama
na biye da shi a baya yana mata magana, tsayawa yayi daga bakin kofa ya bude baki
ganin barnar da tayi, tana ganinsa tayi kusa da Junaid ta tsaya rike da rigarta da
ta juye dankali ciki tana kallonsa, El-Ameen ya karaso palon da sauri cikin fada
yace "Whatt! junaid kana kallonta ta xubar min da abincin da xan ci?" Bai jira
cewar Junaid ba ya nufeta, sake rigarta tayi dankalin ya xube gaba daya kasa tayi
bayan junaid da sauri, har wani bari jikinta yake, Junaid ya dakatar da shi da
sauri yace "Hey, Look Dr, naga in tana da hankali ae baxata yi haka ba, have you
forgotten mahaukaciya ce kamar yanda kake kiranta, wannan ae xalunci kawae kake ma
patient din taka, ba dae yunwar Irish kake ba, kar ka damu I will get yhu enough
idan muka fita" El-Ameen yyi masa wani irin kallo yace "Da'alla my frnd ba kana
kallonta ba ka kyaleta, Better tunda dai xaka siya min wani, but wnn ae iskanci ne
ba rashin hankali ba, don bata da hankali sae ta dinga sa mu aiki?" Junaid yace
"naji xan gyara wajen is that all" Mama dake tsaye palon tana kallonsu tayi
murmushi tace "xan gyara wajen bokon turai, kasan sae a hankali, kuma ma wllh hauka
me tsafta take yi bata da kaxanta ko kadan" El-Ameen yayi kwafa yana kallonta ganin
yanda take lekosa daga bayan Junaid yace "Ni nasan maganin ki ae, kina wani leko ni
da Idanuwan nan naki" Junaid ya d'an tabe baki ya koma ya xauna, Mama ta nufi
kitchen don dauko abinda xata gyara wajen. karasawa gabanta El-Ameen yyi ya kama
hannunta ta fasa ihu, kunnenta ya ja ta nufi sama da ita, Junaid ya bi su da kallo
sannan ya girgixa kai a hankali ya jinginar da kansa jikin kujera. Bayi El-Ameen ya
shiga da ita ya wanke mata hannayenta sannan ya fito da ita ya xaunar gefen gado
sai kallonsa take, wani kayan ya ciro mata ya ajiye gefen gadon, yana kallonta yace
"ki daina kallona haka keh, kuma kika kuskura kika tashi a nan sae na xane ki,
clear?" ita dae kallonsa kawae take, sae ta basa dariya ganin irin kallon, ya
rungume hannu yace "Uhhn! Halan dai kin san ni ne?" murmushi yyi ya juya ya fita
daga dakin. Mama jummai yace ta tafi ta canxa mata kaya bayan ta gama gyara gun da
ta bata, mama tayi shiru sae kuma tace "Naga idonta biyu fa" El-Ameen yayi dariya
ya xauna yace "ae bata komae mama, shi yasa nace ki tafi ki canxa mata, kar ki samu
damuwa bbu abinda xata maki, tana da nutsuwa sosai" mama jummai bata musa ba ta
nufi sama cikin rashin kuxari. Tana nan xaune inda El-Ameen ya bar ta a dakin ta
sameta, kin rufe kofar Mama jummai tayi in case, ta karasa kusa da ita tana d'ari
d'ari ta dauki blue gown din da ya fiddo mata, a hankali mama jummai tace "Baiwar
Allah kaya xan canxa maki kin ji" ko kallonta bata yi ba, hakan ya kuma tsorata
mama jummai, juyawa tayi a sanyaye ta koma Palo tana kallon El-Ameen tace "D'an nan
wallahi tsoro nake ji ni kam, kaga sae tana bacci nake shiryata" dariya yayi ya
mike ya nufi stairs din suka koma sama a tare, junaid ya bi su da kallo. Xaune suka
tar da ta har lkcn sae dai wannan karan windon dakin ta tsura ma ido, El-Ameen ya
karasa kusa da ita, ta juya da sauri tana kallonsa, kayan ya dauka ya mika ma mama
jummai yace "Gashi mama" karasawa tayi ta karba, ya dago ta yana kallonta ya hade
rai yace "Mama xata canxa maki kaya yanxu, stay still kin ji" ita dae kallonsa
kawae take, ya juya ya kalli Mama jummai yace "Toh karaso Mama" a hankali ta karaso
kusa da su, hannunta na rawa ta kai kan maballin rigar xata cire mata, ta fasa wani
ihu tayi bayan El-Ameen da sauri, cikin sakwannin da basu wuce uku ba sae ga mama
jummai can bakin kofa a mugun tsorace bayan ta sake kayan hannunta nan gabansu,
dariya sosai El-Ameen yake yana kallonta yace "Mama baxa fa ta maki komae ba wllh"
tace "A'a d'an nan nafi gane tana bacci wllh" a tsorace take maganan daga haka ta
juya ta koma kasa, murmushi yayi ya juya yana kallon ta bayansa, dawo da ita yayi
gabansa, ya kusa minti biyu tsaye kamar me naxari sai kuma ya leka rigar jikinta
don ganin ko akwai kaya a ciki yaga akwai vest, rufe idanuwansa yyi a hankali ya
balle dogon rigan jikinta snn ya fara cirewa idonsa kulle, ajiyewa yayi bayan ya
cire har lkcn idonsa na rufe ya duka a hankali ya shiga laluban kayan da Mama
jummai ta yar a kasa, yana tabawa ya dauka sannan ya mike, lalubawa yayi yaji bata
wajen kuma, ae ba shiri ya bude ido da sauri yana waige waigen inda xae ganta,
tsaye ya ga perfect fair figure dinta can jikin window, daga ita sai white vest da
ya kusa cinyarta, vest din ya kamata sosai kasancewarsa very elastic, gaba daya
shape dinta ya fito ga long fresh legs dinta da bbu tabo ko daya, kamar xaka latsa
ta jini ya fito tsabar haske, juyawa yayi da sauri kamar wanda ya ga abun tsoro ya
nufi kofa da hanxari, ko me ya tuna kuma sae yyi still bakin kofar ya kusa 3 mins
kafin ya juyo a hankali ya dawo dakin ya nufeta ba tare da ya kuma kallon jikinta
ba, hannunta ya kama yana kallon fuskarta ya shiga sa mata rigar hannunsa, yana
gamawa ya xaunar da ita gefen gado ya hade rai ya dunguri kanta yace "Don't try dat
again" cup ya dauka ya dauraye yayi mata diluting drugs dinta da ruwa sannan ya
dawo kusa da ita ya rike kanta ya kai cup din bakinta, kauda kai tayi da sauri,
yayi mata tsawa ita ma ta fasa
masa ihu, rike kanta yyi ya tura cup din bakinta har sai da ta bude ya xuba mata,
sae da ya tabbatar ta hadiye sannan ya kyaleta tana yatsinan baki tana komawa baya,
jinin da ya gani bakinta yasa ya tsura ma lips din ido, handkerchief ya ciro
aljihunsa ya goge mata bakin yace "Sorry!" Mayar da handki din yayi ya kwantar da
ita ya mike ya fita daga dakin ya ja kofar. Palo ya sauko ya ga ba Junaid, ya kalli
mama dake xaune yace "Mama Junaid fa?" Tace "Ya tafi wai" shiru yayi bae ce komae
ba, can yace "Ohk xan tafi yanxu, da daddare xan dawo, bacci xata yi yanxu" tace
"Toh Allah ya kai mu, Allah kuma ya bata lafiya" yayi murmushi yace "Ameen" sannan
ya fita.

*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

13....

Junaid bai daga kiran ba ya juya yana kallon Khadija, Mikewa xaune tayi ta hade rai
kamar xata yi kuka tace "Ni fa wllh ba chatting nake ba ya A.jay, ita Hajja bata
san komai ba sai dai tayi ta magana" Junaid xai yi magana Humainah ta shigo palon
fuskar nan nata a daure ta xauna gefen Hajja, Hajja tace "ke kuma fa? Ina aiken"
Humainah tace "ko ba yi tayi kamar bata gan ni ba, kuma bata ce min komae ba sai
aikinta take tana wake wake ta bar ni a tsaye" Junaid yace "Wa?" Ta kallesa tace
"Anty sadiya mana" Hajja ta mike rai bace tace "Kambu!! Yaran nan sun raina ni
wllh, don uwarta ni din sa'arta ce da xan aika tayi min abu ta share ki tana wake
wake?" Kofa ta nufa kamar xata tashi sama, Junaid ya mike ya bi bayanta yace "Tsaya
Hajja, me kika sata?" Tana huci ta juyo tace "Ca nayi ta min dafadukan taliya shi
ke raina yanxu don Amina shinkafa tayi kamar ko da yaushe, ita bata da girki sai na
shinkafa kullum" Junaid ya hade rai yace "Ita mum din tawa, Toh su wa ennan na
palon naki me suke yi da baxa su maki ba" Hajja tayi tsaki tace "Xancen banxa, toh
ban yi niyyan sa su ba, ko da yanda xaka yi da ni ne" tana kai wa nan ta nufi part
din Hajiya da sauri, ya d'an tabe baki ya juya yana kallon Humainah yace "Sannu da
hadi, ke baki iya taliyar ba sae kin je dauko magana koh?" Ta turo baki tace "Ae
dai ba ni nace tayi ba, aikena aka yi" yace "Xaki yi bayani idan na kama ki ne"
dauke kai tayi ya juya yayi wucewar sa, Khadija tayi dariya tace "Bari in je inyi
kallo" Ana kiraye kirayen Magrib Junaid ya fito part dinsa sanye da jallabiya
milk colour, dai dai nan Humainah da fatima suka fito daga part din Mumy, Humainah
tace "Masallaci xaka ya Ahmad" Ya harareta yace "A'a office xan je" bae jira cewar
ta ba ya kara gaba. Yana fito wa daga mosque bayan an idar da sllh ya tsaya da wani
frnd dinsa da ke nan layin suna gaisawa, har sai da ya ga shigar Abba gida, snn
yace "Abdul d'an ara min motar ka pls xan dan fita in dawo yanxu" Abdul yace "Toh
mu shiga in baka key" junaid ya bisa suka shiga compound dinsu ya tsaya daga
balcony har ya kawo masa makullin sannan ya nufi parking lot ya dau motar ya fita.
Atm machine ya fara tsayawa ya cire kudi ya siya fruits nan wajajen sannan ya koma
mota ya dau hanyar gidan El-Ameen. A waje yayi parking bayan sun gaisa da mai gadin
ya shiga gidan, Mama jummai na kwance Palo kasan tiles ta shimfida xani da 'yar
radionta a hannu tana saurare, ta mike xaune ganinsa tace "Sannu da xuwa Ahmad"
xaunawa yayi yace "Yauwa mama ina yini?" Tace "Lfya lau, ya gidan?" Yace "Alhmdllh
Mama, El-Ameen ya xo kuwa?" Tace "Ehh bae dade da fita ba, kuma yace min xai dawo"
yace "Ohk, bacci take ne?" Mama jummai tace "Anya! Ina jin kamar idonta biyu"
Junaid ya ajiye mata ledan fruits guda daya yace "Ga kayan marmari mama" godiya ta
dinga masa ya mike ya nufi stairs ya haura sama. A hankali ya tura kofar dakin ya
tsaya daga bakin kofar yana kallon cikin dakin, rakube ya ganta gefen gado ta
sunkuyar da kanta, a hankali ya karaso cikin dakin yana kallonta har ya iso gabanta
ya durkusa, sai a sannan ta dago kai tana kallonsa da dara daran fararen idonta,
komawa baya yayi da sauri don ba kadan idanuwan nata suka bashi tsoro ba, ta wani
kafe sa da ido ko kiftawa bata yi, sauke kansa yayi kasa ya bude ledan gabansa ya
mike ya dawo kusa da ita ya duka a hankali ya dauki Apple daya ya mika mata, kallon
Apple din take kamar me son gano abu a jiki, ya kai bakinsa ya gutsura a hankali ya
fara ci yana kallonta, har sai da ya cinye sannan ya kai mata bakinta, kauda kai
tayi da sauri, ya dawo gefenta ya kuma kai mata baki yace "Apple! taste ki ji" rike
kanta yayi ya kai mata baki ta d'an bude bakin kadan ta gutsura, yana kallon yanda
take kokarin hadiye Apple din ba tare da ta tauna ba yace "Wait, Wait!" Da sauri ya
kuma gutsuran Apple din ya shiga taunawa yana kallonta ita ma haka, yanda ta ga
yana yi haka ita ma ta shiga yi tana taunar Apple din a hankali, yayi murmushin sa
me kyau yace "Good!" Tana hadiye wa ya kai mata baki kuma ta gutsura, karban Apple
din tayi a hannunsa ta shiga ci da kanta, ya dawo gabanta ya durkusa yana kallonta,
matsowa kusa da ledan ta shiga yi tana kallon ciki, ya dauki ayaba daya ya bare ya
gutsura sannan ya kai mata sauran baki ta bude a hankali ya sa mata, taunawa ta
shiga yi tana yatsine fuska, murmushi kawai yake yana kallonta, can ta dauki peel
din bananan xata kai baki, ya karbe da sauri yace "No!" Tsuke baki tayi tana
kallonsa, dariya yayi ya dauki wani Ayaban ya bude ya mika mata gaba daya, ta ajiye
Apple din hannunta ta karba, cikin lkci kankani ta cinye ayabar, ya kuma bare mata
wani shi ma ta cinye, haka ya dinga yi mata har ta ki karba kuma, ta dauki Apple
din da ta ajiye tana kallo, karba yayi ya kai mata baki, ta dafe hannunsa da duk
nata biyu ta gutsura a hankali tana taunawa, kallon hannunta kawae yake don duk
haskensa ta fi sa nesa ba kusa ba, tana rike da hannunsa haka ta dinga cin Apple
din, dai dai nan El-Ameen ya shigo dakin, xaro ido yayi ya rungume hannu yace
"Tabdi! Me kke yi haka captain, she will bite the hell out of yhu wllh!" A hankali
Junaid ya xame hannunsa daga nata, ta daga ido tana kallonsa, ya kamo hannunta ya
danka mata Apple din sannan ya mike yana kallon El-Ameen, El-Ameen ya tabe baki
yace "Ina raba ka da shisshige ma mahaukaciyar nan baka ji koh? Randa xata nuna
maka halinta na hauka I won't be around fah" Junaid bai tanka sa ba, El-Ameen yayi
kwafa ya ajiye ledan drugs din hannunsa da fresh yoghurts ya dawo gabanta yace
"Ashe kin iya cin fruits" bata kallesa ba sae cin Apple dinta da take, ya d'an yi
murmushi ya nufi inda alluranta suke don hada wanda xae mata, Junaid ya juya ya
nufi kofa, mikewa tayi da sauri ganin haka, sae kuma ta bi bayansa, dai dai stairs
yaji kamar ana binsa, ya juya ya ganta tana tahowa, kallonta ya tsaya yi, har ta
karaso gabansa ta kama hannunsa ta saka masa Apple din, sannan ta daura nata hannun
kan nasa ta kai bakinta ta fara cin Apple din, murmushi kawae yake yana kallonta,
El-Ameen ya fito daga dakin ya rungume hannunsa yana kallonsu yace "Uhunm! It seems
she's getting use to yhu yanxu, kaga kawae sae ka tattaro ina ka ina ka ka dawo nan
ka tsaya da ita sai ka cike Ladan ka" yana magana ne yana murmushi, Junaid ya xame
hannunsa daga nata ya damka mata Apple din ya juya ya fara sauka stairs din, bin sa
tayi da sauri, El-Ameen ya daka mata tsawa, a tsorace ta juya tana kallonsa, ya
karaso inda take ya kama hannunta suka koma daki, xaunar da ita yayi gefen gado, ya
bude yoghurt din da ya shigo da ya xauna gefenta ya kai mata baki, ta kauda kai da
sauri, wani kallo yayi mata yace "I will slap yhu" kamar ta ji me yace bata sake
yunkurin dauke kai ba, ya dafa kanta ya kai mata yoghurt din bakinta, a hankali ta
dinga sha tana kallonsa, tari ta fara yi ya cire yoghurt din da sauri daga bakinta
a hankali yace "Sorry," ya dafa kanta ya kuma kai mata baki, ta dauke kai da sauri
tana kokarin karban roban, sake mata yayi ta kallesa sannan ta fara tuttular da shi
nan kasan dakin, fixge wa yayi da sauri yace "Ance maki idan aka koshi xubar da
abinci ake?" Kallonsa kawae take ko kiftawa bata yi, ya ja dogon hancinta yace "Da
wani idanuwanta a wajen" jan hancin ita ma tayi yanda ta ga yayi, yayi murmushi
yana kallonta, yoghurt din hannunsa ya rufe ya ajiye sannan ya mike ya nufi inda
drugs dinta suke, diluting yayi mata a cup ya dawo gefenta ya xauna, matsawa ta
fara yi daga kusa da shi, ya jawo ta ta fasa ihu, d'an buge mata baki yayi tayi
tsit tana kallonsa, ya kai mata maganin baki taki budewa, sae da yayi mata tsawa
sannan ta bude da sauri har jikinta na rawa, ya xuba mata maganin gaba daya, sai da
ya tabbatar ta shanye snn ya mike yana kallonta, banda yatsine fuska bbu abinda
take, yayi murmushi ya juya ya fita daga dakin, downstairs ya sauka ya samu Mama
Jummai kadae palon, yace "Junaid fa Mama?" Tace "Ya fita ae" yace "Ohk, ki taso toh
ki rakata baya tayi fitsari yanxu xata yi bacci tunda na bata magani" mikewa tayi
tace "Toh, ae tana da tsafta yarinyar duk me xata yi naga tana shiga bayi" yayi
murmushi yace "Kin dai yrda bata komai yanxu koh" yar dariya tayi tace "Ehh na
yrda, don daxu ina xaune ta sauko, duk na tsorata ba kadan ba, ae ko in gaya maka
sai gani nayi ta xauna gefe na ta mimmike kafa yanda taga nayi" dariya El-Ameen
yayi yace "Ae wayo gareta, idan Allah ya yrda sama mata lfya baxae wani dau lkci
sosai ba, kila daga nan xuwa wata hudu ko shidda in'sha Allah" Mama jummai tace
"Toh Allah ya yrda, Allah ya ba Baiwar nan tasa lfya, gashi 'yar yarinya da ita"
yayi murmushi yace "Kina ga xata yi shekara nawa" Mama jummai tace "Kai baxata wuce
sha shidda ba wllh, in ma ta kai kenan" yana murmushi yace "Ko kuma sha bakwai ba"
Mama jummai tace "Allah sarki, amma dai ku dinga hada mata da Addu'a kunsan duniya
bbu gaskiya, kar ayi ta na turawa nan kuma kila asiri ne" ya d'an yi shiru kafin
yace "Anya kuwa, bana tunanin jifa ne, don da jifa ne ba lallai ta xama nutsatssiya
haka ba, nd jiya naga tana ta observing wnn tumatir din cikin dankalin da na siyo
kuma ta sha sosai" Mama Jummai tace "Toh Allah dai ya bata lfya amma dai ayi
addu'ar ma" yace "Ameen, xa a hada mama" Sama mama Jummai ta nufa shi kuma ya xauna
palon, bata mata wani gardama ba ta kai ta bayin. Ko da Mama Jummai ta sauko mikewa
El-Ameen yayi ya koma sama, kwance ya sameta idonta lumshe alamar xata yi bacci, ya
gyara mata kwanciya ta bude ido da sauri tana kallonsa, ya rufa ta da bargo, ya
dawo dai dai fuskarta yace "Gudnyt" lumshe ido kawae tayi ya juya ya fita daga
dakin ya rufo mata kofa, yayi ma Mama Jummai sae da safe ya fice daga palon, xaune
ya ga Junaid a balcony, ya d'an bude ido da mamaki yace "Thought ka tafi ai" Junaid
ya mike yace "Sure! Yanxu xan tafi" daga haka ya sauka balconyn yayi hanyar gate,
El-Ameen ya bi sa da kallo sannan ya tabe baki ya bi bayansa, kusan a tare suka
fita compound din, El-Ameen ya kalli motar da Junaid ya nufa yace "Whose car is
that?"
Ba tare da Junaid ya kallesa ba yace "Abdul" daga haka ya bude motar ya shiga, El-
Ameen ya karasa gun motar yace "Yhu are acting strange this dayz Captain, let it
not be kai ma ka fara samun brain disorder'n ne fa, aikin sai yayi min yawa" El-
Ameen ya kare maganar yana murmushi, junaid ma yayi murmushi yace "Sure!" Daga haka
ya ja motar ya bar sa nan tsaye, El-Ameen ya bi motar da kallo yana murmushi yace
"It's Alwayz: 'Yea! Sure! D'an rainin hankali, tasa motar shi ma ya nufa ya bude ya
shiga ya bar anguwar yana tunanin yanda xai yi squeezing time dinsa gobe da safe ya
xo ayi diagnosing dinta.


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain_Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

14.....

Junaid na isa layinsu ya kira Abdul don ya fito ya karbi motar sa, Abdul ya fito
yayi instructing mai gadinsu ya bude gate, yana budewa Junaid ya shiga yayi masa
parking a parking lot din gidan sannan ya fito ya mika masa makullinsa yace "Thanks
Abdul, sae da safe." Masallaci ya fara shiga yayi Isha sannan ya shiga gida, sai da
ya tabbatar Mumy baxata hangosa ba idan ya xo wucewa ta side dinta sannan ya wuce
da sauri. Humainah ce tsaye bakin tap tana diban ruwa, ta bi sa da kallo tace "Daga
ina kake ya Ahmad" ba tare da ya kalli inda take ba yace "Inda kika aike ni" dariya
tayi tace "Mumy fa na ta neman ka" dawowa yayi da sauri wajenta yace "Kice Wllh,
tun yaushe?" ta kyalkyale da dariya tace "Tsaya nan, tun daxu ake neman ka" ya hade
rai yace "Ke wa ya gaya maki?" Ta d'an yatsine fuska tace "Tare mukayi ta neman ka
ae har da Hajja, da Abba, an ma kira layin ka bae xuwa wai switch off" shiru yayi
ya ma rasa tambayar da xae kuma yi mata, ta tabe baki ta kashe tap don bucket dinta
ya cika, Muhibba ce ta karaso wajen, kallo daya tai ma Junaid ta dauke kai, Empty
Bucket din dake wajen ta kalla tace "Ke wa yace ki taba min ruwan da na tara?"
Humainah ta tabe baki tace "Oho, nima haka naga bokitin" cike da masifa Muhibba
tace "Kar ki gaya min maganar banxa ba ni da ke bane a nan xaki wani ce baki sani
ba" hararanta Junaid yayi ya juya xae bar wajen, Muhibba ta yi ball da ruwan da
Humainah ke diba, Humainah ta xaro ido tace "lalala! Wllh sai na rama" dawowa
Junaid yayi da sauri ya rike ta ganin tayi gun Muhibba, yace "Ke Babu ruwa a ciki
ne?" Kamar xata yi kuka tace "Dubi fa abinda ta min ya Ahmad, Hajja ce fa ta aikeni
in debo mata ruwa" yace "Ke kin taba ganin inda ake fada da mara hankali!" Humainah
tace "ohh Kuma fa haka ne" yace "Gud! Ki tafi ciki ki debi ruwan ki" tace "Ko ba
Hajja ta sa mai gadi ya kashe engine ruwan ba tun da rana" yace "Ehh xan je in
kunna yanxu" tace "Toh" juyawa Muhibba tayi fuu ta bar wajen, Humainah ta kyalkyale
da dariya, ya harareta ya juya yayi side din Mumy, da sauri tace "ni fa wasa nake
maka ba a neman ka" juyawa yayi yana kallonta yace "Na fara wasa da ke ne koh?"
Kwafa yayi ya nufi part dinsa. Muhibbah na shiga part dinsu ta xube jikin Hajiya
dake xaune Palon da Rabi'a ta fashe da kuka tace "Hajiya kina ganin fitsaran da
yarinyar nan da suka xo gidan nan da Hajja ta min, har Ahmad na Goya mata baya yana
kirana mara hankali" Hajiya da bacin rai ya bayyana karara a fuskarta tace "ki ka
barta baki ci ubanta kin nakada mata duka ba?" Muhibba na share hawaye tace "Toh ba
yana tsaye gun ba" Sadiya tace "duk uwarsa ke xuga sa yake rashin mutunci a gidan
nan wllh" mikewa Hajiya tayi kamar xata tashi sama ta fice daga palon tayi part din
Junaid, yana xaune rike da remote xae yi powering Tv ta shigo, kallo daya yayi mata
ya dauke kai, cikin fada tace "Ahmad ita Muhibbar kake kira mahaukaciya? Toh in har
Muhibba na hauka to Amina ma haukan take, ita ce ma babban mahaukaciyar..." Mikewa
yayi yana kallonta a nutse yace "Ina ganin girman ki a matsayin ki na matar mahaifi
na, amma kika sake kika taba mahaifiyata girman nan xae xube wllh," a fusace tace
"Ya dade bai xube ba girman don uwarsa, da can ganin girman mu kake munafuki, ai mu
wllh sai dai mu ce Allah ya isa tsakaninmu da Amina duk ta shanye mana miji sai
yanda tayi da shi, kai ma ka taso kana neman xame mana fitina da bala'i a gida to
kun yi kadan daga kai har makirar uwar taka....." Wani irin kallo Junaid ke mata ya
girgixa kai yace "Gaskiya jahilci cuta ne" xaro ido tayi ta dafe kirji tace "Ni
kake kira jahila Ahmad?" Juyawa yayi ya koma ya xauna, ta fashe da kuka ta juya ta
fice daga palon. Ko minti biyar bata yi da fita ba Khadija ta shigo tace "Ya A.jay
Abba na kiran ka" ya kalleta ya dauke kai ta fita, mikewa yayi ya bi bayanta. Part
din Abba ya tafi ya shiga palon da sallama, babu abinda ya daga masa hankali sai
ganin Mumy da yayi a palon, ya karasa a sanyaye ya xauna kasa kusa da ita yana
kallonta, ganin taki kallonsa yasa ya juya ya kalli Abba yaga yanda ya wani hade
rai yana kallonsa, Hajiya na xaune palon sai sharban kuka take, Umma sai wani sauke
ajiyar xuciya take tana tabe baki, ko kadan hakan bai damesa ba yafi tunanin fushin
Mumy a kan ma na Abban, Abba ya mike cikin tsananin fushi yace "Ahmad maimaita
abinda ka fadi ma Hajiya a palon ka daxu" ya d'an kalli Abba sannan yayi kasa da
kai yayi shiru, Abba ya daka masa tsawa yace "Ba magana nake maka ba" nan ma dai
bai dago ba bare yace wani abu, Hajiya aka kuma fashewa da kuka mai sauti, Abba
yayi murmushin takaici yace "Wato ita Hajiyar kake kira da jahila ko Ahmad?" Junaid
ya girgixa kai har lokacin bai dago ba yace "Ni ban kirata da haka ba Abba" Wani
tsawa Abba ya daka masa yace "you are stupid, sharri tayi maka kenan" Junaid ya
girgixa kai, a fusace Abba yace "Toh bari kaji abinda baka sani ba, in har xaka iya
bude baki ka ce ma Hajiya Jahila, to bbu tantantama warcan da ta haife ka ma xaka
iya kiranta da haka, ka sani matsayin uwarka dai dai yake da wa ennan da ka raina a
gidan nan, kuma from henceforth a gidan nan sai ka ma uwarka fitsara ka xauna
lafiya amma idan ka kuskura kace xaka masu sai ka ga the other side of me wllh, I
will deal with you, maxa tashi kaje ka bata hakuri kar in baka mamaki yanxu" Junaid
da yaji kamar an soka masa mashi ya daga kai da kyar yana kallon Mumy, hawaye ya
gani idonta, rudewa yayi ya dawo gabanta ya durkusa yace "Noo plss mum, kar ki
xubda hawayen ki saboda ni, don Allah kiyi hakuri ki yafe min" bude baki Abba yayi
yana kallonsa da mamaki, Hajiya da Umma ma sai kallonsu suke cike da tsana, shi kam
magiya ya dinga yi ma Mumy yana bata hakuri ba tare da ya kuma bin ta kan Abba ba,
mikewa Mumy tayi ta fice daga palon, shi ma ya mike xai fita, Abba yayi masa wani
mugun tsawa, juyowa yayi yana kallonsa a hankali yace "Abba xan je in dawo"

Karfe hudu da rabi Junaid yyi parking a parking area din gidansu, ya dade xaune
cikin mota yana danne dannensa a waya har sai da Humainah ta leko daga part din
Mumy, ganin haka ya kashe motar ya fito ya kulle, wuce ta yayi ya bude kofa ya
shiga, ta bi bayansa tace "Me kake cikin motar ya Ahmad?" Yace "Abinda kika sa ni"
dariya tayi ta bi bayansa, ya xauna Palo yana kallon Mumy a hankali yace "Sannu da
gida Mumy" tace "Welcome, kai dadin xaman mota kawae kake" murmushi yayi ganin Mumy
ta huce gaba daya yace "Na gaji ne Mum" Humainah ta xauna kasa kusa da shi tace
"Sannu da dawowa ya Ahmad" banxa yayi mata, fatima dake palon ma tace "Sannu da
dawowa yaya" yace "Yauwa" sannan ya mike yace "Bari in je in yi wanka Mumy" Mumy
tace "Ba gaisheka Humainah yi ba" yace "Gulma ce fa Mumy, da tana gaishe ni ne"
Mumy ta hararesa yyi murmushi kawae ya nufi kofa, Humainah ma ta bi sa da harara,
Yana shiga part dinsa yayi wanka ya dawo Palo yayi kwanciyarsa, yana son xuwa gidan
El-Ameen amma bai ma san inda xae ce ma Mumy xai je gashi yana ta kiransa tun a gun
aiki ya ki dagawa, ashe akwai ranan da xai ga disadvantage din rashin fitarsa, don
da yana fita da Mumy baxa ta dinga querying dinsa ba idan yace xae fita yanxu,
mikewa xaune yayi jin an bude kofar parlour, Humainah ta shigo ta tsaya daga bakin
kofa tace "Mumy tace ka xo ka ci abinci" dauke kai yayi yace "Naji" ta karaso cikin
parlour'n tace "ni da ita muka yi girkin, tuwo da vegetable soup" ya hade rai yace
"Who ask yhu" dariya tayi tace "Toh don ma na gaya maka" ya tabe baki ya mike ya
dauki wayarsa ya nufi kofa, mikewa tayi ta bi bayansa da sauri, sai da suka fita
yace "Hajja fa?" Tace "Bata nan taje gidan kawarta yau, kasan gobe xa mu koma" ya
kalleta yace "Wa yace maki tare xa ku koma, bayan Abban ki yace ya ba mu ke" hade
rai tayi tana kallonsa tace "Wa yace maka haka" murmushi yayi ya bude kofar
parlour'n Mumy ya shiga ta bi bayansa. Kasa ta xauna tana kallon Mumy tace "Mumy
wae ba da ni Hajja xata tafi ba gobe?" Mumy tace "ba tace nan xata bar ki ba"
hawaye ne ya cika idonta tace "A'a ae ni ban ce xan xauna ba" Mumy tayi dariya tace
"Toh bari idan ta dawo sae ki gaya mata, Meye abun kuka" dariya Junaid yayi yace
"Ae sai dai tayi na jini nan xata xauna ita da fatima da khadija" ta fashe da kuka
tana kallon Mumy, Mumy ta hararesa tace "kaga wuce dinning ka ci abincin ka bana
son haka" mikewa yayi ya nufi dinning yace "Yi hakuri Mumy" mikewa Humainah tayi
xata fita daga parlour'n Mumy tace "Ina xa ki" tana goge fuskarta tace "Xan je in
jira Hajja" Mumy tayi dariya tace "Ai yanxu xata dawo, xo kiyi xaman ki a nan ki
jirata" bata tsaya ba tayi ficewarta a palon. Har aka kira Magrib Junaid na kwance
palon Mumy duk ya rasa yanda xae ce mata xai fita, mikewa yayi ya nufi toilet din
palon yayi alwala ya fita xuwa masallaci, yana dawowa ya nufi part din Abba sanin
ya shiga yanxu, Hajiya ce a parlour'n tana jera masa abincin supper a kasan
lallausan rug din tsakar parlour, ya karasa ciki kansa a kasa yace "Ina yini?" Hade
rai tayi tace "Ka fita don Allah abinci xai ci ynxu" tsayawa kallonta yayi, dai dai
lkcn da Abba ya fito daga bedroom dinsa, Abba ya karaso cikin palon yana kallonsa,
karasawa yayi inda Abba ya xauna, ya xauna daga kasa shi ma, a hankali yace "sannu
da dawowa Abba" Abba yace "yauwa sannu, ya aikin?" Har lokacin bai dago ba yace
"Alhmdllh!" Abba yace "Gud! Daxu baka shigo gaishe ni da safe ba" shafa kansa yayi
yace "Na shigo Umma tace kana bacci" Abba yace "Ohk, amma baka karasa bedroom ba"
junaid ya gyada kai kawae, Abba yace "kafi kowa sanin bana baccin safe ae" shiru
Junaid yayi bai kuma cewa komai ba, kallonsu kawae Hajiya keyi ta gefen ido tana
jera abincin da take rai ba dadi don bata so haka ba, Abba ya sauko kasa ya jawo
babban food warmer, ya dau plate xai dibi shinkafa, Junaid ya karba yace "Bari in
xuba maka Abba" sake masa spoon din Abba yayi, ya dibi shinkafar da stew a gefe da
cow meats, snn ya xuba masa vegetables a kai kamar yanda ake masa, Abba ya dauki
wani spoon din yace "Bismillah" sai da Abba ya fara ci sannan Junaid ya debi
shinkafar a hankali ya kai bakinsa, Hajiya kamar ta hadiye xuciya ganin ko ta kanta
Abba bae bi ba, taunar abincin kawae junaid yake ba don yayi masa ba, banda girkin
Mumynsa babu na wanda yake ci, girki in ba nata bane ko kallonsa bai yi, shiyasa a
ko da yaushe take bata tym dinta tayi masa girki, a tare suka gama cin abincin da
Abbansa, bai yi Mamakin sakkowan Abba da wuri ba don in dai suka hada sa da shi,
bai daukan lkci yake kuma jawo sa jiki, kwata kwata baya fushi mai tsayi da only
son din nasa, hakan ba karamin daga ma su Hajiya hankali yake ba, sun dai rasa
yanda xa su yi da Junaid a gidan, a tare suka tafi masallaci sllhn Isha da Abba,
sae da suka dawo ya ba Abbansa hakuri a kan abinda ya faru jiya, Abba yace "Its
Ohk, ka dai kiyaye halshan ka nan gaba" yace "In'sha Allah Abba" sun jima suna hira
da Abba sannan yayi masa sai da safe ya mike ya fita ya shiga part din Mumy, tana
xaune palo tana kallo, ya xauna gefenta ya dauki remote xae canxa tasha, Mumy ta
karbe remote din tace "ya haka, bari a gama program din mana" kallon Humainah dake
kwance kusa da fatima yayi yace "Har kin hakura xaki xaunan kenan?" ta daga kai
tana kallonsa bata tanka sa ba ta dauke kai, Mumy tayi dariya tace "babban kawai"
bude kofa aka yi hade da sallama, Junaid ya kalli agogo jin muryan El-Ameen, ya ga
tara da rabi, Mumy tace "Kai dai baka jin fitan dare koh El-Ameen" junaid yayi
murmushi yace "Kin manta likita ne Mumy" El-Ameen ya karaso parlon ya xauna yana
murmushi ya gaida Mumy, da fara'a tace "lfya lau bokon turai ya aiki" yace
"Alhmdllh Mumy" Fatima tace "Welcome bro" yace "Thank you sis" kallon Humainah dake
xaune hankalinta na gun kallo yayi sannan ya kalli Junaid, Mumy tace "baki gaida
yayanki ba Humainah" ba tare da ta kallesa ba tana ci gaba da kallonta tace "Ina
yini" idonsa na kanta yace "Lfya lau" hira suka dinga yi da Mumy, ganin hiran ba me
karewa bace Junaid ya mike ya nufi kofa yace "Ina part dina in ka gama karyan"
dariya Humainah tayi a karo na farko ta kalli El-Ameen da ya hade rai yana kallon
Junaid, Mumy ma tayi dariyar tace "Ae dae ya fi ka wllh tun da har yana daurewa
yayi karyar" Junaid dake bakin kofa ya saka dariya yace "Surutun fa iyakansa a gida
Mumy, mutumin da ko magana bai iya yi ma mace ba a waje sai kame kame," El-Ameen
yace "Ehh ae kai naga ka iya d'an rainin hankali" banda dariya bbu abinda Humainah
ke yi Mumy da fatima na taya ta, Junaid ya juya ya fice daga parlorn yana murmushi,
mikewa El-Ameen yayi yace "Bari in je Mumy" Mumy tace "Toh fatima xata kawo maku
abinci" toh kawae yace ya fita, Part din Junaid ya nufa ya samesa xaune a parlor ya
kunna Tv, El-Ameen yace "Yau ban gan ka ba, kuma I was calling tun daxu baka
responding" Junaid yace "I wasn't in a gud mood ne yau" El-Ameen yace "Wacece
wannan yarinyar dake xaune parlorn Mumy" Junaid ya kallesa yace "Ya aka yi" d'an
sosa kai El-Ameen yayi yace "Umm, tana da kyau ne" dariya Junaid yayi yace really?"
El-Ameen yace "What's funny, Allah tana da kyau" Junaid yace "Toh bari ta shigo" ko
rufe baki junaid bai yi ba sai ga ta ta shiga palon da sallamarta rike da tray din
abinci, El-Ameen ya sunne Kai murya can kasa yace "Don Allah ka rufa min asiri kar
kace komai Junaid, wasa nake" Junaid ya fashe da dariya yace "Humainah" ae da sauri
El-Ameen ya mike ya rufe bakinsa da hannu yana xaro ido, junaid ya dinga dariya
yana tura hannunsa amma yaki sake sa, tabe baki tayi ta ajiye trayn hannunta tace
"Mumy tace in kawo" da karfi Junaid ya tura El-Ameen yace "ke kin yi saurayi
likita" ae ko rufe baki bai yi ba, El-Ameen yayi hanyar daki da sauri ya shige ya
rufe kofar, Junaid ya dinga dariya har da rike kai, hade rai tayi tana kallonsa,
can tayi tsaki ta juya ta fice daga parlon, kin fitowa parlor El-Ameen yayi har
kusan Karfe goma, Junaid ya shiga dakin yace "Toh wai a haka xan baka kanwar tawa
kana kunyar ta!" El-Ameen dake xaune gefen gado yace "ta tafi?" Junaid yace "Aa
tana parlor" shiru El-Ameen yayi sai kuma ya mike ya cire shirt din jikinsa ya nufi
bathroom, junaid ya bi sa da kallo yana dariya, wanka yayi ya fito sanye da
bathrobe, ya nufi closet din Junaid ya fiddo pyjamas ya sa sannan ya dawo ya xauna
yana kallon Junaid yace "Amma ba nan xata kwana ba dai koh?" Junaid ya hararesa
yace "Nan din xata kwana" El-Ameen ya daga kafada yace "Ohk ni kam am spending the
nyt here today, its late and bana son ta gan ni, I came purposely because of ur
patient, they've diagnosed her, that is an mata genetic screening, brain scans,
neurological exam i.e (checking of vision, hearing, and balance) and other tests,
and you knw wat?" Shiru Junaid yayi yana kallonsa, El-Ameen yace "They've found out
that she is suffering from post-traumatic stress disorder (PTSD), and this is a
serious potentially debilitating condition that can occur in people who have
experienced or witnessed may be a serious accident, sudden demise of a loved one,
violent personal assault such as rape da sauransu, terrorist incident, or other
life-threatening events, you know! A lot of them....." Daga haka yayi shiru yana
kallon Junaid da ya kafa masa ido ko kiftawa bai yi, junaid ya sauke ajiyar xuciya
ya shafa kansa a hankali yace "But! Is it treatable? I mean can it be cured?" El-
Ameen yayi murmushi ya dafa sa yace "Of course yes! But it is difficult to predict
how, when, or to what degree someone is going to get better, the major treatment
for disorders are Medication, Rehabilation, psychotherapy, and brain surgery, but
we are only going for Medication and psychotherapy yanxu, by Allah's own grace xa a
dace in'sha Allah" d'an murmushi kawai junaid yayi, El-Ameen ma yayi murmushin yace
"Sai dae kuma kudin da xaka kashe fa ba na wasa bane guy, daina murmushi" wani
murmushin junaid yayi yace "Wannan ba matsala bane, Allah ya bata Lfya" El-Ameen ya
d'aga kafada yace "Gud! But kudin treatment
din nawa fa?" Junaid yace "Thought sai ka gama xaka amshi kudi" El-Ameen yyi
murmushi yace "Ohk let leave it then"
*Haske writers association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

15....

Mikewa junaid yayi yace "Ga abinci a parlor" El-Ameen ya d'an bude ido yace "ba
kace tana parlorn ba" Junaid ya hararesa yace "Me xata xauna yi min, ta tafi tun
daxu" daga haka ya shige bathroom ya bar sa xaune dakin, mikewa El-Ameen yayi ya
isa kofa ya bude yana lekan parlorn, ganin bata nan ya fita, sae da ya kulle kofar
parlon da key sannan ya dawo ya xauna gaban abincin, iya wanda xai ci ya diba, ya
dauki remote yayi powering tv yana ci yana kallo, kwanciya yayi bayan ya gama cin
abincin kan dogon sofa yana kallo, Junaid ya fito daga daki sanye da pyjamas, ya
mika masa wayarsa yace "Ummi na kiran ka" mikewa El-Ameen yayi xaune da sauri ya
karbi wayar ya daga ya kai kunne, daga daya bangaren tace "El-Ameen kana ina ne
Abban ku duk ya ishe ni da kira, what's wrong with you this days baka xaman clinic,
yace tun rana rabon ka da can kuma ni baka dawo min gida ba" Kallon agogo yayi yaga
har goma da rabi ya kwantar da murya a hankali yace "Kiyi hakuri Ummi ina gidansu
Junaid bai da lfya ne, so I have to stay over da naga dare yayi" Ummi tace "Karyar
ka kenan kullum kana gidansu junaid, are you alright Ahmad?" Da sauri yace Ummi ga
junaid din ma ki tambayesa ki ji, yana fadin haka ya mika ma Junaid wayar, junaid
ya karba suka gaisa da Ummi, tace "Wai baka da lfya junaid" kallon El-Ameen yayi
sannan yace "Um Ummi" tace "Toh Allah ya sauwake nayi xaton karya yake min, kace
masa ku kira Abba kuyi masa bayani don yana can ya cika" junaid yayi murmushi yace
"Toh Ummi" daga haka suka yi sallama ya ajiye wayar, El-Ameen yace "Kaga situation
din da ka jefa ni ciki yanxu kai da patient din nan taka ko Captain, kai kullum
baka fashin aiki, sannan baka kai wa bayan magrib baka shiga gida ba ni ko ka barni
ina ta gantali a titi ko da yaushe, na ma daina aikina a clinic kullum safe dare
ina hanyar duba mahaukaciyar ka, look am not taken less than 500k idan na gama
treating din mahaukaciyar nan" Junaid yayi murmushi yace "Sure! Wannan ba matsala
bane I will pay you."
Da asuba tare Junaid da El-Ameen suka fita xuwa masallaci, suna dawowa El-Ameen ya
koma yayi kwanciyarsa ya ci gaba da bacci, Junaid yayi murmushi ganin haka, a
xuciyarsa yace lallai kam sleep well, toilet ya shiga cikin minti ashirin yayi
wanka ya fito ya shirya cikin khakin sa, kamshin turarrukansa ne ya tada El-Ameen,
ya mike xaune yana kallon agogo yace "Wai kai barin gari xaka yi haka da asuba ne
da baxa ka bar mutum yayi baccin safe ba captain, duk ka ishe ni ka hana ni bacci
don xaka aiki" Junaid na saka wristwatch dinsa yace "sorry, go back to ur sleep, ni
yanxu ma xan bar maka dakin" Yana fadin haka ya dauki wayarsa da hularsa ya nufi
kofa, El-Ameen yace "Wait, wai Karfe nawa yanxu?" Junaid yace "6:40" daga haka yace
"May be ka same ni part din Mumy in ka fito da wuri" El-Ameen yayi tsaki shi kuma
yayi ficewarsa. Har El-Ameen ya koma ya kwanta ya mike da sauri tunawa da yayi
akwae alluran da yake ma patient dinsa bakwai da rabi. Toilet ya shiga yayi wanka a
gurguje ya fito, cikin mintunan da basu wuce goma ba ya kintsa cikin blue shirt da
black jeans a closet din junaid, ya feshe jikinsa da turare ya dau wayarsa ya fice
daga dakin, yana isa part din Mumy suka kusa cin karo da Humainah xata fito, ae da
sauri ya sunkuyar da kai ya bata hanya ta bi ta gefensa tayi gaba abunta, ya sauke
ajiyar xuciya ya shiga parlon, ko kallon Junaid dake xaune yana shan tea bai yi ba,
ya gaida Mumy ta amsa tace "ga breakfast dinka can a dinning" yace "A'a Mumy sauri
nake wlh, idan naje office xan yi" Mumy tace "Kan ka daya kuwa, Karfe nawa yanxu da
baxa ka tsaya kayi break ba" kallon agogo yayi yace "Mumy wllh am in a haste ne..."
junaid dake kallonsa yace "Da wannan surutun da yanxu ka gama hada tea" hararan sa
yayi sannan ya karasa kusa da shi yayi kasa da murya yace "look akwae wani
injection da xan ma patient dinka ne b4 7:30, shi yasa nake sauri," da sauri Junaid
ya kalli Mumy dake kallonsu yace " Ohh Mumy ashe emergency aka kira sa ne fa" Mumy
ta tabe baki tace "Kwa ji da gulmar ku ba ruwana" El-Ameen ya d'an yi murmushi yace
"Ko xuwa Karfe goma xan dawo inyi wllh Mumy" Mumy tace "Ka fa rantse" dariya yayi
yace "in'sha Allah Mum" mikewa Junaid ma yayi ya shiga bedroom din mumy ya dauki
kardigan dinsa yasa don garin da d'an sanyi, ya fito yace "Mumy sai na dawo" ta
bisa da kallo kafin ta tabe baki tace "Toh dai kar ka manta ku shiga kuyi wa Hajja
sallama don yau xata tafi, ko Abba ma baku shiga kun gaida ba bare mutan gidan"
Junaid yace "Xamu shiga" daga haka suka fita daga parlon, sae da suka fara shiga
part din Abba suka gaida shi sannan suka yi part din Hajja, tana ta hada kaya,
Humainah na xaune gefenta sai rusa kuka take ita ma da tata jakar a gefenta, Hajja
na mata ruwan bala'i tana cewa tayi kadan ta koma da ita tunda dama ba ita tace ta
biyo ta, xamanta daram a gidan ko suma take, Junaid ya fashe da dariya yana kallon
Humainah, ita ko tana ganinsu ta hadiye kukan ta sunkuyar da Kai kasa, Hajja tace
"Atoh, ka dai gan ni da gantalalliyar nan wae sae ta bi ni Amadi, sae kace ance
mata wahalalla nake kamar irin ni na ce ta biyo ni din nan shegiya, nufin ta in
koma da ita muna galallawa a titi, to dadin abun dai ba kudin banxa gare Muhammad
ba, kuma ubansa Ahmad bae ce yaje xae gani ba bare ya biya kujeru biyu na jirgi"
Junaid ya dinga dariya yana kallon Humainah, El-Ameen yyi murmushi ya gaida ta, ta
kallesa ta gefen ido ta ci gaba da abinda take ba tare da ta amsa ba tana ci gaba
da yi ma Humainah masifa, dariya yayi yana shafa kansa don yasan me yasa bata amsa
ba, Junaid ya ciro dubu talatin da ya tanadar mata dama ya ajiye gabanta yace
"Gashi ni da El-Ameen ki sha ruwa da dabbino a hanya kar ki je kina masu amai a
jirgi" ta washe hakora tana kallon El-Ameen tace "Toh Allah maku albarka, ga kuma
amanar jikata a hannun ku, don mayu sun yi yawa gidan, Amina na damka ma ita,
tamkar yanda xata yi ma fatima xata yi mata" Junaid yayi murmushi yace "In'sha
Allah" Hajja ta kara da cewa "Kuma ga maganin tsari kala kala can na kai ma uwarka
idan taga dama ta baka, ka kuma sanma marowacin abokin nan naka don duniya bbu
gaskiya yanxu, barin kai da kiri kiri matan ubanka ke nuna basa sonka" shi dai El-
Ameen sae kallon agogo yake don bai son lkcn nan ya wuce duk hankalinsa yayi gun
patient dinsa, Junaid yace "Toh Hajja" kallon Humainah yyi ya mike yace "Ae sae ki
dauki jakar ki kai bangaren Mumy" ta fashe da kuka, Hajja tace "Tashi ki ban waje
yar wahala, bbu inda xani da ke ki xauna gidan wan ubanki don shi xaki gani ranan
gobe kiyama" Humainah na kallon Junaid cikin kuka tace "Ya Ahmad kace mata don
Allah ta tafi dani wllh bana son in xauna gidan nan kullum fada ake yi" Hajja tace
"A haka xaki saba ki koya ki iya kema" Junaid ya fice yana dariya ta bi bayansa da
sauri, El-Ameen ya kuma yi ma Hajja sallama ya fice shi ma yana danne dariyarsa wai
kullum fada, sae da suka fito compound Junaid ya kama hannunta yace "kinga ki bari
ta tafi sai in maida ke next week I promise" da haka ya lallabata tayi part din
Mumy tana kuka, Umma na daga balcony dinta xaune haka ma Hajiya kamar masu cin
kasuwa kuma duk don sbda sa ido suke yin haka, ko kallonsu bai yi ba yayi gun
motarsa, El-Ameen ma bai kalli idan suke ba ya bi bayansa, duk suka bi su da kallo
ko wanne da tunaninta a xuciya, El-Ameen ya kwace key hannun Junaid ya shiga driver
seat ya tada mota, Junaid yayi murmushi ya xaga daya side din, yana gama ba motar
wuta ya ja suka har compound din bayan masu gadi sun bude gate, gudu kawae El-Ameen
ke shararawa, Junaid yace "Wae lafiya wannan gudun Ahmad" ko kulasa bae yi ba,
Junaid yace "Look kar kaje ka kashe ni ma uwata a banxa, wannan ae hauka ne are we
flying, plss ka tsaya in sauka" nan ma dai bae kulasa ba sai da ya gansa a kofar
gidansa yana kallon agogo yaga bakwae da minti ashirin, yyi ma junaid wani kallo
yace "you heard me ryt daxu amma" daga haka ya bude motar ya shiga gidan, Junaid ya
kalli agogo ganin da sauran time ya fito ya nufi cikin gidan shi ma, bbu kowa
parlon sai kamshi dake tashi Mama Jummai ta tsaftace ko ina, daki El-Ameen ya nufa,
ya tsaya daga bakin kofa bayan yayi sallama yana kallonsu, tana xaune gefen gado
Mama jummai na packing mata gashinta, ta gama shiryata tsaf cikin doguwar rigar
kanti sea green da stones gold colour a jiki, tun daga nesa kana iya ganin white
eyeballs dinta sbda uban kwallin da mama jummai ta sa mata, wanda hakan ya kara
fito da kyan idanuwan nata, kallonta kawae yake sannan ya shigo dakin, Mama jummai
na murmushi ta gaida shi tace "Na ma yi xaton baxa ka xo yau ba ganin har lkcn
xuwan ka ya wuce" murmushi yayi yace "Na makara ne mama" ta mike daga durkushen da
take tace "Bari in hada mata abinda xata ci" daga haka ta fita, ya karasa kusa da
ita ya duka yace "Morning" kallonsa kawae take, sai kuma ta dauke kanta, mikewa
yayi da sauri tuna lkci na wucewa ya nufi gun alluranta, cikin few minutes ya hada
alluran yayi mata, xuwa yanxu ta fara hakura ta tsaya yayi mata alluran ba gardama,
dagota yayi suka fita daga dakin yana rike da hannunta, Junaid na xaune parlor suka
sauko ya bi su da ido, tsakar parlon El-Ameen ya xaunar da ita kan rug, Mama jummai
ta fito daga kitchen rike da bowl din pap tace "Kaga jiya da rana na dama kunu ina
sha naga tana tana kallonsa sai na bata ae ko tasha, kuma da yawa ta sha, shiyasa
ma yanxu nayi mata" El-Ameen yace "Ohk" xaunawa Mama Jummai tayi kusa da ita ta
fara bata, sau biyu ta sha ta fara kokarin amshe spoon din hannunta, shi dai Junaid
kallonsu kawae yake, El-Ameen ya karbe spoon din hannun Mama jummai ganin ta dage
sai ta karba yana mata wani irin kallo, lkci daya ta nutsu, da kansa ya shiga diban
pap din yana kai mata baki tana bude bakin tana amsa, Mama jummai tayi murmushi ta
Mike ta bar parlon don xuwa ci gaba da aikinta, cokali hudu kadai ta karba ta dauke
kai, ya hade rai ya dafa kanta ya kai mata pap din spoon din baki, da kyar ta bude
bakin ya xuba mata tayi saurin maido shi spoon din, wani tsawa ya mata, lkci daya
jikinta ya dau rawa ta bude baki ya kuma maida mata ta hadiye, sake diban wani yayi
ya bata taki karba yace "I will slap you fa" bata fuska tayi tana komawa baya a
hankali, murmushi yayi yana kallonta, sai kuma ya lumshe ido ya kai kunun bakinsa
ya sha, da sauri ya bude ido ya juya yana kallon junaid yaga kallonsa kawae yake.
Jefar da spoon din yayi cikin pap din duk ya daburce yace "I I didn't even realize
wat I was doing faa, hankali na duk baya wajen" ya runtse ido yana yamutse baki da
fuska yace "So irritating" Junaid ya tabe baki ya mike ya dau wayarsa da makullin
motarsa dake ajiye kan kujera ya fice daga parlon, El-Ameen ya bi sa da kallo, ita
ko daukar spoon din tayi ta juya shi upside down cikin pap din ta debo ta Kai masa
baki, murmushi yayi yana kallonta ya kauda Kai, ai ko ta xuba masa a kan hanci ta
kuma debo wani xata kai hancin ya rike spoon din yana dariya yace "Keee" kokuwa
suka shiga yi ita fa sae ta sa masa a hanci ta wani hade rai, da sauri ya bude baki
sae ta xuba masa d'an kunun da ta debo ciki, ya lumshe ido ya shanye Sannan ya
dauke bowl din ya boye a bayansa, xata mike ya komar da ita ya xaunar yace "C'mon"

*Haske Writers Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

16.....

Mama jummai ta shigo palon rike da bucket tace "Har ta shanye?" Yace "A'a barnatar
da shi xata yi shi yasa na boye, ta koshi kuma" mikewa yayi ya dauke bowl din yace
"Xan tafi yanxu, sai na dawo anjima mama" ta karba bowl din tace "Toh Allah ya
tsare" daga haka ya ja dogon hancinta yayi hanyar kofa, mikewa tayi da sauri ta bi
bayansa, Mama ta saka dariya tace "Au, toh gashi xata bi ka" juyawa yayi da sauri
yana kallonta ya galla mata harara yace "I will knock you idan kika xo nan" kamar
ta ji me yace ta tsaya tana cixgar stones din rigarta tana kallonsa, ya juya ya
fice daga parlon, mama jummai ta karaso ta kama hannunta suka koma cikin parlour'n.
El-Ameen na fita ya rike waist a waje tunawa da yayi ai ba mota kuma bbu kudi
hannunsa, tsaki yayi ya nufi main road da kafa ya tsayar da adai daita ya gaya masa
anguwarsu, suna isa yace yana xuwa sannan ya shiga ya fito masa da kudi ya basa ya
koma ciki, Ummi dake parlor sai binsa da kallo take bayan ta amsa gaisuwarsa tana
ganin ya nufi daki tace "Xo nan Ahmad" komawa yayi ya xauna kasa yana kallonta yace
"Gani Ummi" tace "Ina kake xuwa this dayz baka xaman office?" Ya d'an sosa kai
yace "Ummi, dama... To wai Ummi wa yace bana xama office ni da kullum sai na je
clinic" Ummi ta galla masa harara tace "Am not joking Ahmad, wannan sabon salon da
ka tsiran ma rayuwarka ba fishshe ka xai yi ba don b'ata ma mahaifin ka rai kawae
kake" ya sunkuyar da kai bai ce komai ba, Ummi tace "Magana ta biyu kuma tunda kai
ka kasa fito da mata toh ni na xabar maka...." Da sauri ya D'ago kai yace "Ummiii!"
Tana masa mugun kallo tace "Ehh, ni ma xan rakaka gidansu yarinyar da kaina in ma
ya kama ni xan maka maganar sai inyi, kuma ba wata bace facce 'yar abokin Abban ka
Fiddausi" wani xufa ne ya shiga keto masa duk ya ma rasa abinda xae ce, da sauri
yace "Ummi ni fa na riga da na samu yarinyar da nake so" Ummi na hararansa tace
"Wannan kuma ba matsala ta bace, sai dai kuma ka raina ma kanka hankali ba ni ba"
ya marairaice mata yace "Ummi Allah kuwa da gaske, a gidansu junaid ma take" Ummi
tace "Wacece kenan?" Yayi kasa da kai a hankali yace "Humainah take ko wa? kuma
niece din Junaid ce" Ummi tayi shiru tana hararansa yace "Allah kuwa Ummi, naji
kamar ina sonta" tace "Toh ae xanje gidansu junaid din kuwa" bai kuma cewa komai ba
sai tunani yake anya gskya ya fadi ma Ummi kuwa, can dai ya mike yace "Bari in tafi
office Ummi", tace "Allah ya tsare"
Karfe Hudu saura Junaid yayi parking kofar gidan El-Ameen ya fito, ya koma back
seat ya cire hularsa ya ajiye da rigar khakinsa ya dauki well ironed shirt dinsa
dake bayan mota don bae rasa mofti a motar ya saka sannan ya fito ya shiga gidan,
Mama jummai na share parlor ita kuma tana tsaye jikin bango kamar xata shige ciki,
Mama jummai tayi masa sannu da xuwa, ya amsa tare da gaisheta hankalinsa na kanta,
Mama jummai tace "ka ganta can tafi awa biyu tsaye taki xaunawa" murmushi yayi ya
karasa inda take tsaye, ya kama hannunta suka dawo parlorn ya xaunar da ita, ya
rike chin dinsa da duk hannunsa biyu yana kallonta ita ma kallon nasa take, fine
beard din da ya xagaye bakinsa ta kai hannunta ta taba, yayi murmushi ya kama
hannun cikin nasa yana kallon manyan fararen eyeballs dinta cikin sanyin murya yace
"I will call you Jasmine! Do you like dat?" Kwace hannunta tayi daga nasa, ya tsura
mata ido, bude kofar parlor aka yi El-Ameen ya shigo, ae tana ganinsa ta mike da
sauri ta nufesa ta isa gabansa ta tsaya, Junaid ya bi ta da kallo, El-Ameen ya ja
hancinta ya bude hannayensa yace "toh dai bbu abinda na siyo maki" kallon junaid
yayi yace "The great Capt Ahmad Junaid ashe kana nan" mikewa junaid yayi yace
"Sure!" Daga haka ya nufi kofa, El-Ameen yace "ba dai har xaka tafi ba" junaid yace
"Yea daga office nake" daga haka ya fice daga parlorn, bin sa da wani irin kallo
El-Ameen yayi kafin ya fita yayi saurin cewa "Hey a minute" junaid ya tsaya sannan
ya juya yana kallonsa, El-ameen yace "gaskiya ya kamata ka shiga kasuwa ko kuma ka
bada kudi a shiga a sama mana TV a gidan nan, ko ka mance yanda muka yi da kai?"
Junaid yace "I will transfer the money later sae ka samu me siyo maka TVn" yana
gama fadin haka ya fice daga palon, El-ameen ya d'aga kafada ya kama hannunta suka
koma parlor.

As usual ya dade xaune mota bayan yayi parking a lot din gidansu kuma har lkcn bae
kashe mota ba yana danne dannensa a waya, Khadija ce ta fito daga part dinsu ta
karaso gun motar ta bude tace "ina yini yaya A.jay" ya kalleta yace "Lafiya lau" ta
d'an marairaice masa tace "yaya yau ciwo ciki na ke min wllh" tabe baki yayi ya ci
gaba da danna wayarsa, ta dan shagwabe masa tace "Yaya ka d'an ban kudi in siya
magani mana, Umma ta ki bani" dubu daya ya xaro aljihunsa ya mika mata cike da
murna tayi masa godiya ta kara gaba, shigowar motar Suhaima yasa shi kashe motarsa
ya fito ya rufe ya fara tafiya, Hajiya ce suka fito daga part din Umma da wata mata
alamar rakiya xa su mata, duk suka bisa da kallo, ba tare da ya kallesu ba ya gaida
su don dama sai lokacin da yayi suit dinsa yake gaishesu, matar ce kadai ta amsa
shi, bae damu da haka ba yayi part din Mumy, Matar da ta bisa da kallo ta maido da
dubanta gun su Umma murya can kasa tace "Shine yaron hala?" Cike da tsanarsa Hajiya
tace "Ehh wllh" matar tayi wani murmushi murya can kasa tace "Duk ku kwantar da
hankalin ku, ku bar min komai a hannu na baxan baku kunya ba" babu wanda yace komai
cikinsu suka rakata har waje gun motar ta. Junaid na shiga parlon Mumy ya tarda
Humainah kwance da ganinta kasan ba kuka kadan tayi ba, dariya ya saka yace "ohh
shikenan an bar mana ita" mikewa tayi xaune idon ta ya cicciko ta kwalo ma Mumy
kira, Mumy ta fito daga daki tace "be careful Mr" dariya yayi yana shafa kai yace
"Ya hakuri Mumy, ina yini" ta karaso parlorn tace "Nayi xaton ae baxa ka kashe
motar ka shigo gida ba" yyi murmushi yace "Ac fa nake sha Mumy" ta tabe baki tace
"Haka ne, ga abincin ka can" kujera ta xauna tana kallon Humainah tace "Kema kije
ki dau naku abincin ke da fatee, ko baki hakura ba har yanxu" bata ce komai ba tayi
kasa da kai, Junaid ya mike yace "Xan dawo Mumy bari inyi wanka" tace "Ohk," bin sa
da kallo tayi sae da ya kai bakin kofa tace "Canxa kaya kayi office" murmushi kawae
yayi ya fita. Wanka yayi ya kuma canxa kayan jikinsa yyi kwanciyarsa parlor don bai
jin yunwa, ya kusa awa daya kwance Humainah ta shigo parlorn rike da tray dauke da
abincinsa, ta karaso ta ajiye masa, ya mike xaune cike da xolaya yace "Shikenan
fatima ta huta an kawo mana maid kyauta" mikewa tayi a fusace xata fita ya rikota
yana dariya yace "Ke dalla wasa nake maki" ta fixge hannunta tace "Bana son wasan"
ya daga kafada yace "Ni kuma sai nayi din" wani kallo ta shiga yi masa fuska daure,
ya hade rai yace "Toh in kince a biya ki kudin aikin ba sai a biya ki ba ma" hawaye
ya cika idonta ta juya xata fita aka bude kofa El-Ameen ya shigo da sallama, da
sauri ta kuma juyawa tana kallon Junaid da ya bude ido ganin El-Ameen da ya kasa
Karasowa cikin parlorn, Junaid ya mike yana dariya yace "C'mon ka karaso frnd" El-
Ameen yace "Um ban gaida Mumy ba am coming" da sauri junaid ya karasa ya rufe kofar
da key ya cire sannan yace "ba ta kofarta ka wuce ba kafin ka karaso nan" El-Ameen
ya ma rasa me xai ce masa, dawowa cikin parlorn junaid yayi ya xauna yana kallon
Humainah yace "Toh ae sai ki goge hawayen yanxu tunda ga shi ya xo koh, duk kin
isheni kin daga min hankali ina El-Ameen toh ga ki ga shi" Humainah tayi wani kara
ta durkushe wajen ta shiga kai masa duka tana cewa "ni bana son haka ya Ahmad, bana
so" El-Ameen yayi murmushi ya nufi daki, da sauri Junaid ya mike ya rigasa shigewa
dakin ya saka key daga ciki yace "Ji min munafukai" gajiya yayi da tsayuwa ya dawo
parlorn, can nesa da ita ya xauna yace "Ina yini" ta d'an kallesa ta hade rai tace
"Lfya lau" bai kuma cewa komae ba ya dau remote yayi powering Tv, sun kusa minti
talatin parlorn bai ce mata ba bata ce masa ba, kamar wanda ya tuna abu ya mike da
sauri yana kallon agogo ya nufi dakin junaid ya kwankwasa yace "Look captain akwae
drugs din da xanje in ba patient dinka open the door plss ka bude kofar parlor am
leaving" junaid dake kwance ya fara bacci ya mike jin abinda El-Ameen yace ya bude
kofar, El-Ameen yace "D'an rainin wayo bacci ma kake koh" fitowa junaid yayi suka
dawo parlor a tare, kallon Humainah yayi yana murmushi yace "Har kun gama xancen
kanwata" ta hararesa ta dauke kai, shi kam El-Ameen har ya kai kofa, Junaid yace
"toh dai ki ajiye abinda ya baki idan na dawo mu raba, kuma ki d'an gyara min
bedroom saura ki min satan turare ki ga ko ba na saurayin ki xan je in sace ba"
yana fadin haka yyi kofa ya bude ya fice yana dariya, El-Ameen ma ya fita, Part din
Mumy suka shiga El-Ameen ya gaida ta, Junaid yace "Xan d'an rakasa indawo yanxu
Mumy" Mumy tace "Toh sai ka dawo" daga haka suka fice da El-Ameen. suna isa El-
Ameen yace "Baka yi min transfer din kudin Television din ba fa, if you provoke me
xan fa je in siya da kudina" Junaid yace "I forgot xan yi" fitowa suka yi daga
motar suka shiga gidan, Mama jummai na xaune parlor ta daura kanta kan cinyarta
idonta rufe, El-Ameen yace "dama tana bacci ba da daddare ba" Mama jummai tace "Ina
jin bata jin dadi ne yau, sau biyu tana amai ga jikinta da dumi, ita da ko xama
bata yi da rana bare ta kwanta" El-Ameen ya karasa ya durkusa gabansu ya d'ago
kanta ta bude ido tana kallonsa, ya gyara mata gashinta a hankali yace "Malaria...
I guess" xaunawa Junaid yayi shi dai bae ce komai ba, El-Ameen ya d'agota ya xaunar
da ita kan kujera yace "Sorry...." Ya kalli Junaid yace "Ka bada kudi in tafi in
siyo mata drugs da injections" kallonsa kawai Junaid yake bai ce komai ba, El-ameen
ya kalli mama sannan ya kallesa ya juya xuwa harshen turanci yace "It's not a
matter of looking at me dat way captain, don't forget she's ur patient, ur mind
agreed to the terms nd condition of helping her, nd I guess before u jumped into
the conclusion of doing dat, you already know...." Katse sa junaid yayi yana masa
wani kallo yace "did you hear me complain?" El-ameen yayi dariya yace "Not dat I
don't have the money to assist you but...." Tsaki Junaid ya ja yace "Enough plss, I
don't even need ur goddam help," El-ameen yayi murmushi yace "Ni kuwa kake bukatar
taimakona, cos lokacina da na ware for her is far far better then dat money you are
spending, anyway! 20k will do for the test nd everything" Atm junaid ya ciro ya
mika masa ya karba, ya mike ya haura sama syringe ya dauko a daki da plastic tube
na drip ya dawo parlon, da kyar ta bari ya debi jininta don sae da Mama jummai ta
riketa, ya mike yace "Bari in je in dawo yanxu, Mama ki d'an bata kunu ko kadan ne
ta sha" Mama tace "Toh" sannan ya fita daga parlorn, xamowa tayi daga jikin mama ta
kwanta kasan tiles, mama ta d'agota tace "Sannun Kinji Baiwar Allah, Allah ya
sauwake maki" kara ta saki alamar bata son tashi a kasan, Mama ta kyaleta ta tafi
kitchen, mikewa Junaid yayi ya isa gabanta ya durkusa, kallonsa kawae take kafin ta
kauda kanta, ya d'agota a hankali yace "Sorry Jasmine, get well soon" mikewa tayi
ta kwace hannunta a nasa ta fara tafiya, ya bi ta da kallo ganin yanda take tafiya,
can jikin bango taje ta tsaya, ya mike ya koma kujera ya xauna, har mama ta fito
kitchen rike da pap bata bar jikin bangon ba, Mama ta ajiye bowl din hannunta ta
karasa ta kamo hannunta, da kyar ta biyota suka dawo parlor ta xaunar da ita ta
shiga bata kunun amma taki sha, da ta takurata mikewa tayi ta dawo kusa da junaid
ta xauna gefen shi ta jingina jikinsa ta rufe ido gam, duk tayi wani laushi da
ganinta kasan bata da lafiya, shi kam kallonta kawae yake wani tausayinta ya dinga
ji, ya ji dama ciwon ya dawo jikinsa, ya rungumota jikinsa a hankali yace "Sorry My
Jasmine" mikewa mama tayi ta mika masa kunun tace "Toh ka bata Junaid kila ta karba
ko kadan ne" yyi murmushi ya karba ya janyeta daga jikinsa ta bude ido tana
kallonsa, ya debi kunun kadan ya kai mata baki, ta kauda kai da sauri, rasa yanda
xae yi ya bata yayi, kawae ya ajiye, ita ko ta sauka kasa ta kwanta, bayan minti
goma El-Ameen ya shigo parlorn, ya ajiye ledan hannunsa ya d'agota yana kallon
junaid yace "Ta sha kunun" girgixa masa kai kawai yayi, El-Ameen ya jawo bowl din
kunun ya debo ya kai mata baki, ta kauda kae da sauri, ya hade rai yace "I will
knock you, c'mon bude baki" kara ta saki ya xuba mata kunun a baki ta xubar da
sauri, ya daka mata tsawa, nan da nan jikinta ya dau rawa ya debi wani ya bude
bakin ya xuba mata, da kyar ta hadiye hawaye na sakkowa idonta, Junaid ya jinginar
da kansa jikin kujera ya lumshe ido, haka El-Ameen ya dinga bata tana karba da kyar
har tayi four spoon sannan ya ajiye, ya fara hada drip da xai sa mata da alluran da
xai mata, ita ko kwanciya tayi kan tiles ta rufe ido, yana gama hada alluran ya
D'ago ta ta bude ido, gown din jikinta ya d'aga don a lap xae mata alluran, kallon
junaid yayi yaga idonsa na kansu, da sauri junaid ya kauda kai, El-Ameen ya kwantar
da ita yayi mata alluran, tun bai gama ba ta fara kokarin mikewa, duk jikinta yayi
xafi ba kadan ba, ya maidata ya kwantar har ya gama sannan ya dagota yace "Sorry"
komawa baya kawae take hawaye na xuba idonta, El-Ameen ya d'an yi murmushi don
hawayen shaidar wataran xata dawo me hankali ne sai dai fatansa daya kar tayi
loosing memory dinta, kusa da junaid ta koma ta xauna gefensa ta daura kanta a
kafarsa ta rufe ido, yana son ya lallasheta duk da yasan ba gane nufinsa xata yi ba
amma bae son yin hakan gaban El-Ameen ya ya kafa masu ido, hakan yasa ko kallonta
bai yi ba, El-Ameen yayi murmushi ya mike ya nufi kitchen don dauko cup yyi mata
diluting drugs ya bata ta sha, Junaid ya kai fuskarsa dai dai nata a hankali yace
"Sorry Jasmine...." Ta bude idonta da suka sauya launi tana kallonsa, da sauri ya
D'ago jin fitowar El-Ameen, ko kallonsu bai yi ba yi diluting drugs din da ruwa ya
dawo kusa da su ya xauna ya dagota yace "Tashi ki sha magani" kara ta saki ta boye
fuskarta jikin junaid tana shishshige masa kamar xata shiga jikinsa, El-Ameen ya
mata wani tsawa, jikinta na rawa ta rike Junaid tana ihu, janyeta El-Ameen yayi ya
hade rai yace "Keehh" cup din ya kai bakinta ta ki budewa, ya mata wani rankwashi
ta
kwala ihu, da sauri ya jawota ya juye maganin bakinta ya rufe hancinta, sae da ya
tabbatar ta shanye su gaba daya sannan ya cire hannunsa hancinta, lkci daya duk ta
amayo maganin jikinsu gaba daya su ukun, daga nan ta dinga amai gashi bata ci komai
ba, El-Ameen ya mata wani tsawan da ya rikitata ta fasa ihu xata mike ya fixgota da
karfi ta fado kansa ya rungumeta tsam jikinsa, sunkuyar da kai junaid yayi jin wani
abu da bae taba ji ba a xuciyarsa a lkcn, a hankali ya shiga cire shirt din jikinsa
da ya baci da amai, Mama jummai dake tsaye daga bakin kofa cike da tausayinta taji
kamar tayi mata hawaye duk ita ma jikinta yayi sanyi, mikewa junaid yayi har lkcn
bae kallesu ba ya haura sama, El-Ameen ya bi sa da kallo, a hankali ya d'ago kanta
jin ta sakar masa jiki gaba daya ya ga bacci tayi, kamar me rada yace "Jewel!" A
hankali ta bude ido tana kallonsa.


*Haske Writers Association*馃挕
� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

17.....

El-Ameen ya sakar mata murmushi murya can kasa yace "Sorry!" kauda kai tayi, ya
mike ya d'agata suka tafi sama, bin bayansu mama jummai tayi, yana shiga daki ya
xaunar da ita gefen gado ya xauna gefen gadon shi ma yana cire shirt din jikinsa
Junaid ya fito daga bayin rike da shirt dinsa da ya wanke, ko kallonsu bai yi ba ya
fice daga dakin El-ameen ya bi sa da kallo, yana sauka downstairs ya dau makullin
motar El-Ameen ya fice daga gidan. Gida ya tafi, yana gama parking ya fito rike da
shirt din nasa ya nufi part dinsa, su Hajiya dake xaune tsakar gidan suka bi sa da
kallo ganin daga shi sai singlet da jeans, bae ko kallesu ba ya bude kofa ya shiga
parlornsa ya rufe, kallon juna suka yi tare da tabe baki, bathroom Junaid ya shiga
ya sakar ma kansa warm shower, ya fito daga karshe ya shirya cikin jallabiya duk
jikinsa ba kwari ya kwanta har lkcn bae ji xuciyarsa ta dawo dai dai ba. Kiran
magrib yasa shi mikewa ya fita xuwa masallaci, Yana dawowa mosque ya shiga part din
Mumy, Humainah ce kadae xaune parlor tana kallo, ya xauna fuskarsa daure yace "Mumy
fa?" Ta tabe baki ta dauke kai, bae kuma cewa komai ba har Mumy ta fito tace "Har
ka dawo" ya shafa kansa a hankali yace "Eh Mumy" tace "ga abincin ka can, na daxu
ma baka ci ba sai dawo da shi Humainah tayi" xae yi magana aka bude kofa Sadiya ta
shigo ta tsaya daga bakin kofa tana taunar cingam tana kallon Mumy tace "Wae Abba a
kira ki!" Mikewa junaid yayi yace "Ke don uwar ki baki iya sallama bane xaki shigo
ma mutane parlor kamar dabba" Mumy ta hade rai tace "Ahmad!" Wani mugun kallo yake
mata xuciyarsa na tafarfasa, ita ko ta tabe baki ta kauda kai tana murgurda baki,
wani tsawa ya mata ya nufeta Mumy ta fixgosa tace "Xan saba maka wllh Ahmad, kana
da hankali kuwa" Sadiya tayi tsaki ta fice daga parlon fuu, cikin bacin rai yace
"Mumy ko gaisheni fa 'yar iskar nan bata yi a gidan nan yanxu, ni din sa'anta ne"
Mumy tace "Sae me don bata gaishe ka ba, uwar me gaisuwarta xae kara maka, ko da
can gaishe kan take idan ba gulma ba, kaje an bata maka rai a waje xaka xo ka huce
ma mutane a gida, ina raba ka da mutanen nan baka ji koh Ahmad, dole ne sae ka
tanka duk abinda suka yi" shiru yayi bae ce komai ba ya koma ya xauna ya rike kansa
don shi kansa bai san me yasa yayi hakan ba, he just don't know what came over him,
don da can ma ba gaishesa step sis din tasa take ba kuma bai taba ce wa komai ba,
Mumy tayi kwafa ta dau hijab dinta ta fita. dawowa kusa da shi Humainah tayi ta
xauna kasa a hankali tace "Kayi hakuri ya A.jay, nima daga yau baxan sake gaisheta
ba, shikenan na rama maka" kallonta kawae yake bai ce komai ba, sai kuma ya
jinginar da kansa jikin kujera ya lumshe idonsa, ta bata rai tace "Shine ka min
shiru koh" ba tare da ya bude idon ba yace "Anki maki maganan, ke din gaishe ni
kike?" Mikewa tayi ta take kafarsa ta nufi daki tana cewa "Idan ba sai na gaisheta
ba gobe me nake!" ya bude ido da sauri ya bi ta da kallo yana murmushi, Bayan kusan
minti talatin Mumy ta dawo parlor, junaid ya mike ya dawo gefenta ya xauna a
hankali yace "Kiyi hakuri plss mum I don't know what came over me, baxan sake ba
wllh" tace "It's ohk" daga haka bata kuma cewa komai ba shi ma haka, bayan kusan
minti goma yace "Mumy fushi kike da ni I know, don Allah kiyi hakuri plss" ta
girgixa kai cike da takaici tace "uhn naxari kawae nake ne Ahmad, kaji inda yan
gidan nan suka kuma bullowa wae duk me girki shi xae yi girkin gidan gaba daya
yanxu, sae kace da can basu suka ce kowa yayi nasa ba, ko me suke nufi da hakan
kuma oho" junaid ya d'aga kafada yace "Sai su ci kayansu ai, don ni baxan ci
girkinsu ba" daga haka ya mike ya nufi dinning, Mumy tayi murmushi a xuciyarta tace
"Ae dama baxan ma bari kaci abinda ya fito daga bangarensu ba idan Allah ya yarda"

Kwata kwata Junaid bai runtsa daren ranan ba ya rasa dalili, sae dai yafi danganta
haka da tausayin baiwar Allahn da yake, Washegari Wednesday bai yi wani breakfast
din kirki ba ya fita as early as 7, tun daren jiya El-Ameen ke kiransa baya dauka,
a hankali yake driving ya kalli wrist watch dinsa yaga bakwae da minti goma, ganin
yana da sauran time yasa shi nufan gidan El-Ameen, a waje yayi parking ya shiga
gidan, kwance ya tarda El-Ameen a parlor yana bacci kan 3sitter, Mama kuma na
kitchen, ya kusa second ashirin tsaye yana kallonsa sannan ya tabe baki yyi hanyar
stairs, a hankali ya tura kofan dakin ya ganta kwance kan gado cikin bargo, ya
karasa cikin dakin yana kallon empty roban drip din da aka cire mata, gefenta ya
tsaya ya yaye bargon jikinta, ya tsura ma fuskarta ido, Ya fi minti biyu yana
kallonta tana bacci, ya daura hannunsa a hankali a forehead dinta ya ji da d'an
dumi, bude ido tayi da sauri ta mike xaune, kallonsa take ko kiftawa bata yi, lkci
daya ta saki wani kara ta shiga komawa baya tana ihu da karfi, ya koma baya da
mamaki yana kallonta, El-Ameen ne ya shigo dakin da sauri, ya tsaya daga bakin kofa
ganin Junaid a dakin, sauka tayi daga kan gadon tayi kofa da gudu xata fita tana
ihu har lkcn, El-Ameen ya fixgota yace "Keeh Meye haka!" Ihu ta dinga yi xata kwace
kanta tana yi tana waigan Junaid, El-Ameen ya kalli Junaid yace "Ohhh it seems
Khakin nan naka ke tsoratata fa Captain" Junaid ya juya yana kallon kansa a madubi,
farin well ironed navy shirt ne jikinsa, well tucked in cikin navy blue trousers
dinsa, sae hat dinsa a kai, sae black socks din dake kafarsa don ya cire takalmin a
waje, juyawa yayi ya fice daga dakin, sai a sannan tayi tsit sai dai har lkcn
jikinta rawa yake tayi lamo jikin El-Ameen, El-Ameen yayi dariya yace "Toh fah"
xaunar da ita yayi gefen gado yana kallonta yace "That's intresting! kina tsoran
soldiers kenan!" Kauda kai tayi ta xamo kasa ta kwanta, mikewa yayi yana kallon
agogo, da sauri ya fita dakin ya sauko parlor sai dai bai ga junaid ba, ya kalli
Mama dake shara yace "Mama junaid din ya tafi ne?" ta washe baki tace "Anya ya
tafi, kaga makulli can ya ajiye kan kujera, ashe sojan ruwa ne yau na gansa da
khaki" Dariya El-Ameen yayi yace "Ehh Navy ne" tace "Allah sarki, khakin sun masa
kyau" kallon Makullin yayi yaga ta motarsa ce, ya d'an tabe baki ya karasa ya dauka
yace "D'an rainin wayo" fita yayi don ganin ko motar tasa na waje yaga bbu motar
makullin kawai ya kawo masa, girgixa kai yayi ya koma cikin gidan. Junaid na kwance
parlor da yamma b4 magrib yana danne dannen waya, khadija ta shigo parlorn,
Karasowa tayi ta xauna gefensa tace "Ina yini ya A'jay?" Yace "Lfya lau, kar ma ki
fara tambayata kudi don bani da" dariya tayi tace "Kai yayana" sai kuma ta d'an yi
shiru, a hankali tace "Kasan me yaya, karka ci abincin gidan nan yau, just go out
and get somethin to eat ae kasan yanxu an daina girki daban daban koh" yana
kallonta yace "Why!" Ta daga kafada tace "Just, beside ma porridge ne kuma ae bama
ka ci" mikewa tayi tace ina xuwa, ta fice daga parlon, ya bi ta da kallo yana
murmushi. Wayarsa ne ya soma ring ya duba ya ga El-Ameen ke kiransa, sai da ya kusa
katsewa sannan ya daga ya kai kunne bai ce komai ba, daga daya bangaren El-Ameen
yace "You try fa captain, nine ban san dadin gidanmu ba ko, how on earth xaka dinga
bari na ni kadai ina fama da patient din ka?" Junaid ya tabe baki yace "Naga tana
tsorona ne, kai ne bata tsoro dat's why I decided not to show up today" El-Ameen
yayi tsaki yace "Didn't you see dat uniform dinka ke scare dinta, wear mofty while
coming always, yanxu dai I will text u some drugs da xaka siyo idan kana tahowa,
and ka siyo mata fruits taki cin abinci" Junaid ya kuma tabe baki ya katse wayar ya
ajiye. Kallon agogo yayi yaga an kusa magrib, ya mike ya shiga toilet ya dauro
alwala sannan ya fito ya dau makullin motarsa da Atm sae wayarsa ya fita ya rufe
kofarsa. Bangaren Mumy ya fara shiga, yana kallon fatima dake guga yace "Mumy fa?"
Tace "tana bayi" juyawa yayi ya tafi masallaci, ana idar da sllh ya dawo gida, Mumy
da fitowarta daga kitchen kenan tace "Ga abincin ka a dinning can" kallon dinning
din yayi yace "Porridge?" Mumy tace "Shi kake so?" Girgixa mata kai yayi yace "No
khadija ce tace min porridge aka yi" Mumy tace "Ehh amma kai na maka girkin ka
daban" yace "Toh nagode Mum, but xan d'an fita yanxu idan na dawo xan ci" tace
"Fita kuma? Ina xa ka?" Yayi kasa da murya yace "xan d'an raka El-Ameen wani gun
ne, daga can xa mu je kallon kwallo" ta tabe baki tace "Xa dai ku je tadi koh?"
Dariya yayi yace "A'a fa Mumy" murmushi tayi tace "Toh kar dai ka wuce 8:30 a waje,
ka ma shiga gun abbanka kuwa" yace "Ehh daxu na shiga" daga haka ya juya xai fita,
Humainah tace "Ya Ahmad xan raka ka" yace " Nooo" daga haka ya fice daga parlon,
Mumy tayi dariya tace "Ki bari ran lahadi ya xaga da ke katsina" tayi murmushi tace
"Toh Mumy, ko yace A'a kiyi masa masifa sai ya kai ni" sae da junaid ya fara siyan
abubuwan da El-Ameen ya ce masa ya siya ready made din fura da nono sannan ya nufi
gidan, Mama kadai ce kwance parlor kan darduma, ya gaisheta ya bata nata fruits din
da fura tayi ta masa Godiya yayi murmushi kawai ya haura sama. Xaune ya samu El-
Ameen yana danna laptop, ita kuma tana tsaye can jikin bango ta jingina, El-Ameen
yace "Sae da ka ga dama kenan" Junaid bai tanka sa ba ya ajiye ledan hannunsa ya
xauna gefen gado, El-Ameen ya ya juya yana kallonta yace "Ba dai baki ji ba, wait
in tashi xa ki ga abinda xan maki a wajen nan" Junaid ya kallesa kafin ya girgixa
kai a xuciyarsa yace ae Kaine mahaukacin ma, takowa tayi ta karaso kusa da ledan da
junaid ya ajiye ta durkusa, El-Ameen ya daka mata tsawa yace "c'mon ance maki naki
ne" mikewa tayi da sauri, Junaid ya dauki ledan ya mika mata ta karba, El-Ameen ya
mike tana ganin haka ta sake ledan ta koma jikin bangon da take, dariya yayi yana
kallonta yace "kai! Yarinyar nan ba dai tsoro ba" shi dai Junaid ko kallonsa bai yi
ba, Karasowa yayi ya dau ledan ya bude ya fito da bunch din Ayaba ya mika mata, ta
karaso da sauri ta karba, xata juya ya fixgota ya xaunar da ita gabansa, da kansa
ya shiga bude mata ayabar yana mika mata, tana karba tana ci, ana uku ne taki ci,
ta kalli Junaid dake danna wayarsa sae dae gaba daya hankalinsa na kansu, ta matsa
kusa da shi a hankali ta kama hannunsa ta sa mashi Ayaban, tabe baki El-Ameen yyi
ya kuma bare mata wani ta karba ta kuma kama hannun Junaid ta basa, El-ameen ya
hade rai ya kuma bare wani ya bata xata ba Junaid yayi mata tsawa, a tsorace ta
juyo, yace "I will knock you yanxu, ina shan wahala ina bare maki abu kina kyauta
da shi, da xan bar ki yanxu da peel din xaki hade ki cinye," kafa masa manyan
idonta tayi ko kiftawa bata yi, junaid yayi murmushi ya girgixa kai, wayar El-Ameen
ne ya fara ring ya dauka, xaro ido yayi ganin Abbansa ne ke kiransa, ya kalli
Junaid yace "Kasan kuwa ban je clinic throughout yau ba" ko kallonsa Junaid bai yi
ba, ya daga a hankali ya kai wayar kunne, daga daya bangaren Abban nasa yace "ka
taho clinic ka sameni yanxu Ahmad, clear?" yayi kasa da kai yace "Toh Abba" daga
haka ya ajiye wayar yana kallon Junaid yace "Look! Xan je clinic yanxun in dawo,
wait har sai na dawo don't go plss, kaga bata da lafiya karfin hali kawae gareta
she just finished vomiting kafin ka shigo, dats why nake nan har yanxu, am giving
her her drugs before leaving yanxu" Junaid ya xaro ido yace "Idan Mumy ta kira ni
fa, beside 8:30 tace in dawo gida, nd this is almost 8 o clock" Kallonsa El-Ameen
ya tsaya yi sae kuma ya girgixa kai yace "Tashi ka tafi toh, wato nine bansan
darajan parent dina ba koh Captain, nine na iya karya kai baka iya ba, you know am
doing this goddam job for ur sake if you provoke me wllh sae in fasa kawai ka kaita
asibiti, kullum safiya sai na xo nan sbda drugs dinta da injections, at mid day ma
I have to leave whatever i am doing in xo nan bata magani, haka da yamma ma, sannan
da daddare bana barin gidan nan sai kusan sha daya, Haba!" kallonsa kawae junaid
yake bai ce komai ba, tsaki yayi ya mike ya dauko maganinta da cup yayi diluting da
ruwa ya xauna kusa da ita xai bata tana ganin haka ta fara kokarin mikewa ya
fixgota, bbu gardama ta shanye maganin duk jikinta na rawa, ya mike
ya dau makulli da wayarsa yana kallon junaid on a serious note yace "Look! In har
ka bar gidan nan kafin in dawo wllh wllh kaji rantsuwan musulmi koh, toh sai dai ka
san yanda da xakayi da yarinyar nan don ba fina biyayya kayi ba, I am taking my
hands of her case" daga haka ya fice daga dakin, Junaid da ya bi sa da kallo yana
murmushi snn ya juya yana kallonta, yatsine fuska kawae take, ta matso kusa da shi
ta mika masa Ayabar hannunta, a hankali ya sauko daga kan gadon ya karba ya kai
mata baki yana kallonta yace "Eat!" Ta kauda kai da sauri, kallon Ayabar yake yana
son ci amma ya kasa, ajiyewa yayi ya dau Apple ya mika mata, Kin karba tayi, yayi
murmushi ya ajiye shi ma, a hankali ta kwanta nan gefensa, ya tsura mata ido, kamar
warce aka tsikara ta mike xaune da sauri, ya koma baya yana kallonta.

*Haske writers Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

18.....

Amai ta shiga kwararowa a gurin, ya mike yana kallonta har ta gama ta koma xata
kwanta yayi saurin riketa, kara ta saki ta turasa da karfi xata kwanta gun aman
yaki saketa, nan ta shiga kokuwa da shi ita sai ta kwanta, ya rike ta gam yace
"Wait Jasmine..." ta kuma sakin wani ihun da ya tsorata shi, ae da ta turasa sai da
ya kusa faduwa ba shiri ya saketa, ta yi kwanciyarta nan kasa, ya sauke ajiyar
xuciya ya nufi toilet, mop da bucket ya dauko ya dawo dakin, rasa ta inda xae fara
gyara wajen aman yayi, ya ajiye ya fita don kira Mama jummai, tare suka shigo
dakin, ta karaso kusa da ita da sauri cike da tausayinta ta dagota tana mata sannu,
ihu ta sakar mata ita ma ta kwace kanta ba shiri ta saketa ta koma ta kwanta tana
mayar da numfashi, girgixa kai mama tayi ta mike ta shiga gyara wajen, tana gamawa
ta kuma gwada d'aga ta a kasan tiles din still taki tashi, kyaleta tayi ta fita,
Junaid ya mike ya shiga bayi ya dauro alwala ya fito jin kiran isha, a nan dakin
yayi sallah, yana xaune kan darduma ya ga tana juye juye a kasan da take kwance.
Kallonta kawae yake cike da tausayinta don da ganinta kasan tana jin jiki, ta mike
xaune a hankali ta dawo inda yake tana kallonsa ta kwanta kusa da shi, dagota yayi
murya can kasa yace "Sorry Jasmine" lumshe ido tayi ta kwanta nan kusa da shi lkci
daya bacci ya dauketa, ya mike ya koma can jikin gado ya xauna, har Karfe tara El-
Ameen bai dawo ba, duk ya kagu ya dawo ya wuce kafin Mumy fa kirasa, tara da rabi
kiran Mumy ya shigo wayarsa, k'asa d'agawa yayi don bai ma san me xai ce mata ba
har sai da ya kusa katsewa sannan ya daga da sauri, Mumy tace "Where are you Ahmad"
kallon dakin yayi kafin a hankali yace "Mumy, am am with El-Ameen" strictly tace
"You are very stupid, within the next 10 to 15 mins ka tabbatar kana cikin gida if
not xaka ga bacin raina, in kuma kaya ku ka kasa a titi ku ke saidawa da daddaren
nan xaka gaya min" kamar mai shirin kuka yace "Kiyi hakuri Mumy xan dawo" katse
wayar tayi, ya rike kansa, layin El-Ameen ya shiga nema yana ta ring bai d'aga ba,
ya lumshe ido ya jingina jikin gado, he just don't know wat to do, haka yayi ta
kiran El-Ameen bai daga ba, Shivering yaga tana yi daga kwancen da take kan
darduma, ya mike ya karasa inda take ya dago ta ta bude ido da sauri, kan gadon
dakin ya kwantar da ita ya rufa mata bargo, ta cire xata sakko ya riketa da damuwa
yace "You are shivering Jasmine" ba shiri ya saketa a dalilin kara me karfi da tayi
masa a kai, ta sauka nan kasan dakin ta kuma kwanciya. Har goma El-Ameen bai dawo
ba, Junaid ya rasa me ke masa dadi shi da bae taba yi ma Mumy musu ba, yasan kuma
fushi tayi shi yasa bata kara kira ba, da yayi niyar tafiya sae ya tuna abinda El-
Ameen yace masa, ya kuma san xai aikata, shine xaune har sha daya, Mama jummai ta
shigo tace "Kai xaka kwana yau a nan kenan junaid?" D'an murmushi yayi yace "A'a
ina jiran El-Ameen ne yace xai dawo" tace "Toh tafi daki can ka kwanta inda yake
kwana xan kula da ita" Junaid yace "yana kwana nan ne?" Tace "Eh wani lkcn yana
kwana can dakin don akwai alluran da yake mata da sassafe, toh duk ran da xai mata
alluran a nan yake kwana, ni kuma tare muke kwana da ita saboda shiga bayi da
daddare" Junaid ya gyada kai yace "Bari in jira sa a nan Mama ni ba kwana xan yi ba
ai" tace "Toh" sannan ta juya ta fita. Lumshe ido yayi ya jinginar da kansa jikin
gado, wani bacci ya ji na fixgarsa ya bude ido yana kallon agogo yaga sha biyu,
kallonta yayi ya ga ta canxa position, a hankali ya mike ya isa inda take xai
dagata ta bude ido da sauri, birginawa tayi ta bar gun ta juya masa baya, ya mike
ya koma ya xauna kan gadon, xuwa yanxu kam ya gama sanin iskanci El-Ameen yayi
masa, dole ko yaki ko ya so a nan xai kwana hakan ba karamin bata masa rai yayi ba,
sha biyu da rabi ya kuma mikewa jin yana jin bacci sosai ya bude closet ya dau
bargon da ya gani ya koma daya side din gadon ya shimfida a kasa ya kwanta dai dai
yanda xai dinga ganinta, nan da nan bacci ya daukesa.
Bude ido yayi jin an bude kofa don ko k'adan bashi da nauyin bacci, El-Ameen ne ya
shigo dakin yana ganinsa ya dauke kai, kallo daya El-Ameen yayi masa yana murmushi
bai ma san idonsa biyu ba ya karasa gun da take kwance a kasa, durkusawa yayi
gabanta ya dagota, ta bude ido da sauri, lumshe ido yayi jin xafin jikinta a
hankali yace "Sorry, Jewel" xata koma ta kwanta yaki saketa, ya mike ya dauketa ya
nufi kan gado da ita ya kwantar, kokarin sauka ta shiga yi da kyar, ya hade rai
yace "No" bata kuma yunkurin saukan ba, ya gyara mata kwanciya ya mike ya shiga
bayi, duk wannan abun Junaid na kallonsu, ya dawo dakin rike da bowl din ruwan
sanyi ya bude closet ya ciro towel karami da babba ya saka karamin cikin ruwan bowl
din ya dawo kan gadon ya ajiye bowl din kan bedside drawer, ya dagota yana kallonta
don idonta biyu, ya dawo da bowl din ruwan gefensa ya matse ruwan towel din a
hankali yana goge mata forehead dinta da shi, kara ta saki xata sauka ya hade rai
yace "Wait!" Bata kuma yunkurin saukan ba, haka ya ci gaba da goge jikinta da yayi
xafi sosai da towel din yana mata sorry, mikewa Junaid yayi, El-Ameen ya juya da
sauri ya kallesa sannan yayi saurin rufeta da bargo yace "Ohh you weren't sleeping
dama" Junaid bai tanka sa ba ya dauke bargon da ya shimfida kasa ya mayar cikin
closet, El-Ameen ya tabe baki yace "Ni ban ma yi tunanin xan dawo in same ka ba
Mumy's boy, theatre muka shiga da Abba and we came out few minutes ago, saboda
nasan condition din patient dinka shi yasa na fito cikin daren nan, I ought to...."
jin anyi banging kofa El-Ameen ya kalli kofar da sauri don dama yana magana ne yana
matse towel a ruwa, murmushi yayi ganin ficewa yayi, ya ci gaba da abinda yake, har
sai da yayi make sure temperature dinta ya dawo dai dai, still yayi ganin hawaye
idonta, ya sunkuya a hankali ya goge mata fuskar yace "Am sorry Jewel, am only
helping" sauka yayi daga kan gadon yaje ya xubar da ruwan ya shanya towel din a
bayi ya fito, bacci ya sameta tana yi a yanda ya barta, ya gyara mata kwanciya
sannan ya hada allura yayi mata da kyar don a tsorace ta farka ta fara kokuwa da
shi, sai da yaga ta koma bacci sannan ya fita dakin ya shiga master bedroom duk a
tunaninsa xae tarda junaid nan, sae yaga otherwise, tabe baki yayi sanin yana
parlor knn, ya shiga toilet yayi wanka ya fito ya canxa kaya yayi kwanciyarsa
dakin, sai dai before dawn yaje dubata ya fi sau goma duk da a shigowarsa na uku ya
tarda mama jummai a dakin, Karfe biyar da minti arba'in ya sauko parlor ya tarda
Junaid xaune kan darduma, xaunawa yayi kan kujera yana kallonsa yace "A parlor ka
kwana kenan?" Junaid ba tare da ya kallesa ba yace "Yea!" El-Ameen yace "Ohk, gud
morning, yanxu dai you need to transfer some money into my account xuwa later akwae
drugs din da na mata prescribing, and you know wat? Suna da tsada gaskiya or I shud
just text you their names, tell you where to get them, kaje da kanka ka siyo, if
you need my assistance let me know" El-Ameen ya kare maganar yana d'aga kafada,
Junaid ya mike ya dauke darduman da yayi sallah yace "nawa ne kudin?" El-Ameen yace
"100 nd 50k will be enough" Junaid yace "Alryt" ajiye darduman yayi kan kujera ya
kalli El-Ameen yace "Na tafi, I will transfer it later in the day" bai jira cewarsa
ba ya nufi kofa ya fice daga parlorn, makullin motarsa ya ciro a aljihu ya fita
waje inda ya ajiye motarsa ya bude ya shiga ya kama hanyar gida, driving kawae yake
amma gaba daya hankalinsa ba ya tare da shi, bai san yanda xa su kwashe da Mumy ba,
toh ina ma xai ce mata ya je, gidansu El-Ameen? No yasan xata iya kiran Ummi,
murmushi yayi yana tunanin randa xae samu freedom, don ya fara damunsa yanxu on
like before, a waje yayi parking ya fito, gabansa ne ya fadi ganin Abbansa alamar
daga masallaci yake, da kyar ya ja kafa ya isa gun gate ganin Abba ya tsaya har ya
risina xai gaida Abba, Abba ya dakatar da shi yace "Daga ina kake?" Yayi kasa da
kai zai yi magana Abba ya juya ya shiga cikin compound, bin bayansa yayi har suka
isa part din Abba, Hajiya ke ta goge goge a parlon, Abba ya xauna kujera yana
kallon Junaid, a hankali ya xauna kasa ya juya yana kallon Hajiya dake kallonsa da
d'an murmushi mai wuyar fassara a fuskarta yace "Ina kwana Hajiya" tace "Lfya lau
Ahmad" sunkuyar da kai yayi, Abba yace "Daga ina kake Ahmad?" A hankali yace "Tare
muke da El-Ameen Abba" Abba yace "Tare a ina?" Hajiya ta dawo cikin parlon tana
girgixa kai tace "kwata kwata ni hankalina bai kwanta da abotansa da yaron nan wai
El-Ameen ba, yaron da bai da nutsuwa ko maganan iyayensa bai ji, kusan duk dare sai
ya shigo ya fita da shi, Ahmad baxae dawo gidan nan sai kusan sha biyu wani lokacin
har daya, duk ina lura da yake ni ba mai nauyin bacci bace ka sani Alhaji, to amma
kar mutum yayi magana ace hassada ko kuma ace don ba d'an sa bane, amma kwata kwata
Ahmad ya sauya hali a gidan nan, jiya wllh wllh khadija ca tayi min mace ta gani a
motarsa da magariban nan da ya fita, to ina yaje yake dawowa yanxu, kuma duk Hajiya
Amina tana ganin abinda yake baxata ce komai ba saboda ta dauki son duniya ta daura
ma yaro, meye amfanin haka, in ma aure yake so ba sai yayi magana ba, ae ba wae bai
isa bane" tunda ta fara magana Junaid ya kafeta da ido ko kiftawa bai yi, Abba kuwa
sai kallonsa yake bacin rai karara a fuskarsa.

*Haske writers Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�


_By Khaleesat Haiydar_�

19.....

Junaid ya sauke ajiyar xuciya ya lumshe ido a hankali bai dai ce komai ba, Abba ya
kalli Hajiya yace "A kira min Aminar" da sauri Junaid ya bude ido ya marairaice
masa yace "Don Allah don annabi Abba ka min duk abinda xaka min, amma bbu ruwan
Mumy bata ma san bana nan ba, plss..." wani tsawa Abba ya daka masa, babu shiri
yayi tsit, Hajiya ta juya ta nufi kofa lebbenta dauke da wani murmushi, ba a dau
lkci ba ta dawo tace "Suhaima ta tafi kiranta" Abba bai ce komai ba ta nemi waje ta
xauna tana girgixa kafa tana tabe baki, ba a dau lkci ba Mumy ta shigo parlon da
sallama, sai dai duk jikinta yayi sanyi ganin junaid xaune parlon tasan ba abun
arxiki ya sa aka kira ta ba, kujera ta samu ta xauna tare da gaida Abba. Bbu yabo
bbu fallasa ya amsa, junaid ya k'asa dago kai ya kalleta duk jikinsa yayi sanyi,
Abba yace "Ke a tunanin ki so kike nuna ma yaron nan koh Amina, har ya kai matsayin
da Ahmad baya kwana gida yanxu shi ba nyt duty ba kika xuba masa ido koh, toh dama
an sha gaya min ban yarda ba amma yau idona ya gane min komai, don haka ni baxan
bari ya dauko min abun kunya ba ina xaman xama na, just few weeks na basa ya fito
da mata idan ba haka ba xai sha mamaki na wllh....." Mumy da har idonta sun cicciko
ta kallesa cike da takaici tace "Alhaji kar ka manta Ahmad ba mace bane da har kake
tsoron ya dauko maka abun kunya, kuma mace ake ma kulle ba namiji ba, ko yau ya ga
bai son xaman gidan nan yana iya barin sa ya koma duk inda yake so don namiji yake
ba mace ba kuma ya mallaki hankalin kansa, ni na haifi Ahmad na kuma fi kowa sanin
halinsa ko rantsuwa nayi baxan yi kaffara ba baxai aika ta mugun kaxamin kaxafin da
ake son lika masa ba, I know my son" hawaye na bin kuncinta ta kare maganan, Hajiya
ta bude baki ta saki salati tana tafe hannu, Abba ya mike fuskar nan tasa a murtuke
yana kallonta yace "lallai Amina wato ni ke masa kaxafi kenan koh, to bari ki ji,
wllh sati uku na basa yayi aure ya bar min gidana idan ko ba haka ba xai gane
matsayina a gun sa" mikewa Mumy tayi tana kallonsa tace "Toh sai me, bai isa auren
bane!" wani kallon Allah wadaran shaidanin mutum ta jefa ma Hajiya ta fice daga
parlon, Hajiya ta dinga salati tana cewa "kiri kiri mutum yasan gaskiya ya danne
don bai son laifin d'an sa, Allah sarki duniya" Abba ya kalli Junaid yace "Ka dai
ji me nace maka, sati uku na baka wllh, get away" mikewa Junaid yayi da kyar ya
fita daga parlon kansa na juya masa, part din Mumy ya shiga ganin bata parlor ya
shiga bedroom dinta, xaune ya sameta gefen gado tayi tagumi, ya durkushe gabanta,
ya daura kansa bisa kafarta cikin sanyin murya yace "Don Allah forgive me mum, it
wasn't my intention disobeying you yesterday, I.. I am sorry mother forgive me
plss" jin bata ce komai ba ya dago idanuwansa da suka kada yana kallonta, kamar xae
sakar mata kuka yace "Plss Mumy kiyi hakuri!" "Ina ka tafi jiya?" Ta jefo masa
tambayar tana kallonsa, rasa abinda xai ce mata yayi Cause he is not dat gud at
lying, yanxun nan sae ta gano sa, ya kalli agogo, kallon agogon tayi ita ma taga
bakwai saura ta d'an sauke boyayyen ajiyar xuciya tace "Tashi ka tafi" a hankali ya
kamo hannunta yace "Plss Mumy kiyi hakuri nace" a nutse tace "Leave!" Ya kusa minti
biyu durkushe gun sannan ya sake hannunta ya mike a hankali ya juya ya fita daga
dakin ya shiga part dinsa. Cikin minti ashirin yyi wanka ya gama shirinsa, ya fito
sae dai da ganinsa kasan bashi da nutsuwa, part din Mumy ya koma, ya sameta tsaye
dinning tana jera masa breakfast, karasawa yayi yana rike da hularsa, Mumy ta bar
dinning din, sosai jikinsa yayi sanyi ya ja kujera a hankali ya xauna ya dau mug
din tea'n da ta hada masa ya shiga sha ba don yana jin sha ba, tea kawae ya iya sha
ya mike ya dawo parlor yana kallonta yace "Xan tafi aiki Mumy" tace "baka ci
dankalin ba, wa ka bar ma? go back and eat it yanxu" ba musu ya koma ya d'an ci
kadan sannan ya kurbi ruwa ya dawo yace "Na ci Mumy" tace "Allah ya tsare" a
sanyaye ya nufi kofa ya fita, Humainah da fatima sun fito daga part din Abba kenan,
Humainah ta nufesa ganin parking lot ya tafi ya bude motarsa, kan ta iso har ya
shiga, ta bude motar ta wara ido tace "Ya Ahmad Abba yace anjima ka kai ni
islamiyyar su fatima ni ma a min...." Fixgo kofar motarsa yayi ya rufe, tayi still
wajen tana kallon bakin glass din motar, yana gama ba motar wuta ya ja ya bar
wajen, tsaki ta ja sai kuma ta fashe da kuka ta juya suka yi ido hudu da Hajiya da
suhaima dake kallon duk abinda ya faru, Suhaima ta fashe da dariya, da gudu tayi
part din Mumy tana kuka kamar wata jaririya. Haka Junaid ya wuni gun aiki duk bai
da sukuni, colleagues dinsa har tambayarsa suka dinga yi ko lafiyarsa yace he's
just having a slight headache ne, duk ya tuna abinda Abba yace sai gabansa ya fadi
ba kadan ba, wai 3wks, kuma yasan ba lallai yayi kaffara a kansa ba, tunda ya dauki
kudurin taimakon baiwar Allahn nan yake fuskantar challenges iri iri ga shi bashi
da rest of mind as before, and he knows he is only doing it for Allah's sake ba da
wata manufa ba, damuwar da yake ciki bai hanasa yi ma El-Ameen transfer din dubu
dari da hamsin din da yace na drugs dinta ba, Hudu bai karasa ba ya bar gun aiki ya
dawo gida, part dinsa ya nufa ba tare da ya kalli su Umma da Hajiya dake xaune
balconyn Hajiya ba yayi shigewarsa parlor yyi banging kofar, Hajiya ta tabe baki
tace "Ke maganar ki gaskiya ce wllh, tsinannan uwar nan tasa bata bari yaci girkin
mu, ita ke masa da kanta kullum" Umma tayi kwafa tace "Ahaf Ba baki yarda ba da, ae
wannan matar ae sai dai muyi adduar ganin karshenta" Hajiya tace "Toh wai meye kuma
next move din da xa mu dauka tunda gashi ance ya fito da mata nan da sati uku, ke
kar fa kuma yace wannan shegiyar Humainah take kowa, kinsan fa ba kula matan yake
ba, kar uwarsa tace ya fito da Humainahr kawai mu shiga uku, wannan fa shine anyi
ba ayi ba" Umma ta xuba tagumi tana gwalo ido yace "Yo ni ae wannan tunanin bai
fado min ba wllh, kai da mun shiga uku, ni fa Humainahn nan ba karamin tsana nayi
mata ba fa don duk da dududu bata fi sati gidan nan ba naga alama bata da kunya ko
kadan, kuma ko shigowa gaishe mu bata yi, sai ma taga dama take gaishe mun in ta
shigo gun Alhaji, kuma ina ga kamar tsinannar Aminan nan ke xuga ta" Hajiya ta
sauke ajiyar xuciya tace "Xamu san yanda xa muyi da shegiyar ita ma, kuma ma ni ban
ga alamar suna soyayya ba kin san halinsa ai, kuma ni shawarata kawai mu hade kai
mu san yanda xa ayi Alhaji ya hada sa da Suhaima ko Muhibba shikenan sai yanda muka
yi da shi" Umma tace "Toh ai matsalar ynxu kawai kullin da aka bamu mu barbada
kofarsa ne, ya xa muyi? kinsan ba xuwa can bangaren muke ba, muna xuwa yanxu xa a
gano mu, kuma don tsiya wai sai da magriba, dama da rana ne bbu wanda xai lura shi
kuma yana gun aiki, ita kuma sallamammiyar 'yar ki khadija ba bamu hadin kai xata
yi ba" Hajiya ta d'an yi shiru sannan a hankali tace "Suhaima xata yi mana aikin,
nasan halin abata tsaf xata yi ba tare da an xargi komai ba" Umma tace "Toh
Alhmdllh" da haka suka ci gaba da hirarrakunsu cike da rashin tsoron Allah.
Junaid kam wankansa yayi ya dauro alwala ya fito ya shirya cikin kananun kaya yayi
la'asar a dakin sannan ya fito yayi part din Mumy, suna xaune da Humainah tana mata
tsifa, Ya xauna yana kallon Mumy yace "Ina yini Mumy" bbu yabo bbu fallasa tace
"Lfya lau" shiru yayi, Mumy ta hade rai tace "Ka kyauta Ahmad ita 'yar uwar taka ka
walakanta gaban idon makiyan ka koh?" Humainah ta bata rai, sai kuma ta fashe da
kuka, Mumy tace "Ji walakanci, meye haka ke kuma" mikewa tayi fuu ta koma dining
tana rera kuka, Mumy tayi tsaki ta galla masa harara ta shige daki. Murmushi yyi
yana shafa kansa ya mike ya nufi dinning din, kujerar dake kusa da wanda ta xauna
ya ja ya xauna ta mike xata bar wajen ya rikota ya mayar da ita ya xaunar yace "Wai
dama daxu magana kike min" ta fizge hannunta tace "Ohon maka" dariya yayi yace "Ni
fa nayi xaton da kofar mota kike, toh tunda da ni kike yi hakuri..." Ta fashe da
wani sabon kukan tace "Allah bana so" murmushi kawai yake yana kallonta yace "Toh
kar ki so din, har da wani kwalliyarta tayi xaton da El-Ameen xamu dawo" ta dago da
sauri tana kallonsa ta tsuke fuska tana goge hawayen idonta tace "Wani kwalliya
nayi" giranta ya taba a hankali yace "Ba gashi ba har da wani shafa baki kika yi
anan irin yanda kuke yi" ya kuma kallon pink lips dinta yana murmushi yace "Har da
wani shafa jan baki a nan duk don ki burgesa" buge masa hannu tayi fuskarta daure
tace "Tun da kai ka shafa min ba" mikewa tayi xata bar wajen ya rikota da sauri
yana dariya yace "Toh na dai ce kiyi hakuri koh" ta turasa tayi gaba abunta,
murmushi yayi ya tabe baki, fatima dake bakin kofar kitchen tayi gyaran murya tace
"Uhum ya A.jay Humainaj kadai yake ma dariya a gidan nan" wani kallo yayi mata, ta
juya da sauri ta koma kitchen tana dariya, tsaki yyi ya bude food warmern dake
dining din, kadan ya xuba shinkafar ya ci ya dawo parlor don duk bai da Appetite,
kofa ya nufa ya koma part dinsa ya kwanta ya lumshe ido, yana son ya gansa can
gidan El-Ameen ya ga halin da Baiwar Allahn ke ciki amma yasan baxai ma fara cewa
xai fita ba, haka yayi ta juye juye kan kujeran duk ya rufe ido ita yake gani, shi
kam tun da ya fara ganin yarinyar nan nutsuwarsa ya ragu, toh ko dai haushin
taimakon nata da yayi take ji shiyasa ya kasa samun kwanciyar hankali, bude ido
yayi jin an bude kofarsa, ya juya da sauri ya ga Humainah ce, ta hade rai ta
dungure masa bowl din fruit salad din hannunta a kasa, murmushi yayi yace "da kin
xubar ai," ko kallonsa bata yi ba ta fice. Washegari haka ya tafi aiki da safe as
usual, ba laifi Mumy ta d'an kulasa da yaje breakfast, Abba kuwa dama da yaje
gaishesa ca aka yi masa yana bacci, ko ta kan Umman bai bi ba yayi ficewarsa don ya
saba in dai ba Mumy ce da girki ba to ba lallai ya ga Abba ba sae ko a masallaci,
kasa samun natsuwa yayi gun aiki har sae da ya dau excuse din minti ashirin ya fita
ya kama hanyar gidan El-Ameen, su biyu kadae ne parlon ita da mama dake mata kalaba
daga tsaye don taki xama, sae xagaye parlon suke ana kitson a haka, tana ganinsa
suka hada ido ta kurma wani uban ihu da yayi mugun tsorata mama don kan kace me har
ta kai bakin kofa, shi kam tsayawa kallonta yayi, har lokacin ihun take da karfi
tana shisshigewa jikin bango ko ina na jikinta na rawa, lumshe ido yayi a hankali
ya bude ya kalli uniform din jikinsa White navy shirt ne jikinsa da dark trousers
navy blue, ya kalleta ya ga yanda ta runtse ido tana k'uwa, bude kofar parlon aka
yi El-Ameen ya shigo da ledoji a hannunsa, sake ledojin yayi da sauri ya karasa
gunta, ya riketa, bude ido tayi a gigice ta kara fasa wani ihun tana ganin El-Ameen
ta rungumesa, ya rufe bakinta lkci daya tayi shiru tana sauke ajiyar xuciya a
hankali, kallon Junaid yayi ya hade rai yace "Look captain, I've warned you not to
come to this house on uniform again, look how you are scaring the life out of her,
a haka xata samu lafiya? Plss ka daina xuwa nan da uniform" Juyawa Junaid yayi ya
fice daga parlon, Mama dake bakin kofa har lkcn tace "Auuu wae khakin take tsoro?
Allah sarki Baiwar Allah" dago kanta El-Ameen yayi yana kallonta ita ma haka, kama
hannunta yayi yana rike da ita suka haura sama. Junaid na komawa gun aiki ya ci
gaba da harkokinsa sai dai da ka gansa kasan there is something eating him inside,
karfe biyar saura ya isa gida, ya jima xaune motarsa yana danne danne a waya, ganin
motar da ke kokarin parking gefensa ya kashe motar ya fito ya rufe yayi part dinsa.
Yana kwance parlor'nsa dab da magrib yana kallon wani program though absentminded
yaji Humainah na kwalo masa kira daga waje, mikewa xaune yayi jin irin yanda take
kiransa da karfi, ya mike da sauri ya nufi kofa ya bude, tsaye ya ganta d'an nesa
da balconyn rike da kugu tana tafe hannu tace "Taho taho ka ga yaya" yana fitowa
sai kuma tayi bangaren Mumy da sauri tana kwalo mata kira ita ma, wanda hakan ya ja
attention din 'yan gidan da ido da kunnensu na kan duk wani motsi na gidan kamar
masu gadi, Umma ta riga Mumy da fatima fitowa sannan Hajiya, su khadija Rabi'a,
sadiya, Muhibba duk suka fiffito, shi kam Junaid abinda ya daure masa kai bai wuce
na ganin Suhaima tsaye bakin kofarsa tana xaxxaro ido sai kokarin boye abu a
hannunta take, Humainah ta dawo da sauri Mumy na biye da ita a baya haka ma sauran,
Hajiya kam ko ina na jikinta rawa yake ji take kamar ta saki gudawa tsabar rudu
shikenan asirinsu ya tonu, garin yaya Suhaima taje bakin kofar ba tare da ta sa ido
taga bbu kowa a tsakar gidan ba, ita kanta umma sai da hanjin cikinta ya kada sai
dai duk basu nuna a fuska ba, don Hajiya sai ma wani hade ran karfin hali tayi, A
takaice Humainah ta rike kugu tace "Abu naga tana shirin barbada wa bakin kofar ya
Ahmad, duk bata san ina can bakin pampo naje daurayo takalmana ina kallonta ba" ta
fadi haka tana nuni da kusa da bangaren da Hajja ke sauka, Suhaima dake ta salati a
rikice tace "Sharri xa ki min don kin gan ni a nan, na shiga uku na lalace,
Hajiyanmu kina jin abinda yarinyar nan ke cewa" a fusace Humainah tace "koh ba
sharri ba, ki bude tafin hannun ki munafuka, kin wani xo kina yi kamar mage baki
san ina kallonki ba xaki wani ce ina maki sharri, wllh Mumy abu take shirin barbada
masa bakin kofa" Hajiya ta hadiye yawu da kyar tace "Ke yanxu 'yar nan sharrin naki
kan 'ya ta kuma xe sauka, duk shekarunta gidan nan bata taba barbada ma Ahmad abu
ba sai da kika xo munafuka algunguma toh wllh sai Alhaji ya xo ya mana shari'a don
baxan yarda da kaxafin nan ba" fuu Humainah ta haura balconyn ta fixgo hannun
Suhaima dake jin kamar ta saki fitsari tana huci tace "Bude hannun to idan sharri
na maki, ki bude, uwar me ya kawo ki bangaren sa da daddare ke da ko during
daylight ba xuwa kike ba munafukaa, toh wllh sai kin fadi Meye wannan kike shirin
barbada masa ko in gaggalla maki mari a nan don ubanki" Mumy ta sauke ajiyar xuciya
a hankali tace "Humainah!" Humainah na girgixa kai ido rufe tace "Ni dai Mumy Allah
sai ta fadi meye a hannunta ko kuma muje ta barbada shi a kofar uwarta ni baxan
yarda ba"

*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

20.....

Suhaima da duk ta jike da xufa ta fara kokarin kwace hannunta daga rikon da
Humainah tayi mata tana cewa "Na shiga uku ki cika ni, me na maki xaki min irin
wannan sharrin?" Banda murmushi babu abinda khadija take, Hajiya dai da kyar
kafafuwanta ke daukarta ga wani kullewa da cikinta yayi, Umma kuma sai wuwwurga ido
take tana xufa, Sadiya ta haura balconyn a fusace tana kallon Humainah tace "Ke
karamar 'yar iska cika mata hannu kar in baki mamaki yanxu....." Humainah ta juya a
hankali tana mata wani matsiyacin kallo tace "Kambu! Ko kuma ni in baku mamaki ba,
ai wllh sai ta fadi kullin uban meye a hannunta kuma wa ya aikota idan ba haka ba
in karya hannun" Khadija tace "Toh ke Anty suhaima ki bude hannun a ga kullin mana,
ko dai yaji xa ki kai masa?" Hajiya tayi kanta xata cafke ta ai da gudu ta bar
wajen, cike da karfin hali Hajiya na huci tace "Ae sun yi kadan ta bude masu hannu
wllh, sai dai duk...." Fitowar Abba yasa ta kasa karasawa ta fara girgije girgije
ae kawae sae ta fashe da kuka tun kan ya karaso tace "Na shiga uku ni fateema me
muka tare ma mutane a gidan nan ni da 'ya yana" A hankali Mumy tace "Cikata
Humainah" Humainah ta girgixa kai ta cakumi rigarta tace "Noo! Ae sai ta bude
hannunta mun ga ko menene wllh Mumy" shi kam Junaid tsaye kawai yayi ya kasa cewa
komai duk jikinsa ba karfi, Abba na isowa ya shiga tambayar Meye haka, Humainah
tace "Abba wallahi barbade take shirin yi ma Ya Ahmad Allah ya toni asirinta na
kamata kuma ni sai taje bakin kofarsu ta barbada koma Meye xan kyaleta" Hajiya ta
fashe da matsanancin kuka ko ina na jikinta na bari tace "Kana ji ko Alhaji, kana
ji koh...." Abba kam kallonsu ya tsaya yi, can yace "Cikata Humainah" Humainah ta
fashe da kuka tace "Ni wallahi baxan saketa ba Abba, sai ta nuna abinda ke hannunta
kuma muje ta barbada shi a kofarsu, duk bata san ina can ina kallonta ba, ni
wallahi baxan kyaleta ba" dariya khadija ta dinga yi can ciki ciki ganin yanda 'yar
uwarta ke wurga ido kamar barauniya, da kyar Mumy ta haura balconyn ta kamo
Humainah tace "Saketa Humainah" still taki sakinta ita fa sae ta bude hannunta,
Junaid ya lumshe ido ya bude ya karasa kusa da su a sanyaye ya janyeta yace
"Kyaleta Lil sis" fashewa tayi da wani kukan tace "Ya Ahmad abu fa tayi niyar
barbadawa da ban ganta ba" ae Suhaima tun da ta samu Humainah ta saketa kan kace me
har ta sauko kasa tana tuntube, ta fashe da kuka tana kallon Hajiya da Abba tace
"Kudi fa na xo tambayarsa don ta ga ina leke leke shine take cewa barbade xan
masa," Hajiya ta rungumeta ita ma ta fashe da kukan tace "Na sani Suhaima Allah xai
saka mana kiyi shiru" Humainah ta kwace kanta daga rikon da Junaid yayi mata ta
sauko tana kallonta da kyau tace "Kuma wallahi daga yau na kuma ganin kafar ki a
nan wajajen sai na karya su duka biyun, munafuka kawai dama ni Hajja tace min boka
da malamai kuke bi" tsawa sosai Abba ya daka mata, ta turo baki ta bangajeta tayi
part din Mumy fuu tana gunguni, duk suka bita da kallo fatima ta ni bayanta, Abba
ya kusa minti daya bai ce komai ba, can ya kalli su Hajiya yace duk kowa ya koma
ciki, haka duk suka juya Hajiya na kuka har lkcn tana rike da hannun Suhaima Umma
da baki ya mutu na biye da ita a baya, shi ma ya juya yayi part dinsa ana kiraye
kirayen sllhn magrib. Mumy ta juyo a sanyaye tana kallon Junaid, shi din ma duk
jikinsa yayi sanyi ba kadan ba, kasa cewa komai tayi ta sauka ta koma part din ta,
ya lumshe ido ya bude ya bi bayanta. Xaune suka tarda Humainah palo sai rusa kuka
take bakin rai, Mumy tace "lafiya kuma Humainah" cikin kuka tace "Mumy ba shine
baku bari na mata duka ba, wllh wani kulli ne hannunta tana shirin xubawa bakin
kofar na kamata" Mumy ta xauna kusa da ita tana murmushi ta jawo ta jikinta tace
"Kiyi hakuri mu bar su da halinsu Allah ya fisu da shi kuma muka dogara, in'sha
Allah bbu abinda xai same mu kin ji Humainah" kallon Junaid dake tsaye ya kasa xama
tayi tace "Kai kuma ya Ahmad maimakon ka faffala mata mari shine ka tsaya kallonta"
Xaunawa yayi yyi murmushi bai ce komai ba, lallashinta Mumy ta dinga yi har dai ta
samu tayi shiru, Junaid ya mike ya shiga bathroom din dake parlon ya dauro alwala
ya fito ya fita xuwa masallaci, Mumy ta kalleta tace "tashi ki je kiyi alwala" ba
musu ta mike ta shiga bathroom Mumy ma ta tashi ta shiga dakinta don yin alwalan.
Ana idar da Sllh Junaid ya shigo, Humainah na xaune da Mumy da fatima suna cin
abinci, ya xauna yana kallonsu, kwankwasa kofa aka yi lkci daya aka bude aka
shigo, Sadiya ce ta shigo ta tsaya daga bakin kofar fuskarta tamke tace "Humainah
kike ko wa? Abba na kiran ki" Humainah ta galla mata harara tace "A'a Mantawa kika
yi dai, Sadiya sunana" Mumy tace "Ke kina da hankali Humainah?" ta turo baki ta
ajiye spoon din hannunta, Sadiya tayi kwafa tana gyada kai ta fice, mikewa Humainah
tayi, Mumy tace "Ki gama cin abincin tukunna, baxa mu kuma shirya da ke ba idan
kina rashin kunya" kamar xata yi kuka ta nufi kofa Junaid ya bi ta da kallo yana
girgixa kai. Da sallama Shukrah ta shiga parlorn Abba, yana xaune kujera Hajiya da
Umma ma na xaune sai Suhaima da ke xaune kasa, can jikin kujera ta samu ta xauna
tace "Abba gani" a nutse Abba yace "Daga yau kika sake abinda kika yi daxu sai na
yi mugun saba maki, Ashe ke shashasha ce, kina daga can bakin pampo ta ya kika ga
abu a hannunta" Hajiya ta goge d'an guntun hawayen idonta tace "Babu maganan taya
ta gani, wllh sa ta aka yi Alhaji don wnn yar mitsitsiyar hankalinta baxae bata
tayi abinda tayi mana daxu ba, to ni kam me na tsare masu xa su yi ma 'ya ta irin
wannan mugun sharrin?" Kuka ta fashe da sosai, Umma ta sauke ajiyar xuciya tace
"Xancen ki gaskiya Hajiya, amma Allah ya san dai dai, kuma baya bacci" Abba ya
kalli Humainah da ta wani hade rai kiris ya rage ta fashe, yace "Don uwar ki wa
kike ma wannan kallon" mikewa tayi ta fashe da kuka tace "Na rantse da Allah Abba
wani abu ne a hannunta tana son budewa ta barbada fa na kama ta, ni ba karya na
mata ba, meyasa baka ce ta bude hannun ba tun a can..." Wani tsawa Abba ya daka
mata yace "Ke!! Baki san ni ba koh?" Hajiya ta girgixa kai tace "Babu ruwan
yarinyar Alhaji da ba a ce tayi hakan ba baxa ta yi ba" Abba yace "Toh maxa ki tafi
ki tattaro kayanki ki koma gun Hajiya tunda munafurci kike koya can, maxa maxa
yanxun nan ba sai da safe ba" Hajiya ta dan yi murmushi da iyakan sa lebbe, ficewa
Humainah tayi da gudu daga parlon, tayi part din Mumy, Mumy na xuba ma Junaid
abinci ta fado parlon ta xube nan kasa ta dinga rusa kuka kace yar jaririya ce,
Mumy ta karasa da sauri ta dago ta tana tambayarta abinda ya faru, kuka take sosai
tace "Wayyo Mumy ni gidanmu xan tafi wallahi baxan xauna a nan ba, ki bani wayar ki
in kira Hajjah" Mumy tace "Kiyi hakuri, gaya min me ya faru, me Abban yace maki"
cikin kuka tayi ma Mumy tsarin yanda suka yi da Abba, Mumy tayi murmushin takaici
bata ce komai ba, Junaid kam lumshe ido yyi ya jinginar da kansa jikin kujera, tana
ci gaba da rusa kuka tace "Ni wallahi wucewa xanyi baxan xauna ba" Mumy rasa me
xata ce mata tayi, mikewa Junaid yayi ya dago ta yace "Kiyi hakuri, Abba is angry
shi yasa ya maki magana haka, xaki ga ya huce xuwa gobe" tace "A'a ni ka ban
wayarka in kira Hajja tafiya ta xan yi" cikin sanyin murya Mumy tace "Kar ki
kirata, xai iya cewa ni na sa ki kirata" mikewa Humainah tayi ta nufi daki tana
kuka. Junaid ya koma ya xauna, Mumy ta girgixa Kai ta ci gaba da xuba masa abincin
da take yi. Kasa cin abincin Junaid yayi, Mumy ta lura da hakan tace "Dama ka ci
abincinka ka share komai, I keep telling you Junaid never depend on ur father, duk
da nasan you are not depending on him dama, kar ma ka sa rai da komai nasa, sannan
kayi ta bin sa ku rabu lafiya, you can see how things are going this days nasan ba
yin kansa bane, banda hada ka da shi bbu abinda ake yi, lastly be prayerful" a
hankali yace "In'sha Allah Mum" tace "Ya maganan da yayi maka jiya, kasan dai yana
can yana kirga kwanakin da ya baka, ko kuma ince ana can ana Kirga masa koh" shiru
Junaid yayi, Mumy tace "It's better ka kwantar da hankalin ka ka fito da mata tun
kan ya nuna maka matsayinsa gun ka kamar yanda yayi ikirari" ae gaba daya abincin
fita ran Junaid yayi, da kyar ya dinga tutturawa, Mumy na kula da hakan duk
tausayin sa ya rufeta, tasan ba yin kan Abba bane yake masa haka, amma bbu yanda ta
iya sai dai ta dage da Addu'a kamar yanda ta saba. Mikewa yayi jin ana kiran isha
ya shiga bathroom ya dauro alwala ya fito ya tafi masallaci, ana idar da sllh yana
tsaye da Abdul suna gaisawa ya ga tsayuwar motar El-ameen, El-ameen yayi parking ya
fito suka gaisa da Abdul sannan ya kalli Junaid ya shiga gida, part din Mumy ya
nufa suka gaisa ta tambayesa mutan gida yace Duk suna lafiya, ya kalli hanyar
bedrooms yace "Wa ke kuka kuma Mumy?" Mumy tayi murmushi tace "Humainah ce, daga
Abba yayi mata fada wai fa" dariya yayi bai ce komai ba, Mumy tace "toh je ka
lallasheta kila tayi shiru, ni taki saurara na" shiru yayi sai kuma ya mike kamar
munafuki ya nufi bedroom din Mumy, tura kofar yayi ya shiga ya sameta xaune can
karshen gado tana rera kukanta, ya kusa minti biyu tsaye kafin yasa kai ya shiga
dakin, ya karasa inda take a hankali, ya duka yana kallonta, tuni ta hadiye kukan
da take ta kauda kai, ya d'an bude ido yace "Am, dama Mumy ce tace in xo in baki
hakuri wai kina kuka" juya masa baya tayi da sauri, ya d'an sosa kai murya can kasa
yace "Kiyi hakuri" taki cewa komai, a hankali yace "Kin ji" Junaid ne ya shigo
dakin yana ganinsu ya saka dariya yace "Uhnn! har dakin ka biyota Dr, ba sai ka
jira in dawo in kira maka ita ba" El-ameen ya mike yace "Mumy ce tace in xo in bata
hakuri Mr man" daga haka ya fice daga dakin, Junaid yace "ba wani nan da'alla kai
dai fadi gaskiya" Humainah ta mike xata shiga bathroom ya fixgota yana dariya yace
"Oya sorry lil sis" fixge hannunta tayi tace "Ae next time ko boka aka kawo xa a
ajiye bakin kofar ka baxan ce komai ba" dariya yayi sosai yace "Nafa ce kiyi
hakuri, beside
Allah ya fisu I believe" goge mata fuskarta yayi yace "Yanxu sai ki je ki wanke
fuskarki kiyi kwalliya kin ga saurayin ki ya xo" Turasa tayi ta shige bathroom,
yayi murmushi ya fita, a parlor ya tadda El-ameen yace "Mu je" mikewa El-ameen
yayi, Mumy tace "Baxa ka ci abinci ba Ahmad" El-ameen ya girgixa kai yace "Naci
abinci Mumy" Mumy tace "Toh shikenan," har sun fita Mumy ta kira Junaid ya dawo, ya
isa gabanta yace "Gani Mum" tana kallonsa a hankali tace "Kayi addu'a kafin ka
shiga" ya sunkuyar da kansa yace "Toh Mumy" daga haka ya fita daga parlon, suka
nufi part dinsa da El-ameen, yayi yanda Mumy tace masa ya bude kofar ya shiga, El-
ameen ma ya shiga, El-ameen ya xauna yana kallon Junaid yace "Did you tell anyone
about our patient?" Junaid yayi shiru sannan ya girgixa kai yace "Not at all" El-
ameen yace "Ohk, daxu mama Jummai take ce min xata je kauyensu gun dotan ta ta
haihu, amma kwana biyu kawae xata yi, toh I don't know yanda za ayi abun, who will
stay with ur patient during her absent?" Junaid yayi shiru yana kallonsa, can yace
"Or shud we get a new...." El-ameen yace "Noo! Kwana biyu tace xata yi beside
yarinyar tafi sabawa da ita kafin ta saba da wata kuma is something else, yau satin
su kusan uku tare if am not mistaken" Junaid bai kuma cewa komai ba, El-ameen yace
"Hurry plss ina son komawa can gidan kafin in tafi clinic" Junaid yace "I don't
know what to say" El-ameen yace "How about khadija, naga u guyz are close" lkci
daya maganganun Hajiya na daxu da safe ya fado masa wai khadija ce tace mata ta
gansa da mace a mota, girgixa kai yayi yana murmushi coz yasan khadija won't do
that, a hankali yace "Humainah?" El-ameen yace "Baka tunanin xata yi exposing din
mu, beside wannan me kukan me ma xata iya yi?" Junaid yyi murmushi yace "She won't,
matsalar kawai Mumy ce" El-ameen yace "Alright, y not make it look as if gidanmu
xaka kai ta gun Ummi, daga nan dai xa mu san yanda za muyi" Junaid yayi shiru
sannan yace "Ohk Allah yasa ta yrda" mikewa El-ameen yayi yace "Gud, yanda ku ka yi
gobe ka kira ni" Junaid yace "Wait, but kasan da wuri nake barin gida ai" El-ameen
yace "However, just make sure gobe around 12 tana gida na or she shud meet me at
the clinic" Junaid yace "Wait plss don Allah kamar yaushe kake ganin xata samu
lafiya, will it take long?" El-ameen ya wara ido yace "Uhn! Har ka fara gajiya da
kashe kudi kenan?" Junaid ya girgixa kai yace "Not at all, ina son ta samu lafiya
ta nemo 'yan uwanta case dinta ya fita daga hannuna, har kuma hakan ya kasance bana
fatan 'yan gidanmu su san komai" El-ameen ya daga kafada yace "But I hope you
weren't daft the other day I was saying it's difficult to predict how, when, or to
what degree she's going to get better, dat aside ma kayi addu'ar kar tayi loosing
memory idan ma ta samu lafiyan!" Zaro ido Junaid yayi yace "Loosing memory kuma, No
No in'sha Allah hankalinta gaba daya xai dawo, if not ya za muyi da 'yar mutane?"
El-Ameen yayi murmushi yace "Allah dai ya kiyaye hakan" daga haka ya fice daga
parlon yana cewa "Am off!", Junaid ya bisa da kallo sannan ya sauke ajiyar xuciya a
hankali yace "Ya Allah ka ba ma wannan baiwa taka lafiya" mikewa yyi shi ma ya
fita, part din Mumy ya shiga ya tarda El-ameen yana ma Mumy sallamah, Mumy tace
"Yauwa Ahmad ku fita tare ka siyo min fruits" Junaid yace "Toh Mumy" tare suka fita
da El-ameen a motar El-ameen din, Suna isa inda ake saida fruits yyi parking,
Junaid ya fita ya siya fruits leda biyu ya dawo motar, ya ajiye ma El-ameen daya
yace "For our patient" El-ameen yace "za ka raka ni shopping complex xan siya ma
Ummi perfume wai" Junaid yace "Ohk" Suna isa bayan El-ameen yyi parking suka shiga
babban mall din, El-ameen ya nufi gun perfumes, ya debi wa enda yasan Umminsa na
amfani da, junaid dai binsa kawae yake, Suna isa gun teddy bears manya El-ameen ya
dauka wani me kyau yana kallo, Junaid yace "toh fah!" El-ameen yyi murmushi ya
ajiye a basket yace "For ur patient" daga haka suka bar wajen, biscuits da
chocolates me yawa El-ameen ya dauka a trolley din, shi dai Junaid binsa kawae yake
har ya gama daukan abinda xai dauka suka tafi inda ake biyan kudi, Wata yarinya ce
tsaye gabansu sanye da hijab har kasa tana rike da basket dinta, gabanta kuma
mutane biyu ne, El-ameen ya dawo kusa da Junaid murya can kasa yace "Don Allah ka
d'an mata magana kace sauri muke ta bari mu fara biya, dubi fa kayanta da yawa"
Junaid yyi masa wani kallo yace "Tunda kai baka da baki sai ni" El-ameen yyi tsaki
yace "matsalata da kai kenan kamar ba namiji ba" Junaid bai kuma ce masa komai ba,
har aka zo kan yarinyar bude Jakarta tayi xata fito da Atm bayan ta xube kayan da
ta siya kan table ana lissafawa, dube dube kawai take a jakar, El-ameen yyi dariya
can kasa yace "are you seeing what am seeing frnd?" Sharesa Junaid yayi, yarinyar
ta juyo tana duba kasa, Junaid ya tsura mata ido yana tunanin inda ya taba ganinta
amma ya k'asa tunawa, juyawa ta kuma yi tana kallon mutumin dake xaune yana jiran
kudi tace "Malam Atm card dina ne ban gani ba wllh, kayi hakuri ka ajiye kayan
tukun" sai a sannan Junaid ya tuna inda ya taba ganinta ta dalilin muryarta da ya
ji, ya laluba jikinsa yaji bai fito da Atm card dinsa ba, kallon na hannun El-ameen
dake dariya can kasa yana cewa "Karyar banxa wai bata gani ba" ya warce atm card
dinsa ya nufi gun biyan kudin, El-ameen ya xaro ido yace "Kaiii" ko kallonsa Junaid
bai yi ba ya mika masu yace "Gashi ku cire kudin ku" kallonsa yarinyar take ita ma
tana son tuno inda ta taba ganinsa, su ko tuni suka karbi atm ya danna masu pin
suka cire kudinsu har dubu talatin da biyar. A hankali yarinyar tace "Thank you" da
alama ta tunasa ita ma, yayi murmushi yace "Never mind, it pays to be kind"
Murmushi kawai tayi, ya juya yana ma El-ameen wani irin kallo.


*Haske writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

21.....

Karasowa Junaid yayi gun El-ameen da ya wani hade rai yana kallonsa, junaid yayi
murmushi ganin bai da niyar motsi daga inda yake gashi jiransa ake ya karbi basket
din hannunsa ya tafi ya biya kudin kayan ciki, godiya yarinyar ta kuma yi ma Junaid
bayan ta dauki kayanta da aka yi packaging a leda ta bar wajen, El-ameen ya bi ta
da harara har ta fita, Junaid ya dinga danne dariyarsa har aka masa package din
kayan da El-ameen ya siya ya bar wajen yana kallon El-ameen yace "Let move frnd"
wani mugun kallo yayi masa yayi gaba ya bar sa a wajen. Junaid ya dinga dariya ya
bi bayansa, a waje suka ga yarinyar tsaye bakin motar ta, tana ganin sun fito ta
nufe su, Har Junaid xai shiga mota ya tsaya, ta karasowa cikin sakin fuska tace "Am
really grateful, Allah ya saka da khairan" xai yi magana yaji El-ameen ya warce
ledan hannunsa ya xaga ya shige motarsa ya tada ya bar wajen, Junaid ya wara ido ya
bi motar da kallo, haka ma yarinyar ta bi motar da kallon mamaki, can ta maido da
dubanta ga Junaid ta kirkiri murmushi kawai ta juya tace "Sai da safe" ta bar
wajen, Junaid ya sauke ajiyar xuciya sai kuma ya d'aga kafada ya bi bayanta, kusan
a tare suka shiga motarta, ya kalleta yace "Amm drop me plss idan ba damuwa,
abokina ya tafi da motar" ta gyada masa kai tace "Alryt!" Sai da suka hau kan titi
sannan tace "Ina ka nufa?" Ba tare da ya kalleta ba ya gaya mata, ta bude ido tace
"Ohh it's very far, mu nan kusa muke, kaga kafin in kai ka in dawo dare xai yi kuma
Mum xata min fada ne, but nevertheless bari kawai inyi driving xuwa gida idan ya so
sai ka tafi da motar ko gobe sai ka maido min" shiru yayi bai ce komai ba, can yace
"Baxa ace komai a gidanku ba" a hankali tace "I will explain everything to mum"
yace "Toh nagode" cikin mintunan da basu wuce goma ba ta iso anguwarsu tayi parking
kusa da gate din wani kantamemen gida ta juya tana kallonsa tace "Nan ne gidanmu"
yace "Ohhk" bude motar tayi ta fito ta bude back seat ta kwashi kayanta ta rufe
tana kallonsa tace "Tohm sai da safe" bude motar yayi ya fito ya dawo driver seat
yace "Ohk, alryt! Tnx a lot, but sai da yamma xan maido maki motar don da safe nake
fita aiki" tace "Alryt bbu damuwa" har ta fara tafiya yace "Ur Name?" Ta juyo tana
kallonsa tace "Hafsat!" Ya gyada kai yace "Nyc name, am Ahmad Junaid!" Ta d'an yi
murmushi ta gyada masa kai sannan ta juya ta nufi gate dinsu. Tada motar yayi yayi
reverse ya bar anguwar. Sai da ya fara tsayawa gun masu saida fruits ya kuma siya
ma Mumy wani fruits din sannan ya kama hanyar gida. A parking lot yyi park din
motar sannan ya fito ya nufi part din Mumy, Bbu kowa parlon ya ajiye ledan fruits
din ya shiga bedroom din Mumy, ya sameta kwance ya karasa ya xauna gefenta yace
"Mumy na dade ko, kiyi hakuri pls ga fruits din can parlor" tace "Ohk na gode"
mikewa yayi yace "In kawo maki?" Ta mike ita ma tace "A'a bar shi kawai ban jin xan
iya sha kuma bari in sa a fridge" fita tayi daga dakin ya bi bayanta, ya bude
bedroom din fatima ya sameta kwance tana waya Humainah kuma tayi bacci, ya karasa
dakin yana kallon Humainah, murmushi yayi a xuciyarsa yace "Fitinanniya" ya juya
kawai ya fita, a parlor Mumy tace "Gobe idan ka dawo gun aiki wai xaka kai Humainah
gidan Aysha, wai baxa ta xauna ba" shiru yayi bai ce komai ba, can yace "Toh Mumy
kar Abba kuma yayi magana" tace "Ae kwana biyu kawai xata yi ka koma ka daukota"
bai kuma cewa komai ba, har Mumy ta xuba fruits din cikin fridge sannan yace "Sai
da safe Mumy" tace "Allah ya tashe mu lafiya, kayi addu'a kafin ka shiga" yace
"In'sha Allah Mum" daga haka ya fice daga parlon. Yana gama shirin kwanciya ya jawo
wayarsa ya wani hade rai yayi ma El-ameen transfer din dubu talatin da biyar ya
jefar da wayar yayi kwanciyarsa.

Sorry for the short Chappy sisters, I will update you guyz ltr.


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�


22.....

Washegari da safe Junaid ya rasa yanda xai fara ce ma Mumy xai kai Humainah gidansu
El-ameen kamar yanda suka shirya, har ya gama breakfast bai samu courage din gaya
mata ba don yasan dole xata zargi abu, Mumy tace "Kana kallon lokaci ma kuwa" da
sauri ya mike daga dinning ya dau hularsa da waya yace "Am off Mum" tace "Allah ya
tsare, ka shiga gaida Abban ka?" yace "Eh but yana bacci" daga haka ya fice, Hajiya
ya gani tsaye da Umma a bangaren Umman suna kallon bakon motar dake ajiye parking
lot suna kus kus, duk a tunaninsu sabuwa ce, ko kallonsu bai yi ba ya nufi motarsa
ya bude ya shiga, yana warming motar ya hango Khadija a balconynsu tana shara,
y'afito ta yayi, ta ajiye broom din hannunta ta taho, su Umma suka bi ta da harara,
gaishesa tayi, yace "akwai maganar da zamu yi dake a waya, you make sure you are
alone while picking my call kin ji" tace "Alryt big bro" daga haka ya rufe motarsa,
ta koma balcony. Karfe sha daya El-ameen na xaune office dinsa rike da wayarsa yana
jujjuayawa da ganinsa kasan ransa a bace yake, kwafa yayi ya ajiye wayar yana
tunanin walakancin da xai ma Junaid, shi kansa ya rasa gane dalilin da ya sanya ya
kasa cire hannunsa a patient din Junaid, kila don ya fara tausayin yarinyar ne,
sake daukar wayar yayi ya kira Junaid for the 5th time, yanxun ma har ya gama ring
bai daga ba, El-ameen ya fuzar da iska ya ajiye wayar, toh yanxu ina xae samo Wanda
xai kai can gidan ta xauna da ita gashi Karfe sha biyu mama jummai xata tafi, tsaki
ya ja ya jawo files din gabansa, why is he even bothering his self this much, tayi
ta xama ita kadai a gidan after all ba shi ya ajiyeta ba, kwankwasa office dinsa
aka yi ya daga kai yace "Come in" wata nurse ta shigo tace "Sir kana da bakuwa a
waje" ya sauke kafarsa daga kan table yace "is she a patient?" Ta girgixa kai tace
"I don't think so" yace "Ait, let her in" juyawa tayi ta fita ba a dau lkci ba sai
ga ta ta dawo tare da bakuwar, da sallama ta karaso tana murmushi tace "ina yini ya
El-ameen" ya sauke ajiyar xuciyar relieve yace "Lafiya khadija," ta xauna saman
table dinsa tace "Ya Ahmad yace in xo office in same ka" yace "Ya maki bayani ne?"
Tace "Eh daga wajensa ma nake yanxu" kallon agogo yayi ya mike ya dau makullin
motarsa yace "Amma Hajiya baxa ta neme ki ba?" Tace "Gidan kawata nace mata xa ni"
a tare suka sauko reception, ya kalli nurses din yace "If MD shud ask of me tell
him I was called for an emergency" suka amsa masa da yes sir, sannan ya fita
khadija na biye da shi duk suka bi sa da kallo, front seat khadija ta bude ta
shiga, shi ma ya shiga ya tada motar suka bar haraban hospital din. Sai da suka yi
nisa tace "Yaya kai kuma ina ka samo mahaukaciya?" Kallonta yayi, yayi murmushi
yace "Tsarin da ya maki kenan?" Ta d'an bude ido tace "Ehh ca yayi min taimakon ta
kake, a hanya ka tsince ta" dariya El-ameen yayi yace "Gaskiya ne, amma ae shi ya
ban kwarin gwiwan taimaka mata" khadija tace "Toh Allah ya baku lada duka" yace
"Ameen," tace "Toh amma Yaya bata ma mutum komai, ni tsoro nake ji" yace "Bata
komai yanxu, ta d'an saba da mutane, iyaka yanxu kawai xuwa xa kiyi ki xauna da
ita, duk barnar da kika ga xata yi ki hanata, kar kuma ki bari ta fita, sai d'an
potatoe da xa ki soya mata ki cika mata ketchup a ciki," a hankali khadija tace
"Toh, amma ni dai ina jin tsoro" dariya yayi yace "Ke bata komai, you will like
her" suna isa gidan yayi parking a waje ya fita ta bi bayansa, da ganinta kasan a
tsorace take, dariya kawai yake har suka shigo parlon, bbu kowa parlon sai ita
kadai ga 'yar jakar mama jummai da ta hada kaya duk ta watsar da kayan a parlon, da
alamar mama jumman na kitchen, khadija ta labe jikin kofa sai faduwa gabanta yake
tana leko parlon, karasowa kusa da ita El-ameen yayi ya fixge jakar yace "Ke idan
baki yi barna ba baki ji dadi ba ko" daukar kayan tayi ta mika masa, ya fixge ya
ajiye ya xauna ya jawo ta gabansa yace "look. I've brought a new frnd for you, hope
xa ku saba da wuri, she's khadija by name" kallonsa kawai take ko kiftawa bata yi,
yayi murmushi ganin yanda yayi mata maganar kamar wata me hankali, a hankali ya
d'agota ya xaunar da ita gefensa ya juyar da kanta yana nuna mata khadija da taki
karasowa murya can kasa yace "A frnd jewel, ur mate" kauda kanta tayi ta xamo kasa
xata ci gaba da birkita kayan da take, yayi mata tsawa, da sauri ta dawo jikin
kujera tana shisshigewa jiki a tsorace, sosai hakan ya ba khadija da ta kasa daina
kallonta dariya, wani tausayinta ya rufeta ganin irin kyanta amma wai ba hankali,
mama jummai ta fito tace "A'ah Sannu da xuwa Ahmad, har na fidda ran tafiya yanxu
da naga baka xo ba" yace "Warce xata xauna da ita na je daukowa mama, kin ganta
can, kanwar Junaid ce" Mama ta kalli khadija tace "Allah sarki, sannu yarinya
karaso mana" yayi dariya yace "Wai tsoronta take fa" mama tace "Yo ae ita bata
komai wllh" da kyar khadija ta yrda ta shigo tana kallon yarinyar da ita ma ta bi
ta da ido, Mama jummai tace "Amma nan xata dinga kwana da ita koh?" El-ameen yace
"A'a gaskiya xuwa bayan magrib xata koma gida" "Toh wa xai dinga kwana nan da ita"
cewar mama jummai cike da mamaki, ya d'an yi shiru sannan yace "Xan dinga kwana nan
ko kuma junaid" mama jummai ta girgixa kai tace "A'a wannan ba mai yiwuwa bane, ko
kuma kawae in tafi da ita in dai xa ku yrda wannan ba wani abu bane a gu na" Shiru
El-ameen yayi yana kallonta sai kuma yace "Saboda me baxai yiwu ba mama?" Ta xauna
tace "A ina addini ya yarje mana da haka d'an nan" xaro ido yayi sai kuma yayi
dariya ganin inda xancen nata ya dosa yace "kar ki manta mama ba fa lafiya gareta
ba kuma shi ake kokarin ganin an nema mata, karkashin treatment take yanxu, don
haka...." ta girgixa kai tace "A'a gaskiya ba wai ina maku shisshigi bane amma bai
dace ba, sai dai kawae in hada kayanta mu je kuma na maku alkawarin kwana biyu xamu
yi in juyo, kayi mata duk allurorin da xaka mata yanxu" El-ameen ya jinginar da
kansa jikin kujera yana murmushi yace "Komai na hannun junaid mama sai yanda yace"
tace "Toh kirasa" yana ciro wayarsa kiran Junaid ya shigo ya d'aga, Junaid yace
"have you seen khadija?" El-ameen ya hade rai yace "Y weren't you picking my call
daxu?" Bbu yabo bbu fallasa Junaid yace "Was very busy, ya ake ciki yanxu?" El-
ameen yace "Zaka san you were busy ne, mama dai tace xata tafi da ita don bbu wanda
xai dinga kwana da ita a nan," da sauri Junaid yace "What? No, no how can dat be,
idan ta kara gaba fa, No she shud leave her xa mu san yanda xa muyi" El-ameen yace
"Zaka san yanda xaka yi dai" daga haka ya katse wayar ya kalli mama jummai yace
"Kin ji mama wai xai kai ta gun yayarsa ne har ki dawo" mama tace "Atoh hakan ma
yayi bari inje to in hada mata kayanta" El-ameen ya bi ta da kallo har ta haura
sama, ya juya yana kallon khadija dake ta kallonta ko kiftawar kirki bata yi, yace
"Wannan kallon fa" ta kallesa ta sauke ajiyar xuciya a hankali tace "She's so
beautiful brother" murmushi yayi bai ce komai ba ya fara danna waya, tace "wace
yayar ya Ahmad yake fadi" El-ameen yayi dariya yace "Oho" Mama jummai ta sauko rike
da jaka dauke da kaya tace "Ga kayan na hada" El-ameen yace "Sannu mama" kitchen ta
shiga ta fito da plate dauke da potatoe da ketchup a gefe ta ajiye gabanta, El-
ameen yace "Shikenan mama xa ki iya tafiya kar dare ya maki a hanya" Mama tace
"Toh," ta maida dubanta ga khadija tace "Da kin ga ta nufi sama toh kilan bayi take
son shiga, ko kuma tana son xuwa ta xuba ruwa jikinta, tana son tea sosai don Allah
a dinga mata, sai wannan abun da na soya mata da kunu" Khadija tace "Toh" El-ameen
ya ciro dubu talatin ya mika mata yace "Ga kudin mota mama sauran sai kiyi ma mai
jego siyayya" dukawa tayi ta karba tana ta sa masa albarka, ta karasa ta shafa
kanta tace "Sai na dawo diyata, Allah ubangiji ya yaye maki" kamar taji me tace ta
mike da sauri, mama tayi murmushi ta dau jakarta bayan ta gyara kayan da ta xubar
mata, tayi wa El-ameen sallama ta nufi kofa, ai da sauri ta bi bayanta El-ameen ya
mike yyi dariya yace "ta fa gane tafiya xa Kiyi" shigewa jikin mama tayi, mama tayi
dariya tace "Ikon Allah, baxan dade ba 'ya ta jibi xan dawo kin ji" El-ameen ya
karasa ya janye ta daga jikin mama ta fasa wani kara xata kwace kanta yayi mata
tsawa, tsit tayi tana kallonsa, mama ta juya ta fita cike da tausayinta, yana rike
da ita suka koma parlon ya xaunar da ita gefensa hawaye ya gani idonta, khadija ta
xamo kasa ganin hakan a hankali tace "She's crying" kallonta yayi yace "Tafi
kitchen ki debo min ruwa" mikewa tayi ta nufi kitchen din, tana shiga ya dafata ya
lumshe ido a hankali yace "Am sorry jewel, mama xata dawo soon kin ji" dogon
hancinsa ya ji ta ja kamar yanda yake mata ya bude ido da sauri, sai kuma yayi
murmushi ya lakaci nata hancin a hankali yace "Pretty~Jewel"


*Haske Writers Association*
� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

23......

A hankali ya dago kanta yana kallonta, ya ciro handkerchief aljihunsa ya share mata
idonta murya can kasa yace "Am sorry jewel" yana jin fitowar khadija daga kitchen
yayi saurin dauke hannunsa a shoulder dinta ya koma baya, ta karaso parlon ta mika
masa cup din ruwan, ya amsa ya ajiye sannan ya saukar da ita kasa shi ma ya sauko,
dankalin da mama ta ajiye parlon ya jawo ya dauka ya hada da tomatoe ketchup ya kai
bakinta, ta sa hannu ta karba ya sake mata, ta lashe tomatoe din, khadija tayi
murmushi ta dawo kasa d'an nesa da su ta xauna tana kallonta, haka ta dinga shan
tomatoe din kanta a kasa, ya tsura mata ido yana kallo, ta d'ago manyan idonta ta
sauke kan nasa, dauke nasa yayi ya mike ya koma kan kujera yace "tafi kitchen ki
hado mata tea khadija" khadija ta kama hanyar kitchen yana ganin haka ya kuma
saukowa ya dawo ya xauna gabanta ya dau potatoe ya kai mata baki xata kauda kai ya
rike kan ya hade rai ya tura mata dankalin yace "Eat!" taunawa ta shiga yi tana
kallonsa tana yamutse fuska, ya kalli kofar kitchen sannan ya kalli ragowar ketchup
din dake gefen bakinta, ya matso a hankali ya sa yatsa ya kwashe ketchup din ya
lumshe idonsa ya kai baki, dai dai nan aka bude kofar parlon, ya koma baya da sauri
yana goge bakinsa, Junaid ya shigo parlon, kallo daya yayi masu ya sunkuya ya shiga
cire takalmi da safar kafarsa, El-ameen ya mike ya koma kujera yana shafa kai,
karasowa cikin parlon Junaid yayi, yana sanye da trouser din uniform dinsa sai
farin polo, El-ameen na kallonsa yace "Gud you came, so ya xaka yi da ita da nyt?"
Xaunawa Junaid yayi bai ce komai ba, ta dauki plate din gabanta ta mike ta dawo
kusa da shi ta daura kan kafarsa, murmushi ya d'an yi ya rike plate din yace "No!
Thank you" El-ameen ya dauke kai hade da tabe baki, khadija ta fito rike da cup din
tea ta ajiye tana kallon Junaid tace "Welcm bro" yace "Thank you, how about you
telling Hajiya you will be spending the nyt at ur frnd's place?" Shiru tayi sannan
ta langwabar da kai ta xauna tace "Kasan Abba yana nan" shafa kansa yayi bai ce
komai ba ya dauke plate din da ta daura masa a kafa ya ajiye kasa, El-ameen ya
d'aga kafada ya mike ya haura sama, kallon khadija Junaid yayi, tayi murmushi tace
"Wai yaya ka ban labarin inda Ku ka ganta mana, dama kun santa ne?" Junaid yace "I
donno for El-ameen" tablets dinta El-ameen ya dauko a sama ya dawo parlon, sai da
ya fara shiga kitchen yayi diluting dinsu sannan ya fito, ba musu ta bude baki ya
juye mata tana yatsina fuska, Khadija tayi murmushi ta daura kanta jikin Junaid a
hankali tace "I like her Ya A.jay" murmushi yayi bai ce komai ba, El-ameen yace "I
will be going back to clinic yanxu, nan da thirty mins xata yi bacci, duk inda ta
kwanta ki kyaleta kawai" a hankali khadija tace "Ni fa ina jin tsoro, tafiya duk xa
ku yi ku bar mu" El-ameen ya harareta yace "An ce maki bata komai da'alla" Junaid
ya tashi shima yace "Baxata maki komai ba sister, am also leaving" shiru tayi bata
ce komai ba, El-ameen yayi hanyar kofar, Junaid ya bi bayansa, da sauri ta mike ta
nufe su khadija ta bi ta da kallo gabanta na faduwa, gun Junaid ta nufa, El-ameen
ya juya yana kallonsu, shima Junaid kallonta ya tsaya yi, tsaki El-ameen yayi ya
xaro mata ido yace "C'mon koma kar in baki knock" kara ta saki kamar ta ji abinda
yace, El-ameen ya fice daga parlon, Junaid yayi murmushi ya kama hannunta suka koma
parlon ya xaunar da ita yana kallonta yace "Look Jasmine xa mu dawo anjima kin ji,
khadija will be staying with you har mu dawo" Khadija tace "Waow yaya sunanta
Jasmine?" Da sauri ya kalleta don ya manta gaba daya tana gun, yace "Ohh! Did I
call her dat" khadija tayi dariya tace "Ehh mana" ya mike yace "No I didn't" ihu ta
fasa ta mike da sauri ganin ya tashi, Khadija ta langwabar da kai tace "Yaya ba ka
baro gun aiki ba, stay with her plss, bata son ka tafi" yace "Am hungry, gida nake
son tafiya in ci abinci" khadija tace "Ae Akwae food stuffs a nan ba sai in girka
maka ba" shiru yayi sannan yace "Alryt ki min indomie kawai" tace "Toh" ta mike ta
shiga kitchen, xaunawa yayi ya xaunar da ita gefensa yayi murmushi ya ja dogon
hancinta yace "I will stay with you Jasmine" suna nan xaune har khadija ta dawo
parlon rike da tray me dauke da indomie da fried egg a gefe sai roban ruwa da cup
ta ajiye kasa tace "Gashi yaya" saukowa kasa yayi ita ma ya sauko da ita suka xauna
sai kallon indomien take kamar idonta xai fito, murmushi yyi ya kalli Khadija yace
"Ke baxa ki ci ba" ta girgixa masa kai tace "Na koshi" daukar fork din yayi ya debi
indomie kadan ya kai mata baki bayan ya d'an huce, wani kara da yasa shi sakin fork
din tayi khadija ta mike da sauri ta bar wajen, ta dinga ihu tana komawa baya tana
kallon indomien duk ta ruda shi, ya riketa yana cewa "What happen jasmine, bakya so
ne" ihu kawae take tana komawa baya, ya kalli khadija yace "Take it away" dauka
tayi ta nufi kitchen da sauri, tsit tayi ta bi khadija da kallo, ta dawo kusa da
shi ta xauna, shi kam kallon mamaki kawai yake mata, hannu ta sa ta taba long
lashes dinsa, yayi murmushi ya cire hannunta yace "Indomie kike tsoro Jasmine"
khadija ta fito tace "Yaya kila tsoron shi take ji, kaje kitchen ka ci" ya girgixa
kai yace "no idan naje gida xan ci abincin" kallonta Junaid yayi jin ta jingina
jikinsa ya ga bacci ya fara daukarta, ya mike ya kwantar da ita kan kujeran,
khadija tace "Baxa ta fadi ba yaya?" Yace "Ehh, bari in tafi gida in dawo yanxu tun
da tayi bacci" a hankali khadija tace "Toh amma ka dawo kafin ta tashi plss Allah
tsoronta nake ji" Junaid yace "Ohk" yana fita ta dawo kusa da ita a hankali ta
xauna tana kare mata kallo, doguwa ce yar siririya da ita, ta tsura ma kyakkyawan
fuskarta ido da d'an karamin jan bakinta dake sheki, Khadija ta kama long fingers
dinta a hankali tace "I like you sister, Allah ya baki lafiya" kallon hular kanta
tayi ta dawo wajen ta d'an cire hular tana lekan kanta ta ga bakin gashinta sai
sheki yake, fito da gashin ta shiga yi ta bude ido ganin tsayin gashin, ta lumshe
ido tace "Waoww!" Haka tayi ta xama kusa da ita tana kallonta, komai na jikinta me
kyau ne, mamaki ta dinga yi inda suka samota har suke son warkar da ita, to yan
uwanta fa?? Mikewa tayi jin ana kiran la'asar taje tayi alwala tayi sallah, sannan
ta d'an gyara gidan ta dawo ta xauna ta ci gaba da kallonta daga inda ta tsaya,
bude kofa taji anyi ta juya da sauri, taga El-ameen ne, ya karaso parlon yace "Capt
ya tafi ne" ta gyada masa kai, ya iso kusa da su yana kallonta yace "She's still
sleeping koh?" Ta gyada masa kai, ajiye ledan hannunsa yayi ya tada ta ya tafi sama
da ita, khadija ta hade rai ta bi sa da kallo, haka kawae taji haushin abinda yayi,
ta ja tsaki ta dauke kanta hade da tabe baki ta mike ta koma kujera ta xauna, ba a
dau lokaci ba ya sauko, kallonta ya tsaya yi ganin yanda ta hade rai yace "Ke in
kin gaji ne tashi ki tafi gidan ku" mikewa tayi ta dau Jakarta ta fice fuu, yayi
tsaki ya dau wayarsa da ke ring. Tana fita ta kira Junaid yana d'agawa yace "Ta
tashi ne?" tace "Wani tashi? Bayan ya wani ce wai in tafi" Junaid yace "Wa?" Tace
"Ya El-ameen mana, wai wani in tafi gida" shiru ya d'an yi kafin yace "Saboda me?"
Tace "Oho masa, ya wani dauketa ya kai ta daki bayan bacci take" mikewa Junaid yayi
daga zaunen da yake parlon Mumy yace "daki kuma, ke kina ina?" Khadija tace "Ehh
mana, ni na riga na fito ma tafiyata xan yi" katse wayar yayi kawai ya ajiye, Mumy
dake ta kallonsa tace "Wani dakin? Kuma da wa kake waya" Kallonta yayi da sauri don
ya mance tana wajen yace "Ohh dama, dama na aiketa ne, shine... no wai ce min tayi
yayarta ta kulle ta a daki, khadija ce" Mumy na masa wani irin kallo tace "Karya
kake" ya xaro ido yace "Mumy karya kuma" ta girgixa kai tace "Ahmad am beginning to
suspect you this days, behaviours dinka sun fara canxawa, i notice kana boye min
wani abu, but be careful" daga haka ta shiga bedroom, Humainah dake xaune parlon
ita ma tana gyada kai tace "ta tashi ne? uhnn ko waye ya tashi oho, daki kuma? Uhnn
ko wani dakin yake nufi oho, ke kina ina? Uhn ko wacece haka oho, hmm we are
beginning to suspect you this days Captain be careful" wani harara ya watsa mata ta
mike tayi masa gwalo tace "In tayi tsami ma ji dai" da sauri ta shige dakin Mumy
ita ma. Ya shafa kansa a hankali don yasan ko hauka yake baxae bari Mumy taji
xancen mahaukaciyar nan ba, tabdi! mikewa yayi da sauri ya dau makullin motarsa ya
fita, waje ya fita don bai shigo da motarsa compound ba ya hau motar ya nufi gidan
El-ameen, cikin few mins ya isa, yana Parkin ya fito ya shiga gidan, xaune ya tarda
El-ameen balcony yana waya, ya tsaya yana kallonsa har ya gama ya hade rai yace "Y
did you send khadija away?" El-ameen yace "Haka tace maka, to let me get hold of
her" Juyawa Junaid yayi jin an bude gate, wata mace da baxata wuce 27 ba ta shigo,
ta karaso balcony ta gaida Junaid, ya gyada mata kai kawai, mikewa El-ameen yayi
yace "Welcm, ki shiga daga ciki" ba musu ta shiga parlon, El-ameen yace "we are
hiring her for 2 dayz kafin Mama ta dawo, sai ka biyata 10k, old nurse din clinic
din mu ce" Junaid ya daga shoulder yace "Anyhow" juyawa yayi yace "sai gobe, na
tafi" El-ameen yace "Wato xuwa Kayi ka ga what I was up to da nace khadija ta tafi
koh?" Junaid yayi murmushi bai ce komai ba yayi gaba abunsa, El-ameen yayi kwafa ya
shiga parlon. Karfe shidda da wani abu Junaid ya shigo gida, ya ga khadija tsaye
nesa da balconynsu, Hajiya da Umma na xaune sai Sadiya da Suhaima, Sadiya sai cewa
take "Kawai ki bar min komai a hannuna Hajiya idan na lallasa ta xata fadi inda
taje wllh" Umma tace " Ni tun da ta fara mu'amala da shegiyar 'yar da aka kawo
gidan nan Humainah take kowa, dabi'un ta suka canxa, ke har kin kai matsayin da xa
Kiyi karyan xuwa gidan kawa ki fita tun safe sai yanxu kike shigo mana gida don
Kazan ki" junaid ya karasa wajen ya gaida su yace "Hajiya tare muka fita, ta rakani
ne" Umma ta watsa masa wani kallo tace "Da yake ba Aysha bace ko Fatima dole ka
kareta mu bar ta ta lalace" Juyawa khadija tayi fuu ta nufi part din Mumy, Hajiya
ta shiga kwala mata kira tana cewa "Kika kuskura kika shiga wajen nan mai raba ni
da ke sai Allah, kuma wllh kin ji na rantse sai kin fadi daga inda kike"


*Haske writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

24.....

Junaid ya juya shi ma ya bar wajen, Hajiya ta bi bayan khadija tana huci, a balcony
ta tsaya ta tura kofar tana cewa "Kar ki bari in shigo parlon nan khadija, tun muna
mu biyu ki fito ki wuce" tsayawa Junayd yayi yana kallon ikon Allah, Humainah dake
xuge jakar kayanta da ta gama hadawa a parlor ta tabe baki ta mike, ta dauki remote
din TV ta kure maganar gaba daya, Hajiya ta xaro ido tana kallonta, ji take kamar
ta shaketa kawai ta huta, can dai tace "Ke wai ni sa'ar uwar ki ce kika raina ni
haka a gidan nan, ina magana za ki kure min TV?" Humainah ta rike kugu tace "Ni ba
dai uwata ba wllh" Sadiya ta karaso bakin kofar parlon tana cewa "Bata fito bane
Hajiya" Hajiya ta fashe da kuka tace "Yanxu ni yarinyar nan take ma rashin kunya
Sadiya, a haihuwar kaji ban yi jika da shegiyar ba" a fusace Sadiya ta shige parlon
tayi kan Humainah, Junaid na ganin haka ya bi bayanta, ai tuni Humainah tayi dakin
Mumy da gudu tana kwala mata kira, hakan kuma bai hana Sadiya bin ta ba tana
kunduma mata xagi, wani tsawa Junaid yayi mata tun kan ta shiga dakin Mumy ya
fixgota ya nuna mata kofa yace "Get out, ko a mafarki kika kuskura kika yi attempt
din t'aba ta wllh sai na ba66allaki a gidan nan" kallonsa kawai take fuskar nan
nata daure don tasan tana iya magana yanxu ta sha mari, Hajiya ta shigo parlon tana
huci tace "Wllh Ahmad idan ka bari na saka ka gaba a gidan nan sai xaman duniyar
nan gaba daya ta gagare ka, kayi hankali da ni ka bi ni a hankali, bani da kyau
wllh, amma in dai ni ce mu je xuwa sai ka gwammace uwar ka bata haifo ka gidan nan
ba, xaka san da ni kake" Mumy ta fito tana ma Hajiya wani kallo tace "Babu abinda
kika isa ki masa wanda Allah bai masa ba, mu da Allah muka dogara, aniyar ki ta bi
ki kuma" Hajiya tayi shewa tana murmushi tace "Toh mu xuba da ku," daga haka ta
juya fuu ta fice, Sadiya ta bi bayanta. Junaid ya girgixa kai ya juya ya fice daga
parlon, shi gaba daya xaman gidan ma ya ishe sa kawai. Mumy ta kwalo ma Humainah
kira ta fito, strictly tace "ina raba ki da mutanen nan baki ji ko Humainah, ina
ruwan ki da su wai da har xaki dinga shiga tsabgarsu, kinsan Allah baxa mu shirya
ba idan magana za ki dinga dauko min, so kike su sa ki gaba kema koh? To maxa gama
hada kayan ki yanxun nan Ahmad ya tafi da ke inda xai kai ki kafin Abba ya dawo su
kuma hada ki da shi" Juyawa Humainah tayi ta koma daki kamar xata yi kuka, Khadija
ta fito daga daki tace "Mumy kiyi hakuri," Mumy tace "Kinga idan kin yi laifi ki
daina yo wa nan khadija, sai ki tsaya can ki basu hakuri" Khadija ta turo baki ta
koma dakin su fatima. Junaid na shigowa bayan yayi wanka ya canxa kaya Mumy tace
"Maxa kai ta gidan Aisha kan dare yayi Ahmad" ya kalli agogo don dama fita xai yi
ya maida motar jiya, yace "Toh Mumy" Mumy ta kwalo ma Humainah kira tace "Dauko
jakar ki da hijab" tana kumbure kumbure ta fito rike da 'yar jakar kayanta da
Hijab, Junaid ya mike yace "Sai na dawo Mumy" Mumy tace "Allah ya kiyaye, amma
motar waye ka dawo gidan nan jiya da?" Ya d'an shafa kai yace "A frnd, idan na
ajiyeta xan mayar ne ma" Mumy tace "Ohk," ya fita Humainah na biye da shi a baya,
Mumy tayi murmushi tace "Ba sallama Humainah" kamar xata yi kuka ta daga mata hannu
ta fice, Mumy tayi dariya tace "Lallai Humainah" As usual Hajiya da Umma na
balcony, duk suka bi su da hararan tsana, tsayawa yayi har Humainah ta karaso inda
yake ya karbi jakar hannunta suka nufi parking lot, Umma ta kalli Hajiya tace "Ke
wllh naga kamar sonta yake, dubi fa har da wani rike mata jaka, sai ya iya yiwuwa
ma ya fito da ita a matsayin warce xai aura idan lokacin da Alhaji ya dibar masa
yayi" Hajiya ta xaro ido tace "Ae ko da mun banu mun lalace, meye abun yi Bilki?"
Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "ba mu ga ta xama ba,"
Humainah ta kalli motar da Junaid ya shiga tace "Motar waye wannan?" Kallonta yayi
ya bude ido yace "Naki" ta hararesa ta xaga ta shiga, yana warming motar ya kira
El-ameen, bugu biyu ya d'aga, Yace "kana ina ne Dr?" El-ameen yace "ina gida"
Junaid yace "Ohk plss ka fito mu hadu kasan layin ku" El-ameen yace "Why?" Junaid
yace "kai dai ka fito, it's urgent, kuma ka taho da motarka" daga haka ya katse
wayar, ya ja motar suka bar gidan, Humainah tace "Amma ya Ahmad gidan Anty Aysha
aka ce ka kai ni fa xaka wani ce ku hadu a kasan layi, to yawo xaka yi da ni a
mota" ba tare da ya kalleta ba yace "Ni tricycle ma zan je in saka ki yanxu ya kai
ki" ta xaro ido tace "Ehh!" Yace "Yess!" yana isa layin su El-ameen ya hango
motarsa ya isa gun motar yayi parking ya fito, xuge glass El-ameen yayi yana
kallonsa a bit surprise yace "Whose car is dat?" Junaid yace "A good samaritan's,
jiya da ka yasar da ni a titi ka wuce...." El-ameen yayi tsaki yace "Kayi mugun
bata min rai jiyan nan, don me yarinya xata shirga karya wai ta mance Atm card a
gida ka yi amfani da kudina ka biya uban kayan da ta siya" Junaid yace "Ba dai na
mayar maka da kayan ka ba, keep dat matter aside kar kayi provoking dina" El-ameen
ya tabe baki yace "Ni Mama jummai ma na ba kudin da xata tafi daxu, and dat's ur
responsibility not mine" Junaid yace "Whatever, gidan Aisha xaka taimaka ka kai
budurwar nan taka, ni ina son maida motan mutane ne kar ayi tunanin guduwa nayi da
shi" El-ameen ya leka motar suka hada ido da Humainah, da sauri ya dauke kai ya
bude ido yana kallon Junaid, Junaid yayi 'yar dariya yace "Ehh ita din ce" daga
haka ya juya yana kallon Humainah da ta hade rai cikin mota ya duka yana kallonta
da kyau yace " Oya fito saurayin ki ya kai ki ni....." Kuka ta sakar masa tana
yarfe hannu tace "Wayyo ni, wallahi kai aka ce ka kaini bbu inda xan bin sa" ya
bude ido yace "Ke ba motata bace wannan, xan maida ma me shi ne" ta marairaice masa
cikin sigar shagwaba tace "Plss mana ya Ahmad don Allah ka kaini" murmushi kawai
yake yana kallonta, can ya mike ya juya gun motar El-ameen da ya wani hade ya daga
kafada yace "Kaji wai tsoronka take ashe, don haka plss frnd just excort me in
maida motar sai mu tafi gidan Ayshan da naka motar" El-ameen yayi masa wani kallo
yace "I don't have dat time, dama kiran da ka min kenan?" Junaid yayi murmushi yace
"Toh shikenan, idan mun je can xa mu samu tricycle" daga haka ya xaga ya koma
driver seat ya tada motar ya bar layin, tsaki El-ameen yayi ya bi motar da harara
can ya tada nasa motar ya bi bayansa, Junaid na ganin haka yayi murmushi don dama
yasan sai ya biyo sa. Cikin mintunan da basu wuce sha biyar ba ya iso layinsu
Hafsat, yayi parking inda tayi jiya, ya fara kalle kalle don bai karbi numberta ba,
Humainah tace "Ya Ahmad ina ne nan" yace "gidan su budurwata" kallonsa kawai take
ya bude motar ya fita ya xaga ya bude mata ta fito, dai dai nan El-ameen ma ya fito
ya rungume hannu ya hade rai yana kallonsa, murmushi Junaid yayi ya daga kafada ya
nufi gate din gidan, yana danna bell maigadi ya leko, Junaid yace "Amm ina yini,
Hafsat nake nema a gidan nan," Mai gadin yace "Toh bari a mata magana" komawa
Junaid yayi kusa da El-ameen ya tsaya yace "Da ma ka saki ranka kar Humainah tace
ta fasa" shi dai El-ameen bai tanka sa ba, Humainah kam ko kallonsu bata yi ba,
bude gate din gidan aka yi ta fito sanye da jan atamfa sai farin Hijab, xaro ido
El-ameen yayi yana kallonta sai kuma ya kalli Junaid, murmushi tayi ganin Junaid
sai dai lokaci daya murmushin ya bace ganin El-ameen gefensa da tayi, ta karaso
kusa da su ta gaida su, Junaid ne kadai ya amsa don shi El-ameen juyawa ma yayi ya
shige motarsa, banda kallonta babu abinda Humainah take, Junaid ya shafa kansa yace
"Ga motar ki, tnx a plenty, am grateful" ta kirkiri murmushi kawai tana gyada masa
kai, ya mika mata makullin motar ta karba, ya kalli Humainah yace "ga kanwata can
ku gaisa" karasawa tayi gun Humainah tana kallonta murmushi dauke fuskarta tace
"Sannu, ina yini?" Humainah ta dauke kai babu yabo bbu fallasa tace "Lafiya" juyawa
tayi ta bar wajen duk jikinta yayi sanyi, ta kalli Junaid tace "Toh nagode" yace
"Ni ne da godiya" kallon Humainah yayi yace "Taho mu wuce" kamar xata tashi sama ta
karaso ta bude bayan motar El-ameen ta shige, Junaid ya ciro wayarsa ya mika ma
Hafsat yace "Sa man digit dinki mu dinga xumunci" karba tayi ta sa numberta ta mika
masa suka hada ido da El-ameen dake kallonsu, da sauri ta dauke kanta, shi ko ya
tabe baki, Junaid ya mata godiya ya xaga ya bude front seat ya xauna, El-ameen ya
figi motar suka bar layin. Sai da suka hau main road El-ameen yace "Da nasan inda
xaka kenan wllh ban xuwa, yaushe ka xama haka Captain, yaushe ka fara ware ma mace
lokacin ka har da wani karban numberta, Tabdi" har suka iso gidan Aysha ana kiraye
kirayen Magrib Junaid bai ce ma El-ameen komai ba, ya juya yana kallon Humainah
yace "Toh gashi mun kawo, ki gaida ta" daukar jakarta tayi ta bude motar ta fice ta
nufi gate, Junaid ya bi ta da kallo sai kuma ya bude motar ya bi bayanta, tsaki El-
ameen ya ja ya danna masa horn, har gate Junaid ya shiga ya fixgota ta hade rai
tace "Meye kuma" ya wara ido xai yi magana, ta fashe da kuka, kallonta ya tsaya yi,
can ya d'ago kanta yace "What happen?" Ta fixge hannunta taki cewa komai, yace
"Baki son xama gun Ayshan ne kuma?" Ta girgixa masa kai tana goge hawayen dake kuma
sakko mata tace "To wace wannan yarinya" kallonta kawai yake sai kuma yayi murmushi
ya ciro wayarsa daya a aljihu ya mika mata yace "Anjima xan kira ki in gaya maki
wacece" juyawa tayi zata bar wajen ba tare da ta karba wayar ba, ya kuma dawo da
ita ta fashe da kuka, murmushi yayi ya kama hannunta ya saka wayar, ya juya ya fita
daga gate din don El-ameen ya danna horn ya kusa sau biyar, yana shiga motar El-
ameen ya figi motar yana cewa "Wai meyasa kake min abinda ka ga dama ne Capt, ka
wani shanya ni a mota kana biye ma karamar yarinya 'yar cikin ka, ga baiwar Allah
can ko abinci nasan bata ci ba...." Junaid yace "Budurwar ka fa na rako" El-ameen
ya tabe baki yace "No, ni ban ce ina sonta ba kawai nace tana da kyau ne, kuma ni
ba budurwa ta bace, warce nake so ma ta fi ta komai" dariya Junaid yayi yace "Xa ma
ka fadi gaskiya ne, a ina ka samo warce kake son kai da kake tsoron mata" El-ameen
yace "Am serious, ni bana son mace me tsiwa da jaraba, warce nake so is very
gentle...." Junaid yayi dariya yace "Ita ma bata son mai tsoron mace" El-ameen yayi
tsaki yace "Can gidan fa nake son in je don nasan baxata ci abinci ba sai naje
shine ka wani bata min lokaci" Junaid ya tabe baki yace "Irin kamar ka damu da ita
din nan koh" El-ameen yace "Of course na damu, nama fi ka, kai da baka da aiki sai
na bada kudi, ni kuma lokacina gaba daya na bata, a yanxu haka I know her likes nd
dislikes, duk motsin da xata yi nasan me yake nufi, I've studied her more than you
can imagine, kai you are only showing dat you are a millionaire kana nuna kai kadai
ma xaka iya kashe ko nawa ne ba sai ka nemi assistant ba, ni kuma...." Junaid ya ja
tsaki yace "Aikin banxa kenan, don without that money you are talking about all
this you are listing won't come to action, kai da kake kyashin kashe mata naira
biyar din ka, my frnd ka daina listing kan ka a wa enda suka taimake ta ma a
rayuwa, you are only decieving ur self, coz I hired you and am paying you for the
job, yau nace bana bukatan service dinka you are gonna quit!" Parking El-ameen yayi
yana kallonsa yace "Haka kace Ahmad?"


*Haske Writers Association*

*Captain Ahmad Junaid*


_By Khaleesat Haiydar_
25....
Junaid yayi dariya yace "Of course haka nace ko nayi karya, ka fadi sisin da ka
taba kashe mata in biya ka, kai yanxu har ka nuna mun ka fi ni damuwa da ita, wanda
da na biye ka tun farko da baxa mu daukota ba ma, wani irin discourage dina ne baka
yi ba, wani irin dariya ne baka min ba kan yarinyar nan..." El-ameen bai ce komai
ba ya ci gaba da tukin sa, banda dariya babu abinda Junaid yake, ganin El-ameen
hanyar gidansu ya nufa Junaid yace "Ohh ka fasa xuwa ka bata abincin ne?" Shi dai
El-ameen bai tanka sa ba har ya isa bakin gate din gidansu, ya juya yana kallonsa
yace "Idan kaga na kuma bi ta kan patient dinka, ka gaya min wanda ya fi wannan,"
daga haka ya fice daga motar ya shige gida. Junaid yayi murmushi yana shafa kansa
yace "Uhum wai fushi yayi?" D'aga kafada yayi ya koma driver seat ya ja motar ya
bar layin, gida shi ma ya nufa abun sa. Washegari Junaid na gun aiki ya dinga kiran
El-ameen ya ki d'agawa, shi dariya ma abun ke basa, don bai ga abun fushi ba daga
fadin gaskiya, Karfe biyar ya baro gun aiki, ya canxa uniform din jikinsa xuwa
mofti ya tafi can gidan nasa, a hankali ya tura kofar parlon, nurse din dake kula
da ita na tattare biscuits din da yayi littering din tsakar parlon, ita kuma tana
kwance nan kasa tana bacci, Junaid ya karaso ya amsa gaisuwar da nurse din ke masa
yace "Dr El-ameen ya xo yau kuwa?" Ta girgixa kai tace "Bai xo ba, na kirasa ma
he's not responding" Junaid yayi murmushi ya xauna yace "Ohk, amma ta ci abinci?"
Nan ma ta girgixa masa kai tace "tun jiya ma taki cin komai, kaga biscuit din nan
ma na fiddo mata shima bata ci ba ta watsar, yanxun ma da kyar ta kwanta tun safe
taki xama na rasa me take nema, duk ta ki yarda da ni" Junaid yace "Ohk, me yace
maki ta fi so, I mean abinda take ci?" Tace "Kasan yace xai dawo jiya toh bai dawo
ba bare ya gaya min, kuma duk yau ba a mata allura ba tunda bai gaya min yanda zan
yi ba" Tabe baki Junaid yayi ya mike ya fice daga parlon. Gidansu El-ameen ya nufa
Ummi tace ai tun safe yana clinic, ya mata sallama ya fito ya kama hanyar clinic
din, Yana isa nurses din dake reception suka ce masa ai baya nan, yace "Ohk haka
yace maku ku ce min idan na xo" kallonsa suka tsaya yi, ya haura sama ya tafi
office dinsa, ya murda kofa yaji da gasken baya nan, tsaki yayi ya sauko ya fice
daga asibitin, a mota ya dinga kiransa ya ki dagawa, shi ya rasa abun jin haushi a
maganarsu ta jiya, daga fadin gaskiya, tsaki yayi ya tada motarsa ya tafi gida abun
sa. Wasa wasa har 2 dayz El-ameen yaki xuwa can gidan, ya ma kashe wayoyinsa gaba
daya, shi ma Junaid ya fita harkarsa bai kuma bin ta kansa ba, matsalarsa daya
yanda Jasmine taki cin komai, gashi da ganinta xaka san abu na damunta, duk taki
sakin jiki, though in yaje gidan da yamma ta kan je ta kwanta gefensa ko ta xauna
kusa da shi, amma duk yanda xai yi da ita ta ci abinci bata ci, sai dai k'adan shi
ma da kyar, in ya takurata tayi masa ihu, bini bini xaka ga ta kalli kofa ko taje
can ta tsaya kamar dai tana jiran wani, on the third day Mama jummai ta dawo ya
sallami nurse din, yasan yanxun xata fara cin abincin tunda ga mama jummai kila
dama don bata saba da nurse din bane amma sai yaga otherwise don yi ma tayi kamar
bata taba ganin mama jumman ba, ta kuma ki cin abincin still, da mama jummai ta
tambaye Junaid El-Ameen ce mata yayi, yayi tafiya ne, duk abinda mama jummai tasan
tana so sai da ta yi ta bata duk taki sai ketchup da take ta sha, duk baiwar Allahn
ta rame. Yau Junaid na barin gun aiki ya nufi gidansu Faisal, yayi sa'an shi ma
dawowan shi daga aiki kenan, Faisal yayi mamakin ganinsa barin da yaga ko canja
uniform din jikinsa bai yi ba. Junaid ya xauna bayan sun gaisa yace "Ina son muyi
wata magana da kai ne frnd" Faisal ya maida hankalinsa sosai yace "Am ol ears"
Junaid ya shafa kai a nutse ya soma basa labarin mahaukaciyar tun daga farkon
haduwarsa da ita, Faisal ya kwalalo ido yana kallonsa baki bude, har Junaid ya kai
karshen labarin yana murmushi, Faisal ya sauke ajiyar xuciya yana gyada kai yace
"Babban magana, but El-ameen bai kyauta ba, kuma ni ban ga abun fushi a nan ba,
sabon da tayi da shi ne ya hanata sakin jiki da bata ganinsa, shiyasa take kin cin
abinci!" Junaid ya tabe baki yace "Yanxu dai you are a Doctor, so nake plss ka gaya
min yanda xaman psychiatry yake, is it advisable in kai ta can babu matsala?"
Faisal ya kuma sauke wani ajiyar xuciyar yace "Gaskiya ina ga na gida kamar yanda
El-ameen ke mata ya fi, kuma gashi har ta saba da shi samun lafiyarta ba lallai ya
dau lokaci ba, yanxu dai kar ka damu xan je in same sa, nasan..." Junaid yace "No!
no bana bukatan sa kuma, he shud hold on to his medication, idan taje psychiatry
din suma xata saba da su" murmushi Faisal yayi, Junaid ya mike yace "Plss ka
binkitar min psychiatryn da ka ga is ohk... I might come back later ko kuma in kira
ka. Don yanxu Mumy xata fara kirana its almost six o'clock" Faisal ya bi sa da
kallo har ya fita sannan ya shafa kai yace "Lallai Junaid da El-ameen, mahaukaciya
kuma???" Mikewa yayi shi ma ya dau makullin motarsa ya fita xuwa gidansu El-ameen
din, Ummi ce da Sumayya xaune parlor, ya gaida Ummi, ta amsa da fara'a tana
tambayarsa mutan gida yace "Duk Suna lafiya Ummi, El-ameen na nan kuwa" tace "Ehh
yana daki" dakinsa ya nufa ya tura kofar ya shiga da sallama, Ummi ta kalli Sumayya
tace "Ki kai masa drink, ki tambayesa ko xai ci abinci" mikewa tayi ta nufi
kitchen, kwance faisal ya sami El-Ameen da laptop a gefensa sai dai wayarsa yake
dannawa, El-Ameen ya mike xaune ganinsa, Faisal yana murmushi ya karaso ya xauna
gefensa yace "Yane the great Dr Ahmad El-ameen" El-ameen yayi murmushi shi ma ya
mike xaune yace "Daga ina haka da yamma?" Faisal na kallon fuskarsa ganin yanda
manyan idanuwansa suka fito yace "You look pale, are you ohk?" El-ameen ya lashe
lebbensa yace "Stress ne frnd, ya aikin?" Faisal yace "Alhmdllh, Ya captain
naka...." Dai dai sanda Sumayya ke kokarin shigowa dakin da faranti me dauke da
drink da ruwa jin an ambaci Junaid ta tabe baki ta tsaya jikin kofar, El-ameen yace
"Yana gidansu!" Faisal yayi dariya yace "Kuna nan har yanxu kamar 'yan biyu abun
ku" El-ameen yayi murmushi yace "Sure!" Faisal yace "Uhmm!" El-ameen na kallonsa
yace "Ya aka yi?" Faisal yayi murmushi yana girgixa kai yace "Bana tunanin akwai
abinda ya isa ya hada ka da Captain..." Sumayya ta gyara tsayuwa da kyau ta baxa
kunnuwa, El-ameen yace "Ban fahimta ba" Faisal yace "Daxu ya xo ya sameni ya kuma
ban labarin baiwar Allahn da ku ke kokarin ganin kun ceto rayuwarta daga....." El-
ameen ya katse sa yace "No! Da yake kokarin ganin ya ceto rayuwarta dai" Faisal
yayi murmushi yace "Haba Dr, bayanin da Captain yayi min is not enough ace kayi
fushi haka, kuma naga kun saba haka a tsakanin ku, kar ka manta lada ba kadan ba
xaka samu idan yarinyar nan ta dawo hankalinta" El-ameen yace "No ni bn yi fushi ba
faisal, just dat nayi quit ne, ya nemi wani likitan ko ya kai ta psychiatry..."
Faisal yace "No pls, kar kace haka Dr, ba don Junaid xaka yi ba don Allah xaka
yi...." El-ameen yayi murmushi yana girgixa kai yace "You know what?" Faisal ya
girgixa kai, yace "Wllh wllh ban yi kuma, I've quit, he shud take her to the
psychiatry, ka dai ji rantsuwar musulmi na maka, but babu damuwa xai iya ci gaba da
amfani da gidana" Sumayya dake jikin kofa har lokacin duk tayi confuse ta rasa gane
kan maganar, to wace yarinya suke magana a kai, yanke shawaran kiran Suhaima tayi
tasan xata bata labari, El-ameen ya mike yace "kaga am going to clinic yanxu
faisal" faisal ya sauke ajiyar xuciya yace "Ban ji dadin rantsuwar da kayi ba El-
ameen, don Allah xaka yi ba don Junaid ba" El-ameen ya koma ya xauna yace "Look
faisal, kullum! I mean everyday, karfe bakwae na safe baya karasawa nake barin gida
in tafi gun yarinyar don akwai injections din da nake mata a lokacin, before
leaving kuma sai na tabbatar tayi breakfast dat's around to eight, ina barin gidan
xan kuma dawowa nan gida inyi wanka in shirya inyi breakfast snn in tafi clinic, a
can clinic duk abinda nake da xaran sha daya da rabi yayi xan bari koma meye kuwa
in tafi gun yarinyar don bata drugs dinta, in tilasta ta taci abinci sannan in kuma
komawa clinic, duk abinda nake Karfe uku da rabi xan bari in kuma komawa gun
yarinyar don bata drugs, sannan in sake komawa asibiti, Karfe bakwai da rabi a
gidana yake min don a wannan lokacin ma tana da injections, baxan kuma bar gidan ba
sai after ten don kafin ta kwanta Akwae drugs da xata sha, kasan sau nawa Junaid ke
xuwa gidan?" Faisal yayi shiru yana kallonsa, El-ameen yace "Sau daya! shi ma sai
da yamma ko kuma after magrib, kuma da ya xo xaka yi tunanin tsikararsa ake a gidan
da kayi magana yace maka Mumy, ni ne ban san dadin tawa Mumyn ba, kasan matsalar da
nake fuskanta yanxu gun parent dina kan yarinyar nan kuwa? yace ko biyar ban taba
kashe mata ba I agree kuma dat is as a result of yana nuna shi me kudine, baya
bukatan assistant din kowa, kasan dai yanda yake abubuwansa na girman kai, ni kuma
kallonsa kawai nake don in kudin account dinsa sun yi wuta wllh basu wuce million
uku ba in ma sun kai, kuma medication din hauka ba karamin kudi mutum xai kashe ba,
yau da gobe yana cire dubu Dari dubu hamsin dubu dari biyu, dole kudin xai yi kasa,
at dat time ko waye ubansa dole xai ce min i shud help ni kuma hakan nake jira
dama, don kai kanka kasan waye ni idan baka tambayeni ba wllh baxan baka ba, in ko
ka tambaya ko last card dina ne xan baka, kuma yace inyi excluding kai na a wa enda
suka taimaketa a rayuwa tuni nayi hakan, don haka ka rakasa ya kaita psychiatry
kawai frnd"
*Haske Writers Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�


26.....

Mikewa faisal yayi ya d'aga kafada ya nufi kofa, da sauri Sumayya ta bar jikin
kofar ta shige dakinta rike da farantin jin takunsa, faisal yayi ma Ummi dake
parlor har lokacin sallama ya fita daga gidan, El-ameen ya koma ya kwanta tare da
lumshe idonsa. Suhaima ce ta shigo parlor rike da waya tana kallon Hajiyarsu tace
"Hajiyarmu yanxu sumayya ta kira ni...." Da sauri ta kalli khadija da ke kwance
parlon sai kawai ta juya ta koma daki, Hajiya ta mike ta bi bayanta, khadija ta
tabe baki ta ci gaba da danna wayarta. Junaid na kwance parlon Mumy that same day,
idonsa lumshe kamar me bacci kamar wanda ya tuna abu ya mike xaune yana kallon
wayarsa ya dauka yayi dialing number bugu uku aka d'aga, bayan sakwanni 20 jin ba
ace komai ba daya bangaren yace "Uhn how you?" Jin an ki cewa komai still, yace
"sai in kashe wayata ne" kamar xata yi kuka tace "Toh ina ruwana ni nace ka kira"
murmushi yayi yace "Ohk, sai anjima" da sauri tace "Noo Ya Ahmad don Allah ka xo ka
dauke ni, gida nake son dawowa" yace "Anki, xaman ki a can ya fi maki, sai kiyi ta
neman fitina da Jawahir!" Katse wayar yayi ya ajiye yana murmushi, can ya mike ya
fita ya koma part dinsa don tun da ya dawo daga gun faisal yake kwance parlon Mumy
ko uniform bai cire ba, yana bedroom ya fito daga wanka yana shiryawa yaji an murda
kofar parlor, juyawa yayi yana kallon kofar dakin har aka bude, faisal ya shigo da
sallama, Junaid ya sauke ajiyar xuciya yace "Glad you came" faisal ya karaso ya
zauna gefen gado yace "ka jira har El-ameen ya sauko Captain, yayi sama da yawa,
beside ni ban...." Da sauri Junaid yace "Xuwa kayi ka samesa?" Faisal ya d'aga masa
gira, Junaid yace "Ohhh shit! Why? Meyasa xaka min haka, why did you go faisal,
gaskiya ka bata min rai, who's he da yake tunanin without him Allah baxai bata
lafiya ba, shi din banxa, bana bukatansa a lamari na kuma, bana bukata...." Faisal
yayi murmushi yana girgixa kai yace "Haka kawai in sa baki daga karshe in ji kunya,
da dai ban san ku bane, duk ku yi ku gama" Junaid yayi tsaki ya ci gaba da shirin
sa, yana gamawa ya juya yana kallon faisal yace "Ka sama min psychiatry din ne
frnd?" Faisal yace "Psychiatry me kyau sai Abeokuta or Lagos, but I will advice you
to take haka to na Abeokutan ya fi, Neuro Psychiatric hospital Aro" Junaid yace
"Har Ogun state? No plss samo min a nan north" faisal yace "Toh ai na can yafi
komai ne, ga qualified neurologist..." Junaid ya xauna gefen gadon yace "Abeokuta
kuma? Or kasan me I shud just look for a private neurologist for her...." Faisal
yayi murmushi yace "That's money frnd, hospital ya fi!" Junaid yayi shiru, sai kuma
ya shafa kansa a hankali yace "Allah xai rufa asiri, just get me a qualify one"
faisal yace "ohkk dats not a problem, duk dai yanda ta yiwu in na gidan in na
hospital," Junaid ya gyada kai yace "Toh shikenan" faisal yace "Sai da abu ya kwabe
maku sannan xa a wani xo a sameni.... Ni kallonku kawai nake kai da El," Junaid
yayi murmushi ya mike yace "Kaga xan kai mata fruits can gidan yanxu, muje part din
mumy sai inyi kamar rakaka xan yi" faisal yayi dariya yace "Plss do and get ur
freedom captain! You are getting old fa Mumys boy!" Junaid yace "Uhum kaga in
tafiya xaka yi ka taso mu tafi!" Mikewa faisal yayi ya bi bayansa yana dariya, suka
nufi part din Mumy, faisal yayi mata sallama, Junaid na shafa kai yace "Mumy bari
in rakasa!" Mumy tace "Toh sai ka dawo" fita suka yi faisal na dariya, Suhaima dake
tsaye bakin tap ta bi su da kallo tana tunanin xancen da Sumayya ta mata a waya,
ajiyar xuciya ta sauke tana tunanin ta ina xata fara binciken da Hajiya ta sa ta,
wai Mahaukaciya, tab, har Allah Allah take washegari yayi! Suna fita gidan Junaid
ya kalli faisal yace "Kaga ban fito da mota ba, da taka xa mu je can gidan daga can
sai ka ga Mahaukaciyar," faisal ya buda ido yace "Da take neman hada aminai biyu
ba!" Junaid ya tabe baki yace "No bata hada mu ba, frndship din ne ya xo karshe
dama" dariya kawai faisal yake, Junaid ya karbi makullin hannunsa ya shiga motar ya
tada. A hanya suka siya fruits sannan suka kama hanyar gidan El-ameen, mama na
sharan parlon suka shigo, ta mike tana masu sannu da xuwa, Junaid sai kalle kallen
inda xai ganta yake, mama jummai ta lura da hakan ta nuna masa gefensu tace "Ga ta
can" juyawa yayi ya ganta xaune ta jingina da bango ta d'an dukar da kai alamar
bacci take, xai yi magana Mama jummai tace "Babu yanda banyi da ita ta bar wajen
nan ba ta ki, kuma ta ki kwanciya, ni dai na rasa gane kan baiwar Allahn nan, ko
abinci taki ci, dama Aminu kadai yasan kanta, rashin cin abincin nan ba karamin
daga min hankali yake ba, toh ko dai bata da lafiya ne" Junaid ya tabe baki bai ce
komai ba, faisal kuwa kallonta kawai yake, duk da ba ganin fuskarta yake ba, Junaid
ya kallesa sannan ya karasa kusa da ita ya duka kamar me rada yanda bbu wanda xai
ji sa a hankali yace "Jasmine!" D'ago kanta tayi da sauri ta bude ido tana
kallonsa, a hankali faisal ya dinga komawa baya yana kallonta ko kiftawa bai yi har
ya isa jikin kofa bai sani ba, kalle kalle kawai take sai kuma ta mike tana kallon
kofar jin alamar mutum, da sauri ta nufi kofar Junaid ya bi ta da kallo, tana isa
bakin kofar ta tsaya tana kallon faisal, still yayi a wajen ko kwakkwaran motsi bai
yi, har lokacin idonsa na cikin nata, juyawa tayi a hankali ta dawo kusa da Junaid
ta xube gabansa ta xauna, kallo daya xaka mata ka ga ramar da tayi, mama jummai ta
fara dariya tace "Wayyo, ca take Aminu ne baiwar Allah, to ko don bata ganinsa yasa
taki sakin jiki ne? Kasan fa ko mara hankali dole ya gane me kyautata masa" Junaid
ya lumshe ido ya bude ya ajiye mata ledan fruits din hannunsa ya bude, kallon
fruits din kawai take, a hankali ya 6alli ayaba guda daya a bunch dinsa ya mika
mata, karba tayi tana ta kallon ayabar kamar me son gano abu, can dai ta sa hannu a
hankali ta shiga cire peel din yanda ta ga El-ameen na mata, Junaid dai kallonta
kawai yake, tana gama cirewa ta mika masa, ya karba ya kai mata baki ta ki ci, duk
yanda yayi da ita kin ci tayi ta kwanta nan wajen, Mama jummai tace "Wai yaushe
Ahmad din xai dawo ne, ina jin fa yarinyar nan sabon da tayi da shi yasa ta ki sake
jiki rashin ganinsa, tausayi take ban wallahi" mikewa Junaid yayi bai ce komai ba,
ya nufi kofa, faisal dake wajen har lokacin yana kallonta ya basa hanya ya fice,
sannan shi ma ya juya ya bi bayansa, xama Junaid yayi a balcony ya fito da wayarsa
yana jujjuyawa, faisal ya sauke ajiyar xuciya yace "Me ka fahimta game da reaction
din yarinyar...." Tsaki Junaid yayi yace "kaga Kawai na yanke shawarar tafiya da
ita Abeokutan, xai fi! Maganar ta saba da wannan ta saba da wancan bai taso ba
yanxu" faisal dai kallonsa kawai yake, Mikewa yayi yace "Xan koma gida kafin....."
Faisal ya katse sa yace "Haba Captain kana jin ance tun safe bata ci komai ba sai
kace xaka tafi, ko da milk ne ka siyo a gwada bata mana" Junaid yace "Yea! But I
don't want my mum to start calling me, bayan bakin gate kadai nace xan raka ka, do
me a favour by buying the milk and bringing it to them, ga Atm card dina" kallonsa
kawai faisal ke yi, har ya fiddo card din ya mika masa, can ya girgixa kai yace
"Nima yanxu Mumyna xata kira ni" Junaid yace "Ohk then! Let me send the gate
keeper!" Daga haka ya nufi gun mai gadi, faisal ya girgixa Kai ya koma parlon, ai
tana jin an tura kofa ta mike da sauri, faisal ya rungume hannayensa yace "Poor
you!" Komawa tayi a hankali ta xauna. Ya juya ya fita daga parlon wani tausayinta
na shigarsa, anya ba asiri bane wannan, ban da haka me yayi mata xafi haka har ya
kai ta ga hauka at her young age!" Ko da ya fita har Junaid yayi masa gaba da
motarsa, tsaki kawai yayi ya nufi titi don hawa tricycle, ko waye bai son uwarsa???

Washegari Junaid na office ya kira faisal, bayan sun gaisa yace "Plss frnd make
arrangement for me ko xuwa gobe ko jibi sai a tafi da ita can din, ta flight"
faisal yace "Who's going der with her?" Junaid yace "Yea xan ce ma Mumy an min
transfer din sati daya xuwa lag, kaga kafin sati dayan duk xa ayi abubuwan da ya
kamata, bari dai xan xo idan na bar gun aiki sai muyi magana" faisal ya tabe baki
yace "Ohk," sannan ya katse wayar. El-ameen ne xaune office ya hade kai da table,
ya ji an bude kofar office din, dagowa yayi da sauri don ganin waye, sanin ya gaya
ma nurses din ya gama attending ma patients for that day, ganin faisal ne ya kalli
agogo yaga uku ya gota, faisal ya karaso yace "What's the problem El?" El-ameen ya
shafa kansa tare da lumshe ido yace "Bacci!"


*Haske Writers Association*馃挕

Thanks all for the prayer Allah bar xumunci.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_Khaleesat Haiydar_�
27.....

Faisal yace "Uhn wai bacci!" Kallonsa kawai El-Ameen yake da lumsassun idonsa,
faisal ya xauna kan table yace "Ya aikin?" El-ameen yace "Alhmdllh" faisal yayi
murmushi yace "Abokin ka xai tafi da patient din ku Abeokuta soon..." El-ameen ya
d'aga kafada yace "Dat's nyc, Allah ya bada sa'a, ita kuma ya bata lafiya," faisal
yace "Ameen, and you know what?" El-ameen ya girgixa kai, faisal yace "Ta ki cin
komai yarinyar, from all indication, she is missing you" El-ameen ya girgixa kai
yace "No! Idan aka takurata kuma aka tsoratata xata ci" faisal yayi shiru, sai kuma
yace "Don Allah ku bar wannan childishness din kai da Junaid ku hada kai ku taimaki
baiwar Allah, ni banga abun xuciya a nan ba, ga yarinyar 'yar karama da ita...."
El-ameen ya hade rai yana kallonsa yace "Look nace banyi kuma, ba gashi xai kaita
asibiti ba, don Allah ka bar ni in ji da abinda ke damuna" shiru faisal yayi kafin
yace "But ni ina tunanin anya ba asiri aka mata ba, banda haka me xai ja mata brain
disorder at her young age...." El-ameen ya girgixa kai yace "Na fa yi diagnosing
dinta, brain disorder ne, she's suffering from post-traumatic stress disorder!"
Faisal ya d'an bude ido yace "And what's the cause?" El-ameen ya lumshe ido ya bude
yace "Serious accident, sudden demise of love one, terrorist incident, a lot of
them..." Faisal ya sauke ajiyar xuciya yace "Allah sarki, Allah ubangiji ya bata
lafiya" El-ameen yace "Ameen!"

Kusan a tare Junaid ya shigo compound da Suhaima da tayi kamar bata san mota ce
bakin gate din ba sai tafiyarta take, ya kusa bugeta da motar ya nufi parking lot
abun sa, bude baki tayi bayan tayi tsalle ta bar wajen ta bi motar tasa da kallo,
ya fito ya rufe motar ya nufi part din Mumy, tsaki tayi ta shige part din Hajiyarsu
tun daga parlor ta dinga kwala mata kira ta fito da sauri, Suhaima tace "Uhn in
gaya maki haka maganan take Hajiya, Mahaukaciya Ahmad ya tsinta yanxu haka tana
gidan El-ameen ana kula da ita wai, don ma Sumayyar bata san gidan bane da mun je"
Hajiya tana tafe hannu baki bude tace "Ikon Allah, mahaukaciya kuma? xan ko je in
samu uwar Aminun yanxu ba sai gobe ba" Suhaima tace "Amma fa Hajiya xai ma iya
yiwuwa Khadija ta san komai" Hajiya tace "Ae baxa tayi magana ba shegiyar, bari ina
zuwa in je gun balki mu san abun yi" dankwali ta dauka ta fice tayi bangaren Umma.
Junaid na bude kofar Mumy Humainah dake labe jikin kofar tayi masa k'ara a fuska,
turata yayi har sai da ta kusa faduwa ya hade rai yace "baki da hankali ne"
kallonsa ta tsaya yi kamar xata yi kuka, ya galla mata harara ya juya ya fita daga
parlon, parlon sa ya tafi ya kwanta, duk ya rasa me ke masa dadi, bayan isha yana
xaune parlor Fatima ta tace Abba na kiransa, bai tanka ta ba har ta fita sannan ya
mike ya fita ya tafi part din Abban, Mumy ce parlon tana yanka masa watermelon sai
Umma da ita ma shigowarta kenan, ya xauna kasan rug din tsakar parlon yana kallon
Abban nasa yace " Sannu da dawowa Abba" Abba yace "Yauwa, ya maganar mu ta ranan
ban ji ka sake cewa komai ba" Junaid ya d'ago da kyar yana kallonsa, a hankali yace
"ina sane Abba..." Abba xai yi magana Umma ta riga sa tana murmushi tace "Toh ko
dai har yanxu baka samo mana surkar bace Ahmad" ko kallonta bai yi ba bare ya tanka
ta, Mumy dai bata ko kallesu ba tana ta yankar kankanar gabanta, Abba yace "Toh ina
sauraranka, don kwanakin da na dibar maka ya kusa" kai kawai Junaid ya iya kada
masa ya mike ya fita daga parlon jikin sa a sanyaye, part dinsa ya koma ya kwanta
duk jikinsa ba kwari, shi yanxu a ina xai samo mata ana xaune kalau gashi sati daya
da 'yan kwanaki kadai ya rage a kwanakin da Abba ya dibar masa, gaba daya daren
ranan kasa baccin kirki yayi, ya mike ya dauro alwala ya fito ya hau sallahn nafila
a dakin, washegari da safe haka ya shirya cikin rashin kuzari ya tafi gun aiki, da
ka gansa kasan akwai damu tattare da shi sosai, after Asr ya nufi gidan El-ameen,
driving kawai yake amma gaba daya hankalinsa bai jikinsa ga wani mugun sara masa da
kansa yake, ya rasa wanda xai gaya ma damuwarsa a lokacin, da da ne da yanxu ya
kira El-ameen ya sanar da shi, yana isa gidan yayi xaman sa cikin mota bai fito ba
har bayan kusan rabin awa, can ya fiddo wayarsa yayi dialing number faisal, bugu
biyu faisal ya d'aga, Junaid ya lumshe ido yace "Plss faisal ka taho gidan El-ameen
if you are less busy" faisal yace "Ohk" katse wayar Junaid yayi, sai ya ji kamar ya
kira El-ameen sai ya fasa, yana nan xaune har faisal ya iso layin bayan kusan minti
ashirin, Yana gama parking ya fito Junaid ya danna masa horn don ya gane yana cikin
motar, faisal ya nufi motar ya bude yana kallonsa yace "Mummy's boy...." Shiru yayi
ganin yanayinsa, can ya shiga motar yace "Ya aka yi Captain" Junaid ya lumshe ido
ya bude kamar baxai ce komai ba, faisal ya tabe baki yace "Haka fa, ni ba El-ameen
ba ina kai ina gaya min, but kiran me ka min?" Junaid yayi murmushi yace "Mu shiga
ciki" daga haka ya bude motar ya fita, faisal ma ya fito suka shiga gidan a tare,
mama ce xaune parlor ita kuma tana kwance jikinta tana gyara mata gashinta, suka
gaida Mama ta amsa da murmushi tana masu sannu da xuwa, Junaid ya xauna idonsa a
kan jasmine, haka ma faisal, a hankali ta bude ido tana kallonsu don dama ba bacci
take ba, Junaid yace "Ta fara cin abincin mama?" Mama jummai tace "A'a daxu dai na
bata kunu ta sha ba laifi, sai dai jikinta da dumi" Junaid bai kuma cewa komai ba,
faisal yace "Toh ta sha madarar jiya?" Mama ta girgixa kai tace "A'a" Junaid dai
sai kallonta yake, faisal ya mike ya isa gabansu ya duka a hankali ya daura
hannunsa kan forehead dinta, tayi wani kara da ya sa shi mikewa da sauri ya koma
baya, mama jummai tayi dariya tace "Toh bata sanka ba" faisal yace "Uhun na ga
alama" murmushi Junaid yayi ya mike ya nufi kofa, mama tace "Kai dai Ahmad ka iya
tafiya ba sallama" juyawa yayi yace "A'a ban tafi ba mama ina waje " mama tace "Toh
yaushe Aminu xai dawo, ka ga maganinta ya tsaya yanxu" yace "Xai dawo, amma ba
yanxu ba shi yasa ma yanxu nake shirin kai ta asibiti a ci gaba da dubata a can
kafin ya dawo" daga haka ya nufi kofa ba tare da ya jira cewarta ba, ta bi sa da
ido lkci daya jikinta yayi sanyi jin abinda yace, faisal ya juya ya bi bayansa,
hawaye ne ya cika idon mama jummai ta dago jasmine tana kallonta tace "Yanxu raba
mu xa ayi?" Junaid na fita balcony ya xauna, faisal ya xauna gefensa yace "Nayi
kadan in ji damuwar ka ko Junaid" Junaid ya kallesa yayi murmushi yana girgixa masa
kai, bayan kusan minti biyu cikin sanyin murya ya soma gaya ma faisal matsalar da
yake ciki, faisal yayi shiru yana kallonsa cike da tausayinsa, can yace "Toh kai
yanxu baka da budurwar da ta maka ne" Junaid ya girgixa masa kai yace "I don't
have!" faisal ya sauke ajiyar xuciya yana kallonsa, bayan kusan minti daya murya
can kasa yace "You know what Capt?" Junaid ya kallesa bai ce komai ba, faisal yace
"ka auri yarinyar nan kawae...." Junaid yace "Wacce yarinya?" A hankali faisal yace
"Baiwar Allahn nan da kake kokarin ganin an sama ma lafiya, I assure you ba karamin
lada xaka samu ba, sannan yarinyar bata yi kama da 'yar kananun mutane ba, ina da
yakinin 'yar babban gida ce, you won't regret it frnd....." Kallonsa kawai Junaid
yake da mugun mamaki, faisal ya girgixa kai yace "Its for ur good, for her good
Capt, yanxu misali kayi aure dole baxa ta ke samun attention gun ka ba as before
and ba ko wace mace bace xata yarda da taimakon ta da kake, kaga wannan shine anyi
ba ayi ba don gidan jiya yarinyar xata koma, but idan ka daure ka aureta kaga ka
rufe bakin parent dinka, ita kuma sai ka ji dadin kula da ita sosai tunda you now
have ur freedom har Allah ya bata lafiya, then sai ka sauwake mata idan baka da
ra'ayin xama da ita ta tafi ta nemi 'yan uwanta, in ka mata haka ka mata komai na
rayuwa, kai kadai ne gatan yarinyar nan Junaid, ka ajiye batun mahaukaciya ce ka
aureta, I assure you dat you won't regret helping her...." Katse sa Junaid yyi yace
"What the hell are you saying faisal, a haukacen xan gabatar da ita gun su Abba?
Sai ince ina danginta da 'yan uwanta suke, kuma kasan dai dole sai na kai ta gida
gun Mumy, this is totally out of it...." faisal yace "Uhmm! Toh nemo wani solution
din" Junaid ya sauke ajiyar xuciya yace "Don nayi aure baxai sa in ki ci gaba da
taimakonta ba, ni nayi niyyar nema mata lafiya, babu kuma macen da ta isa don na
aureta tayi controlling dina, da aurena ko ba aurena I will help her kamar yanda
nayi niyya, yanxu dai xuwa gobe nake son gama arrangement din tafiya da ita" faisal
ya d'aga kafada yace "Ohk Allah ya shige mana gaba, yanxu mu je in siya drugs ka
kawo mata don akwai xaxxabi jikinta"
El-ameen ne kwance dakinsa bayan magrib, Ummi ta shigo dakin tana kallonsa tace
"What's ur problem Ahmad, are you ohkay?" Mikewa xaune yayi a hankali yace "Slight
headache ne Ummi" tace "Toh ka fito ka ci abinci ka sha magani mana ko kwanciyar ne
xai sama maka relieve" daga haka ta juya ta fita tana naxarin maganan da Hajiya
fati ta xo mata da shi daxu, wai sun ajiye mace can gidansa shi da Junaid, she
trust her son, ta kuma san abinda xai yi da wanda baxai yi ba, ganin condition
dinsa tun da ya dawo daga gun aiki yasa bata yi masa magana ba, ta kuma yanke
shawarar ba ma sai ta masa ba kawai sawa xata yi aje a gano mata kuma idan har
hakan ne ta tanadi abinda xata yi masa don she's a no nonsense ita, bayan minti
kusan goma da fitan Ummi dakin Faisal ya xo, yayi mamakin ganin El-ameen din kwance
yana bacci, ya tada sa yace "Lafiyarka kuwa El kai da baka bacci da wuri" El-ameen
ya kuma lumshe ido yace "ina jin xaxxabi ne ke son kama ni, am not feeling OK"
faisal yace "Toh ka sha magani?" Girgixa masa kai El-ameen yayi, faisal yace
"Saboda me? patient dinku ma na can ita ma xaxxabin take, na dai siya mata drugs
Junaid ya kai mata..." Mikewa xaune El-ameen yayi da sauri yace "Xaxxabi kuma, tun
yaushe? Wani drugs din ka siya mata?"


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

28.....

Faisal yace "Normal drugs na xaxxabi mana" El-ameen yace "Ohk, Allah ya bata
lafiya" faisal yace "Ameen, idan Allah ya kai mu gobe xa a tafi da ita kudu" El-
ameen ya d'aga kafada bai ce komai ba, faisal yace "Kayi wanka ka ci abinci sai ka
sha magani xaka fi jin dadin jikin ka," ba musu El-ameen ya mike ya shiga bathroom,
faisal na ganin haka ya jawo wayarsa da sauri ya nemo number Junaid, cikin hanxari
ya shiga rubuta masa text kamar haka "Ban yi tunanin akwai abinda ya isa ya shiga
tsakaninmu da kai har ya hada mu haka ba, all the same Allah ya huci zuciyarmu, ba
wai don ka hakura kuma na maka text din nan ba sai don in nuna maka ni babba
ne...." Daga haka faisal ya tura text din sai da ya tabbatar ya tafi sannan ya maxa
yayi deleting ya mayar da wayar ya ajiye, ko minti goma faisal bai kara a gidan ba
yayi gaba. Junaid na xaune parlon Mumy yana cin abinci text din ya shigo wayarsa,
yayi mamakin ganin sunan El-ameen, ya bude text din ya karanta content din,
murmushi kawai yayi ya ajiye wayar, can ya mike ya dawo parlor ya d'an saci kallon
Humainah dake kwance tana danna wayar fatima, karbe wayar yayi yace "Ke baki iya
gaisuwa ba ne" mikewa tayi xata wuce daki ya fixgota, ta kusa fadowa kansa, turasa
tayi kmr xata yi kuka tace "Ni ka kyaleni," ya matso kusa da ita yace "Anki" ta
bata fuska xata yi kuka, yayi murmushi yace "Abinda kika fi iyawa kenan ai" saketa
yayi ya fita daga parlon ta bi sa da harara. Karfe takwas saura na dare El-ameen ya
fito rike da makullin motarsa xai tafi clinic a bisa umarnin dad dinsa, bin sa da
kallo Ummi tayi har ya fita, yana shiga motarsa driver din Abbansa ya karaso kusa
da motar, xuge glass yayi yana kallonsa yace "Ya aka yi Umar?" Drivern ya d'an sosa
kai yace "Yallabai dama, ji nayi Hajiya xata aika wasu xuwa can gidan ka, ina jin
akwai fa binciken da take, xuwa anjima xa su je, nine ma xan kai su wai...." El-
ameen ya firfito da ido yace "Gidana kuma, me tace maku xa ku je ku yi?" Umar yace
"Wllh ban san me tace masu xa su je yi can ba, ni umarni kawai ta bani in kai su"
El-ameen da hankalinsa ya gama tashi yace "Ohk ohk nagode kwarai Umar..." Umar din
yace "Amma yallabai ka rufan asiri, naga kai din mutum ne mai kirki shi yasa nace
bari in ankarar da kai, in ma da matsala ne sai ka gyara" El-ameen yace "nagode
kwarai umar, kar ka ji komai" daga haka ya ja motar ya bar gidan, sai da ya fara
tsayawa a atm machine ya cire kudi sannan ya nufi gidansa direct. Yana isa gidan
yayi parking waje ya fita ya shiga ciki, murda kofar parlon yayi a hankali ya tura
ya shiga, bbu kowa parlon sai Jasmine da plate din potatoe gabanta ta kifar kasa,
mikewa tayi jin an bude kofa ta kalli kofar da sauri, ya tsaya ya rungume
hannuwansa yana kallonta, a hankali ta shiga tahowa tana kallonsa itama har ta iso
gabansa ta tsaya, murmushi ya sakar mata murya can kasa yace "Jewel!" Ita dai
kallonsa kawai take, ya matso kusa da ita a hankali ya ja hancinta yace "Did you
miss me" taba nasa hancin tayi a hankali ita ma, ya wara manyan idonsa yana 'yar
dariya sai ga mama jummai ta sauko daga stairs rike da jakunkuna biyu, ai tana
ganin El-ameen tayi still, ya kalleta ya kalli jakar da mamaki, lkci daya murmushin
dake dauke fuskarsa ya bace yace "Ina kuma xaki da jaka mama?" Ae sai ta fashe da
kuka tace "Yo naji Ahmad na cewa gobe xai kai ta asibiti ta xauna a can, a gida ma
ana yi bata warke ba sai wani asibiti can, ku bar ni in je a mata na gargajiya mana
tun da ba a dace da na baturen ba, don Allah ni a bar ni da ita xan kula da ita har
Allah ya bata lafiyan. Idan ya so sai in baku addreshin kauyena, ku yarda da ni
baxan cuce ta ba..." El-ameen kallonta kawai yake da mugun mamaki, yanxu da Allah
bai kawo sa ba tafiya da ita kawai xata yi, karasowa parlon yayi yace "Ehh wannan
kuma gaskiya ne mama kin kawo shawara me kyau, Amma bari muyi shawara da Junaid din
koh" tana matsar kwalla tace "Toh" xaunawa yayi yana kallon Jasmine dake ta binsa
kamar xata shige jikinsa, yayi murmushi ya xaunar da ita ya jawo ragowar potatoe
din da ta xubar ya dau daya ya kai mata baki, ta bude bakin ya saka mata, kallon
Mama jummai dake kallonsu tana 'yar murmushi yyi yace "Mama xaki d'an siyo mata
fruits a bakin titi don Allah," tace "Toh" ya fiddo kudi ya mika mata yace "Na dubu
xa ki ce a baki" karban kudin tayi ta fita sabe da gyalenta, jasmine ta bi ta da
kallo, mikewa yayi ya isa kofa yana lekan ko ta tafi sannan ya juyo ya kusa cin
karo da Jasmine da har ta biyosa, murmushi yayi ya isa gun jakunkunan da mama
jummai ta sauko da, ya bude yaga wanda ke dauke da kayan Jasmine din, duddubawa
yayi ya fiddo da hijab ya sa mata, sannan ya dauki jakunkunan biyu ya rike hannunta
suka fita daga gidan ya kulle da key, yana rike da hannunta ya nufi gun mai gadi,
yace "Kana ji na Usman, xa mu dan yi tafiya ne amma baxa mu dade ba" ya fiddo kudi
aljihunsa ya mika masa yace "Ga kudin ka na wannan watan, yanxu xaka tafi xan kulle
gidan ne, sai ka tsaya bakin gate har mama ta dawo ka bata Jakarta da kudin nan ita
ma, da xaran mun dawo xan neme ka" Mai gadin da ko kadan bai ji dadi ba yace "Toh
shikenan yallabai, Allah ya kiyaye hanya, ya dawo da ku lafiya" El-ameen yace
"Ameen, d'an je ka canja min wutan gidan xuwa na gen" ba musu maigadin yaje yayi
yanda yace masa gidan ya dawo ba wuta gaba daya, ya dawo shima ya hada nasa kayan,
suka fito gaba daya, El-ameen ya kulle gidan yace "Don Allah ka jira har tsohuwar
ta dawo ka bata hakkinta da kayanta," mai gadin yace "In'sha Allah yallabai" daga
haka El-ameen ya nufi motarsa da ita da sauri yana rike da nata jakar kayan, ya
bude front seat yasa ta shiga, ya ajiye jakar kayanta a bayan motar ya rufe, ya
xaga ya shiga motar ya tada ya bar wajen, kafin ya isa titi ya ga Mama jummai na ta
xabga uban sauri rike da ledan fruits, ta basa tausayi sosai, yasan tsakaninta da
Allah take son yarinyar amma cutar dake damunta na asibiti ne ba na gargajiya ba,
kuma tun da ta fara tunanin guduwa da ita wataran ko ba yanxu ba sai ta gudu da ita
din, may be some other time xa su kuma nemanta, kallon jasmine yayi yaga yanda ta
kafa ma glass din motar ido ko kiftawa bata yi tana kallon motoci dake tafiya kan
titin kamar me son gano abu, yayi murmushi ya kamo hannunta yace "Jewel" kallonsa
tayi da sauri, ya sakar mata murmushi, ta maida dubanta kan titi, sosai yake
tausayinta don a yanxu dai bata da gata a duniya sai nasu, murmushi yayi tunawa da
yayi axumi uku ya hau kansa fa. Tafiya kawai yake ba tare da yasan takamaiman inda
xai kai ta ba ma, duk he's just confuse, yasan ko ya kira Junaid yanxu ma ba fitowa
xai yi ba yana can Mumy ta gama basa abinci ta lullubesa yayi bacci, tsaki yayi
yana girgixa kai.


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

29....

Parking yayi a gefen titi yana tunanin inda xai kai ta, gidan frnds dinsa masu
mata? girgixa kai yayi don yasan ba lallai basu yi thinking negatively ba, Hotel?
Ya girgixa kai coz it's not decent, to ina xai kai ta? Dafe kansa yayi cike da
confusion, can ya dago ya juya yana kallonta ya ga ita ma shi take kallo, yayi
murmushi a hankali yace "Ina xan kai ki jewel?" Dauke kanta tayi ta jinginar jikin
glass din motar tana lekan waje, ya tada motar ya kuma hawa kan titi ya dinga
driving din kamar bai son yi, cikin mintunan da basu wuce ashirin ba ya iso clinic,
yayi parking a wajen da aka tanadar don ajiye mota, kalle kallen haraban hospital
din ya dinga yi, ganin patients ne Kawai ya fito, ai tana ganin ya fita ta fasa ihu
ita ma xata fito, ya juyo da sauri yace "Wait jewel yanzu xan bude maki" xagawa
yayi daya side din ya bude motar ya fito da ita, kalle kalle ta shiga yi, ya rike
hannunta ya shiga asibitin da sauri, bai saurari nurses din dake gaida sa ba ya
haura sama da ita ya bude office dinsa suka shiga, key ya sa ma kofar sannan ya
juya yana kallonta ya sauke ajiyar xuciya yace "We've got a good solution koh" kama
hannunta yayi ya nufi bedroom din dake office din ya xaunar da ita kan gado yana
kallonta, kwan kwasa office dinsa ya ji ana yi ya mike da sauri ya fita, mikewa
tayi ita ma da saurinta ta bi bayansa, ganin ta biyosa yasa bai bude kofar ba yace
"Who's there?" Muryar nurse yaji tace "ur attention is needed at the theatre sir" a
fusace yace "Toh da ban xo ba fa" shiru tayi yyi tsaki ya kama hannun Jasmine ya
maida ta dakin, xaunar da ita ya kuma yi a hankali yace "Look jewel, yanxun nan xan
dawo kar ki bi ni plss" ya kusa second goma yana kallonta sannan ya mike a hankali
xai fita ita ma ta tashi da sauri, yace "Ohhw ina xan kai ki jewel?" Fita yayi ta
bi bayansa, ya isa show glass din dake office din me dauke da magunguna da ruwan
allurori ya bude ya dauki wani kwalban allura ya rufe, syringe ya dauka ya juya
suka kusa cin karo, yace "Sorry!" kama hannunta yyi suka koma dakin ya sa ta xauna,
cikin few minutes ya hada alluran yayi mata a lap, 'yar kara kawai tayi masa tana
bata fuska, yayi kasa da murya yace "Sorry jewel!" sun kusa minti goma xaune yana
yi yana kallon agogo, yaji an kuma kwankwasa kofa, ya mike da sauri ita ma ta mike
sai dai da ganinta kasan duk jikinta ya mutu, rike hannunta yayi ganin yanda take
layi ya fito office din yace "Yes!" Muryar Abbansa yaji yace "S'ako na bai iso gare
ka bane, ka wani garkame office kana ce min yes" xaro ido yayi yace "Ohh No, kaya
nake canzawa ne Abba gani nan xuwa yanxu" Abba bai kuma cewa komai ba, hakan yasa
ya kama hannunta suka koma dakin, kwantar da ita yayi ta lumshe ido, ya sauke
ajiyar xuciya ya mike ya bude inda kayan shiga theatre dinsa suke, ya cire na
jikinsa ya saka sannan ya lullubeta ya fito daga dakin ya rufe da key. Sha biyu
saura ya fito daga theatre, yana komawa office ya bude dakin yaga bacci kawai take,
toilet din dake nan ya shiga yayi wanka ya fito ya saka kananun kayansa ya fito
office ya xauna ya kifa kansa kan table don bacci yake ji, wata nurse ta shigo rike
da cup din coffee ta ajiye masa kan table tace "Sir" dagowa yayi yace "Thanks" har
ta kai kofa xata fita yace "Nurse Sharifah" juyawa tayi ta dawo tace "Sir?" Yace
"Nan sama kike ko k'asa yau?" Tace "a nan nake duty" yace "good, akwai patient a
dakina, i want you to stay with her throughout the nyt, mental disorder gareta, in
case xata farka cikin dare ki rakata restroom" shiru tayi tana kallonsa tsoro
bayyane fuskarta, murmushi yayi yace "She won't hurt you, bata komai, just in case
kar ta tashi ne yasa nace ki tsaya da ita" a hankali tace "Ohk sir... Let me
explain to..." Katse ta yayi yace "No! Xan je in mata bayani" daga haka ya mike ya
fita. Ta lallaba ta isa kofar dakin ta tura a hankali ta leka ta ganta tana bacci
cikin bargo, a haka ya dawo office din yace "Ki shiga baxa ta maki komai ba nace"
gyada masa kai tayi ta shiga dakin, ya dau coffee dinsa ya sha bayan ya huce sannan
ya mike yayi kwanciyarsa kan kujeran dake office din. Can misalin Karfe uku ihunta
ya farkar da shi ya mike da sauri ya nufi dakin dai dai lokacin da nurse din ma ta
fito da gudu, shiga dakin yayi ya ganta tsaye sai ihu take, ya karasa da sauri ya
rike hannunta yace "Jewel!" Tsit tayi tana kallonsa, ya sauke ajiyar xuciya ya
xaunar da ita gefen gado, ya juya xai fita ta mike ta bi sa da sauri, nurse din na
tsaye bakin kofar fita office har lokacin yace "Taho ki rakata restroom nace babu
abinda xata maki" da kyar ta karaso ta shigo dakin, shi ya kaita toilet din, ya
juya yana kallon Nurse din ta karaso a hankali ita ma ta shiga toilet din ya juya
ya fita. Da asuba yana kwance idonsa lumshe bayan ya dawo daga mosque yaji mutum
kusa da shi, bude ido yayi da sauri ya mike xaune yana kallonta, murmushi ya sakar
mata yace "Good morning jewel" dagota yayi ya xaunar da ita gefensa, remote ya
dauka ya kunna mata tv, wani kallo ta dinga yi ma TVn kamar idonta xai fito, dariya
ta basa ya mike ya shiga daki yaga nurse din rakube kasan gado tana bacci, yace
"Nurse Sharifa" mikewa tayi da sauri tana murxa ido duk da ganinta kasan a tsorace
take, yayi murmushi yace "Kin yi sllh?" Tace "Yes sir" yace "Good" toothbrush da
paste dinsa ya dauko ya mika mata yace "Xaki wanke mata baki" ta karba tana
kallonsa, ya fito ya dagota taki tashi idonta kyar kan TV ko kiftawan kirki bata
yi, dariya ta basa sosai ya kuma dagota ta fasa masa ihu har lokacin bata dauke
idonta kan kallon ba, ya dau remote ya kashe tvn, sai a sannan ta juya ta kallesa,
yayi murmushi ya dagata ta mike ya shiga daki da ita, kin yarda nurse din ta wanke
mata baki tayi, hakan yasa ya wanke mata da kansa, ganin hadiye komai take yasa bai
mata amfani da ruwan toilet din ba, ya fita ya dauko table water ya bude ya bata ta
sha ya kama hannunta suka fita, ya kalli nurse din yace "Tea xaki je ki hado min
plss" ba musu ta fita sai ga ta ta dawo da cup din tea ya karba yace "Thank you,
kafin ki tafi ki dawo" tace "Ohk sir" sannan ta fita, jasmine ya shiga ba tean, ta
sha kadan taki shan sauran da alama tea bai dameta ba, mikewa yayi ya tafi ya wanke
bakinsa toilet, juyawan da xai yi ya ganta tsaye bayansa, murmushi yayi ya kama
hannunta suka fito office, ya xaunar da ita sannan ya shanye sauran tea'n, TV ya
kunna mata don yana son fita ya gaida Abbansa, ai ko ta nutsu sosai tana kallon
mutanen dake yawo a tvn, ya mike a hankali yanda baxata lura ba ya fita ya haura
last floor xuwa office din Abbansa, wani aikin Abban nasa yasa sa, ransa bai so ba
amma bai yi musu ba ya shiga yi, yana cikin yi aka yi interrupting power, ya xaro
ido sanin kila yanxu xata fara ihu, da sauri ya dinga signing files din, cikin
minti sha biyar ya gama ya fice, ya sauka xuwa office dinsa, yana budewa yaga wayam
daki ya nufa ya tura nan ma wayam, ya xaro ido ya shiga toilet nan ma bbu ita, wani
mugun tashi hankalinsa yayi ya fito da sauri ya dinga dube dube ya sauko har
downstairs yana kallon nurses din yace "wata patient bata sauko ba yanxu" bai jira
cewarsu ba ya fita haraban asibitin da sauri, ya dinga dube dube bai ganta ba, gun
masu gadi ya nufa da sauri ya tambayesu suka ce basu ga kowa ba, komawa reception
yayi ya dinga yi ma nurses din masifa basu ga wata ta sauko ba yanxun nan, nan suka
shiga dube dube su ma cikin ward,haka aka yi ta nemanta cikin asibitin har da
likitoci da cleaners, wasu na tunanin anya kuwa Dr El-ameen dai dai kansa yake
ganin yanda ya wani rikice nurse Sharifa ma duk hankalinta ya tashi barin da tasan
ba mai hankali bace patient din, har Abba sai da ya sauko jin wai ana neman patient
daga bakin wani likita, kallon d'an nasa kawai yake yana son sanin wace patient ce
wannan wanda shi kadai yasan da ita a asibitin, Salatin da Dr Ibrahim wanda office
dinsa ke kallon na El-ameen yayi ya ja hankalin nurses da wasu likitocin, da
hanxari duk aka karasa wajen aka gansa tsaye bakin office din yana kallon ciki da
mamaki, El-ameen ya karasa shima yana kallon office din, tsaye take a office din
duk tayi kaca kaca da uban files din dake kan table dinsa, ta bude show glass duk
ta watsar da magunguna da allurorin dake ciki, El-ameen ya d'an saci kallon Abbansa
da ya rungume hannu yana kallon ikon Allah, daga likitocin har nurses din kallonta
suke su kalli El-ameen, hakan ya bata tsoro sosai ganin yanda aka taru bakin kofar
ana kallonta, ta fasa wani shegen ihu da karfi tana kallon El-ameen, sunkuyar da
kansa yayi, ta dinga ihu can ta tafi bayan glass da gudu ta labe har lokacin ihu
take, da kyar ya dago kai yana kallon Abbansa yace "Abba... Brain disorder gareta,
I..I... She's under medication ne Abba, jiya da xan xo na taho da ita..." Wani
mugun kallo Abba ke masa yace "Asibitina yayi kama da na mahaukata?" Sosa kai yayi
xai yi magana Abba ya masa wani uban tsawa yace "Uwar ka xaka gaya min, wasu
mahaukatan iyayen ne suka baka 'yar su ka sata under medication har kake yawo da
ita?" Ya lumshe ido ya bude a hankali yace "No, A gida nake mata treatment din
Abba, dama...dama akwai injection da nake mata da daddare ne to kuma ka kirani
clinic shi yasa na taho da ita... Yanxu ma xan maida ta gidansu..." Abba yace "Amma
arnaye ne iyayenta koh?" Shiru yayi bai ce komai ba, Strictly Abba yace "Ka maida
masu 'yar su ka basu shawaran su kai ta asibiti, na kuma hanaka aikin nan daga yau,
in ma kana son concentrating a field dinka na neurology ne yanxu you can go and
apply for work a psychiatry ba ka dinga yawo da mahaukata ba har kana kawo min su
asibiti suna min barna" daga haka Abba ya juya ya bar wajen, nurses din ma duk suka
juya, jiki a sanyaye El-ameen ya karasa cikin office din ya kamo hannunta suka
fita, sai wani shisshigewa jikinsa take a tsorace, likitocin dake gun suka bi sa da
kallo, hijab dinta ya sa mata suka fita xuwa gun motarsa yasa ta shiga ya tada mota
yyi warming ya bar haraban hospital din. Hotel ya nufa da ita don dat was the only
option a lokacin, yana
parking a haraban hotel din kiran Junaid ya shigo wayarsa, yayi mamakin ganin
kiran don yasan bai xuwa can gidan da safe bare ace yaje ne ya gani a rufe, ya
kalli agogo yaga bakwai da wani abu, daga kiran yayi daga daya bangaren Junaid yace
"I saw ur text jiya, kuma I hail you da ka nuna kai babba ne" El-ameen yace "what's
he talking about" Junaid yace "Really! There's no need of pretending, kana ina
yanxu" El-ameen ya kalli inda yake sannan ya gaya masa, Junaid yace "Me kake a
hotel" El-ameen yayi shiru sannan yace "Why are you even asking?" Junaid yace
"Magana xa muyi, shud I come over..." El-ameen yace "aikin fa?" Junaid yace "Na dau
hutun sati daya..." El-ameen ya sauke ajiyar xuciya yace "Good! Taho ka same ni
yanxu" daga haka ya katse wayar, junaid ya sauke ajiyar xuciya ya dafe kansa don
maganar da faisal yayi masa jiya ya tsaya masa, so yake yaji mai El-ameen xai ce
game da shawaran faisal, in har shima ya basa go ahead xai jaraba ya ga ko me
yiwuwa ne.


*Haske writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

30.....

Bude motar El-ameen yayi ya fito ya xaga ya fiddota yana rike da hannunta suka
shiga reception din hotel din, babu wanda xai ganta yace mahaukaciya ce, xa a fi
tunanin daga kauye ta fito duba da yanda take kalle kalle kamar idonta xai fito,
tana kuma shisshige sa, daki yyi masu book aka basa makulli ya haura sama yana rike
da hannunta, xaunar da ita yayi a dakin yana kallonta, tausayinta kawai yake a
hankali yace "Allah ya baki lafiya jewel" ta dawo kusa da shi tana kallonsa,
wayarsa ne ya soma ring ya dauka ganin Junaid ne ya d'aga ya gaya masa numbern room
din da yake, cikin few minutes Junaid ya iso dakin ya murda kofa ya shigo, tsayawa
yayi daga bakin kofa yana kallonsu da mamaki, El-ameen ya mike ya d'aga kafada yace
"Ummi ta kusa gano abinda muke, so I had to take her away daga gidana" Junaid ya
xaro ido yace "Da gaske?" El-ameen ya koma ya xauna yace "nafi tunanin gulma aka
kai mata, nd I suspect that khadija" junaid ya girgixa kai yace "No! Khadija baxa
taba exposing dinmu ba, kila dai kanwarka ce sumayya..." Kallonsa El-ameen ya tsaya
yi yace "Sumayya kuma? Ae bata san komai ba" tabe baki Junaid yayi ya karaso dakin
yana kallon Jasmine da ita ma idonta ke kansa, ya juya ya kalli El-ameen yace "Nan
ku ka kwana kenan" El-ameen ya girgixa kai yace "Clinic, nd you know what sai da ta
tona min asiri ta sa Abba ya ganta and he wasn't happy" Junaid bai ce komai ba ya
xauna gefen gadon dakin, ta mike a hankali ta dawo kusa da shi ta tsaya tana
kallonsa, ya d'an bude ido yana kallonta shima yace "Good morning!" El-ameen da ke
kallonsu ya dauke kai yace "I heard you are taking her to Ogun state" Junaid yace
"Yea but na canxa plan yanxu" El-ameen ya kallesa yace "To Which?" Junaid ya rufe
ido na kusan second ashirin sannan ya bude a hankali yace "Faisal ya bani shawaran
in aureta kawae, you know gidanmu an takura in fito da mata nan da few weeks, but
kaga frnd ban san yarinyar nan ba, ban san daga inda ta fito ba, ban san meye
sanadin haukatan ta ba, infact ban ma san ko matar aure bace, kana ganin shawaran
faisal yayi, ya bani good reasons da yasa yace in aureta but am not even sure it
will be possible ba lallai 'yan gidanmu su yarda ba" tunda ya fara magana El-ameen
ke kallonsa ko kiftawa bai yi, Junaid ya kallesa jin bai ce komai ba yace "You are
quite" El-ameen yayi saurin lumshe ido tara da yin wani murmushin da xa a iya
kiransa da na karfin hali yace "Yea shawara ce mai kyau, may be xa a fi samun
nutsuwa gun nema mata lafiya babu fargaba...." A hankali Junaid yace "Toh how xan
kai ta gida a matsayin warce xan aura a haukace, kuma sai in ce ina iyayenta?" El-
ameen yace "Ai tana da nutsuwa, shiryata kawai xa ayi ka hada ta da budurwa kamarta
irin ace kawarta din nan ku je tare, bai fi kuyi xaman ten minutes ba ku fito just
dat ka tabbatar kana kusa da ita kar ka bar wajen, matsalar da xa a samu a nan
shine baxata yi magana ba but wannan ba komai bane Kawar sai tayi mata xa ayi
tunanin kunya ne da ita, kuma ai gun Mumy kadai xaka kaita komai xai xo da sauki,
iyaye kuma ba matsala bane xa mu san yanda xa muyi...." shiru El-ameen yayi
xuciyarsa na bugawa ya rasa dalili, Junaid yace "Uhunn will this be possible kuwa?"
El-ameen ya kallesa ya dan yi murmushi yace "idan Allah ya yarda" junaid ya lumshe
ido yace "Toh Allah ya sa, idan Allah ya bata lafiya sai in sauwake mata ta nemi
'yan uwanta" kallonsa El-ameen yayi da sauri sai dai bai ce komai ba, Junaid yace
"Toh ita mama dake kula da ita ina ka kaita?" El-ameen yace "Na sallameta" Junaid
ya kallesa da sauri yace "ohh Why?" El-ameen yace "I had to, don Ummi ta tura a
duba gidan" junaid ya girgixa kai yace "Toh yanxu ya za ayi da ita a nan?" El-ameen
yace "I don't know" Junaid yace "Ka kira wannan nurse din na ranan mana" ba musu
El-ameen ya fiddo wayarsa bayan sun gaisa ya gaya mata dalilin da ya kirata ya kuma
gaya mata inda xata samesa, kafin awa daya ta iso gun, El-ameen yace "Ga kayanta
nan xaki shiryata, you will be staying with her na 2 dayz plss..." Nurse din tace
"But sir ina da duty a asibiti da daddare" kallon junaid El-Ameen yayi, jin bai ce
komai ba yace "Ohk xa mu san yanda xa ayi xuwa ltr" Daga haka ya mike yace ma
junaid xai tafi gida, Junaid yace "But am also leaving" kudi ya ciro a aljihunsa ya
mika ma nurse din yace "Gashi ki siya maku abinda xa ku ci kar ki kuma bar ta ita
kadai a daki" shi dai El-ameen fita kawai yayi, junaid ya bi bayansa, tana ganin
haka ta mike da sauri xata bi su a rikice amma tuni suka rufe kofar, nurse din ta
kamo hannunta sanin bata komai ta ja ta suka koma dakin. Umma ce xaune tare da
Hajiya a parlon hajiyar, da ganinsu kasan abun duniya ya dame su, Umma ta sauke
ajiyar xuciya tace "Toh Allah shi kyauta, amma ita suhaima don uwarta bata tabbatar
da abu ba xata xo ta fadi yanxu da ta xo gidan nan ya xa muyi, ga shi matar nan ba
mutunci ne da ita ba, mu dai Allah bai yiwo mu masu sa'a ba kila" Hajiya tace "Ae
ni naji dadi da abun ya tsaya iya waya balki, sai kin ji maganganun da ta gayan
wllh, wai in cire ido kan d'anta, maganganu dai bbu dadin ji, sai dai ban to fa ba
don mu muka ja ma kanmu, uhum Allah shi kyauta dai, duk Suhaima ce ta ja mana" Umma
tace "Xai kuma iya yiwuwa fa kawai rufa ma d'an nata da junaid din asiri tayi,
wannan tattaccen d'an nata, kinsan kuma fa bakinsu daya da Amina" Hajiya tace "Ni
wllh duk abun ya ishe ni, duk inda muka billo ba nasara wannan wace irin fitina ce,
gashi ni gabana kullum cikin faduwa yake kar yace tsinannar Humainan nan yake so,
kai ni na tabbata ma ita uwar xata ce ya fito da, kinga fa 'yan kwanaki suka rage
wllh duk hankalina a tashe yake" Umma tayi tagumi tace "ga dukkan alama uwar nan
tasa ba a xaune take ba ita ma abinda muke shi take yi, baki ga yau tun safe ta
fita ba, ita da bata xuwa ko ina" Umma tace "Toh ke sai yau kika sani, ni ai tun ba
yau ba nasan ita ma a tsaye take, bar ganinta haka green snake under the green
grass ce wllh, amma dai akwai wani plan din da nake ta shiryawa a raina sai dai
wllh ni kaina tsoronsa nake, amma hakan kadai shine mafita ba boka ba malam cikin
kwanciyar hankali, sae dai kuma plan din na bukatan hadin kan mu ne, bbu bakin ciki
ko nuna banbanci bare kyashi in suhaiman inma muhibbar" Hajiya tace "Haba balki, Ae
mun xama daya wllh kawai gaya min wani plan ne wannan" shigowar motar junaid suka
ji ko wannen su tayi shiru tana tabe baki, Umma tayi kwafa tace "ka kusa shigowa
hannu yaro" Junaid na gama parking ya shiga part din Mumy, bbu kowa parlorn jin ana
soye soye kitchen ya nufi kitchen din, Humainah ce kitchen din tana suyan nama,
tana ganinsa ta hade rai ta dauke kai ta ci gaba da abinda take, karasowa kitchen
din yayi ya rungume hannayensa yace "Fitsara kika koyo gidan Ayshan kenan?" Daure
fuska tayi sosai ta kashe gas din ta rufe naman da ta soya ta juya xata fita ya
fixgota ta fado jikinsa, 'yar kara tayi ya Rungumeta yana kallonta, tuni jikinta ya
dau rawa ta fara turasa tana cewa "Meye haka ya Ahmad ka sake ni..." D'ago kanta
yayi ta kasa kallon fuskarsa sai kokarin kwace kanta take, yayi murmushi murya can
kasa yace "Ba fitsara ba!" Ta girgixa kai da sauri ba tare da ta bari sun hada ido
ba tace "don Allah kayi hakuri ban gane kai bane, baxan kara ba" Muryar fatima da
ya ji yasa ya saketa da sauri, ko second uku bata kara ba ta fice daga kitchen din
tana tuntube, juyawa yayi shi ma ya fita yana mamakin hakan da yayi don bai taba
shigen haka ba, mumynsa kadai yake runguma a rayuwarsa. Karfe hudu da wani abu yana
kwance part dinsa kiran El-ameen ya shigo wayarsa, ya d'aga daga daya bangaren El-
Ameen yace "ka dai ji abinda nurse din nan tace daxu, kuma baka kira kace ga yanda
xa ayi ba, kai fa matsala gare ka" junaid ya d'an yi shiru sai kuma yace "Wllh ban
san yanda xan ce xa ayi ba friend, baxai yiwu ka kaita ko gidan frnds dinka masu
mata ba?" El-ameen yace "Kai ma ai naga kana da frnds din masu mata, ka kai ta
mana" daga haka ya katse wayar, junaid ya tabe baki ya ajiye wayarsa ya koma ya
kwanta, wata old time frnd El-ameen ya kira don xuwa tayi spend din daren da
Jasmine ganin time na wucewa. Khadija ce kwance parlonsu misalin takwas da rabi ta
fara bacci, Muhibba dake parlon ita ma xaune ta buge kafarta tace "Baxa ki kai ma
ya Ahmad ruwan lipton dinsa ba ne wai kina neman kiyi bacci" kallonta khadija tayi
tana murxa ido tace "Lipton kuma, a gun Mumy yake sha ai" Muhibba tace "Amma daxu
ya aiko Humainah wai ki dafa masa ki kai masa, ohh bakya parlon ashe" mikewa
khadija tayi tace "Da gaske" Muhibba ta tabe baki ta ci gaba da kallo abunta tace
"A'a karya" Hajiya dai abincin gabanta take ci amma duk hankalinta na Kansu haka ma
Suhaimah dake parlon, Hajiya tace "Shegiya da nice na tashe ki yanxu ki dafa min
Lipton da baxa kiyi ba, amma da yake Ahmad ne, wato uban da ya haife ki ai kin
tashi..." Turo baki tayi ta mike ta nufi kitchen, Muhibba ta kalli Hajiya, Hajiya
tayi murmushi ta ci gaba da cin abincinta, khadija na shiga kitchen din ta shiga
dafa masa ruwan Lipton da kayan kamshi sosai kamar dai yanda yake so, Hajiya ce ta
kwalo mata kira ta fito, Hajiya tace "Tafi ki dauko min wayata a sama" tana haurawa
sama Hajiya ta kalli Suhaima tace "tashi..." Da gudu Suhaima ta nufi kitchen din ba
a dau lokaci ba ta fito da sauri tayi xamanta, dai dai lokacin da Khadija ta sauko
ta mika ma uwarta wayar ta nufi kitchen, cikin few minutes ta fito rike da mug mai
murfi ta fice daga parlon duk suka bi ta da kallo. Junaid na xaune parlor yana
kallon kwallo sai dai duk sonsa da kwallo ranan baya masa dadi, gaba daya tunanin
yanda xai fara kawo jasmine gun mumy ran lahadi kamar yanda El-Ameen ya basa
shawara yake, kwankwasa kofa aka yi ya juya da sauri lokaci daya khadija ta bude ta
shigo da sallama tace "Gashi yaya" kallonta ya tsaya yi kafin yace "What's that?"
Tace "Lipton mana, wai Humainah tace kace in dafa maka" ya d'an bude ido bai dai ce
komai ba, ta karaso ta ajiye masa ta juya ta fice, bude mug din yyi ya lumshe ido
ganin Lipton din yanda
yake so, dama can ita ke masa Mumy ta hana wai bata son yana cin duk abinda xai
fito daga side dinsu, rufewa yayi ya ci gaba da kallonsa.


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

31.....

Kallon agogo junaid yayi yaga tara ya kusa, ya jawo wayarsa ya shiga kiran El-ameen
don ya ji ko ya samu inda xai kai ta, har ya gama ring bai d'aga ba, mikewa yayi ya
dau mug din Lipton din ya shiga daki ya xauna gefen gado ya bude ya shiga sip dinsa
a hankali, kusan rabi ya sha ya rufe ya ajiye sannan ya mike ya shiga bayi don yin
wanka, da kyar ya iya fitowa daga bathroom jin kansa na wani irin juya masa, ya
xauna gefen gado sanye da bathrobe, shi kansa baxai ce ga abinda ke damunsa a
lokacin ba, kwanciya yyi yayi rub da ciki, a haka ya ji an bude kofar parlor aka
karaso har bedroom, kasa dagowa yayi yaga ko waye jin wani axababben ciwo da
cikinsa ke masa, tsaye Muhibba tayi bakin kofar tana kallonsa, tuni kamshin
turarenta ya gauraye dakin, ya juyo da kyar yana ganinta dishi dishi, rufe kofar
tayi ta karaso cikin dakin ta xauna gefensa cike da kissa tace "Ya Ahmad dama Abba
ne yace ka ban dubu biyar xan yi amfani da shi" mikewa xaune yayi don ta muryarta
ya gane ko wacece ya rike kansa duk da yanayinsa hakan bai hanasa hade rai ba yace
"How dare you xaki shigo min daki?" Mikewa tayi ta nufi kofa irin ta ga ko xae
tsayar da ita, har ta isa bakin kofar bata ji yace komai ba sai komawa da yayi ya
kwanta ya runtse ido, cije lebe tayi ta kuma dawowa ta hau kan gadon da damuwa
kamar gaske ta dafa sa da duk hannunta biyu tace "Wai baka da lafiya ne ya Ahmad"
ai bai san lokacin da ya fixgota ba ta fado kansa ya kankameta, wani murmushi tayi
tana kallon kyakkyawan fuskarsa don har lokacin idonsa rufe suke, ta dake tace
"Meye haka ya Ahmad, ka kyaleni" ko kadan bai jin abinda take cewa ba, lkci daya ya
koma kamar mara hankali, wani farin ciki ya rufeta ba kadan ba ta sakar masa jiki,
cikin mintuna kadan yanayinsa ya bata tsoro, tun tana daurewa har dai tsoron ya
fara bayyana, gashi ba rikon wasa yayi mata ba, turasa ta fara yi a tsorace daga
karshe tana neman kwace kanta duk da ba haka suka yi da su Umma ba, amma ta gama
tsorata da shi gaba daya, kin saketa yyi ta saka kuka tace "Don Allah ya Ahmad
kayi hakuri ina rokon ka" ko sanin abinda take cewa bai yi ba, ihu ta fasa a rikice
tana turasa tana kwala ma Umma kira amma ya ki saketa, bude kofar dakin da aka yi
lokaci daya da karan tarwatsewan bowl me dauke da fruit salad ne ya sa shi sakinta
da sauri, ta ja bargo ta rufe jikinta tana kuka jikinta na rawa, shi ko dama
bathrobe na jikinsa, kallonsu Humainah ta tsaya yi a bakin kofa jiki a sanyaye, ya
sauko da kafafuwansa kasa ya rike kai xuciyarsa na bugawa ya dinga nanata
innalillahi... A xuciyarsa, Muhibba ma ta xamo daga kan gadon tana kuka har lkcin
ta jawo hijab dinta ta sa ta fice da sauri sai ka rantse ba ita ta kawo kanta ba
ganin yanda take kukan jiki na rawa, da kyar Humainah ta juya xata bar dakin ya
dago kai yayi kafin halin kiranta, amma ko juyowa bata yi ba ta fice da sauri, sake
rike kansa yayi ya runtse ido duk ya kasa tuna yanda abun ya faru, mikewa yayi yana
jin jiri ya shiga bayi, ya kusa awa daya bayin sannan ya fito ya fada kan gado
lokaci daya bacci ya daukesa. Muhibba kuwa tana komawa part din uwarta ta gansu duk
xaune suna jiran dawowarta, Hajiya ta mike da sauri tana kare mata kallo tace "Ya
naga kin fito da wuri, ko dai bai sha ba" ta bata fuska tana goge guntun hawayen
idonta tace "Ya sha mana, ni dai tsoro nake ji wllh" Umma da Hajiya suka yo waje da
ido suka hada baki wajen cewa "Me? Kina nufin bai maki komai ba??" ta fashe da kuka
tace "Ni Allah tsoronsa naji Umma, ni dai baxan iya ba a tura suhaima" Umma tayo
kanta a fusace tace "Nashiga uku ni balki, Allah wadaran ki yar iska kawai, tsoron
uban me, innalillahi... Shikenan ta bata plan din" Hajiya da idonta ya kankance don
bacin rai tace "Ni nasan a rina dama kawai nayi shiru ne, da Suhaima ce ko dar baxa
ta ji ba kika ce mu tura debabbar yar nan taki gashi ta rusa mana budget, wannan
wace irin fitina ce" Umma ta kwalo ma suhaima kira tace "Maxa ke ki je..." Muhibba
tace "Humainah fa ta shigo ta ganmu!" Juyawa suka yi da sauri Suna kallonta, Hajiya
ta xaro ido tace "Allah?" Muhibba ta tabe baki tayi hanyar daki, Umma ta jabe kan
kujera ta dafe kai tace "Allah ya tsine ma tsiya!" Tsaki Hajiya tayi ta fice daga
part din kamar xata tashi sama. Ray din rana ne ya farkar da Junaid da safe, ya
mike xaune da sauri yana kallon agogo yaga bakwai da kusan rabi, xaro ido yayi
lokaci daya abinda ya faru jiya da daddare ya dawo masa gabansa ya fadi, kalle
kallen dakin ya shiga yi yana tunanin what just came over him jiya, rike kansa dake
sara masa yayi, ya mike tsaye da kyar ya shiga toilet, wanke baki yayi, yayi wanka
snn ya dauro alwala ya fito, ya jima xaune kan pray mat bayan ya idar da sllh daga
bisanni ya mike ya isa bakin kofa ya tattara pieces din bowl din jiya da Humainah
ta fasa bakin kofar ya gyara wajen ya goge ya fitar da mug din Lipton din ma.
Parlor ya fito ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujera ya lumshe ido. Ganin har
Karfe tara ya kusa ya sa ya mike a sanyaye ya fita ya nufi part din Mumy, kasa
shiga parlon Mumy yayi don bai san da wani ido xai kalli Humainah ba, da kyar ya
tura kofar daga karshe ya shiga, bbu kowa parlon sai kamshi me dadi dake tashi, ya
karasa ciki jiki ba kwari ya xauna, Mumy ce ta fito daga daki tana kallonsa tace
"Sai yanxu ka tashi?" Kasa kallonta yayi ga wani faduwa da gabansa yake don gani
yake kamar Humainah ta gaya mata, ya dukar da kai ya gaisheta, tace "Meye haka kake
kamar munafuki" dagowa yayi da sauri ya kalleta yace "A'a kaina ke min ciwo Mumy"
tace "Toh ga breakfast dinka can a dinning sai ka sha magani idan ka gama" mikewa
yayi ya tafi dinning din ta bi sa da kallo, tabe baki tayi ta koma daki, tea kawai
ya iya sha sai dube duben inda xai ga Humainah yake, mikewa yayi daga karshe ya
tafi dakinsu, kwance ya sameta ita kadai fatima kuma ta tafi boko, mikewa xaune
tayi ganinsa ya rufe kofar dakin tana ganin haka ta fashe da kuka tace "Ni wllh ka
fita kar in kira maka Mumy" tsayawa yayi yana kallonta, tana share fuskarta tace
"Ni dai ka fita" ganin ya nufota tsoro ya kamata ta fasa ihu tana kiran Mumy, still
yayi yana kallonta, Mumy ta bude kofar dakin tana kallon ciki da mamaki tace "Meye
haka?" Ta fashe da kuka tana kokarin sauka daga kan gadon, Mumy ta kallesa tace "Me
ya shigo da kai nan?" Rasa abun cewa yayi ya fara kame kame, can yace "Ni ban
san..." Wani tsawa Mumy tayi masa tace "Get out!" Juyawa yayi ya fice daga dakin,
Mumy ta kalleta tace "Ihun me kike ma mutane ke kuma" share fuskarta tayi a hankali
tace "Ba komai" Mumy ta kusa second ashirin tana kallonta sannan ta juya ta fita
daga dakin. Junaid kam part dinsa ya koma ya dau makullin motarsa ya fito ya tafi
parking space ya dau motarsa ya fice daga gidan, hotel din jiya ya nufa yana gama
parking ya fito ya hango El-ameen ya fito, kallo daya El-ameen yayi masa ya nufi
gun motarsa dake ajiye har ya bude xai shiga Junaid ya bi sa da sauri yace "Hey..."
Wani kallo El-ameen ya watsa masa yace "A haka xaka auri yarinyar ka kula da ita?"
Junaid yayi tsaki ya xaga ya bude seat mai xaman banxa ya xauna, girgixa kai El-
ameen yayi ya shiga motar shi ma, junaid yace "Kasan me frnd ina cikin damuwa wllh"
El-ameen ya kallesa yace "Me ya faru kuma?" Dafe kansa yayi na kusan second goma
sannan ya dago ya shiga gaya masa abinda ya faru bai boye masa komai ba, murmushi
kawae El-ameen yake yana kallonsa can kuma ya fashe da dariya har da kyakyatawa,
junaid ya tsaya kallonsa da mamaki lokaci daya ransa ya baci, bude motar yayi xai
fita El-ameen ya tsagaita dariyarsa ya rikosa yace "Haba it's very funny mana, daga
shan lipton? Seductive aka xuba maka cikin ruwan lipton din, its a plan, ba dai
kace kayi trusting wannan khadijar ba kana tare da wahala," Xaro ido Junaid yayi
yace "Seductive kuma?" El-ameen ya kuma fashewa da dariya yace "Of course, ita kuma
warce aka turo maka taji maxa ta tsorata... Ohhh my God! Kai ban taba ganin makirci
a xahiri irin na yan gidan nan naku ba" Junaid kallonsa kawai yake don kansa ya
gama daurewa, El-ameen ya daga kafada yace "Allah ya taimakeka ka nuna mata kai din
ba na wasa bane, da kawai sharri xa a maka ace kayi raping dinta you know daga nan
ka kuma shiga wani case kila ma daga karshe Abba yace sai ka aureta, tunanin da
Humainahn ma ta yi kenan kuma gwara da Allah ya kawo ta a lokacin don da komai xai
iya faruwa" junaid ya rike kansa yace "Innalillahi......" El-ameen ya tabe baki
yace "Allah ya kyauta! Ni dai am going to clinic Abba ya Kirani yanxu" junaid ya
dago kai ya bude motar xai fita jiki a sanyaye, El-ameen ya d'an bude ido yace "But
wait! ina xa ka yanxu? Uhn.... kar kuma pills din bai gama sakin ka ba kaje ka afka
ma....." Kasa Karasawa El-ameen yayi ya dinga dariya, junaid ya hade rai yace "Wai
mahaukaciyar?" Shi dai El-ameen bai ce komai ba sai dariya yake, Junaid ya dawo ya
xauna yace "Look ko da ace na aureta yanxu me kuma xan ma mahaukaciya, infact ko ta
samu lafiya sauwake mata xanyi ta tafi ta nemi yan uwanta frnd" El-ameen yayi shiru
idonsa a kansa yace "Promise dat!" Shiru Junaid yayi shima yana kallonsa can yace
"Promise what?" El-ameen yace "That tana samun lafiya xaka sauwake mata kuma baxa
ka taba 'yar mutane ba" junaid bai ce komai ba can ya tabe baki yace "Do i need to,
ba dai ni nayi niyyar yin hakan ba, ohk I promise" A hankali El-ameen yace "Kuma
alkawari dai kaya ne" junaid ya masa wani kallo yace "Na fi ka sanin wannan" El-
ameen yace "Good, yau Thursday sai ka fara shirye shiryen kai ta gidan ku on
Sunday, I promise xan yi iya kan kokarina in ga everything goes smoothly" Junaid
yace "But ni ban san wanda xai mata shiri me kyau ba irin na xamani" El-ameen yace
"Ba sai kayi hiring a xo har hotel a mata ba" junaid yace "Ohk" bude motar junaid
yayi ya fita ya nufi cikin hotel din El-ameen ya bi sa da kallo.


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

32....

Yau ya kasance Saturday Junaid na xaune tare da El-ameen sai Jasmine da ake ma
gyaran gashi cikin hotel room din, nurse din da ke kula da ita ma na xaune dakin,
kyar El-ameen ya kafeta da ido yana kallon yanda kwararriyar hairdresser din ke
mata gyaran dogon gashinta, da ta yi motsi xai xaro mata ido hakan yasa ta nutsu
sosai duk da taki tsaida kan gu daya sai bin ta matar take, da ganinta kasan bata
so, tsoron El-ameen dake gabanta yasa bata nuna hakan ba, shi kam Junaid wayarsa
kawai yake dannawa, har bayan kusan minti talatin matar ta gama mata gyaran gashin,
nurse din sai murmushi take tana kallon yanda gashin ke sheki ga tsayi, ita kanta
hairdresser din sai kallon jasmine take da sha'awa bata taba kawowa mahaukaciya
bace an dai ce mata bata da lafiya, El-ameen ya warce wayar hannun Junaid ganin bai
ma san an gama ba, Junaid ya kallesa da sauri yace "What?" El-ameen yace "Your I
don't care attitude xai kai ka ga halaka fa" Junaid ya hade rai yace "Shi gyaran
gashin xan tsaya kallo kamar yanda ka ke kallo ko me?" Tsaki yayi ya mike yana
kallon hairdresser din ya fiddo dubu biyar aljihunsa ya mika mata yace "Thanks
madam" ta karba da hannu biyu tana murmushi tace "Baxa a mata kunshi ba?" Ya juya
ya kalli El-ameen, El-ameen ya kauda kansa, d'aga kafada yayi yace "A'a no need"
matar tayi masu sallama ta fita daga dakin da jakar kayan aikinta. Sai a sannan
Junaid ya kalli kan jasmine dake xaune har lokacin bata tashi ba sbda El-ameen,
kauda kai yayi ya koma ya xauna yana kallon El-ameen yace "Look frnd ni ban san da
warce xan hada ta mu tafi ba fa gobe... Am confuse" El-ameen yace "Kai baka san da
warce xaka hada ta ba sai ni?" Tsaki Junaid yayi yace "Ni matsalata da kai kenan,
cikin nurses din clinic din ku babu sa'arta??" El-ameen yace "Babu!" Kallonsa kawai
Junaid yake, El-ameen yace "Ba na ga kwanaki ka tsaya kula wata yarinya a mall ba
har da karban numberta, just call her ka nemi favour wajenta, naga wayayya ce"
Junaid yayi shiru yana kallonsa lokaci daya yana son tuno sunanta, can yace "Koh?"
El-ameen ya d'aga kafada, Junaid yace "But ni ban taba kiranta ba fa, sai in ce
mata me?" El-ameen yace "Ka fini sanin me xaka ce" Junaid ya dau wayarsa yana son
tuna sunan da ya sa mata, can sunan ya fado masa yace "Yes Hafsat I think" numberta
ya duba yayi dailing, bugu uku ta d'aga ya kalli El-ameen sannan ya mata sallama,
amsawa tayi daga daya bangaren, yace "Hafsat?" Tace "yea" ya d'an shafa kansa yace
"Ahmad Junaid, wanda kika ara ma motar ki kwanaki" tace "Ohk kwana biyu?" Yace
"Alhmdllh, kina gida ne?" Tace "No ina school," yace "Which?" Tace "Al-qalam..."
Yace "Alryt xan xo in same ki later, I will cal you idan na xo" tace "Ohk.."
Sallama yayi mata ya katse wayar, El-ameen ya tabe baki ya mike ya karasa kusa da
jasmine ya dagota sanin saboda shi ne taki tashi, ae da sauri ta mike ya dawo da
ita kusa da su, ya dauki ragowar Irish dinta ya ajiye mata gabanta. Da yamma El-
ameen na office Junaid ya xo ya samesa, ya ja kujera yace "Na je na sameta, i've
explain everything to her and tace babu damuwa, gobe around Eleven xa mu tafi
saboda sai ta fara xuwa makaranta" El-ameen ya tabe baki yace "Ohk" Junaid yace "I
prefer ta sa hijab then veil" El-ameen yace "Ohk, sai ka je kasuwa ka siyo mata
sabo har kasa milk colour tunda kalan gold ne kayan" Junaid yace "Ka raka ni
mana..." El-ameen yace "as you can see am busy, idan tsoron mutanen kasuwan kake
sai ka ba nurse din dake wajenta kudi taje ta siyo kai sai ka tsaya da ita kafin
nurse din ta dawo" Junaid ya mike yace "Ohk" sannan ya juya ya fita, bin sa da
kallo El-ameen yayi yana girgixa kai, can yayi murmushi ya ci gaba da abinda yake.
Washegari lahadi junaid ya rasa me ke masa dadi, bai san yanda Mumy xata dauki
jasmine a matsayin warce yake shirin aure ba idan aka gano bata da hankali, Karfe
takwas da wani abu ya shigo parlon Mumy, Humainah ce ke ta goge goge a parlon, tana
ganinsa tayi hanyar daki ya bi ta da kallo, tun daga incident din ranan take
avoiding dinsa, dakin Mumy ya tafi ya sameta tana gyaran dakin, ya gaidata ta amsa
tare da cewa "Jiya Karfe nawa ka dawo gidan nan?" Ya shafa kansa yace "Tara saura,
naga kamar kin yi bacci ne shi yasa ban shigo ba" bata ce komai ba ya juya kamar
munafuki ya fita, a tsatstsaye yayi breakfast ya fita xuwa gaida Abbansa, Hajiya ce
parlon tana hada masa breakfast, ya xauna kasa ya gaida Abbansa sannan ya gaisheta,
tayi murmushi tace "Lafiya lau Ahmad" ya kusa minti biyar xaune parlon jin Abba bai
ce masa komai ba ya mike yayi masa sallama ya fita. Karfe goma saura Junaid ya
shirya yayi ma Mumy sallama ya fita, Mumy dai jin sa kawai take da yace ranan xai
kawo mata surkarta, yana fita gidan Hajjo ta diro da 'yar Jakarta babu notice.
Junaid na isa hotel din ya tarar warce yayi hiring don gyara Jasmine har ta xo, El-
ameen yayi tsaki ganinsa yace "Sai yanxu ka ga daman xuwa tata da kai" Junaid yace
"Ehh" simple make up aka yi ma jasmine da kyar don har cixon me make-up din sai da
tayi, wajen sa mata kaya ma a bayi sai da suka yi karamin yaki don sai da El-ameen
ya mata jan ido ta tsaya, shi dai Junaid wayarsa kawai yake dannawa, sai da aka dau
kusan awa daya wajen shiryata, tayi wani sanyayyan kyau, sai dai da ganinta kasan a
takure take cikin kayan, da ta sa hannu xata cixge El-ameen xai mata wani irin
kallo, lokaci lokaci Junaid kan sata kallonta, har matar ta gama ta sa mata hijab,
tayi wani kara xata fixge El-ameen ya mata tsawa, sake hijab din tayi tana
kallonsa, ya sakar mata wani lallausan murmushi, can Junaid ya mike ya fita daga
dakin, waya El-ameen ya dauka ya dawo kusa da ita ya shiga daukan ta hoto sai
kallon yanda wayar ke Haske take kamar idonta xai fito, wanda hakan ya kara mata
kyau ba kadan ba, ya dauketa ya kusa goma, can ya dawo kusa da ita ya xauna ya
matso da ita a hankali sannan ya masu selfie, mai make up dai sai kallonsu take da
sha'awa don sun yi mata kyau sosai, bude kofa Junaid yayi El-ameen ya mike ya koma
inda yake, Junaid ya ciro kudi ya mika ma matar tayi masa godiya ta fita, Junaid ya
kalli El-ameen yace "Hafsat na jiranmu" El-ameen yace "Ohk Allah ya kiyaye hanya,
no matter what kar ka yarda ka bar kusa da ita" Junaid yace "Ohk" dagota El-ameen
yayi ya kama hannunta, kin tafiya tayi tana kallon flat shoe din kafarta, El-ameen
ya jawota ta fasa ihu tana son cire takalmin, Junaid dai sai kallon ikon Allah
yake, El-ameen yace "Baxa ta iya tafiya da takalmin ba kenan" dukawa yayi ya cire
mata takalman ai ko sai gashi ta fara tafiya, Junaid ya xaro ido yace "Haka xa mu
je ba takalmi?" El-ameen yace "Ae hijab din ya kai kasa sosai, bbu komai kawae ka
ba Hafsat din ta rike mata, hope ka dai gaya mata brain disorder gare ta?" Junaid
ya sauke ajiyar xuciya yace "Tabdi!" Daga haka ya juya ya fita, El-ameen yayi
murmushi ya bi bayansa yana rike da hannunta, kallonsu kawai ake tun daga cikin
hotel din har suka fito haraban hotel din, junaid na isa gun motarsa ya juya yana
kallonsu, wani mugun faduwa gabansa yayi suna hada ido da ita, ya tsura masu ido su
biyun, a hankali take tahowa kamar me tausayin kasa, El-ameen na rike da ita har
suka iso gun motar ya bude front seat ya shigar da ita, junaid ya lumshe ido ya
bude a hankali yace "Jikina na bani baxa mu yi nasara ba..." El-ameen ya girgixa
kai yace "No! Allah xai daura ka kansu, just pray before going in, nd ka nuna masu
ba ta da lafiya ka taho da ita, kaga hakan baxae sa a takurata tayi magana ba, kuma
duk me aka ajiye mata kayi saurin dauka ka bude ka bata, if not saukowa kasa xata
yi ta xauna ta jawo gabanta, though in TV a kunne yake ma ba lallai ta lura da
komai na parlon ba attention dinta gaba daya xata ba Tvn, idan kaga kallon xai yi
yawa kawae ka kashe Tvn ma, don't force her on anything don sai ta iya maka ihu" a
hankali junaid yace "Ohk!" El-ameen yayi murmushi ya gyada masa kai, juyawa junaid
yayi ya bude mota ya shiga ya tada suka bar haraban hotel din, a hanya ya dau
Hafsat kamar yanda suka shirya, sai kallonta Hafsat take gaban mota don ita bata ga
alamar hauka tare da ita ba, junaid na kallonta ta madubi yace "Bata yi kama da
mahaukaciya ba koh?" Murmushi kawai tayi bata ce komai ba har suka iso gida, a
parking lot ya ajiye motar, sai a sannan yaji gabansa na faduwa, ya juya yana
kallon Hafsat yace "plss xaki kama hannunta..." Ta yi shiru sai kuma tace "Baxa ta
min komai ba" ya gyada mata kai yace "Yea baxata maki komai ba" bude motar yayi ya
fito ita ma ta fito, ya xaga xuwa daya side din ya bude ya fito da ita, kalle kalle
kawai take idon nan Maa shaa Allah, Hafsat ta kasa karasowa don duk tsoro ya cika
ta, Junaid yace "No plss kar ki sa a xargi abu, wllh baxata maki komai ba, xo ki
riketa plss" da kyar ta karaso tana kallon Jasmine, yana d'aga kai yaga Umma da
Hajiya xaune balcony as usual wani mugun bugu xuciyarsa yayi, ya dauke kai da sauri
yana kiran Allah a xuciyarsa. Hafsat na mika hannu xata rike nata tayi bayan junaid
da sauri, kiris ya rage xuciyarsa ya shige cikinsa don yayi xaton ihun nan nata
xata yi, ganin yanda su Umma ke ta lekosu yasa kawai ya kama hannunta ya nufi part
din Mumy, Hafsat ta bi bayansa da sauri.


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_

33.....

Mikewa Hajiya tayi da sauri tana kallon kafar Jasmine tace "Balki tashi ki ga ikon
Allah" da sauri Umma ma ta tashi ta bude baki tana kallon kafarta, a hankali Junaid
ya tura kofar parlon ya shiga gabansa na faduwa, babu kowa parlon ya karasa ciki
yana rike da hannunta har lokacin ya isa 3 sitter ya xaunar da ita shi ma ya xauna
ya kalli Hafsat ya nuna mata gefen jasmine, ta karaso ta xauna suka sa ta tsakiya,
kalle kallen parlon kawai jasmine ke yi, yana son xuwa ya sanar ma Mumy xuwansu
amma yana tsoron kar ta bi sa, haka suka ta xama parlon, Hafsat dai sai kallonsa
take ganin bai da niyar ta shi ya sanar da mutan gidan xuwansu, fatima ce ta fito
parlon, ta d'an xaro ido ganinsa tace "Lah Ya Ahmad!" yace "Kira Mumy" kallon
Hafsat tayi ta gaida ta, Hafsat ta amsa da murmushi, ta juya tana kallon Jasmine
ita ma ta gaida ta, kallonta kawai Jasmine ke yi kmr idonta xa su yi magana, Junaid
yace "Leave ki je kiyi abinda na sa ki" juyawa tayi ya bar parlon tana mamakin
abinda yasa taki amsa gaisuwarta, Junaid ya kalli Hafsat da sauri yace "Tana fitowa
sai ki gaisheta duk me xata ce kiyi ta bata amsa kawai" Hafsat ta gyada masa kai,
ba a dau lokaci ba Mumy ta fito parlon, kwata kwata bata dauka da gaske Junaid yake
ba, murmushi dauke fuskarta ta karaso tana kallonsu ta xauna tace "Sannun ku da
xuwa" Hafsat tace "Yauwa Mama ina yini" tace "Lafiya lau, ya hanya" Hafsat tayi
kasa da kai tace "Alhmdllh," ganin hankalin Mumy na kan Hafsat Junaid yyi saurin
cewa "Tana gaishe ki Mumy" ya fadi hakan yana nuna Jasmine, Mumy ta kalli Jasmine
don ita dai bata ji tace komai ba, ta dai yi murmushi tace "Lafiya lau, sannun ku
da xuwa" Hafsat tayi saurin cewa "Yauwa Mama" Mumy ta kira fatima ta fito tace
"Dauko masu ruwa fatima" kitchen ta shiga ta fito da tray ta nufi fridge ta bude ta
fiddo ruwa da drink ta dawo parlon, kusa da Jasmine ta ajiye tray din ta kuma
komawa kitchen ta dawo da snacks, Jasmine ta kalli Junaid da gabansa ke ta faduwa
ta fara kokarin sauka kasa ai da sauri ya riketa yanda bbu wanda xai lura, ya jawo
remote yayi powering tv, tvn na kawowa ta koma ta xauna tana kallo, sallaman su
Umma da Hajiya yasa xuciyarsa kusan shigewa cikinsa, suka karaso parlon su Suhaima
na biye da su a baya ko warce da murmushinta a fuska, Hajiya tace "Ashe bakuwar har
ta iso ko a sanar da mu, sannun ku da xuwa," Mumy tace "Ae kuwa, da wai idan sun
tashi tafiya xa su shiga su gaida ku" Umma tace "Allah sarki" Hafsat tace "Ina
yinin ku" suka amsa mata a tare, Mumy dai sai kallon mamaki take ma jasmine dake ta
kallo kamar her life depend on it ganin bata gaida su ba, Junaid ya lura da hakan
hankalinsa ya tashi ba kadan ba, su kansu su Umma kallonta suke, Hajiya tace "Toh
wai wacece surkuwar ta mu a ciki" Junaid na shirin cewa Hafsat ce, Hafsat ta riga
sa ta hanyar nuna masu jasmine, ya xaro ido don shkkn tasa ta samesa, Umma tace
"Ikon Allah, sannu Amaryar mu" nan ma dai ko dagowa Jasmine bata yi ba idonta na
kan TV, Hajiya tace "Toh fah, anya amaryar nan na jin mu kuwa" Hafsat tayi saurin
cewa "ba ma ta jin dadi ne muka fito..." Umma tace "Ikon Allah, ana burin auren
lafiyayya shi kuma ra'ayinsa kenan bawan Allah, Allah sarki naga ma kamar ciwo
gareta a kafa don bbu takalma ku ka shigo" lumshe ido Junaid yayi a hankali ya
bude, shi kam ya shiga uku da matan ubansa, Mumy dai bata tanka su ba ta kalli
fatima tace "Xubo masu abinci fatima" Guri Hajiya ta nema ta xauna tana cewa "Tun
da baki gare mu bari mu xauna" Junaid ya watsa mata wani kallo ta gefen ido, Umma
ma ta xauna tana cewa "Toh baxa a kai ta gun Hajja ba tun da tana nan..." Gaban
Junaid yayi wani mugun faduwa jin sunan warce ta kira, Mumy tace "Xa su je" Hajiya
tace "Ya kamata kam, ai da mun san da xuwansu da ko 'yar girki ne mun yi" kallonsu
kawai Hafsat take ko ba a gaya mata ba tasan matan ubansa ne, Fatima ta fito daga
kitchen rike da warmer din abinci da plates da spoon, Junaid ya kalli Mumy a
hankali yace "Baxa su ci ba Mumy" Hajiya tace "Suka gaya maka? Ke xo ki ajiye masu"
Ko kallonta bai yi ba, fatima dai ta dire abincin gabansu, a hankali Mumy tace
"Xuba mana" Bude kofa aka yi Humainah da Khadija suka shigo Hajja na biye da su a
baya tana cewa "Don jaraba mutum ya kwaso uban tafiya a rasa abinda xa a hada sa da
sai wani tsinannen taliya can, tsiya dai a gidan Muhammadu ta kare..." Khadija na
ganin Jasmine tayi still bakin kofa da mamaki, Humainah kam kallo daya ta masu ta
nufi daki, Hajja ta karasa shigowa parlon tana bin kowa da kallo tace "Xaman me ake
haka, me ya faru" Hajiya tayi murmushi tace "Kishiyar ki Ahmad ya kawo mana mu
gaisa" Hajja ta washe hakora tace "Ikon Allah, tana ina" lumshe ido Junaid yayi ya
jinginar da kansa jikin kujera don yasa tasa ta kare kawai, Umma tayi murmushi ta
nuna mata jasmine tace "Ga ta can kamar bebiye ba uhm ba uhm uhm," Hajja ta karaso
baki har kunne tace "Ke don baki da kunya har gida xaki xo kwacen miji, to ahir
dinki ni da Amadi mutu karaba" shi dai Junaid har lokacin yaki bude ido, ji yake
kamar yayi tsuntsu ya bar parlon, Hafsat ma duk ta rasa abun yi a lokacin, fatima
ta bude kulan me dauke da hadadden spaghetti ta shiga xubawa, Hajja ta dunguri
Jasmine tace "Ya hure maki kunnen kar ki gaisheni kenan koh, to ba karamin aiki na
bane in kora ku ke da shi wllh" juyowa Jasmine tayi da sauri tana kallonta, wani
kara da ya tsorata occupants din parlon ta saki da karfi, Hajja na tuntube tayi
kofa da gudu tana salati a tsorace, fatima ma dake gabanta tuni ta rufa ma Hajja
baya, Hajiya da Umma da su Suhaima duk aka mike a tsorace, Mumy ma ta mike tana
kallon Junaid, juyowa Jasmine tayi ganin ta kora Hajja, idonta ya sauka kan
spaghettin da fatima ta fara xubawa a plate, wani karan ta kuma saki a rikice ta
daga kafarta tana matsawa kusa da Junaid kamar xata shige jikinsa tana kallon
taliyar, ae sai ga Umma da Hajiya ma bakin kofa da gudu 'ya yansu na biye da su a
baya, Mumy kanta barin wajen tayi, Khadija ta karaso da sauri ta dauke taliyar
tunawa da tayi haka ta ma indomie ranan, Hajiya ta saki salati tana tafa hannu tace
"Al-qur'an mahaukaciya ce" Hajja ta dafe kirji tace "Mahaukaciya kuma" Mikewa
Junaid yayi ya dagota, da gudu Hajja tayi waje su Hajiya suka rufa mata baya da
gudu su ma, Mumy tace "Ahmad" tsayawa yayi ya juyo a hankali yana kallonta, sake
hannun Jasmine yayi ya karasa kusa da ita cikin sanyin murya yace "Na'am" jin bata
amsa ba ya dago kai yana kallonta ganin yanayin fuskarta yasa jikinsa yayi sanyi
sosai, strictly tace "Wacece yarinyar nan" kasa ce wa komai yayi ta masa wani tsawa
tace "Ba magana nake maka ba" a hankali yace "Ita nake son aure, Mumy it's a long
story... Am sorry i hide everything for you, tana da brain disorder ne, so..." Mari
Mumy ta sauke masa, Humainah dake tsaye bakin kofar daki tana kallon duk abinda ke
faruwa ta juya a hankali ta bar wajen, lumshe idonsa yayi ya bude, Hajiya na tafe
hannun ta saki shewa tace "Maganar Suhaima dai ya tabbata...." Hajja ta leko parlon
tace "Amma na tausaya ma gwalma'da'dden rayuwar ka Ahmad, ka rasa shegiyar da xa ka
kawo mana matsayin surka sai mahaukaciya, to Allah sai ya mana hisabi da kai, kuma
maxa ku kira min ubansa duk inda yake ya dawo yaga me ya haifa ma kansa..." Hafsat
da tausayin Junaid ya rufeta ta juya ta nufi kofa, da sauri Suhaima ta fincikota
tace "Ke kuma algunguma munafuka har da yi ma mahaukaciyar jagora koh....." Mari me
lafiya Hafsat ta sauke mata, Hajja tace "Kambu Ramaa!" Tun kan ta rama Hafsat ta
kuma sauke mata wani, Muhibba da Sadiya suka yi kanta, ta fixgi wani vase dake
parlon tace "Duk yar iskar da ta matso kusa da ni wlh sai na buga mata kuma babu
abinda xai faru don baku son wanene ubana ba, yau Allah ya ga dama kuma sai ya
daura maku haukan nan, kuma mahaukaci ai mutum ne, ba sonku Allah ya fi yi a kanta
ba da ya bar ku da hankalin ku, ku ba abun farin cikin ku bane d'an ku xai yi
jihadi ma, ga dai gida kamar babba amma karami ne" jefar da vase din hannunta tayi
ta fice daga parlon, Hajja tace "Kaji gantalalla k'awar mahaukaciya kawai, uban
waye hamagon uban naki, to mu dai xuri'armu babu mahaukaci, ke ubanki yayi jihadin
ya aureta mana yar buhu kawai" tuni Hafsat ta kusa gate abunta, Hajja ta fashe da
kuka tace "Ni kuu kira min Muhammadu ya xo ya ga abun da muke gani, Ahmad ya cuce
mu, ya xo ya ga sa6on da Ahmad ya tafka, amma duk laifin uwarsa ce wllh kuma mu dai
Allah ya isa, ina laifin ka fiddo 'yar uwar ka Humainah a matsayin warce xaka aura,
ko ka xabo cikin kannin nan naka Suhaima da Muhibba, toh ni ina ya samo
mahaukaciyar ma tukun" Mumy da har idonta ya kawo ruwa ta kalli Junaid da kansa ke
kasa tace "Maida ta inda ka daukota kuma minti talatin kawai na baka kaje ka dawo"
juyawa yayi yana rike da ita ya nufi kofa, Hajja da su Hajiya da suka ji kamar suyi
shewa ana rige rigen gudu aka bar bakin kofar. Junaid na ganin dishi dishi ya nufi
mota da ita, driving kawai yake amma bai ma ganin gabansa da kyau ji yake kamar a
sama yake tafiyar ma, ihun da jasmine tayi da karfi yasa idonsa ya bude sosai, sai
a sannan yaga irin tukin da yake da ihun da jama'a ma suke yi, kokarin kauce ma
babban motar da yake kokarin karo da yayi, amma hakan bai yiwu ba don sai da suka
yi karo bayan haka ya juya kan motar yayi gefen titi yayi cikin jama'a nan ma yaje
ya buge da pole, sama sama ya dinga jin abinda Jasmine ke cewa, iya karfinta take
cewa Umminta.... Umminta, Wayyo Umminta.... daga haka bai sake jin komai ba kuma
bai sake sanin abinda ke faruwa ba.

*Haske Writers Association*馃挕


� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

34.....

El-ameen ne xaune cikin special ward


ya hade kai da gadon dake kusa da shi, bude kofar ward din aka yi ya dago da kyar,
dai dai lokacin da Hajja ta karaso gun gadon da gudu ta daura hannu a ka ta saki
wani uban ihu tana salati su Hajiya ma suka shigo ko wanne tana salati, mikewa El-
ameen yyi ya fice daga ward din, ba a dau lokaci ba nurses har hudu suka shigo suka
fitar da Hajja da su Hajiya, kuka Hajja take rusawa iya karfinta tana cewa "Ku gaya
min ko mutuwa yayi don Allah, wayyo mahaukaciya ta cuce mu, kila yana tukin ta
shake mana shi ya saki steering, wayyoo ni Dijee" Su Hajiya dai sai matsen kwalla
ake kamar gaske, El-ameen ne ya xo wucewa Hajja ta bi sa da gudu tana cewa "Tsaya
Aminu gaya min me ya samu Ahmad din, don Allah gaya min ya mutu ne? Wayyo an
kassara Muhammadu don shi daya gare sa" Tafiya kawai El-Ameen yake tana binsa da
gudu har ya isa ward din ya shiga ya rufe kofar yasa makulli, ta fashe da
matsanancin kuka tace "Allah ya isa tsakani na da kai dan iska" A hankali El-ameen
ya karasa gadon da Junaid ke kwance yana kallonsa, a shoulder dinsa yaji ciwo banda
nan bbu wani waje kuma sai dai har lokacin he's unconscious, juyawa yayi yana
kallon Jasmine dake kwance a wani gadon har lokacin ita ma bata farfado ba, ya
xauna ya hade kai da gado, shine mutum na farko da aka fara kira aka sanar ma
hatsarin wanda hakan na nuni da shine mutum na karshe da suka yi waya da Junaid
din, bude kofar ward din aka yi Abbansa ya shigo da wata nurse biye da shi a baya
da clinic tray, mikewa yayi Abba yace "Meye amfanin saka su gaban da ka xo kayi ga
injections ba a gama ba....." Baya ya koma Abba ya dafa goshin Junaid ya kuma yi
masa gwaje gwaje sannan ya juya ya koma gun jasmine, a forehead dinta ta ji ciwo
sai kneel dinta daya, ita ma ya mata gwaje gwajen da xai yi ya juya yana kallon El-
ameen yace "Ka karbi injections din hannunta ka masu, in ka gama ka xo office ka
dau wanda xaka xuba a ruwa" daga haka ya juya ya fita, nurse din ta karaso ta mika
masa tray din hannunta ya karba ta juya ta fita, Junaid ya fara yi ma sannan ya
karasa gun Jasmine ya mata a lap. Kasa fita daga ward din yayi ya koma ya xauna duk
jikinsa ba kwari, Abbansa ne ya kuma dawowa tare da Abban Junaid, Abba ya karasa
gun gadon yana kallon Junaid da ganinsa kasan kawai yana boye tashin hankalinsa ne,
Allah ya basa lafiya kadai yace ya juya ya fita Abban El-ameen ya bi sa a baya, El-
ameen ya koma ya xauna, har bayan azahar babu wanda ya farka cikinsu, har lokacin
kuma Hajja na asibitin tana rera kuka har an gaji an kyaleta, su Hajiya duk sun
koma gida, kiran la'asar ya sa El-ameen ya fita daga ward din don xuwa yin sallah,
yana fito ko minti biyar ba a yi ba jasmine ta bude idonta a hankali, bin dakin ta
shiga yi da kallo a hankali har idonta ya sauka kan Junaid, kokarin mikewa xaune ta
yi taji kamar an tsikara mata allura a kneel ga kuma drip din da ta gani jikinta,
ta koma da sauri ta kwanta tana kallon drip din hannunta, fixgewa tayi ta ajiye, ta
kusa minti bakwai xaune kamar me son tuno abu wanda hakan da take yi yasa kanta
yayi mata wani mugun nauyi ga tsara mata da yake kamar xai tsage, kara tayi ta rike
kan da hannu biyu taji abu kamar hula a xagaye mata, da sauri ta cire hannunta,
bayan kusan minti biyu taji ciwon ya rage, saukowa ta shiga yi a hankali daga kan
gadon, kamar me tsoron tiles din dakin ta dinga tafiya tana dingishi har ta isa
gadon da Junaid ke kwance tana lekan fuskarsa, komawa baya tayi da sauri, sai kuma
ta saka kuka tana yarfe hannu lokaci daya tana kare ma dakin kallo, a hankali tace
"Ummi...." Sake lekan fuskarsa tayi ta kusa minti biyu idonta a kansa kafin ta juya
a hankali ta bar wajen, muryoyi taji daga waje ta nufi wani kofa da ta gani da gudu
ta bude ta shige ta fashe da kuka, ji tayi an bude kofa can waje tayi saurin
jingina a jikin kofar bathroom din, kallon gadonta kawai El-ameen yake da mamaki,
can ya juya ya kalli Junaid, da sauri ya nufi toilet tana jin ya murda ta juyo da
sauri ta tura kofar da duk hannunta biyu, sau daya ya tura kofar ya bude ta koma
baya da sauri tare da juya masa baya, kallonta ya tsaya yi da mamaki, a hankali
yace "Jewel" xaro ido tayi zuciyarta na bugawa har lokacin kuma bata juyo ba,
karasawa yayi ya dafata yace "Jewel" k'ara tayi da karfi yyi saurin juyo da ita
yace "Hey It's me jewel" tsit tayi tana kallon fuskarsa xuciyarta na bugawa,
murmushi ya sakar mata ya kama hannunta yace "Am glad you are fine!" fixge hannunta
tayi da sauri ta fashe da kuka tace "Ummina!" Tana fadin haka ta sake juya masa
baya tana rera kuka, still yayi na kusan second ashirin sautin xaxxakan muryarta na
kai kawo a kunnensa, ya kifta ido ya kusa sau biyar, can ta juyo a hankali suna
hada ido ta sunkuyar da kai ta raba ta gefensa xata fita yyi hanxarin tare hanyar,
da kyar ya iya bude baki yace "Wait! Wait Ina...ina Ummin naki?" Kallonsa kawai
take sai kuma a hankali ta buda masa hannu alamar bata sani ba, cikin sanyin murya
yace "Baki sani ba?" Ta gyada masa kai hawaye ya gangaro fararen idonta, murmushi
ne yayi slipnn lips dinsa a hankali yace "Ohh! Alhmdllh!" lokaci daya murmushin ya
bace tunawa da yayi sai fa ya iya xama kuma tayi loosing memory ya girgixa kai da
sauri yace "No! no gaya min ya sunanki?" Kallonsa kawai take yi, ya gyada mata kai
yace "Yyees tell me, ya sunanki?..." Gefensa ta kuma rabawa xata fita ya rikota, ta
juyo da sauri ta warce hannunta tana masa wani irin kallon da yasa hanjin cikinsa
kadawa, komawa baya yayi da sauri ta fice daga toilet din ya bi ta da kallo
xuciyarsa na bugawa.

*Haske Writers association*馃挕

Ba yawa kuyi sorry, na gaji ne yau

*Captain Ahmad Junaid*


_By Khaleesat Haiydar_
35.....
Da kyar El-ameen ya iya juyawa ya fita daga bathroom din, ya ganta tsaye kusa da
kofa tana kokarin budewa, tsayawa yayi yana kallonta har ta bude xata fita yayi
saurin cewa "Wait wait ina xa ki" ko kallonsa bata yi ba ta fice, xaro ido yayi ya
juya yana kallon Junaid kamar idonsa biyu din nan, bayanta ya bi da sauri ya tarar
har ta sauka stairs tun kan ta karasa shiga reception ya sha gabanta, xuciyarsa na
bugawa ya dake yace "Look, kin ga baki da lafiya ina xa ki" shiru tayi tana
kallonsa, ya kasa kallon cikin idonta, cikin sanyin murya yace "Kiyi hakuri ki bari
ki kara samun lafiya sai a kai ki gidan ku kin ji?" Jin bata ce komai ba ya dago da
kyar yana kallon kwayar idonta, hawaye ya gani fal idon, ya dauke kansa, a hankali
yaji tace "Toh ina ne nan?" Ya kuma dagowa da sauri yana kallonta yace "Asibiti,"
maimaita abinda ya fada tayi a sanyaye ya gyada mata kai, tace "Meye hakan?" Buda
ido yayi yana kallonta lokaci daya jikinsa yayi sanyi, ya girgixa kai da sauri yace
"Ki gaya min sunan ki tukun!" Shiru tayi tana kallonsa, can tace "Suna?" Ya gyada
mata kai, kafa masa ido tayi kamar dai tana son tuno sunan, a xuciyarsa ya dinga
furta innalillahi, k'ara tayi ta dafe kanta xata durkusa, yayi saurin rikota ya
dagata ya nufi sama da ita, addu'a ya dinga yi a xuciyarsa na cewar Allah yasa ba
abinda yake tunani bane, lokaci daya jikinsa yayi sanyi, gadon da take ya mayar da
ita ta kwanta ta rufe ido, ya ja kujera ya xauna kusa da gadon yana kallonta, ta
kusa minti biyar bata bude idon ba, can ta bude a hankali tana sauke ido kansa ta
mike xaune da sauri tace "Ummina" gefen gadon ya xauna yace "Toh gaya min inda take
in kai ki" ACn dake ward din ta tsura ma ido da ganinta kasan tunani take, wani
karan ta kuma yi ta runtse ido ta dafe kanta, lumshe ido yayi shi ma ya dafe kai
tausayinta na shigarta, a hankali ya dago yana kallonta cikin sanyayyan murya yace
"Ki kwanta ki huta kin ji, anjima xa ki tuna inda Ummin ki take in kai ki" bude ido
tayi tana kallonsa ya sakar mata murmushi ya gyada mata kai, komawa tayi ta kwanta,
yace "Xa ki ci abinci" ta kallesa tace "Abinci?" Kamar me koyon word din tayi
maganan, jiki a sanyaye ya mike ya fita daga dakin ta bi sa da kallo, yana rufo
kofar ta mike xaune tana kallon gadon da Junaid yake, saukowa tayi a hankali ta isa
gun gadon ta duka tana lekan fuskarsa, ta kusa minti biyar tana kallonsa can ta
kamo hannunsa a hankali murya can kasa tace "Daddy!" Mikewa tayi da sauri kamar
warce ta tuno abu, runtse ido tayi ta dafe kanta hade da yin ihu, sosai kanta ke
juya mata wanda hakan yasa ta fadi kan gadon, ta dau lokaci bata dago ba, can ta
bude ido a hankali ta ganta kansa, xaro ido tayi ta mike da sauri tana kallon
shoulder dinsa dake jini duk da bandage din dake nan alamar ta fama masa, kuka ta
fashe da ta duka a hankali tana kallon shoulder din, bandage din dake kanta ta taba
ta sa hannu biyu ta fixge da karfi har sai da ya fita ta matso kusa da shi ta duka
ta daura bandage din kan kafadar nasa, bude kofa aka yi El-ameen ya shigo rike da
plate da cup din tea, tsaye yayi bakin kofar yana kallonta ta juyo ita ma tana
kallonsa ta nuna masa kafadar Junaid tace "Ciwo!" Tana fadin haka ta d'an bude ido
tana kallon abinda ta kira da ciwo kamar me son gano abu, karasowa El-ameen yayi
sanin she's trying hard ne ta tuna abu yace "yes ciwo ne, taho in sa maki wani
bandage din you are bleeding" gadonta ya nufa, ta bi bayansa jiki a sanyaye, ya
nuna mata inda xata xauna ta hau gadon ta xauna, ya ajiye plate din hannunsa ya
dauko wani bandage din da plaster ya gabanta, runtse ido tayi tun kan ya taba kan,
yana kallon fuskarta har ya gama sa mata bandage din, murya can kasa yace "Bude
idon" a hankali ta bude tana kallonsa, ya mata murmushi ta sunkuyar da kanta,
abincin ya bude ya dau spoon ya mika mata, ta karba tana kallon cokalin, yace "Eat"
ganin yanda take kallon cokalin yasa ya karba ya debi abincin ya kai mata baki, ta
bude bakin a hankali ya xuba mata, kallon yanda take tauna abincin yake, aka bude
kofar ward din Abbansa ya shigo da wata nurse, ajiye spoon din yayi da sauri, Abba
ya karaso yana kallonta yace "Maa sha Allah, Alhmdllh ashe ta farka baka sanar min
ba, to ina 'yan uwan nata ita" rasa abun cewa El-ameen yayi, Abba dai sai kallonta
yake ganin she looks familiar, lokaci daya ya tuna inda ya taba ganinta ya kalli
El-ameen da sauri yace "Wannan ba mahaukaciyar nan bace da ka kawo min nan ranan,
me ya hada ta da Ahmad?" El-ameen da xuciyarsa ke bugawa ya mike don ya ma rasa
abun cewa, tsawa Abba yayi masa yace "Are you daft?" Da kyar yace "Abba ta samu
lafiya ma, dama iyayenta, Abba gida...." Strictly Abba yace "Kana son ganin the
odza side of me ko Ahmad?" Sunkuyar da kai yayi, Abba yace "Maxa fitar min da ita
daga nan ka maida ta gun iyayenta, mutumin banxa kawai" juyawa Abba yayi ya bar
wajen ya isa kusa da Junaid yyi gwaje gwajensa, ya jima yana kallonsa kafin ya
kalli nurse din yace "We might need to diagnose his brain, ya dau lokaci bai
farfado ba" daga haka ya juya ya fita nurse din ta bi bayansa, tun da El-ameen ya
ji abinda Abba yace gabansa ya fadi ba kadan ba, ya karasa gadon da sauri yana
kallon Junaid, kansa ya dafa na kusan minti uku sannan ya cire hannunsa a hankali
cikin sanyin murya yace "Come back pls frnd, for the sake of ur patient...." Juyawa
yayi yana kallonta ya ga hawaye idonta ya karasa da sauri yace "Me ya faru?" Ta
fashe da kuka, shiru yayi yana kallonta don ya lura ba ko wani magana ma take
ganewa ba, kamo hannunta yayi a hankali yace "Kiyi hakuri kin ji, xan kai ki gidan
ku" ita dai kallonsa kawai take, tunanin inda xai kai ta yake, sanin in har Abba ya
dawo ya kuma ganinta ransa xai baci, gashi bai son barin Junaid, murda kofar dakin
aka yi, ya juya da sauri Mumy ta shigo tare da Humainah da fatima, jikinsa yayi
sanyi ya sunkuyar da kai. Humainah ce tayi karfin halin karasawa kusa da gadon da
Junaid yake ta durkusa ta fashe da kuka, fatima ta juya ta fice daga ward din, Mumy
bata iya ta karaso cikin dakin ba, Humainah ta kamo hannunsa cikin rawar murya tace
"plss ka tashi ya A.jay..." El-ameen ya karasa kusa da ita yace "He will be fine ki
daina kuka kin ji" juyawa Mumy tayi ita ma ta fita daga dakin, Humainah ta kallesa
hawaye na bin kuncinta tace "Toh me yasa har yanxu bai tashi ba" dagota yayi yace
"Xai tashi nan da few minutes in'sha Allah" kallon jasmine dake ta kallonta tayi
kawai ta juya ta fice daga ward din tana kuka sosai, juyawa yayi yana kallon
Jasmine ya karasa kusa da ita, hawaye ne ya gangaro idonta a hankali tace "Yayanta
ne?" Kallon mamaki yake mata don in tayi wani maganar kamar ba ita ba, gyada mata
kai yayi yace "Ehh!" Daga haka ya xauna ya ci gaba da bata abincin, kadan ta ci ta
dauke kai xai yi magana aka bude kofa mikewa yayi da sauri, gabansa ya fadi ganin
Abba ne ya dawo, yace "Abba ynxu xan fita da ita wllh" wani kallo Abba yayi masa
sannan ya nufi gadon da Junaid yake, wani ruwan ya sa masa ya juya yana kallon El-
ameen yace "tana gama karban sauran treatment dinta gobe ka fitar min da ita a
asibiti, don't let me repeat my self tomorrow" kai ya gyada da sauri yace "Yess
sir" juyawa Abba yayi ya fice, El-ameen ya sauke ajiyar xuciya ya xauna yayi
tagumi, da dukkan alamu tayi loosing memory ko ba duka ba, kuma xai dauki months
kafin ta dawo dai dai shima sai tana shan drugs ana kuma yi mata abubuwan da ya
dace, in kuma Allah yasa tayi toxali da wani nata kila ya dawo gaba daya, a hankali
ya daga kai yana kallonta ya ga ta jingina jikin gado idonta lumshe, mikewa yayi da
sauri ya kwantar da ita ta bude ido ya sakar mata murmushi yace "Sleep jewel!" A
hankali tace "Sleep" ya gyada mata kai daga haka ta lumshe idonta. Har sha biyun
dare yana dakin, hankalinsa ya tashi sosai ganin Junaid bai farfado ba har lokacin,
wata nurse ce ta xo tace Abba na kiransa ya mike ya fita jiki ba kwari, yana fita
jasmine ta farka ta mike xaune da sauri tana kalle kalle a hankali tace "Ummina" ta
kusa minti goma xauna ta ga Junaid na motsi, ido ta kafa masa, can ta sauko a
hankali ta iso kusa da gadon ta duka tana kallonsa, a hankali ya bude idonsa ya
shiga kalle kallen dakin idonsa ya sauka kanta, ta d'an koma baya tace "Sleep"
kallonta kawai yake, ta d'an yi murmushi ta buda masa manyan idonta ta kuma cewa
"Sleep"
*Haske writers association*

*Captain Ahmad Junaid*


_By Khaleesat Haiydar_
36.....
A hankali ta koma baya jin bai ce komai ba har lokacin idonsa na kanta, ta d'an
bata fuska ta juya masa baya dai dai shigowar El-ameen ward din, da sauri ya karaso
gun gadon yana kallonsa ganin idonsa bude, murmushi ne yayi escaping lips dinsa
yace "Ohh Captain! You are back" Lokaci daya murmushin ya bace ganin yanda Junaid
ke kallonsa, dukawa yayi a hankali yace "Ahmad!" Nan ma dai kallonsa kawai Junaid
ke yi, El-ameen ya girgixa kai da sauri yace "No plss say something frnd, kana ji
na..." D'aga sa yayi xaune yace "Ahmad talk to me" dafe kai El-ameen yyi a
xuciyarsa ya dinga furta innalillahi.... Jasmine ta matso kusa da shi a hankali
tana kallonsa, Dagowa yayi da kyar ya kuma kallon Junaid yace "Captain!" Dukawa
tayi kamar yanda yayi ita ma cikin sanyayyan muryarta tace "Captain!" El-ameen ya
juya yana kallonta, ta buda masa ido tace "Captain" juyawa yayi ya maida dubansa ga
Junaid yaga kallonta yake, mikewa El-ameen yayi jiki a sanyaye ya nufi kofa,
jasmine ta bi sa da kallo har ya fita sannan ta juya tana kallon Junaid tace
"Captain" kallonta kawai yake, ta matso kusa da shi tana kallon shoulder dinsa a
hankali tace "Ciwo!" Sai kuma tayi murmushi tace "Yana ma zafi?" Kallonta Kawai har
lokacin ko kiftawa bai yi, shiru tayi kamar me naxarin abinda ta fada can ta rike
kanta ta sulale nan wajen tayi k'ara tana cewa Umminta dai dai shigowar El-ameen da
Abbansa sai wani Dr faruqh, Junaid ya lumshe ido ya bude, El-ameen ya karasa da
sauri ya dagota yana kallonta, Abba ya girgixa kai tare da yin kwafa yace "When I
say tomorrow I mean tomorrow" a sanyaye El-ameen ya maida ta kan gadon da take ya
kwantar da ita har lokacin ta ki bude ido, Abba dake ta kallon Junaid ya duka
gabansa a hankali yace "Ahmad?" Junaid ya dago ya kallesa sannan ya maida kansa
kasa yace "Na'am" Abba ya juya ya kalli El-ameen da ya xaro ido yana kallon Junaid,
da sauri ya karaso har lokacin idonsa a kansa, Abba yyi murmushi yace "Alhmdllh!
Ina ke maka ciwo yanzu?" Junaid yayi shiru, a hankali Abba ya kuma cewa "Ahmad" ya
dago ya kallesa yace "Ba ko ina Abba" Abba yace "Are you sure?" Ya gyada masa kai,
Abba yace "Maa sha Allah, Allah ya tsare gaba bari a kawo maka tea yanzu sai ka sha
drugs" daga haka Abba ya juya ya fita, Dr faruqh yayi murmushi yace "Allah ya kara
kiyayewa Captain Junaid" Junaid yace "Ameen" daga haka Faruqh ya juya ya fita, El-
ameen ya sauke ajiyar xuciya yace "gaskiya kana da matsala junaid, ni meye nawa xa
ka share ni" Junaid bai tanka sa ba ya sauka daga kan gadon ya nufi toilet, El-
ameen ya bi sa da kallon mamaki, girgixa kai yayi ya juya yana kallon jasmine ya ga
har ta fara bacci, ya karasa kusa da ita ya duka murya can kasa yace "Jewel" bude
ido tayi tana kallonsa, ya mata murmushi yace "Sleep" cikin sanyin murya tace
"Captain!" Yayi shiru yana kallonta kafin ya girgixa mata kai a hankali yace
"Doctor!" Rufe idonta tayi bata sake budewa ba ya mike ya gyara mata kwanciya ya
rufa mata bargon da ke kan gadon, junaid ya fito ya nufi gadon da yake, El-ameen ya
bi sa da kallo yace "patient din ka ta samu lafiya" Ba tare da junaid ya kallesa ba
yace "Naga alama" El-Ameen yayi murmushi yace "Hakan kuma ya faru ne ta dalilin
accident din da ku ka yi, nd this clearly shows dat hatsari ne cause din haukanta,
sai dai kuma ga dukkan alamu tayi loosing memory...." Wata nurse ce ta shigo da cup
din tea ta karasa kusa da Junaid ta mika masa ya karba ya fara sha, ta ajiye
magungunan hannunta ta gwada masa yanda xai sha ta bude fridge ta fiddo masa ruwa
ta ajiye sannan ta fita, El-ameen yace "Ina magana xaka wani min shiru?" Junaid ya
kallesa yace "Ai na ji ka, and am glad ta samu lafiya dama abinda nake so kenan,
yanzu abinda ya rage shine in sama mata inda xata fara rayuwa har memoryn ta ya
dawo....." El-ameen yace "inda xa ka sama mata kamar ina?" Junaid ya kallesa sannan
yace "Inda xata xauna ta ci gaba da rayuwa nace" El-ameen yace "Toh ai ban gane
irin gun da kake fadi bane" Junaid yace "Ko mama jumman nan sai in sa a nemo min in
damka mata ita ta rike har tayi recalling abubuwa ta nemi iyayenta" El-ameen yace
"Haba, she still need medication har ynxu fa....." Junaid ya kallesa yace "Nayi iya
taimakon da xan mata a yanzu, idan mama jumman ma ta dauketa dole xan basu kudi
that will be enough for der needs....." El-ameen yace "No plss ba sai an kai ta
kauye ba, ka bari ka cike ladan ka kawai" Junaid yayi masa wani irin kallo yace
"Bana ketare maganar mahaifiyata, tace in maida ta inda na samo ta and dat's wat am
going to do..." Shiru El-ameen yayi na wani lokaci kafin yace "Amma baka mata
adalci ba" Junaid yace "Look ka bar ni in ji da abinda ke damuna yanzu El-ameen,
ban san da idon da xan kalli mahaifiyata ba, ban san ta wani sigar Abbana xai dauki
batun nan ba, I've tried my best na mata iyakar abinda ya kamata tunda gashi ta
dawo hankalinta...." El-ameen bai kuma cewa komai ba ya lumshe ido ya bude sannan
ya fita daga ward din. Junaid ya jinginar da kansa jikin bango daga xaunen da yake
ya lumshe ido, har kusan Karfe biyu El-ameen bai dawo dakin ba, ya juya yana kallon
gadon da take kwance, saukowa yayi daga kan gadon da yake ya karasa nata gadon yana
kallonta, lumshe ido yayi cikin sanyin murya yace "Na so taimakon da xan maki ya fi
haka Jasmine, I can't help, baxan iya tsallake umarnin Mumyna ba, am very glad kin
dawo mai hankali, nasan you will cope da new environment din da xa ki samu kanki
har tunanin ki ya dawo" ya kusa minti goma kusa da ita kafin ya mike a sanyaye ya
koma gadonsa. Ciwon kai bai bar sa ya runtsa ba har Karfe hudu, yana nan kwance aka
bude kofar El-ameen ya shigo, lumshe ido yayi kamar me bacci, El-ameen ya karasa
kusa da shi yana kallonsa, ya daura hannunsa kan forhead dinsa ya ji da dumi sosai,
kallon magungunan da ke gefensa yayi da mamaki ganin bai sha ba, ya jima tsaye
kansa kafin ya juya ya koma gun jasmine, kwata kwata daren kasa bacci yayi sbda
tausayinta, da ya tuna abinda Abbansa yace kan gobe bai son ganinta asibitin sai
jikinsa yayi sanyi, in kuma ya tuno furucin junaid ma sai yaji tausayinta sosai,
dukawa yayi yana kallon fuskarta, yaga ta bude ido da sauri, komawa baya yayi ta
mike xaune tana mitstsika ido tace "Captain!"
*Haske Writers Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

37/38

Murmushi El-ameen ya mata yace "Good morning" ita ma a hankali tace "Good morning!"
Ya gyada mata kai yana murmushi har lokacin, duk abun nan da suke Junaid na
kallonsu, yana ganin El-ameen xai juyo yayi saurin lumshe ido, El-ameen ya nufi
kofa ta bi sa da kallo kafin ya fita tayi saurin cewa "Captain!" Juyawa yayi ya
kalleta ya girgixa mata kai yana murmushi yace "No, Am doctor!" A hankali tace
"Doctor?" Ya d'an bude ido yace "Yess" juyawa yayi ya fice. Saukowa tayi daga gadon
ta nufi gadon Junaid ta duka tana kallon long eyelashes dinsa don har lokacin
idonsa a lumshe yake, a hankali tace "Captain!" Ya bude ido da sauri yana kallonta,
tayi murmushi tace "Good morning!" Mikewa xaune yayi ya mayar mata murmushin yace
"Morning jasmine, how you?" A hankali tace "Am fine, and you?" Shiru tayi da sauri
kamar me naxarin abinda tace, can ta runtse ido ta dafe kanta ta durkusa wajen, ya
sauko da sauri yana kallonta, ta kusa minti biyar a haka shi dai bai dagota ba bai
kuma san ma me xai ce mata ba, mikewa tayi a hankali tana rike da kan ta juya ta
bar wajen ya bi ta da ido, xama tayi kan kujeran da ke kusa da gadonta ta kifa
kanta ta inda ba ciwo, komawa yayi ya xauna har lokacin yana kallonta. El-ameen ne
ya shigo dakin bayan an idar da sllhn Asuba, ya samu Junaid xaune kan darduma, ya
ajiye ledan hannunsa ya ja kujera ya xauna yana kallonsa yace "Good morning
captain, ya jikin?" Junaid yace "Alhmdllh" kallon magungunansa El-ameen yayi yace
"Jiya baka sha drugs din ka ba ashe?" Junaid bai ce komai ba El-ameen ya tabe baki
ya mike yana kallon jasmine dake xaune har lokacin kan kujera kanta kife kan gado,
karasawa yayi yana kallonta ya ga bacci ma take a haka, ya dan duka yace "Hello!"
Bude ido tayi da sauri tace "Hi" murmushi yayi yace "Good, tashi kiyi sllh" dago
kai tayi da sauri tana kallonsa tace "Sallah?" Ya gyada mata kai, tayi shiru tana
kallonsa kamar bata taba jin Kalmar ba, shi dai Junaid kallonsu kawai yake, El-
ameen yace "Am coming" daga haka ya juya ya fita, ba a dau lokaci ba ya dawo tare
da wata nurse rike da hijab, ya kalli nurse din yace "Ki rakata bayi, ki gwada mata
yanda xata yi alwala" nurse din ta kalli jasmine sannan ta kallesa tace "Ban gane
ba sir" Yace "Yes alwala xaki yi tana gani tana bin ki" nurse din ta kuma kallon
jasmine dake kallonta ita ma ta ajiye hijab din hannunta tace "Toh sir" El-ameen ya
kalli Jasmine yace "Tashi ki bita kiyi duk abinda tayi kin ji" mikewa tayi tana
kallonsa ya gyada mata kai yace "Yes follow her" tace "I should follow her?"
Murmushi yayi ganin yanda take catch up da sauri yace "Yes follow her" kamar me
tausayin kasa haka ta dinga bin nurse din a baya har suka shiga toilet din, nurse
din ta rufe kofar tana kallonta tace "Do you want to urinate?" Kallonta kawai
Jasmine take kamar me naxarin word din, a hankali tace "Urinate?" Matar ta gyada
mata kai, girgixa mata kai tayi, matar ta dau kettle daya ta mika mata ita ma ta
dau daya tace "Kiyi duk yanda ki ka ga nayi" a hankali Jasmine ta durkusa tana
kallon nurse din runtse ido tayi jin xafi a kneel dinta, nurse din dai sai kallonta
take har ta bude idon, sannan ta yi bismilla ta fara alwalan tana kallonta, jasmine
ta wanke hannunta ita ma kamar yanda ta ga nurse din ke yi, haka tayi ta kwaiwayon
ta har suka kare alwalan nurse din ta fito tana biye da ita a baya, har lokacin
junaid na xaune kan darduma, El-ameen ma na xaune yana jiran fitowar su, mikewa
yayi yana kallon junaid yace "Pray mat malam" junaid ya tabe baki ya mike ya koma
kan gado, El-ameen ya shimfida ya kuma dauko wani ya shimfida a baya, ya dau hijab
ya mika mata yace "Ki saka" karba tayi tana kare ma Hijab din kallo, ya mata alama
da tasa, kokarin sakawa ta shiga yi ta kasa don bata san ma yanda xata saka din ba,
ya karaso yana murmushi ya karba ya saka mata, Junaid ya kauda kai hade da tabe
baki, El-ameen ya nuna mata inda xata tsaya kan darduman yace "Kiyi duk yanda kika
ga nayi" shiru tayi tana kallonsa, yace "Kin ji?" A hankali ta gyada masa kai, ya
koma darduman gaba ya tada sllh, haka ta dinga binsa sllhn tana yin duk yanda taga
yayi da kyar sbda kneel dinta, har suka idar ya juya yana kallonta, jini ya gani
Hijab dinta ya dawo kusa da ita da sauri yace "Ohh!" Hannu yasa xai daga hijab din
ta koma baya sauri tana masa wani kallo, komawa baya yayi cikin sanyin murya yace
"Yi hakuri," mikewa yayi ya fita, ta juya tana kallon Junaid da ke kallonsu, dauke
kanta tayi tana nan xaune har El-ameen ya dawo da nurse, nurse din ta duka kusa da
jasmine tace "Sannu" daga hijab din tayi tana kallon kneel din, kayan aiki El-ameen
ya miko mata nan ta fara gyara mata wajen, rufe idonta tayi da ganinta kasan
daurewa kawai take, El-ameen ya durkusa kusa da ita yana mata sannu, har nurse din
ta gama, a hankali ta bude idonta da ya kada, yace "Sannu" ta kallesa sannan ta
sunkuyar da kanta, mikewa nurse din tayi ta fita da kayan aikin, tashi yyi ya dauke
darduman da yake kai ita ma ta mike ta dauke dayan, Junaid ya dauke kai tun kan su
kallo inda yake, ledan da El-ameen ya shigo da ya nufa ya bude ya fiddo da sabbin
toothbrushes da toothpaste, ya ajiye ma junaid daya ya bude daya ya matsa
toothpaste ya mika mata yace "Tafi ki wanke bakin ki" karasowa tayi ta karba tana
kallonsa, murmushi yayi sanin bata gane ba kenan, yace "Follow me" da sauri tace
"Follow her" dariya ta basa yace "No, follow me dai" daga haka ya shiga toilet ta
bi bayansa, yana kallonta yayi mata alama da hannu da ta wanke baki da brush din,
saka brush din tayi a baki ta tsaya, yace "Toh wanke bakin" tsotsan toothpaste din
tayi ta cire brush din tana yamutse fuska, yace "No ba haka ba" ya mika mata hannu
alamar ta basa ta mika masa ya kai brush din baki, nan ya shiga gwada mata yanda
xata yi sannan ya mika mata, yanda taga yayi haka tayi yana kallonta har ta gama
sannan ya nuna mata gun xuban ruwa yace "Wash ur mouth," karasawa tayi tana kallon
wajen, yayi murmushi ya karaso ya bude mata ruwan ya tara da hannunsa ya kai
bakinsa ya kuskure ya xubar sannan ya kalleta yace "Haka xa ki yi" tara hannunta
tayi ita ma, ya tsura ma fararen hannun nata ido har ta kai ruwan baki ta kuskure
kamar yanda ta ga yayi" murmushi ya mata yace "Good gal" juyawa yayi yace "Mu tafi"
ta bi bayansa suka fito, bai yi mamakin rashin ganin junaid dakin ba, yana lafiya
ma ya aka kare bare yanxu, kujera ya nuna mata ta xauna yace "Am coming" sannan ya
nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita. Ba a dau lokaci ba ya dawo da bowl me
dauke da apples, ya jawo table karami ya ajiye kusa da ita sannan ya daura bowl din
kai yana kallonta yace "Eat" kallon bowl din kawai take, can ta sa hannu ta dau
apple daya a hankali ta kai bakinta, bude kofa aka yi duk suka juya, gabansa ya
fadi ganin Abbansa, Abba ya karaso dakin yana kallon gadon junaid yace "Where is my
patient" El-ameen yayi saurin cewa "Ya d'an fita ne yanxu Abba" Abba yace "Ya fita
da sassafen nan ya je ina?" El-ameen da gabansa ke faduwa yace "Ina jin ya fita ne,
no cewa yayi xae fita ya sha iska" wani kallo Abba ke masa sannan ya kalli Jasmine
dake kallonsa yace "Bana son in sake shigowa in ga yarinyar nan a nan Ahmad" kallon
Abban nasa yayi a sanyaye yace "Toh Abba" Abba yace "Mutumin banxa kawai, kuma maxa
kaje ka dubo min patient dina yanxu" daga haka ya juya ya fita, El-ameen ya juya
yana kallon Jasmine, murmushin karfin hali ya sakar mata yace "Eat your apple"
sunkuyar da kanta kawai tayi, ya juya a sanyaye ya fita daga dakin. Babu inda bai
duba ba a asibitin amma bai ga junaid ba, abun yayi mugun basa mamaki kar dai gida
ya wuce, dawowa sama yayi bai kuma yi gigin xuwa gaya ma Abba bai gansa ba don
yasan baxai ji da dadi ba, office dinsa ya fara tafiya ya dau makullin motarsa
sannan ya tafi ward din da jasmine take ya ganta har lokacin rike da apple din bata
ci ba, ya karasa kusa da ita yace "Eat mana jasmine" bata kallesa ba ya kama
hannunta xai dago ga ta fixge hannun tana masa wani kallon da ya fadar masa da gaba
ya d'an koma baya a hankali yace "kiyi hakuri" ya gane bata son a taba ta kenan,
mikewa tayi tsaye, ya fara tafiya yace "Mu je" har ya isa bakin kofa ya juyo yaga
bata biyosa ba, yafito ta yayi sai gashi ta fara tahowa, Suna tafe yana juyowa yaga
ko tana binsa har suka fito haraban hospital din ya nufi parking space da ita,
gaban mota ya bude mata ya mata alamar ta shiga, still tayi tana kallon motar kamar
warce ta tuno abu, can kuma ta kallesa kamar xata yi kuka, accident dinsu na jiya
ne ya fado masa lokaci daya ya gane abinda yasa taki shiga, girgixa mata kai yayi
yace "babu abinda xai faru jewel, shiga" kin shiga motar tayi still, ya xaga ya
bude driver seat ya shiga ya tada motar kallonsa kawai take daga waje, can ta fara
kalle kallen asibitin, a hankali ta shiga daga karshe yayi murmushi ya rufo motar,
yana gama warming ya ja motar suka bar haraban asibitin bayan an bude masa gate,
driving kawai yake ba tare da yasan inda xai kai ta ba, duk tausayinta ya cika shi,
a hankali yace "Ina xan kai ki Jewel?" Kallonsa tayi ba tare da ta ce komai ba,
Kanwar Abbansa ce ta fado masa kawai ya yanke shawarar kai ta can gidan, Karfe
takwas da wani abu suka isa gidan, ya bude motar ya fito ya xaga ya bude mata ita
ma ta fito, yana gaba tana biye da shi a baya suka shiga gidan, bbu kowa parlon ya
nuna mata kujera ta xauna, cousin sis dinsa ta fito daga kitchen da mamaki take
kallonsa tace "Toh fa, yaya daga ina haka?" Yayi murmushi yace "Gida, kira min
Mumy" daki ta tafi tana cewa lallai yau akwai ruwa da kankara, Hajiya salmah Kanwar
dad dinsa ta fito parlon tana kallonsa tace "Kayi batan hanya ne Ahmad?" Yayi
murmushi yana shafa kai yace "A'a Mumy ina kwana" ta tabe baki ta amsa tana kallon
Jasmine, sunkuyar da kai jasmine tayi, El-ameen yace "Mumy na xo neman alfarma ne a
gun ki pls" tana kallonsa tace "Na me fa Ahmad" yayi kasa da murya ya shiga mata
bayanin Jasmine, kallonsa take baki bude har ya kai karshe tace "Ehh lallai Ahmad,
wato kai ne baka jin maganar naka
iyayen koh, kai ne baka san darajar su ba, to wllh maxa ka maida masa ita shi da
ya jajubo ta, maganar banxa kawai, shi me wayo yaji maganar tasa uwar sai kai ne da
baka san darajan naka uban ba koh....." Mikewa El-ameen yayi bai kuma sauraranta
ba, Jasmine na ganin ya tashi ita ma ta tashi da sauri, ya nufi kofa ta bi bayansa,
small mum din tasa ta bi sa da harara tace "D'an rainin hankali kawai, mara wayo,
kuma wllh sai na kira yaya na gaya masa yasan baka dauke sa bakin komai ba." Har ya
fice daga parlon bai tanka ta ba.

Junaid na fita daga asibitin dama trekking yayi har ya isa bakin titi duk da jirin
da yake gani ga wani ciwo da kansa yake masa da shoulder dinsa, singlet ne da jeans
jikinsa. shi matsalar sa daya Mumy bai san ta inda xai soma bata hakuri ba, ya jima
tsaye bakin titi wani tricycle ya tsaya yana tambayarsa ko tafiya ne, ya shiga ya
gaya masa inda ya nufa, Suna isa gida ya fito yace masa yana xuwa, gun mai gadi ya
karbi dari biyar ya basa sannan ya shiga gidan, Hajja ce ta fito daga side dinta
rike da wani katon kwandon kwanuka ta xuba kulolin abinci har uku da flask sai cup
ta daura a kai, xaro ido tayi ganinsa ta sauke kwandon da sauri cikin daga murya ta
ce "Alhmdllh jama'an gida Bilki, Fatee da Amina ku fito gashi ya ji sauki ya
dawo.... Amadina ya dawo, yaron kirki ya dawo...." Haka ta dinga yi kamar ta samu
waka, Umma ce ta fara fitowa da sauri su Muhibba na biye da ita, sai Hajiya da
khadija, fatima ma ta fito, da gudu khadija ta tafi ta rungumesa cike da murna,
yake su Hajiya da Umma aka shiga yi ana gode Allah ana jajantawa, Shi dai junaid
bai kallesu ba ya nufi part dinsa Hajja ta bi bayansa da sauri tana cewa "Amadina
ya dawo, yaron kirki ya dawo" tun kan ta iso ya sa ma kofar key ya shige bedroom,
ruwan xafi ya hada yayi wanka a toilet ya fito ya shirya, sai dai singlet kadai
yasa da bakin jeans sbda kafadarsa, kwanciya yayi jin xaxxabi na neman rufesa, ko
minti goma bai yi da kwanciya ba aka bubbuga kofar parlon ya mike da kyar ya bude,
fatima ya gani tsaye, ta gaishesa ta masa ya jiki ya amsa sannan tace Abba na
kiransa. Gyada mata kai yayi ta juya ta tafi, ya koma ya xauna parlon gabansa na
faduwa ya kusa minti biyar sannan ya mike jiki ba kwari ya fita daga parlon ya tafi
part din Abba, da kyar ya iya shiga parlon ganin dukka mutan gidan xaune da alaman
shi ake jira, bai bari sun hada ido da kowa ba, kansa a kasa yayi surveying inda
xai xauna ya xauna kawai, sai a sannan ya d'an dago kai yaga kusa da Humainah ya
xauna, sunkuyar da kai yayi, banda kallonsa babu abinda ake yi a parlon, Mumy kadai
ne bata ma kalli inda yake ba, Abba ya soma gaisarwa, sannan Hajja dake ta kallonsa
baki har kunne, sai kuma Hajiya da Umma, bayan nan ya daga kai yana kallon Mumynsa
cikin sanyin murya ya gaisheta, ta amsa ba tare da ta kallesa ba, Abba yace "Meye
dalilin ka na baro asibiti ba a sallame ka ba?" Sunkuyar da kansa yayi bai ce komai
ba, Abba ya girgixa kai yace "Toh ka kyauta, Ahmad ban yi mamakin abinda ka aikata
jiya ba, don dama ni na dade da sanin kai ma mahaukaci ne, iyayen ka ne dai basu
sani ba......" Hajja ta kyalkyale da dariya har da kwanciya tace "A'a Muhammadu
wllh nima ina sane kawai dai ban taba fadi bane, tunda hannun ka baya rubewa ka
yanke ka yar, amma Amadi kam mahaukaci ne" sunkuyar da kai junaid yayi, Hajiya da
Umma sai danne dariyarsu suke, Humainah tayi murmushi ta sunkuyar da kai ita ma,
Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh Allah ya kyauta, amma kafin haukan naka ya
xame mana bala'i na yanke shawarar yi ma aure nan da sati biyu kawai, ko kwandalar
ka bana bukata xan maka komai, shi yasa ma nace xan maka aure, alkawari ne wannan
na daukar ma kai na" dagowa yayi da sauri yana kallon Abba, su Hajiya duk aka
kwalalo ido, Hajja tace "Atoh" kallon Mumy junaid yayi yaga idonta na kan TV, xufa
ya dinga ji na keto masa, a hankali yace "Abba!" Abba ya dakatar da shi ta hanyar
daga masa hannu yace "No, ba shawarar ka nake nema ba, ba kuma xan maka abinda xai
cutar da kai ba."


*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

39.....

Junaid bai kuma cewa komai ba ya sunkuyar da kansa, Abba yace "Tashi kaje, idan
lokaci yayi xaka san matar taka" da kyar Junaid ya mike ya nufi kofa ya fita daga
parlon, part dinsa ya koma ya kwanta, lokaci daya yaji xaxxabi na neman rufesa, ya
jima kwance kafin bacci ya daukesa. Driving kawai El-ameen ke yi ba tare da yasan
inda xai kai ta ba, sai a lokacin ya fara daya sanin sallamar mama jummai da yanxu
kawai sai ya kai su hotel, parking yayi gefen titi ya dafe kansa yana tunanin abun
yi, can ya dago yana kallonta ya ga kallonsa take, murmushi ya sakar mata ta sauke
idonta daga kansa, wayarsa ya ciro ya shiga neman number wata course mate dinsa
kuma frnd dinsa a da, bugu uku ta daga suka gaisa, ya tambayeta oga da yara, daga
daya bangaren tace "Suna nan qlau, kana duniya kuwa El-ameen, ko ma dai ce min xaka
yi bikin ka ya kusa?" Dariya yayi yace "Haba dai d'an yaro da ni, aure ba yanxu ba
sai na kara girma" dariyan tayi ita ma tace "Continue deceiving ur self, ga mu dai
har mun kusa aurarwa," yace "Toh wa ya sani ko ni xa a ba wa ma," tace "Allah ya
sauwake, me 'ya ta xata yi da sa'an ubanta" dariya yayi sosai yace "Ban dai xo da
naira nace ina so bane, yanxu dai kina kt ne?" Tace "Ina nan ina xa ni," yace "Toh
a gaya ma oga gani nan xuwa dai" tace "Sai kace gaske" yace "Allah kuwa, gani xuwa
favour xan xo nema gun ku" tace "Toh sai ka xo, ina xuba ido" yace "Alryt tnx" daga
haka ya katse wayar, juyawa yayi yana kallon Jasmine dake ta kallonsa, ya buda ido
hade da mata murmushi, sunkuyar da kai tayi, ya ja motar suka bar wajen, cikin
minti ashirin ya isa gidan Dr Sumayya, bakin gate yayi parking ya kirata, tana
dagawa yace "Ga ni a waje" tace "Toh ka shigo mana" yace "Ohk" bude mota yayi ya
fito ya xagaya ya bude mata ta fito ya rufe sannan yace "let go" a hankali tace
"Ohk" wara ido yayi ya gyada mata kai yace "Good" daga haka ya fara tafiya ta bi
bayansa, Dr Sumayya ce ta bude masu kofa tana murmushi tace "Sannu da xuwa Dr, ashe
tare da bakuwa ku ke" yace "Exactly Mrs Sumayya" parlor suka shigo tace "Sannun ku
da xuwa" xaunawa tayi suka kuma gaisawa, ya tambayeta yara tace sun tafi sch,
yace "Maa sha Allah, bakuwata na kawo maki ta d'an yi kwana biyu" ta kalli Jasmine
tace "Da gaske?" Yace "Serious" murmushi tayi tace "Ohh she's welcome, budurwar ka
ce?" D'an wara ido yayi yace "No, no, xan ma iya cewa patient dita ce" Dr Sumayya
ta kyalkyale da dariya tace "Ohhh I see" murmushi yayi yace "Ohhh serious" kallon
Jasmine tayi tace "Sannu 'yan mata ina kwanan mu" El-ameen ya kalleta ya dawo
gefenta yace "Tell her good morning jewel" kallon matar Jasmine tayi a hankali tace
"Good morning" matar ta dan bude ido tana dariya tace "Toh fa" murmushi El-ameen
yayi yace "She just recovered from posttraumatic stress disorder, and tayi loosing
memory yanxu" Dr Sumayya jikinta yayi sanyi tace "Allahu Akbar, toh ina iyayenta"
girgixa kai yayi yace "Its a long story Dr, bamu san iyayenta ba, Abokina Captain
Junaid ne helper dinta, shi ya tsinto ta ya bada suggestion in mata treatment, gaba
daya expenses din kuma shi yayi volunteer....." Dr Sumayya tace "Ahmad Junaid dai
dana sani me ji da kan nan?" Dariya El-ameen yayi yace "Ohh Really? Toh shi!" Tace
"Ikon Allah, ashe yana da mutunci da taimako" El-ameen yace "Sosai ma, don baku
xauna da shi bane" Dr Sumayya tace "Kai amma yarinyar ta ban tausayi wllh, Allah
sarki" El-ameen yace "Kwana biyu xata yi a nan, akwai d'an matsala ne kuma we are
trying to fix it up, ki dinga bata pain relieving drugs sbda injury din kanta" Dr
Sumayya tace "In'sha Allah" mikewa yayi yace "Ni xan koma office" tace "Toh
shikenan take care!" Mikewa Jasmine ma tayi da sauri ya juya yana kallonta yace
"You will stay with aunt kin ji...." Hawaye ne ya ziraro idonta, jikinsa yayi sanyi
yace "No kar ki yi kuka I will be back soon" Dr Sumayya ta karaso ta kama hannunta
tace "Kar ki damu xai dawo kin ji 'yan mata" El-ameen yayi murmushi ya juya ya nufi
kofa, Dr Sumayya ta tafi daki da ita tana lallashinta. Junaid bai farka ba sai
kusan Karfe uku na rana, ya mike xaune da kyar, rike kansa dake masa ciwo sosai
yayi, can ya mike ya nufi toilet ya dauro alwala ya fito ya tada slln azahar,
parlor ya fito bayan ya idar ya ga abinci ajiye parlon, sai a sannan ya fara jin
yunwa don tun tea din da ya sha a asibiti jiya da daddare bai sake cin komai ba,
xaunawa yayi ya bude food warmern, ya ga shinkafa ne da miya, ya dau plate ya dibi
kadan ya fara ci, kwata kwata bai jin dadin abincin a bakinsa, spoon hudu yayi ya
ajiye ya jinginar da kansa jikin kujera, kwankwasa kofar parlon aka yi ya juya yana
kallon kofar kauda kai yayi dai dai lokacin da aka bude, colleagues dinsa na gun
aiki ne har su hudu dukkansu sanye da uniform suka shigo parlon, ya d'an bude ido
yana kallonsu har suka karaso parlon, daya daga cikinsu Captain Umar yace "Ohh ko
mu koma ne A.jay" Murmushi yayi yana shafa kansa yace "Uhnn it's surprising, sannun
ku da xuwa" xama suka yi gaba daya, nan suka gaisa, Daya daga cikin su yace "sai
muka ji bad news Ahmad" junaid yayi murmushi, Capt Umar yace "Toh ya jikin?" "Jiki
Alhmdllh, tun da gashi har na dawo gida" duk suka yi masa Allah ya sauwake, mikewa
yayi ya nufi fridge din dake parlon ya bude ya kawo masu ruwa da drink ya ajiye
masu, sun d'an taba hira na minti sha biyar suka ce masa xa su koma, fruits da
drinks suka ajiye masa yayi masu godiya ya rakasu part din Mumy su gaida ta, da
fara'a ta tarbe su basu jima ba suka mata sallama suka fito, Umma da Hajiya sai
kallonsu suke daga balcony, shi kuma bai ce su gaida su ba, yi ma yayi kamar bai
taba ganinsu ba, hakan yayi mugun kona masu rai, ya raka frnds din nasa har waje
gun mota, sannan ya komo cikin gida, part din Mumy ya tafi, duk suka bi sa da kallo
ko wanne da tunanin da take a ranta, yana shiga parlon Mumy Hajiya ta sauke ajiyar
xuciya tace "Yaro man kaza" Umma ta tabe baki tace "Ke yanxu kin yi farin ciki da
hukuncin da Alhaji ya yanke kansa?" Hajiya tace "Ina fa nayi farin ciki, kika san
warce xai aura masa? Kema dai kin san ba lallai ya xabi 'ya yanmu ba, na ma fi
tunanin kila yace shegiyar Humainahn nan, kuma da mun shiga uku mun lalace..." Umma
tace "Ba abun mu koma gun malam ba yanxu ya hada mu da k'ulli yace sai an barbada
ko sai anyi wani abun daban asiri ya kuma tonuwa ga Hajja mayya a gida" Hajiya tace
"Mu je ki ji ina da wata shawara Allah ya bamu sa'a wannan karan" mikewa Umma tayi
da damuwa tace "Ameen" ta bi bayanta suka shiga parlor. Bedroom junaid ya shiga
ganin Mumy bata parlor, ya karasa gabanta ya durkusa ba tare da ya bari sun hada
ido ba, cikin sanyin murya yace "Don Allah kiyi hakuri Mumy, forgive me plss kar
kiyi fushi da ni" jin bata tanka sa ba yasa ya dago yana kallonta, a hankali yace
"Kin ji Mumy!" Tana kallonsa da kyau tace "Ka min wani abu ne?" Shiru yayi bai ce
komai ba, tace "Toh baka min komai ba tashi ka fita" kasa tashi yayi, tace "Ka
tashi na ce" a sanyaye ya mike ya fita daga dakin. Kallo daya yayi ma Humainah dake
parlor ya nufi kofa ya fita, dai dai fitowar Hajja daga part din Abba, ya dauke kai
kamar bai ganta ba xai wuce tace "Kai Amadi mu muka dauro maka hatsarin nan ne xaka
wani dinga sha mana kamshi a gida don fitsara, to Allah shi kara, kuma ka tafi ka
gaida ubanka Abubakar ya xo tun daga Abuja" yi yayi kamar bai san da shi take ba ya
fara tafiya xuwa part dinsa, da karfi ta kwalo masa kira yanda tasan Abba xai ji
cike da masifa tace "Ni din sa'ar uwar ka ce ina maka magana kake tafiya kake min
tsaki, toh Muhammadu ka fito ka ga rashin kunyar da Amadi ke min gaban jama'a, don
an maka gata an raba ka da gagarumar mahaukaciya sai ka dau gaba da 'yan gida..."
Tsayawa yayi yana kallonta fuskar nan nasa a daure, tace "D'an banxa kawai, ka wuce
ka gaida ubanka Abubakar nace" part din Abbansa ya tafi ta bi sa da harara, da
sallama ya shiga parlon ya xauna kan carpet kansa a kasa ya gaida Small Abban nasa
dad din Humainah, Alhaji Abubakar yace "Lafiya lau Ahmad ya jikin?" Junaid yace
"Alhmdllh Abba ya hanya" "Hanya mun baro ta, ya aikin?" Cewar dad din Humainah yana
kallonsa, Junaid yace "Alhmdllh" dad din Humainah yace "To Maa sha Allah" kallon
Abbansa yayi yaga idonsa a kansa, yayi kasa da kai ya mike yayi musu sallama har ya
kai bakin kofa Abba yace "Ka koma asibitin?" Girgixa kai Junaid yayi yace "Yanxu
xan tafi Abba" Abba yace "Toh ka kira Abdul ya kai ka, ga makullin mota" komawa
cikin parlon yayi ya dau makullin yayi masa godiya ya juya ya fita. shiryawa ya
tafi yayi a part dinsa ya fito, sai da ya fara shiga ya gaya ma Mumy xai tafi
asibiti snn ya fito ya tafi parking space ya dau motar Abbansa ya fita don xai iya
driving din. Abban El-ameen ne ya duba sa da kansa a office dinsa, wani likita yayi
masa allura ya basa drugs dinsa, ya kusa awa daya office din sannan dad din El-
ameen yace xai iya tafiya ya dawo da daddare karban allura, godiya Junaid yayi masa
ya mike ya fita daga office din, yana saukowa second floor ya tsaya yana kallon
kofar office din El-ameen, karasawa yayi ya murda handle din door din ya tura,
xaune ya gansa ya jinginar da kansa jikin kujerar da yake idonsa rufe, har ya
karasa cikin office din bai sani ba, yayi knock din table din gabansa, da sauri El-
ameen ya bude ido ya gyara xama, Junaid yace "Sleeping at work" El-ameen ya shafa
kansa yace "Our run away patient" Junaid ya ja kujera ya xauna yana kallonsa yace
"ka bani number mai gadin can gidan naka nasan baxai rasa sanin whereabout din mama
jummai ba, El-ameen ya bude hannu yace " I don't have!" Junaid ya d'an bude ido
yace "Da gaske?" El-ameen ya gyada masa kai, junaid yace "Toh yanxu ya xa muyi?"
El-ameen yace "Na kai ta gidan old frnd dita Dr Sumayya" junaid yyi shiru kafin
yace "har xuwa yaushe?" El-ameen yace "I told her kwanaki kadan xata yi, dama
mijinta bai nan ne nasan xata rike ta but kasan halin su mata" Junaid ya sauke
ajiyar xuciya yace "Or mu kai ta orphanage home kawai tunda dai hankalinta ya dawo"
wani kallo El-ameen
yayi masa yace "tunda ca tayi maka bata da iyaye ba, ko kuma ance maka manya suke
dauka" Junaid yace "Toh yanxu kasan inda iyayen nata suke, ka sani ma ko suna da
rai, kaga ni iya taimakon da nasan xan iya yi ma yarinyar nan kenan sbda parent
dina, ba don su ba xan iya yi mata komai na taimako a rayuwa, I just can't keep on
disobeying my mother, beside am getting married in 2wks time kamar yanda Abbana
yace, to ya kake son inyi da 'yar mutane, ina xan kai ta idan ba orphanage home
ba?" El-ameen ya lumshe ido ya bude hade da shafa kai yace "Aure xa a maka! Toh me
xai hana ta xauna gidan ka tare da matar ka har memory dinta ya dawo junaid, last
gatan da xaka yi ma baiwar Allahn nan kenan a rayuwa" junaid yayi shiru yana
kallonsa can yace "Gidana kuma?" El-ameen yace "Yes, ko tare xaku tare da Mumy?"
Murmushi junaid yayi yace "Idan matar bata yarda ba fa?" El-ameen ya hade rai yace
"Gidan ubanta ne ko kanta xata xauna?" Junaid ya jinginar da kansa jikin kujera ya
lumshe idon yana naxarin shawarar El-ameen.


*Haske Writers Association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

40/41

Mikewa Junaid yayi yace "I will think about that!" Daga haka ya nufi kofa El-ameen
ya bi sa da kallo har ya fita. A haraban hospital din suka hadu da faisal, faisal
yace "Ohh my God, ashe abinda ya faru kenan captain shine ko ku sanar da ni kai da
El-ameen? da Childishness din ku ne ya tashi da har gida xa ku xo ku sameni" junaid
yayi murmushi yace "I thought ka sani ne ai," faisal yayi tsaki yace "Ta ina xan
sani?" Daga haka ya bar sa nan tsaye ya shiga asibitin, murmushi junaid ya kuma yi
ya shiga mota ya bar asibitin. Yana isa gida part dinsa ya tafi yayi alwala yayi
sllhn asr sannan ya kwanta parlor, har ya fara bacci yaji an bude kofar parlon,
bude ido yayi ya mike xaune da sauri, Humainah ce ta shigo parlon ta tsaya daga
bakin kofa ta d'an hade rai tace "Xamu tafi tare da Hajja!" Yana kallonta yace "Ina
xa ku" tace "Gidanmu!" Shiru yayi kafin yace "Ohk, yaushe xa ki dawo?" Ta tabe baki
tace "Baxan sake dawowa ba, da kayana duka xan tafi ma" murmushi Junaid yayi yace
"Ohk Allah raka taki gona" tace "Ameen" daga haka ta juya ta fice daga parlon, ya
koma ya kwanta. Tana fita hajja ta shigo sabe da gyalenta da 'yar jakar da ta taho
da shi, tace "Toh Amadi ni dai xan tafi sai kuma na dawo kai maka amarya ko kaki ko
ka so sai in ga ta tsiya, idan har ynxu ra'ayin rayuwa da mahaukaciya kake to sai
ka haukatar da warce za a kai maka hakan xai fi maka rufin asiri" daga haka ta juya
ta fita ya bi ta da kallo hade da tabe baki, ranan da daddare Ummin El-ameen ta xo
gidan, duk yanda ta so ya gaya mata ko El-ameen yasan komai kan xancen yarinya
mahaukaciya kin gaya mata yayi yace babu ruwan El-ameen, ba don ta yarda ba ta
kyalesa don tasan bakinsu daya, can tace "Na ji labarin aure xa ayi maka, saura
abokin ka, shi wannan kauye ma xanje dauko masa mata wallahi xan basa mamaki,"
Dariya Junaid yayi yace "Kai Ummi, kauye kuma" bata tanka sa ba ta mike ta fice
daga parlon. Shirye shiryen biki aka dinga yi gidansu Ahmad Junaid babu kama kafar
yaro, cikin kankanin lokaci aka hada lefe akwati shidda, shi dai Junaid kallon ikon
Allah kawai yake wai shi xa ayi ma aure, auren ma na dole kamar wani mace kuma har
lokacin bai san matar ba dariya ma kawai abun ke basa, ana saura sati bikin ya dawo
aiki da yamma yana kwance sai dai gaba daya tunaninsa na gun Jasmine yana son sanin
halin da take ciki yana kuma son ganinta, kiran El-ameen ne ya shigo wayarsa ya
daga, daga daya bangaren El-ameen yace "Uhm duk xumudin xama angon ne yasa ka mance
da patient dinka captain?" Junaid yace "If that's what you are thinking...." El-
ameen yace "Toh yayi kyau, amma idan baka manta the very first day da ka fara xuwa
min da batun ta sai da na baka shawarar ka raba kanka ka ki, yanxu ka xo kayi
abinda ya dame ka, ka bar ni da 'yar mutane, ko irin ka dinga kira ka tambayi
lafiyarta babu, to Dr sumayya dai ina a week time xa su yi tafiya da mai gidanta
wai..." Junaid yace "Yea! Then an min auren sai ta dawo gidana kamar yanda ka ce"
El-ameen ya tabe baki ya katse wayar. Karfe biyar da wani abu Junaid ya shirya ya
tafi part din Mumy yace mata xai dan fita, sabuwar motar da Abba ya basa ya dauka
ya fita daga gidan, a hanya ya kira El-ameen, yana dagawa yace "Kana ina?" El-ameen
yace "Me xan maka?" Tsaki Junaid yayi yace "Dalla ni ka gaya min" katse wayar El-
ameen yayi, junaid yayi parking ya ji kamar ya juya, sai dai baxai iya ba sbda son
ganin jasmine da yake, sake kiransa yayi yana dagawa yace "How dare you xaka katse
min waya daga tambaya" El-ameen yace "Ashe ba dadi kai kake ma mutane, ni da ma kai
ka haukacen wllh kayi loosing memory ko xaka rabu da wnn worst attitude din naka,
gashi it's getting worst nowadayz, ni ina gida anything?" Katse wayar junaid yayi
hade da yin kwafa, ya kusa minti goma xaune motar ya kuma yin wani kwafan ya ja
motar ya nufi gidan nasu, Ummi dake parlor ya gaida tace "Ni ban ga kai da abokin
naka kuna shirin bikin nan ba Ahmad" junaid yayi yake yana shafa kai yace "Ae
abinda ya kawo ni kenan" Ummi tace "Toh yayi kyau, da an gama naka da sati biyu in
an huta xan kai nasa lefen kauye" Junaid ya fashe da dariya yace "Wllh xan maki
driving din" Ummi ta hade rai tace "Am serious, dan ma ka gaya masa nake gaya maka"
dakin El-ameen ya nufa yana dariya, El-ameen ya tura laptop din gabansa yace "What
is making him laugh" Junaid ya buda ido yace "Baka ji a bakin Captain ba, yanzu dai
tashi ka kai ni in duba yarinyar nan tunda gori ka min daxu" El-ameen yace "As you
can see am busy, sai dai in baka address" junaid yace "Ba fa dadewa xa mu yi ba"
"yess! ko minti daya xa muyi" cewar El-ameen yana kallonsa da kyau. Junaid ya kusa
minti goma tsaye yana kallonsa kafin ya juya ya fita daga dakin, El-ameen yace
"Byee!" Da daddare yana kwance bedroom Humainah ta fado masa, tabe baki yayi ya
dauki wayarsa ya shiga kiranta, sai da ya kusa katsewa ta daga yace "don ma kin
samu na kira ki" tace "I didn't beg for ur call" shiru yayi sannan yayi murmushi
yace "True! Yaushe xa ki dawo?" Tace "Ana saura kwana biyu bikin ka xamu dawo da
Hajja" yace "Bikinsu dai" daga haka ya katse wayar, Har ya ajiye wayar ya tuna
Hafsat, tun ranan da abun ya faru bata kira ba bai kirata ba, numberta ya duba ya
shiga kiranta bugu uku ta daga ya mata sallama ta amsa daga daya side din hade da
gaishesa, ya ce "Ya kike?" Tace "Qlau" rasa me xai sake ce mata yayi, can dai yace
"Am sorry for what happened Hafsat," tace "Ohh ba komai, ya wuce ai" yace "To
nagode" tace "welcome! But a ina ka san yarinyar?" D'an shiru yayi kafin yace "It's
a long story" tace "really?" Yace "Yeah!" Labarin yanda ya fara ganin jasmine tun
daga rana ta farko ya fara bata har xuwa ranan da ya kai ta gida gun parent dinsa
da abinda ya faru bayan barinsu gida, Hafsat da duk jikinta yayi sanyi tace "Yanxu
kana nufin ta dawo hankalinta?" Yace "Yea, amma tayi loosing memory" Cike da damuwa
Hafsat tace "Allah sarki, to yanxu tana ina?" Ya lumshe ido ya bude yace "Tana gun
frnd dina, buh am getting married in a week time sai ta dawo gidana har tayi
regaining memory, Hafsat tace "Dat's nyc Allah ya sanya alkhairi, ya bada xaman
lafiya," Yace "Ameen thank you" shiru tayi ya kalli agogo ya ga har sha daya ya
wuce, yace "Xa ki kwanta koh?" Tace "Yeah" yace "Ohk good nyt, tnx a lot ki gaida
mutan gida" tace "Ayt bye!" Daga haka ya katse wayar ya ajiye yayi addu'an
kwanciya. Washegari da yamma junaid na kwance bayan ya dawo daga aiki El-ameen ya
shigo parlon, kallo daya ya masa ya dauke kai, El-ameen na daga tsaye bakin kofa
yace "In ka shirya ka taso mu tafi" ko kallonsa junaid bai yi ba, El-ameen yace
"Ohk nayi tafiya ta" daga haka ya fice. Junaid ya mike ya shiga bedroom ya daura
shirt dinsa ya dau Atm ya fita, a part din Mumy ya tarda El-ameen, ya jira har ya
gama surutun sa snn yace "Mumy xa mu d'an fita yanxu mu dawo" Mumy tace "Toh Allah
ya tsare" ya juya ya fita. A mota yayi ta jiran El-ameen har sai da yaga dama ya
fito, El-ameen ya xaga daya side din ganin junaid a driver seat yana shiga junaid
ya tada motar suka bar layin, tun a hanya El-ameen ya kira Dr sumayya ya sanar da
ita xuwansu, a visitor parlor suka sauka dotan Dr Sumayya 'yar shekara sha uku ce
ta kawo masu ruwa da drink ta xauna kusa da El-ameen tana ta basa labari, junaid
dai makala earpiece yayi yana danna waya, bayan kusan minti biyar Dr Sumayya ta
shigo parlon suka gaisa da El-ameen, El-ameen ya fixge wayar sai a sannan ya dago
yana kallon Dr Sumayya yace "Ina yini!" Tace "Lafiya lau ya aiki," yace "Alhmdllh,"
mikewa tayi ta fita tana fita sistern ta warce xata yi mate din jasmine ta shigo
parlon tare da jasmine din, xama tayi kan kujera ta nuna ma Jasmine gefenta ta
xauna sannan ta gaida su El-ameen, ya amsa mata da murmushi yace "Ya sch?" Tace
"Alhmdllh" kallon jasmine tayi tace "Baby baki ce masu ina yini ba" sunan da Dr
Sumayya ke kiranta da shi kenan a sati daya da 'yan kwanakin da tayi a gidan, shine
duk yan gidan ke kiranta da haka, shima El-Ameen dake yawan xuwa gidan sai ya dinga
kiranta da haka, jasmine ta kalli farida sannan ta kalli El-ameen a hankali tace
"Ina yini?" Murmushi kawai yayi mata ta sunkuyar da kai, Junaid dai sai kallonta
yake ta gefen ido, El-ameen yace "Toh baki gaida wannan ba Baby" Ya fadi hakan yana
nuna mata Junaid, kallonsa tayi tace "Ina yini?" Ya dago kai shi ma yana kallonta
yace "Lafiya lau" daga haka ta sunkuyar da kai, El-ameen yace "Baby dawo ki xauna
nan ki gaya min abubuwan da Farida ta koya maki yau" mikewa tayi ta dawo kusa da
shi ta xauna kasa, Junaid ya kalli agogon wrist dinsa sannan ya ci gaba da danna
wayarsa, El-ameen yace "Gaya min mana" dago kai tayi ta kallesa cikin sanyayyan
muryarta tace "tace min girki ne abinda muka yi" dariya yayi yace "Da gaske, to me
ku ka girka?" Ta kalli farida tace "Ya ma?" Dariya farida tayi tace "A'a tuna dai"
shiru tayi kamar me naxarin sunan girkin, da sauri farida tace "Ohkk okk fried rice
ne da coconut drink muka yi baby" tayi hakan ne don yanxun nan sai ta iya rike kai
ta fara ihu hakan kuma zai ja Dr Sumayya ta bata mata rai, shi kansa El-ameen ya
san in dai tayi stressing brain dinta wajen son tuno abu nan da nan kan xai fara
mata ciwo, kuma yana daukan lokaci bai daina ba. Jasmine ta kallesa tace "Fried
rice and coconut drink Mumy tace mu yi" yayi murmushi yace "Good kuma kin iya
yanxu?" Girgixa masa kai tayi alamar A'a, zai yi magana junaid ya mike yace "Toh ni
xan koma" El-ameen yace "ohK bani makullin motata" hade rai yayi yace "Xan yi
amfani da shi ne" El-ameen ya mike ya warce makullin ya koma ya xauna, juyawa
junaid yayi ya fice daga parlon. Da daddare yana kallon wani program khadija ta
shigo parlon da sallama ta ajiye masa mug din hannunta, yana kallonta yace "Meye
wannan?" Tace "Lipton mana" yace "Wa yace ki kawo min?" Tace "Ance kace wai in
maka" yace "Ohk tnx" mikewa tayi ta fita, ya girgixa kai ya ci gaba da kallonsa,
bayan kusan minti talatin yaji kamar motsi a balcony, mikewa yayi ya kashe wutan
parlon ya rage na tv kadai ya dawo
ya xauna, a hankali aka murda kofar parlon, ya jinginar da kansa jikin kujera
idonsa na kan tv, Suhaima ce ta shigo parlon da hijab dinta har kasa, ta tsaya daga
bakin kofar tana lekosa, shi dai bai juyo ba har lokacin, cikin sassarfa ta karaso
cikin parlon ta na kallonsa tace "Ya Ahmad?" Bai tanka ta ba hakan yasa ta d'an yi
murmushi ta xauna kusa da shi tace "Amm dama...." Mikewa yayi yana kallonta fuskar
nan nasa kamar bai taba dariya ba yace "me ya shigo da ke nan?" Gabanta yayi mugun
faduwa ta mike tace "Oh dama..." Juyawa tayi da sauri zata bar wajen ya fixgota, ya
sauke mata wani mari me lafiya cikin tsawa yace "Nace me ya kawo ki nan" jikinta ya
dau rawa tace "Wayyo kudi xa ka ban" wani marin da ya gigitata ya kuma kai mata, ya
ja ta ya nufi daki da ita, kuka ta dinga yi a tsorace tana cewa "Kudi wllh na xo
karba" belt ya dauka ta fasa ihu a rikice tana kiran Hajiyarsu, ya ja ta suka fito
parlor ya xabga mata a jiki, wanda hakan sai da ya kusa sa ta sakin fitsari,
dukanta yake kamar an aikosa, ta dinga ihu iya karfinta tana kiran Hajiya da Umma,
Dama suna labe balcony, Hajiya ta saki murmushi haka ma Umma a tare suka ce
"Alhmdllh" duk suka sauko compound din, sosai suke jin ihun Suhaima, Hajiya ta saki
salati da karfi tana kwala ma suhaimar kira tana cewa "ina kike, me ya same ki"
Umma ma ta dinga kwalo mata kira duk suka cika tsakar gidan da hayani, su khadija
ne suka fara fiffitowa sannan fatima, Hajiya tuni ta nufi part din junaid har
lokacin tana kwalo ma Suhaima kira, Abba ne ya fito shi ma jin hayaniya, Ya kalli
Umma yace "Meye haka?" Umma tace "Yo ina muka sani Alhaji, ihunta kawai muke ta ji
mun rasa inda take" Fitowa Mumy ma tayi jin abinda Umma tace, Tuni Hajiya ta isa
kofar junaid ta shiga bubbuga kofar tana kiran Suhaima, bude kofar junaid yayi
bayan ya lallasata iya son ransa da belt ya cillota waje ya kulle kofarsa, birgima
ta dinga yi tana cewa "Wayyo Hajiyarmu bai sha ba" Hajiya da idanuwanta suka
firfito ta dagota da sauri ta toshe bakinta a jikinta tace "Ba kya ji Suhaima kin
tsokanesa kenan koh?" Abba ne ya karaso yana kallonsu yace "Meke faruwa ne wai?" Da
sauri Hajiya tace "A'a ita ce bata ji Alhaji fitsara tayi masa daxu, mu je kawai
maganinta kenan" Abba ya kwalo ma junaid kira Hajiya da zuciyarta ya kusa shigewa
cikinta tace "oh Alhaji don ya hukuntata shine wani abu, bata dawowa da wuri ne
daga makaranta yayi mata magana tayi masa fitsara shine ya xaneta, ai ni ya min dai
dai, mu je kawai Alhaji" Mumy ce ta karaso wajen Hajiya tace "Ohh Amina ku rabu da
yaron nan, don ya doketa ya hukuntata shine me... Yanxu da fatima ce ai baxa ki ce
komai ba" juyawa kawai Mumy tayi ta bar wajen, Abba ya girgixa kai shima ya koma
part dinsa, Sumsum Hajiya ta ja Suhaima da ke kuka tana soshe soshen suka bar
wajen, Umma ta hadiye yawu da kyar ita ma tayi part dinta. Wasa wasa har biki ya
rage kwana biyu, banda shirye shirye babu abinda ake a gidan kamar irin shi ya zabi
matar din nan, tuni 'yan uwa da abokan arxiki aka fara xuwa daga garurruwa daban
daban, sai a lokacin Junaid abun ya fara damunsa on like before da lamarin ke basa
dariya, babban damuwar tasa rashin sanin wacece iyayen sa suka xaba masa, babu
yanda bai yi da Mumy ta gaya masa ba ita ma tace bata sani ba, Tashin hankali gun
Umma da Hajiya baya faduwa don sun rasa abun yi, komai suka yi ba nasara ciki gashi
basu san wacece shegiyar da xa a aura masa ba don basu ga alamar daya daga 'ya
yansu bane, da yammacin ranan Hajja ta diro gidan, magiya junaid ya dinga mata kan
ta gaya masa wacece matar tasa tace ubansa yayi kadan balle shi, sosai hankalinsa
ya tashi, bayan magrib Abba yasa a kira sa, yana shiga parlon ya xauna Abba yace
"Babu wani shirin da za kuyi ku, ko walima ne?" Ya gigixa kai yace "A'a Abba,
walimar da xa ayi a nan gida ya isa" Abba yace "Toh shkkn, hakan it's Ohk" ranan
kasa bacci junaid yayi har kusan karfe dayan dare, wayarsa ya jawo daga karshe ya
shiga neman number Humainah don yasan baxa ta rasa sanin matar ba, har ya gama
ringing bata daga ba ya sake kiranta sai gashi ta dauka, cikin sanyin murya yace
"Kina ji na Humainah" "Um" kawai tace masa kamar anyi forcing dinta, ya lumshe ido
ya bude yace "Plss nasan baxa ki rasa sanin warce xa a aura min ba, ki gaya min
wacece plss" taki cewa komai na kusan second talatin har sai da yace "Hello" sannan
tace "Ban sani ba nima" yace "Plss" kamar xata yi kuka tace "Ban sani ba," tsaki
yayi ya katse wayar ya jefar. Washegari alhamis da asuba yayi shirin fita aiki ya
fice ya bar masu gidan, haka ya wuni bai da sukuni ranar, yana barin gun aiki
Clinic ya tafi gun El-ameen, da damuwa yace "Frnd har yanxu fa ban san wacece matar
nn ba" El-ameen yayi murmushi yace "gobe idan mun kai ka xaka ganta, sbda son da
Abba yake maka shi yasa yake son surprising naka" Junaid yace "Plss ka daina bata
min rai more, what sort of surprise is this, and what if fitinanniya ce taki yarda
da xaman yarinyar a gidan?" El-ameen ya hade rai yace "Sai ka korata nasu gidan don
bata xo maka da gida ba, and tana tarewa gobe ita kuma xata tare ran lahadi don
ranan Dr Sumayya xa su yi tafiya, tsaf ita ma kuma xa a gyara mata nata dakin"
Junaid ya dafe kai yace "Ba haka ba frnd, kasan tana iya xuwa tayi reporting ma su
Abba fa" El-ameen yace "Shit, gashi har xa a maka aure gobe baka xama mature person
ba, ka ki girma har yanxu junaid, look yanxu you are going to leave a free.... When
I say free I mean a free life, no more Mumy Mumy Mumy, you are going to head a
family of ur own don haka ko wani decision kayi a gidan ka is right ba sai wanda
parent dinka suka maka ba, from tomorrow you will be on ur own" junaid yace "Uhum?"
Tsaki El-ameen yayi, can yayi kwafa yace "da rabon matar nan ta rainaka idan ta
lura you don't have a say of ur own!" Mikewa Junaid yayi yace "Baka san ni ba
kenan" daga haka ya fice daga office din.


*Haske writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

43.....

Washegari da ya kasance Friday tun sassafe El-ameen ya xo da leda me dauke da sabon


dinkin dakakkiyar farar shadda me tsada sosai, dinkin yar ciki da babban riga, sai
hula da takalma duk sabbi, tsokanarsa kawai yake yana dariya, shi dai Junaid
wayarsa kawae yake dannawa daga kwancen da yake fuskar nan tasa babu yabo bbu
fallasa, gefensa El-ameen ya zauna yace "Ko fa d'an gyaran fuska da gashi baka yi
ba captain, haka xa mu kai ka?" Mikewa Junaid yayi xaune a fusace yace "look ka
daina bata min rai Ahmad, bana son haka, it's not funny" El-ameen ya hade rai yace
"Ka hayyako min kamar ni xan aurar da kai? Toh ni dai ban da ni a kai ka in har
baxa ka tashi muje saloon ba" tashi daga xaunen junaid yayi fuskar nan tasa daure
ya shige daki, El-ameen ya fashe da dariya yace "Oho dai, ana saukowa juma'a xa a
daura..." Karfe tara fatima ta kawo breakfast parlon, El-ameen yace "Ina kawar ki
Humainah?" Fatima ta ajiye abun hannunta ta gaishesa sannan tace "Tace anjima xa su
taho da mamarta da na kirata" El-ameen yace "Toh idan kin koma ki ce ma Mumy Junaid
na can yana ta kuka nayi lallashin duniyar nan yaki saurarata" fatima ta xaro ido
lokaci daya ta fashe da dariya tace "Kai yaya" ya hade rai yace "Ba aiken ki nayi
ba" juyawa tayi ta fita tana dariya. Karfe sha biyu da wani abu junaid ya shiga
wanka, kan ya fito El-ameen har ya fito masa da sabbin kayan ya feshe su da uban
turare, kallo daya junaid ya ma kayan ya nufi closet dinsa ya bude ya fito da wani
blue shaddarsa, El-ameen yace "Ya haka ango ga sabon dinki nayi maka?" Ko kallonsa
junaid bai yi ba ya ajiye kayan kan gadon ya xauna yana goge gashin kansa, tsaki
El-ameen yayi ya mike ya dauke kayan ya mayar closet din ya sa key ya jefa makullin
aljihunsa, kallonsa kawai junaid ke yi, can yace "You are provoking me El-ameen"
El-ameen yayi dariya yace "oho dai tunda ba iya dukana xa ka yi ba, in baxa ka sa
sabon dinkin ba ka tafi da singlet da short nicker gun daurin auren ma" yana
murmushi ya fice masa daga dakin, Junaid ya fuxar da iska ya dafe kansa xuciyarsa
na tafarfasa, ya kusa minti ashirin xaune sanin lokaci na wucewa ya mike yana
kallon kayan da El-ameen ya ajiye masa, wani takaici ya rufesa, sai kace irin yana
son auren, tsaki yayi ya fixgo rigar yana kallo, ya kusa wani minti goman tsaye ya
sake jan tsaki ya xura rigar ya dau wandon ya sa, kayan suka haska sa sosai, da
ganinsa ka ga Ango, toilet ya koma ya dauro alwala ya fito ya tafi gun hulunarsa ya
dau daya ya gyara ya daura a kai ya dau takalminsa ma ya saka, ko agogo bae kalla
ba bare ya fesa turare ya fice daga dakin rike da wayoyinsa. Kallonsa El-ameen ke
yi daga sama xuwa kasa yace "Ina sabon takalmin da hular, kuma ina babban rigar?"
Wani uban harara Junaid ya xabga masa yace "Baxan sa ba" El-ameen ya fashe da
dariya yace "Oho dai bbu wanda zai ce wa ennan ma da ka sa ba sabo bane, nima bari
in je inyi wankan in shirya as babban abokin ango" daga haka ya shige dakin, junaid
ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujera ya lumshe ido, banda faduwa babu abinda
gabansa yake wai shi xa a daura ma aure yau. Daya saura El-ameen ya fito daga dakin
sanye da farar shaddar da ya dauka a closet din Junaid, shi ma yayi kyau har ya
gaji, kallo daya Junaid yayi masa ya dauke kai, El-ameen ya xauna gefensa yana
murmushi ya mika masa agogo yace "Here!" Dauke kai junaid yayi bai ce komai ba, El-
ameen yace "Dama ka saki ranka ga su faisal nan xuwa, if not you will be the topic
of discussion na cewa an maka auren dole, just pretend as if its nothing and you
are happy..." Ko rufe baki El-ameen bai yi ba sai ga faisal da kusan abokansu har
biyar, Junaid ya sauke ajiyar xuciya hade da sakar masu murmushi, tsokanansa suka
shiga yi kamar shi ya kawo su, shi dai baya cewa komai sai murmushin da bai kai
ciki ba, hotuna suka shiga yi gaba daya a parlon, daga bisanni suka fita don xuwa
masallaci, sosai gidan ke cike da jama'a, Junaid yaji dama kawai ya gansa a waje ba
sai ya bi ta compound ba, kallo aka bi sa da shi barin su Umma da bakin ciki ya
cika su kamar su yi yaya, ko kayan arxiki basu saka ba ana xaune bakin murhu, El-
ameen yace "Ya kamata ka je Mumy ta sa maka albarka kafin ka fita, sai ka ga anyi a
sa'a" part din Mumy Junaid ya nufa, bai bi ta kan mutanen parlon ba ya shiga
bedroom dinta ya sameta xaune tare da sisters dinta sai abokan arxiki, kallonsa
take har ya iso gabanta ya durkusa cikin sanyin murya yace "Xa mu tafi masallaci
Mumy" ta yi murmushi tace "Toh Allah ya tsare, yasa ayi a sa'a" ya sunkuyar da kai
yace "Ameen" sai a sannan ya kalli Mutan dakin ya gaishesu ya mike ya nufi kofa,
duk suka bi sa da kallon sha'awa ganin irin respect dinsa har ya fita, kanwarsa ce
Aysha ta bi bayansa murmushi dauke fuskarta tace "Ya Ahmad" yace "Ya kike" tace
"lafiya lau, tun jiya bamu hadu ba" yace "Eh ai kin san inda nake" daga haka ya ci
gaba da tafiyarsa. Ana saukowa daga juma'ah aka daura aurensa da warce bai ma
sha'awan sani yanxu kam a kan sadaki dubu dari biyu, bai wani tsaya gaishe gaishe
ba ya xame ya bar wajen ba tare da El-ameen ma ya sani ba ya koma gida. Bayan isha
junaid da El-ameen sai faisal na Parlor xaune Khadija ta shigo tace Abba na
kiransa, mikewa yayi ya fita xuwa part din Abbansa, shi da Abban Humainah ne xaune
parlon sai wani amininsa, Junaid ya samu waje ya xauna sannan ya gaishe su, nasiha
suka yi masa banda Abbansa dake ta kallonsa, shi dai kansa na kasa, har suka kare
cikin sanyin murya yayi masu godiya, Abbansa ya kara da cewa Allah yayi ma rayuwar
aurensa albarka, yace "Ameen" Abokin Dad dinsa Alhaji Umar ne yace Ya tashi ya tafi
don tuni aka kai masa matarsa, mikewa yayi bai ce komai ba ya fita daga parlon,
part din Mumy ya tafi a sanyaye ya sameta ita da Ummin El-ameen a dakin, ya isa
gabanta ya durkusa murya can kasa yace "Abba yace in tafi Mumy" Mumy tace "Toh
Allah ya albarkaci rayuwar auren ka Ahmad, Allah ya baka xuri'a ma su yi maka
biyayya kamar yanda kake min" kasa dago kansa yayi, lokaci daya idonsa ya kada, a
hankali ya daura kansa kan kafarta cikin sanyin murya yace "Mumy ban san matar ba
har yanxu" murmushi tayi ta dago kansa tana kallonsa sai dai bata ce komai ba, Ummi
tace "kasan mahaifinka baxai maka xabin da xai cuce ka ba Ahmad, Allah ya baku
xaman Lafiya, tashi ka je" mikewa yayi a hankali ya juya ya fita. Karfe tara saura
suka bar gidan shi da El-ameen da faisal, xuwa yanxu kam sun daina tsokanarsa ganin
yanayinsa, El-ameen ji yake kamar shi aka yi ma hakan yaji tausayinsa sosai, gun
masu gasassun kaji El-ameen yayi parking ya fita ba a dau lokaci ba ya dawo rike da
ledan kaji da drinks, tafiyar kusan minti talatin suka yi suka isa gidan Junaid,
El-ameen ya sauke ajiyar xuciya ya juya yana kallonsa bayan yayi parking a compound
din, gidane duplex mai kyau da girman gaske, compound din ya kawatu da kayan shuke
shuke iri iri ga haske ko ina kamar rana, faisal sai danne dariyarsa yake ganin
yanda Junaid ya hade rai yana kallon gidan, El-ameen yace "Toh ni dai a nan xan bar
ka, gobe da safe zan kawo maka motar ka" junaid ya kallesa yace "Haka koh?" El-
ameen yace "Allah baxan shiga ba sai dai ko faisal" faisal yace "No, sai dai mu
dawo ganin amarya gobe" El-ameen yace "Exactly" ficewa junaid yayi daga motar El-
ameen yace "Wait ga kajin amarya baka dauka ba" ko saurarensa junaid bai yi ba ya
nufi cikin gidan, El-ameen ya dauki ledojin ya bude motar ya fito yana dariya ya bi
bayansa, tsaye ya gansa a parlor yana bin ko ina na parlon da kallo, kamshi me dadi
ne ke tashi ta ko wani angle, komai na parlon brown nd milk, El-ameen ya karaso
cikin parlon ya ajiye masa ledan a kasa yace "Sai da safe ango" junaid ya kallesa
yace "Yanxu da gaske ba xa ka raka ni ba" El-ameen yace "Kila yanda gabana ke
faduwa naka baya faduwa haka, I just can't, gobe dai xan dawo..." Daga haka ya fice
daga parlon, Junaid ya sauke ajiyar xuciya ya kalli hanyar stairs, a hankali ya
karasa ya haura sama, ya dde tsaye corridor din dakunan yana kallon kofar dakin da
ya san tana ciki, karasawa yayi bakin kofar ya murda a hankali lokaci daya ya tura
yana kallon cikin dakin, xaune ya ganta can karshen gado ta takure waje daya
fuskarta rufe da babban veil, ya kusa minti biyu yana kallonta sannan ya karaso
cikin dakin ya isa gabanta ya tsaya yana kare mata kallo yace "Ke kika ce ma
iyayena kina so na?" Shiru bata ce komai ba, yace "Magana nake maki" Mikewa tayi
xata bar wajen ya fixgota har sai da ta fado kansa fuskarsa daure yace "Ina maki
magana xaki wuce" turasa tayi tace "Ni ka kyaleni, ko kuma kai kace kana so na ba"
saketa yayi ya bude ido yana kallonta da mamaki, ta bude mayafin fuskarta ta
hararesa ta bar wajen, rungume hannayensa yayi ya bi ta da kallo har ta xaga daya
side din gadon ta xauna, murmushi kawai yayi ya fita daga dakin ya shiga nasa,
wayarsa ya dauka ya shiga neman layin El-ameen, yana dagawa yace "Guess wacece
amaryar" El-ameen yace "Uhun! Humainah!" Junaid yace "Ohh dama ka sani?" Dariya
yayi yace "No! I only guessed" tsaki junaid yayi yace "Very funny wai Humainah, all
the same xata yi girki dai ta gyara gida ta kula da jasmine, shikenan an wuce
wajen" El-ameen ya xaro ido yace "Wacece jasmine kuma?" Shiru junaid yayi can yace
"Sai da safe" daga haka ya ajiye wayar ya shiga cire kayan jikinsa, wanka yyi yayi
alwala ya fito ya canxa xuwa jallabiya snn yayi shafa'i da wutr ya jima xaune kan
darduma daga bisanni ya mike ya koma kan gado, har ya kwanta ya mike xaune,
murmushi yayi da ya tuna wai fa Humainah ce matar da aka aura masa, wai Humainah,
dariya ya fara yi, ita wannan har ta isa aure yarinyar da ko secondary bata kare
ba, though yaji dadin da ya kasance ita ce don baxa ta wani bada wani matsala gun
kawo jasmine gidan ba, tabe baki yayi ya mike ya fita ya koma dakinta, kwance ya
sameta ta takure waje daya tana bacci, tabe baki yayi ya kashe wutan dakin yayi
kwanciyarsa can nesa da ita, ya kusa awa daya kwance kafin bacci ya daukesa, can
cikin dare ya ji tana tashin sa, ya mike xaune ya kunna
bedside lamp yana kallonta da kumburarrun idonta alamar ba kuka kadan tayi ba,
yace "What?" Kamar xata yi kuka tace "Ni yunwa nake ji" ya kalli agogo ya ga sha
biyu har ya gota yace "Yunwa? Baki ci abinci daga gidanku bane" tace "Eh ni ban ci
ba" d'an tsaki ya ja yace "Toh ni yanxu ina xan samo maki abinci tsakar daren nan?"
Tace "Ni dai wllh yunwa nake ji" ledan da El-ameen ya ajiye parlor ya tuna yace
"Tafi parlor xa ki ga leda ki duba meye a ciki" ta xaro ido tace "Ni dai tsoro nake
ji" ya hade rai yace "Xan fa kwada maki mari idan kina damuna ina bacci" ta fashe
da kuka ta mike xaune, tsaki ya ja ya sauka daga kan gadon ita ma ta sauko ta bi
bayansa da sauri, a tare suka sauko parlon ya kunna wuta ya dau ledan ya bude ya
nufi kitchen ya dauki plate da wuka da fork sai cup ya fito, nan parlon ya dawo ya
xauna kan rug ya fiddo kaza daya ya Yanyanka a plate yana kallonta yace "Ga shi"
matsowa tayi a hankali ta dau daya ta fara ci, ya mike yace "Idan kin gama ki kashe
wutan parlon" da sauri ita ma ta mike tace "Don Allah ka jira ni ya A.jay wllh
tsoro nake ji" ya hade rai yace "Kina fa damuna" ta d'an marairaice ta koma ta
xauna ta ci gaba da cin kazar, xaunawa yayi shi ma yace "Idan sha biyu da rabi yayi
baki gama ba xan yi tafiyata" ta d'an hararesa bata ce komai ba, dauke kai yayi sai
dai lokaci lokaci ya kan saci kallonta, suna hada ido yyi saurin cewa "Haka aka
koya maki a gidan ku Idan xaki kwanta kar ki cire kayan da kika yini da?" Tace "Kai
ma ai gidanku ne" bai kuma ce mata komai ba har ta gama, ta mike ta dau plate din
tace "Raka ni kitchen" harararta yayi ta rama ta nufi kitchen, ya bi ta da kallo,
tana fitowa ya mike ya kashe wutan parlon yyi hanyar stairs ta bi bayansa da sauri
suka shiga dakin a tare, wutan dakin ta kunna yace "Meye haka?" Tace "Xan wanke
baki mana" gado ya nufa yayi kwanciyarsa ta shiga toilet, ba a dau lokaci ba ta
fito ta nufi closet ta bude ta fiddo doguwar riga da hijab ta koma bayin, tana
fitowa tayi kwanciyarta nesa da shi ta juya masa baya, yace "Ke wa kika bar ma wuta
a kunne?" Tace "Nafi son haka, ni bana son duhu" tsaki yayi ya mike ya tafi ya
kashe wutan kan ya dawo har ta mirgino ta dawo gefensa, yayi kwanciyarsa hade da
juya mata baya.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

44/45

Da asuba Junaid ya dade xaune gefen gado daga bisanni ya mike, kallo daya ya ma
Humaina dake bacci ya shiga toilet ya dauro alwala ya fito har xai fita xuwa
masallaci ya dawo ya isa kusa da gadon ya buga kafarta, bude ido tayi a hankali
tana kallonsa ya juya ya fita daga dakin, ko da ya dawo daga masallaci samun ta
yayi kwance tana bacci har lokacin, bayi ya shiga ya debo ruwa ya fito ya watsa
mata, ta mike xaune da sauri tana kallonsa, yace "Sllh!" Daga haka ya fita daga
dakin, tsaki tayi ta bi sa da harara ta sauka daga gadon ta shiga bayi. Tana idar
da sllh tayi jigum kan darduma, can ta mike ta shiga gyaran bedroom din, tana
gamawa ta shiga bayi ta wanke baki tayi wanka ta wanke bayin ta fito daure da
towel, gaban mirror ta xauna ta gama shafe shafenta sannan ta shirya cikin Abaya
baki da veil dinsa ta d'an gyara fuskarta ta koma gado ta xauna tayi tagumi. Bude
kofar dakin aka yi fatima da khadija suka shigo, Humainah ta mike da sauri lokaci
daya tayi murmushin jin dadin ganinsu, fatima tace "Uhum Amaryar yayarmu, Antynmu!"
Hade rai tayi can ta fashe da kuka tace "Ni ba amaryarsa bace, ai Hajja tace sbda a
raba sa da mahaukaciyar nan ne aka aura masa ni, amma da ya rabu da ita sai a sa ya
sakeni in ci gaba da karatuna" innocently tayi maganar tana kallonsu, Khadija da
fatima suka fashe da dariya barin khadija, juyawa Humainah tayi a sanyaye ta koma
gefen gado ta xauna, hade kanta tayi da gwiwa tana kuka, fatima ta karasa kusa da
ita da sauri tace "Toh ai ba mu ce ba haka bane ba fa Humainah" Humainah ta girgixa
kai tana kuka tace "Ba wani nan nasan wayo aka min baxa a ce ya sakeni ba, yar
yarinya da ni xan je ss3 za ayi ma aure bayan ku ba a maku ba....." Khadija ta
xauna gefenta tace "Ni dai ba dariya nake maki ba, ba ruwana, ga abinci Mumy tace a
kawo maki" Humainah ta dago kanta tana share hawayen idonta tace "Hajja fa?"
Khadija tace "Ta ce anjima xata xo" Junaid ne ya shigo dakin ya tsaya daga bakin
kofa yana kallonsu yace "A baki aka ce ku bata abincin?" Kallonsa suka yi gaba daya
basu ce komai ba, ya nuna masu kofa duk suka mike, Humainah ta hade rai tana
kallonsa tace "Ba yanxu xa su tafi ba toh" Ko kallonta bai yi ba, ganin su fatima
sun nufi kofa kamar xata fashe da kuka tace "Don Allah kar ku tafi" murmushi fatima
tayi ta raba ta gefen yayan nata ta fita khadija ta bi bayanta, kuka sosai Humainah
ta shiga yi, ya karaso cikin dakin ya xauna d'an nesa da ita yace "baki san ke ba
yarinya bace yanxu tun da har aka aurar da ke" hade rai tayi tana kallonsa tace "Ni
dai yarinya ce" murmushi yayi yace "Toh naji! tsoron xama ke kadai kike a dakin da
kike son su xauna da ke?" Ta kallesa hade da gyada masa kai, yace "Toh xan samo
maki warce xata dinga taya ki xama ai kina so?" Tana kallonsa tace "Amma babba ce?"
Ya girgixa mata kai yace "No yar yarinya ce kamar ki sai ta dinga taya ki xama kuna
kwana ma tare" sosai ta hade rai tace "A'a bna so, xan iya xama ni kadai" shiru
yayi yana kallonta, can yace "Saboda me?" Ta mike tace "Haka nan kawai, xan iya
xama ni kadai abuna" daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, lumshe
ido yayi ya bude yana naxarin abinda ta ce, Mikewa yayi shima ya fita daga dakin ya
koma nasa. Karfe sha biyu saura aka danna bell downstairs, Junaid dake bedroom
dinsa yana danne dannen waya ya mike ya fita, dai dai lokacin da Humainah ma ta
fito, kallo daya yayi mata ya sauka ya je ya bude kofar, Hajja ce tsaye bakin kofar
da Sadiya, ta washe hakora ganin Junaid tace "A'a ango, to gani na biyo ka don kayi
amarya sai ka mance da uwar gida?" Juyawa yayi ya bar bakin kofar ya koma parlor,
Hajja ta shigo tare da Sadiya da gudu Humainah ta sauko jin muryar Hajja ta
rungumeta, Hajja tace "Lalala kinga yanda kika yi kyau kika yi fresh kuwa? Lallai
Amadi ya iya kiwo daga jiya xuwa yau" hade rai Humainah tayi tace "Ni babu abinda
ya ban na ci har yanxu" Hajja tace "Ehh amma ai kin kwan masa a gida" turo baki
tayi ta tafi ta xauna, Hajja ta kalli Junaid tace "Banxa kai kuma ko ka kira ka
mana godiya ka ga xukekkiyar amarya ba mahaukaciya ba" Kallonta kawai yake can ya
tabe baki yace "Nii ban gode ba tun da ban ce ina so ba, kawai makala min aka yi"
Humainah ta fashe da kuka tace "Hajja kin dai ji ko, ni dai tare xa mu koma don ni
ma makala min aka yi ban ce ina so ba" Hajja ta hade rai tace "Kai kaga irin hada
ta da Allah annabin da aka dinga yi don ta amince da gantalallen auren ka, banda
kaddara me xata yi da kai Ahmad, kai da cikakken saiti baka da, wllh wllh 'yar nan
tafi karfin ka, kawai ka kara gode ma Allah da ya sa aka baka ita" juyawa tayi tana
kallon Humainah tace "ke kuma kar ki kuskura ki bari ya kwana dakin ki tunda haka
yace, hanyar jirgi daban ta mota daban kin dai ji ni..." Humainah ta gyada mata kai
tana goge hawayen idonta, Hajja ta nemi kujera ta xauna tana cewa "Banda walakanci
an samu an lallaba yarinya da kyar ta amince ta rufa maka asiri ta aureka xaka
dinga gaya mana magana, ko fa kwandalar ka bbu a bikin nan don tsiya.... Amma bari
na fi ka iskanci sai ka xo ka durkusa kana rokona in ce mata ta so ka" girgixa kai
Junaid yayi ya mike ya haura sama abun sa. Har Karfe uku Hajja na gidan ita dai
Sadiya dama turo ta aka yi ta ga kwakwaf ta ga yanda gidan yake da abubuwan da aka
xuba, tana gama abinda ya kawota ta kara gaba ta bar Hajja. Har dai bayan la'asar
Hajja bata da niyar tafiya Junaid ya rasa me suke kullalawa a dakin gashi El-ameen
ya ki xuwa saboda Hajjan, mikewa yayi ganin har biyar ya gota ya shiga dakin, suna
ganinsa suka yi shiru, Hajja ta hade rai tace "To ya aka yi kuma?" Ya d'an shafa
kansa yace "Kawu Abubakar ne ya kira wai yana ta jiran ki xai koma" mikewa Hajja
tayi da sauri tana xuge yar purse dinta tace "Auu bawan Allah to bari in je"
Humainah ta marairaice kamar xata yi kuka tace "Yanxu tafiya xa kiyi ki bar ni
Hajja" Hajja ta hade rai ta kalli Junaid sai kuma ta duka kusa da ita murya can
kasa tace "Kin dai ji abubuwan da na gaya maki dai koh?" Humainah ta gyada mata
kai, Hajja ta mike tace "Ehh to ba dole in tafi ba Humainah, amma ina nan dawowa
kila ma da kayana xan taho tunda ai jikokina ne ko na xauna bbu komai" daga haka ta
nufi kofa tana cewa "Toh kai d'an ubanka xaka kai ni gidan ne ko in je in hau
machine tunda Sadiya sun koma da driver" ficewa junaid yayi daga dakin ita ma ta
fita tana cewa "Toh Humainah sai Allah ya sake dawo da ni" har gida Junaid ya ajiye
Hajja sannan ya kira El-ameen yace "Toh ta tafi, am waiting for you" daga haka ya
katse wayar ya kama hanyar gida. Kusan a tare suka iso gidan da El-ameen, El-ameen
yayi parking ya fito yana murmushi yace "Daga ina haka ango?" Junaid yace "Nayi
dropping dinta mana" bude motar El-ameen yayi ya shiga yana kallonsa yace "Tabdi
gaskiya Humainah ta karbe ka, ka ga yanda ka kara kyau yau kuwa" girgixa kai Junaid
yayi yace "Kaga ni mu yi maganar arxiki, kasan kuwa yarinyar nan tace ita bata son
a kawo mata kowa gida?" El-ameen ya hade girar sama da ta kasa yace "Kamar ya? Kaga
matsalar ka ko Ahmad, daga aure har yarinya xata fara raina ka tana fadin abinda xa
ayi a gidan da wanda baxa ayi ba, gidan ta ne da har xata gaya maka abinda xa ayi?
Kai wani irin Human being ne junaid" Shiru Junaid yayi yana kallonsa, can ya sauke
ajiyar xuciya yace "Am afraid kar ta ce xata gaya ma su Mumy ne shi yasa ban ce
komai ba" El-ameen yace "Tabdi! Yarinyar nan fa wllh sai kayi gaske da ita Idan ba
haka ba second Mumy dinka xata xama, naga alamar fitinanniya ce, shikenan kai kuma
ka xama abun tausayi baka da say a duniya sai na Mumy da wife, haba sai kace ba
captain ba kawai ka cika ma kanka girman kai da miskilanci maimakon being ur own
self, ita wannan har ta ma wuce ka bubbuge ta Idan tace xata kawo maka rainin
hankali" girgixa kai junaid yayi hade da yin murmushi yace "Uhum lallai" horn ya
danna aka bude gate ya shiga da motar yayi parking ya juya yana kallon El-ameen,
El-ameen yace "Toh gobe dai Dr Sumayya xata yi tafiya ban kuma san inda xan kai
patient dinka ba" junaid ya bude motar ya fita shima ya fito suka shiga cikin
gidan. Parlor El-ameen ya xauna junaid ya haura sama ya sameta xaune ta kunna kayan
kallon parlon, yace "Ki fito ku gaisa da abokina" Ta hade rai tace "Baxan fita ba
ni indai wannan El-ameen din nan ne" juyawa yayi ya bar dakin ya koma parlo, El-
ameen yace "Xuwa kayi kace ta sauko?" Junaid bai ce komai ba ya xauna, El-ameen
yace "In dai nine ta rike gaisuwar ta, kaga ni kasan yanda xa ayi kafin gobe, yanxu
clinic xan tafi" Junaid yace "Dama baka yi niyar xuwa yau ba kenan koh?" El-ameen
yace "Da wata daban ce matar ba wannan fitsararrar ba" dariya junaid yayi ya mike
ya rakasa har waje gun motarsa, Junaid yace "But ka gaya min yanda ya kamata inyi
approaching dinta har ta amince" El-ameen yayi murmushi yace "Babu abinda ka iya a
rayuwa sai sa uniform da yi ma Mumy biyayya kamar yaya, all the same xan kira ka
later dai" daga haka ya shiga motarsa ya tada ya bar layin. Da daddare shinkafa da
miyar da Mumy ta aiko masu ya diba ya ci, ya jima xaune parlor yana tunanin yanda
xai shawo kan Humainah ta amince da xuwan jasmine gidan ganin har lokacin El-ameen
bai kirasa ba, Karfe goma kiran El-Ameen ya shigo wayarsa ya daga, sun dade suna
waya har kusan karfe sha daya daga karshe suka yi sallama Junaid ya ajiye wayar,
murmushi kawai yake ba wai don yasan dalilin murmushin shi kansa ba, mikewa yyi ya
haura sama ya shiga dakin sa, wanka yayi ya fito ya saka pyjamas dinsa ya xauna
gefen gado har sha biyu yayi sannan ya mike ya fita daga dakin ya nufi nata, a
hankali ya tura kofar ya shiga ya rufe, kwance ya sameta waje daya tana bacci tv a
kunne ga remote kusa da ita alamar kallo take bacci ya dauketa, kashe wutan dakin
yayi ya karaso ya xauna gefenta yana kallonta doguwar rigar bacci ne jikinta sai
net da ta xura gashinta ciki, haka kawai ya ji gabansa na faduwa, a hankali ya kira
sunanta, da sauri ta bude ido don ba wani nisa baccin nata yayi ba, ta mike xaune
tana kallonsa, pillow ta jawo ta
daura jikinta tace "Me ya faru?" Ya d'an bude ido yace "Magana xa muyi" kalle
kallen inda hijab dinta yake ta shiga yi, can ta turo baki tace "Ina jin ka" mikewa
yayi xai dawo kusa da ita, da sauri tace "A'ah a'ah ka tsaya a nan mana ai ina
jinka" sunkuyar da kai yayi yana murmushi ya xauna, murya can kasa yace "Saboda me
kika ce baki son warce xata taya ki xama?" Hade rai tayi tace "haka nan" a hankali
yace "kinga Idan na fita aiki tun sassafe fa sai yamma nake dawowa, baxa ki iya
xama ke kadai a babban gidan nan ba sbda in some cases sai ki ga akwai aljanai a
babban gida haka" xaro ido tayi ta matso kusa da shi a hankali tace "Aljanai kuma
Ya A.jay?" Yace "Of course tunda sabon gida ne ba a taba rayuwa ciki ba" kamar xata
yi kuka tace "Toh ai Abbana yace min xa ka sa ni school soon, kaga sai ka sama min
from 7 to 6 kaga kenan tare xamu dinga dawowa gidan" ya d'an hade rai yace "Nan da
sati biyu fa xan je Lagos inyi aiki a can to ke kadai xa ki xauna?" Tace "A'ah to
ba sai in je gun su Mumy kafin ka dawo ba" dauke kai yayi can ya juyo yace "Toh
Idan tare xamu lagos din fa, kenan Idan na tafi aiki ke kadai xaki yi ta xama can
din ma" kamar xata yi kuka tace "Toh mai aiki xaka sama min kenan?" Ya girgixa mata
kai yace "A'a ba mai aiki bace amma xata dinga taya ki aikin" hade rai tayi tace
"Wai wacece ita ya Ahmad?" Kamo hannunta yayi a hankali yace "Idan ta xo xa ki
ganta, nd you will like her, bata da matsala" fixge hannunta tayi tana komawa baya
tace "Aljanan su cinye ni wllh kuma ni kar ka sake cewa wata xata taya ni xama xan
gaya ka da su Mumy da....." jawota yayi jikinsa ba shiri tayi tsit ta fara turasa
tace "Meye haka ya A.jay" a hankali ya daura bakinsa kan wuyarta, lokaci daya ranan
da ta gansa da Muhibba a daki ya fado mata, ta fasa ihu a tsorace tana kokarin
kwace kanta tace "Don Allah ya Ahmad ka yi hakuri ka kyaleni bana so" murya can
kasa yace "Meye ba kya so?" Da kyar muryarta na rawa tace "Toh to naji wacece xata
taya ni xaman?" Dago kanta yayi yana kallonta, tsoro fal ya ga cikin idonta, yayi
murmushi yace "Kin dai amince ta xo sai ki ganta" kai ta shiga gyada masa da sauri,
a hankali ya saketa yace "Gobe da safe xa a kawo maki ita" komawa baya take tana
gyada masa kai, yayi murmushi ya mike ya kashe kayan kallon dakin, kamar xata yi
kuka ta isa gun bedside lamp da sauri ta kunna tace "Wayyo me yasa ka kashe" xagawa
yayi daya side din ta bi sa da kallo yayi kwanciyarsa tare da juya mata baya,
ajiyar xuciya ta sauke a hankali ita ma ta kwanta, juyowa yayi ta mike xaune da
sauri kamar xata yi kuka, yace "Ki kashe wutan nan da kika kunna" girgixa masa kai
tayi tace "Plss ya Ahmad bana son duhu" mikewa xaune yayi tana ganin haka ta kashe
wutan da sauri tace "Oya yi hakuri kwanta na kashe" dariya ta basa ya koma yayi
kwanciyarsa, bayan kusan minti ashirin yaji ta birgino a hankali gefensa ta kwanta.
Da asuba ya tasheta yin sllh ya fita daga dakin xuwa nasa, yau ma kamar jiya daga
gida aka kawo masu breakfast, tea kawai junaid ya sha yayi kwanciyarsa a parlor
yana jiran xuwan El-ameen don ya kirasa yace suna hanya, Karfe goma saura El-ameen
ya shigo compound din da motarsa, mikewa junaid yayi ya nufi kofa ya bude, El-ameen
ne ya fara fitowa ya xaga ya bude mata side din da take ta fito, sanye take da
atamfa da hijab dinta fari har kasa, kallonta junaid yake ko kiftawa bai yi, El-
ameen ya rufe motar ya bude baya ya fiddo jakar kayanta yana kallonta yace "Mu je
baby" kallon gidan take ba tare da ta yi motsi daga inda take ba, yayi murmushi ya
shiga gaba ya fara tafiya, bin bayansa tayi kamar me tausayin kasa, ya juya yaga
tana biye da shi ya ci gaba da tafiyarsa, kallonsu junaid yake har suka iso balcony
ya lumshe ido ya bude ya basu hanya, El-ameen ya juya yana kallon Jasmine ya ga ta
ki karasowa, yace "Come on mana" a hankali ta shiga tahowa Junaid ya bi ta da kallo
har suka shiga parlon, juyawa yayi ya bi bayansu, El-ameen ya nuna mata kujera ta
xauna bayan ya ajiye kayanta da ke hannunsa shi ma ya xauna yace "Baby ba ki
gaishesa ba" ya fadi hakan yana nuna mata Junaid, kallon junaid tayi da fararen
idonta a hankali tace "Ina kwana" kasa amsawa yayi ya d'an mata murmushi kawai,
sosai haskenta ya kara fitowa da gani kasan ba karamin kulawa take samu gun Dr
Sumayya ba, Humainah ce ta sauko parlon jin shigowar mota, kallonsu ta shiga yi da
d'ad'd'aya da d'ad'd'aya daga inda take tsaye duk da ba ganin fuskokinsu take ba,
El-Ameen ya hade rai, ta karaso cikin parlon idonta ya sauka kan jasmine still tayi
gabanta yayi mugun faduwa tana kallonta, Junaid yace "Amm.... Kin ganta she will
keep you accompany ana kiranta da Baby...." Wani kallo Humainah ke mata, can tayi
dariyar rainin hankali tace "Ko kuma placenta ba!" Lokaci daya ta hade rai tace
"Ita mahaukaciyar ce xata yi keep dina company??" Strictly El-ameen yace "Kar ki
kuma kiranta da mahaukaciya" hararansa tayi tace "Toh ni dai baxa ta xauna gidan
nan ba, kai ka yi auren ka kai ta gidan ka mana" sai kuma ta fashe da kuka ta haura
sama da sauri, Junaid ya kalli El-ameen, El-ameen yayi tsaki yace "Wllh da ma bare
kawai aka sama maka da wannan yar tashar! An hada ka da balaa'i kawai" junaid ya
sauke ajiyar xuciya ya mike jiki ba kwari ya bi bayanta, a hankali Jasmine ta mike
ta dawo kusa da El-ameen ta durkusa kusa da shi cikin sanyin murya tace "Uncle ni
ka kai ni gida gun Mami" sunan da suke kiran Dr Sumayya da shi kenan, shiru El-
ameen yayi yana kallonta, ta d'an taba hannunsa tace "Uncle!" Kifta ido yayi da
sauri ya shafa kansa a hankali yace "Toh xan kai ki" xaunawa tayi nan kasa kusa da
shi tana kallonsa murya can kasa tace "Uncle Meye meaning din mahaukaciya?" Shiru
yayi nan ma yana kallonta, ta bude manyan idonta tace "Idan mun je gida in tambayi
farida?" Murmushi ya mata hade da gyada mata kai.


*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

46.....

Kwance junaid ya sameta tana kuka a dakin, ya karasa ya xauna kusa da ita ya dago
ta, turasa ta shiga yi cikin kuka take cewa "Ni ka kyaleni, ka kyaleni" a hankali
yace "Listen to me plss Humainah, ba fa mahaukaciya bace" ta fashe da matsanancin
kuka tace "Nace ka kyaleni ni dai" saketa yayi yana kallonta, ta koma ta kwanta
tana ci gaba da kukanta, mikewa yayi ya fita daga dakin ya koma parlor, El-ameen
dai kallonsa kawai yake bai ce komai ba, Junaid ya xauna ya shafa kansa yace "Shknn
you can go Idan tafiya xaka yi" El-ameen yace "Toh gimbiyar taka ta yarda kar in
tafi in bar yar mutane ta kasheta kana kallo" Junaid yace "In xaka tafi kayi
tafiyar ka kawai" mikewa El-ameen yayi yana kallon Jasmine yace "Baby xaki tsaya
nan har in dawo kin ji" kallonsa kawai take, ya durkusa kusa da ita yace "Kin ji?"
Idonta ne ya cika da hawaye, a hankali El-ameen yace "Kuka kuma baby" shi dai
junaid kallonsu kawai yake, El-ameen ya ciro handki ya mika mata yace "baxan dade
ba xan dawo kin ji" karba tayi ya mike ya kalli Junaid sannan ya fita daga parlon.
Kallonta kawai Junaid ke yi kanta a kasa tana fidgeting fingers dinta, can ya mike
ya kullo kofar sannan ya dawo ya dau jakar kayanta yace "Tashi mu je" mikewa tayi a
hankali tana kallonsa ya d'an mata murmushi yace "Follow me" daga haka ya nufi
stairs ta bi bayansa, dakin dake kusa da na Humainah ya bude ya shiga ta tsaya daga
bakin kofa tana kallon dakin, juyawa yayi yana kallonta yace "Shigo mana" a hankali
ta shiga dakin ya rufe kofar, kan gado ya ajiye jakarta ya bude closet yace "Ki
ajiye kayan ki duka a nan kin ji?" Sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, ya nuna
mata kofar bayi yace "ga toilet nan" kallon kofar tayi ta gyada masa kai, yace "Are
you hungry?" Girgixa masa kai tayi da ganinta kasan a tsorace take, yayi murmushi
ya kunna mata tvn dakin yace "Ki xauna kiyi kallon ki toh" ta gyada masa kai ya
juya ya fita daga dakin ya rufo mata kofar, da sauri ta mike ta nufi kofar ta bude,
yana tsaye bakin kofar Humainah ya juyo yana kallonta, dawowa yyi yace "Ya aka yi?"
Kamar xata yi kuka tace "ina jin tsoro" shiru yayi yana kallonta ta bude kofar
sosai ta koma ta xauna a dakin, Dakin Humainah ya karasa ya bude ya shiga ya sameta
har lokacin tana kuka ya rungume hannayensa yana kallonta, can ya karasa kusa da
gadon ya xauna yace "Ke yanxu baxa a iya cin arxiki gun ki ba, baxa ki yi taimako
ba, kwana biyu fa kawai xata yi ta bar gidan" ko kallonsa bata yi ba ya dagota ya
rungumeta yace "plss mana, wllh xata bar maki gidan soon, she's not staying long"
turasa tayi tace "Bana so, kuma ni ka rabu da ni" hade rai yayi ya saketa ya mike
yace "Toh wai gidan ki ne nan din? Ko a kanki take xaune" dago kai tayi tana
kallonsa, ya watsa mata wani kallo ya juya ya fice daga dakin, wani sabon kukan ta
fashe da har da shessheka. Dakin sa ya koma ya kwanta yana tunanin anya decision
din da yayi na kawo jasmine gidan yayi daidai kuwa, har aka kira Azahar yana
kwance, mikewa yayi daga karshe ya shiga bayi ya dauro alwala ya fito, nan dakin
yayi sllh yana xaune kan darduma bayan ya idar aka danna bell din gidan, mikewa
yayi ya fita har lokacin dakin da jasmine take a bude yake, parlor ya sauka ya
bude kofa, fatima da khadija ne bakin kofar rike da flask din abinci, gaishesa suka
yi ya karba yace "Mun gode, ku gaida mutan gidan," daga haka ya kulle kofar ya dawo
cikin parlor, plate ya dauko a kitchen ya dibi couscous din dake cikin flask din ya
bude na miya ya diba sannan ya rufe ya dau goran ruwa da cup da spoon ya haura
sama, dakin da jasmine ke ciki ya shiga, kwance ya ganta a kasa ta takure waje daya
tana bacci, ya shigo dakin ya ajiye abincin hannunsa yace "Jasmine" sau uku yana
kiranta ganin bata tashi ba ya durkusa gabanta ya d'an taba ta, bude ido tayi ta
mike xaune da sauri ganinsa, yayi mata murmushi ta sunkuyar da kai, yace "Me yasa
baki kwanta kan gadon ba" shiru tayi bata ce komai ba, ya dauko darduma ya shimfida
a kasa yace "Dawo nan" mikewa tayi ta xauna kan darduman ya ajiye mata abincin da
ruwa a kai yace "ga abinci ki ci" kai ta gyada masa, yace "Toh ci mana" a hankali
ta dau spoon din da dibi abincin ta kai baki tana kallonsa, murmushi ya mata yana
kallon yanda take tauna abincin, yace "You like it?" Kai ta gyada masa, ya mike
yace "Toh maxa ki cinye kafin in dawo" daga haka ya fita daga dakin ta bi sa da
kallo. Ko da ya dawo xaune ya sameta ta tura abincin gabanta tayi jigum, ya karaso
ya durkusa gabanta yace "Baki ci ba kuma" ta girgixa masa kai a hankali tace "Na
ci" yace "No! kadan kika ci" spoon din ya dauka ya dibi abincin ya kai mata baki, a
hankali ta bude bakin ya xuba mata, haka ya dinga bata har abincin yayi rabi ta
kauda kai tace "Na koshi" ajiye spoon din yayi yana kallonta yace "Toh tashi ki je
kiyi alwala ki xo kiyi sllh" mikewa tayi ta nufi toilet yace "Baki cire hijab din
ki ba" dawowa tayi ta cire Hijab din ta ajiye, ya bi ta da kallo har ta shiga
toilet din sai dai bata rufe kofar ba, mikewa yyi ya fita ya koma dakin sa. Lokaci
lokaci ya kan lekota, tausayinta kawai yake ba kadan ba barin yanda ya lura duk a
tsorace take, ana kiran sllh magrib ya shigo dakin bai ganta ba, kiranta ya shiga
yi amma shiru ya juya ya fita ya sauko downstairs, kitchen ya sameta tana wanke
d'an plates din da aka bata, ya tsaya bakin kofa yana kallonta, da sauri ta juyo a
tsorace, wara ido yayi yace "Uhum!" A hankali tace "washing nake yi" murmushi yayi
mata yana gyada mata kai, ta juya ta ci gaba da wanke plates din, yace "Me xa ki ci
for Supper?" Ta juyo tace "Supper?" Ya gyada mata kai yace "Yea dinner" ta d'an
langwabar da kai a hankali tace "na koshi" wara ido yayi yace "me kika ci?" juyawa
tayi ta ci gaba da wanke wankenta. Har ta gama yana tsaye bakin kofar, ta juyo tana
kallonsa, murmushi yayi mata ya fita daga kitchen din ta bi bayansa suka haura
sama, yace "Tafi kiyi sllh" kai ta gyada masa ta shiga dakin da take, shi ma ya
shiga nasa. Ana idar da sllh ya tafi siyo masu abinci, ajiye abincin yayi a parlor
bayan ya dawo ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujera, can ya mike ya shiga
kitchen ya dauko plate ya dau take away daya ya juye ya sa spoon ya dau ruwa ya
tafi sama, xaune ya sameta bakin kofar dakin tana ganinsa ta mike tsaye, yace
"uhum!" a hankali tace "Tsoro nake ji" kallonta ya tsaya yi kafin ya shigo dakin ya
ajiye mata abincin hannunsa yace "Toh xo ki ci abinci" ta karaso ta xauna inda ya
ajiye mata abincin, bin sa da kallo tayi har ya fita sai dai bai rufe mata kofar
ba. Har xai shiga dakinsa ya tsaya ya kalli dakin Humainah, karasawa yayi ya bude
kofar, xaune ya ganta can karshen gado kanta hade da gwiwa, a hankali ya karasa
kusa da ita ya xauna yace "Still crying?" Mikewa tayi xata bar wajen ya fixgota ya
ce "Ina xa ki?" Ta fashe da kuka sosai, rungumeta yayi a hankali yace "Alryt am
sorry, kiyi hakuri... She's going tomorrow tun da baki so" boye fuskarta tayi
jikinsa tana kuka a hankali, yace "Toh ba nace kiyi hakuri gobe xata tafi ba"
muryarta na rawa tace "Toh wacece ita" dago kanta yayi yana kallonta, can yace "Ohk
I will tell who she is" janyeta yayi a jikinsa ya koma baya yana kallonta yace
"Amma fa it's a long story" sunkuyar da kanta tayi, nan ya fara bata labarin ynda
ya hadu da jasmine har xuwa wannan lokacin, kallonsa kawai take ko kiftawa bbu bata
kuma ce komai ba, ya lumshe ido ya bude yace "Tana regaining memorynta Idan Allah
ya yarda xa ta koma gun iyayenta, ita din abun tausayi ce, a yanxu bata da kowa sai
mu da muka taimaketa" dauke kai Humainah tayi, ya matso kusa da ita yace "Baki ce
komai ba" turo baki tayi tace "Toh ka kai ta gidansu El-ameen mana" murmushi yayi
yace "In tambaye ki" ta dago kai tana kallonsa, yace "wai kishi na kike Humainah?"
Hade rai tayi tace "Kamar ya? Sbda me xan yi kishin ka" yace "Toh me sa baki son ta
xauna nan?" Tabe baki tayi tace "Ta xauna mana ni ina ruwana, kawae abinda na sani
ka kai ni sch next week" murmushi yayi ya mike ya fita daga dakin, abinci ya dauko
mata ya ajiye dakin yace "Ga abinci!" Ko kallonsa bata yi ba ya fita daga dakin.
Karfe tara da wani abu ya mike daga kwancen da yake ya fita xuwa gun Jasmine, xaune
ya sameta bakin kofa tayi jigum, ya d'an bude ido yace "kina nan har yanxu" mikewa
tsaye tayi kamar xata yi kuka tace "Ni kadai xan yi bacci a nan?" Kallonta kawai
yake ya ga hawaye idonta, girgixa mata kai yayi yace "A'a ba ke kadai xaki kwana
ba, ina xuwa" daga haka ya fita ya shiga dakin Humainah, xaune ya sameta daure da
towel gaban madubi, hade rai tayi tace "Kaya xan sa" yace "Uhm did I hold you?"
Marairaice masa tayi tace "Ka fita plss" karasowa yayi kusa da ita ta mike da
sauri, ya d'an bude ido yace "what?" Kamar xata yi kuka tace "Ka fita plss" yace
"Alryt xan fita, amma abokiyar kwana xan kawo maki" kallonsa tayi da sauri tace
"Kamar ya?" Yace "ku kwana tare da yarinyar plss" da mamaki take kallonsa tace "Mu
kwana?" Matsowa yayi kusa da ita ta koma baya da sauri tace "Wayyo ya A jay ka fita
plss" ya langwabar da kai yace "Toh in kawo maki ita?" Gyada masa kai tayi da
sauri, yayi murmushi ya juya ya fita ta bi sa da kallo, tsaye ya samu Jasmine a
daki tana ganinsa ta nufesa da sauri ta juya masa baya tace "Cire min abun" kallon
Zip din kawai yake daga sama xuwa kasa na kusan minti daya, ta juyo a hankali tana
kallonsa, kifta ido yayi da sauri yace "Na'am" a hankali tace "Ban iya cirewa ba,
Mami da farida suke cire min" gyada mata kai ya shiga yi kamar kadangare, ta kuma
juya masa baya, yayi baya da sauri yace "Ohk Ohk mu je a cire maki nima ban iya ba"
daga haka ya nufi kofa ta bi bayansa, dakin Humainah ya shiga ita ma ta shiga,
kallonta kawai Humainah ke yi daga sama xuwa kasa gabanta na faduwa, karasawa
Jasmine tayi kusa da ita ta juya mata baya a hankali tace "ki cire mun abun" kallon
Junaid Humainah tayi, ya gyada mata kai yace "Help her wai bata iya ba" da kyar
Humainah ta daga hannu ta xuge mata Zip din, kokarin cire rigar ta shiga yi da
sauri Junaid ya juya har yana
buge kofa ya fita daga dakin, Jasmine ta kuma kallonta tace "Baki cire dayan ba"
Humainah ta balle mata bra din ta koma gaban madubi, bin ta da kallo Jasmine tayi
tace "Ina san inyi wanka" ko kallonta Humainah bata yi ba, Jasmine ta bi ta tace
"Xan yi wanka" ba tare da Humainah ta kalleta ba ta nuna mata kofar bathroom,
Jasmine ta nufi kofar ta bude ta shiga, a bude ta bar kofar, Humainah ta mike ta
koma gefen gado ta xauna xuciyarta na bugawa, har Jasmine ta fito daure da towel
dinta, ta gefen ido kawai Humainah ke kallonta, ta iso kusa da ita tace "cloth
dina" Humainah ta hade rai tace "ki saka wanda kika cire mana" "toh" kawai jasmine
tace ta tafi inda kayan da ta cire yake ta dauka ta sa ta kuma dawowa ta durkusa
kusa da ita tace "Sa min" xuge mata Zip din Humainah tayi ta kwanta abunta, jasmine
ta mike ganin ta kwanta ita ma ta kwanta nan kasa. Junaid na fitowa daga wanka ya
dau wayarsa dake ring ya ga El-ameen ne ke kiransa, dagawa yayi El-ameen yace
"Matar taka ta hakura dai koh?" Junaid yace "May be" El-ameen yace "Kasan me, bata
yarda fa ta kwana ita kadai ya xa ayi gashi amarci ku ke ci...." Junaid yace "Ko
kuma angwanci ba" El-ameen yace "Serious xata yi ta maku ihu ne cikin dare bata
yarda ta kwanta ita kadai" junaid yace "ta gaya min, tana dakin Humainah yanxu ma"
El-ameen yace "Ohk bata waya plss" Junaid yace "Kace mata me?" El-ameen yace "kai
dai ka bata" shiru junaid yayi can yace "Naji" katse wayar yayi hade da yin tsaki
ya saka jallabiyarsa ya fita daga dakin, da sallama ya tura kofar dakin Humainah ya
d'an bude ido ganin jasmine kwance a kasa ya karasa ya durkusa kusa da ita yace "Me
ya sa kika kwanta a nan" shiru tayi bata ce komai ba, ya kalli Humainah ya ga rufe
idonta ma tayi, jasmine ya kuma kallo yace "Tashi ki hau gado" mikewa tayi ya nuna
mata daya side din gadon ta xaga ta hau ta kwanta, a hankali ta matso kusa da
Humainah shi dai kallonta kawai yake, wayar hannunsa ne ya fara ring ya kalli
screen din, sai da ya kusa katsewa ya daga ya mika mata, karba tayi tana kallonsa
yace "Kiyi magana" wayar ta kai kunnenta tace "Na'am" El-ameen yace "Baki yi bacci
ba baby?" Ta kalli Junaid da ke kallonta ta sunkuyar da kai a hankali tace "Xan yi"
juyawa junaid yayi ya fice daga dakin, "Kin ci abinci kuwa" tambayar da El-ameen
yayi mata kenan ta gyada masa kai tace "Eh da afternoon ya bani wannan small rice
da miya, na ci kadan Saboda ba dadi sai ya xo ya bani a baki" shiru El-ameen yayi
bai ce komai ba, Humainah ta bude ido da sauri tana sauraren abinda take cewa
gabanta na faduwa, El-ameen ya sauke ajiyar xuciya yace "Da ya baki a bakin sai
kika ci?" Kai ta gyada masa tace "Eh da ya bani na ci, uncle he's kind, I like him
just like Abba" mijin Dr Sumayya kenan, katse wayar El-ameen yayi, Humainah ta
mike xaune xuciyarta na tafarfasa can ta mike ta fice daga dakin, da sauri Jasmine
ta mike ta bi bayanta ita ma, dakin Junaid Humainah ta shiga ta gansa tsaye yana
saka pyjamas dinsa, juyawa yayi yana kallonta ta xube wajen ta fashe da kuka sosai,
karasowa yayi kusa da ita ya durkusa gabanta da mamaki yace "Me ya faru?" Jasmine
ce ta shigo dakin ta karasa kusa da su a hankali ta durkusa ita ma tana kallon
yanda Humainah ke kuka.


*Haske Writers association*馃挕

Kar ku watsa min sand a ido my group members, ku kadai nake ma post da hannuna don
soyayya.

[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

40/41

Mikewa Junaid yayi yace "I will think about that!" Daga haka ya nufi kofa El-ameen
ya bi sa da kallo har ya fita. A haraban hospital din suka hadu da faisal, faisal
yace "Ohh my God, ashe abinda ya faru kenan captain shine ko ku sanar da ni kai da
El-ameen? da Childishness din ku ne ya tashi da har gida xa ku xo ku sameni" junaid
yayi murmushi yace "I thought ka sani ne ai," faisal yayi tsaki yace "Ta ina xan
sani?" Daga haka ya bar sa nan tsaye ya shiga asibitin, murmushi junaid ya kuma yi
ya shiga mota ya bar asibitin. Yana isa gida part dinsa ya tafi yayi alwala yayi
sllhn asr sannan ya kwanta parlor, har ya fara bacci yaji an bude kofar parlon,
bude ido yayi ya mike xaune da sauri, Humainah ce ta shigo parlon ta tsaya daga
bakin kofa ta d'an hade rai tace "Xamu tafi tare da Hajja!" Yana kallonta yace "Ina
xa ku" tace "Gidanmu!" Shiru yayi kafin yace "Ohk, yaushe xa ki dawo?" Ta tabe baki
tace "Baxan sake dawowa ba, da kayana duka xan tafi ma" murmushi Junaid yayi yace
"Ohk Allah raka taki gona" tace "Ameen" daga haka ta juya ta fice daga parlon, ya
koma ya kwanta. Tana fita hajja ta shigo sabe da gyalenta da 'yar jakar da ta taho
da shi, tace "Toh Amadi ni dai xan tafi sai kuma na dawo kai maka amarya ko kaki ko
ka so sai in ga ta tsiya, idan har ynxu ra'ayin rayuwa da mahaukaciya kake to sai
ka haukatar da warce za a kai maka hakan xai fi maka rufin asiri" daga haka ta juya
ta fita ya bi ta da kallo hade da tabe baki, ranan da daddare Ummin El-ameen ta xo
gidan, duk yanda ta so ya gaya mata ko El-ameen yasan komai kan xancen yarinya
mahaukaciya kin gaya mata yayi yace babu ruwan El-ameen, ba don ta yarda ba ta
kyalesa don tasan bakinsu daya, can tace "Na ji labarin aure xa ayi maka, saura
abokin ka, shi wannan kauye ma xanje dauko masa mata wallahi xan basa mamaki,"
Dariya Junaid yayi yace "Kai Ummi, kauye kuma" bata tanka sa ba ta mike ta fice
daga parlon. Shirye shiryen biki aka dinga yi gidansu Ahmad Junaid babu kama kafar
yaro, cikin kankanin lokaci aka hada lefe akwati shidda, shi dai Junaid kallon ikon
Allah kawai yake wai shi xa ayi ma aure, auren ma na dole kamar wani mace kuma har
lokacin bai san matar ba dariya ma kawai abun ke basa, ana saura sati bikin ya dawo
aiki da yamma yana kwance sai dai gaba daya tunaninsa na gun Jasmine yana son sanin
halin da take ciki yana kuma son ganinta, kiran El-ameen ne ya shigo wayarsa ya
daga, daga daya bangaren El-ameen yace "Uhm duk xumudin xama angon ne yasa ka mance
da patient dinka captain?" Junaid yace "If that's what you are thinking...." El-
ameen yace "Toh yayi kyau, amma idan baka manta the very first day da ka fara xuwa
min da batun ta sai da na baka shawarar ka raba kanka ka ki, yanxu ka xo kayi
abinda ya dame ka, ka bar ni da 'yar mutane, ko irin ka dinga kira ka tambayi
lafiyarta babu, to Dr sumayya dai ina a week time xa su yi tafiya da mai gidanta
wai..." Junaid yace "Yea! Then an min auren sai ta dawo gidana kamar yanda ka ce"
El-ameen ya tabe baki ya katse wayar. Karfe biyar da wani abu Junaid ya shirya ya
tafi part din Mumy yace mata xai dan fita, sabuwar motar da Abba ya basa ya dauka
ya fita daga gidan, a hanya ya kira El-ameen, yana dagawa yace "Kana ina?" El-ameen
yace "Me xan maka?" Tsaki Junaid yayi yace "Dalla ni ka gaya min" katse wayar El-
ameen yayi, junaid yayi parking ya ji kamar ya juya, sai dai baxai iya ba sbda son
ganin jasmine da yake, sake kiransa yayi yana dagawa yace "How dare you xaka katse
min waya daga tambaya" El-ameen yace "Ashe ba dadi kai kake ma mutane, ni da ma kai
ka haukacen wllh kayi loosing memory ko xaka rabu da wnn worst attitude din naka,
gashi it's getting worst nowadayz, ni ina gida anything?" Katse wayar junaid yayi
hade da yin kwafa, ya kusa minti goma xaune motar ya kuma yin wani kwafan ya ja
motar ya nufi gidan nasu, Ummi dake parlor ya gaida tace "Ni ban ga kai da abokin
naka kuna shirin bikin nan ba Ahmad" junaid yayi yake yana shafa kai yace "Ae
abinda ya kawo ni kenan" Ummi tace "Toh yayi kyau, da an gama naka da sati biyu in
an huta xan kai nasa lefen kauye" Junaid ya fashe da dariya yace "Wllh xan maki
driving din" Ummi ta hade rai tace "Am serious, dan ma ka gaya masa nake gaya maka"
dakin El-ameen ya nufa yana dariya, El-ameen ya tura laptop din gabansa yace "What
is making him laugh" Junaid ya buda ido yace "Baka ji a bakin Captain ba, yanzu dai
tashi ka kai ni in duba yarinyar nan tunda gori ka min daxu" El-ameen yace "As you
can see am busy, sai dai in baka address" junaid yace "Ba fa dadewa xa mu yi ba"
"yess! ko minti daya xa muyi" cewar El-ameen yana kallonsa da kyau. Junaid ya kusa
minti goma tsaye yana kallonsa kafin ya juya ya fita daga dakin, El-ameen yace
"Byee!" Da daddare yana kwance bedroom Humainah ta fado masa, tabe baki yayi ya
dauki wayarsa ya shiga kiranta, sai da ya kusa katsewa ta daga yace "don ma kin
samu na kira ki" tace "I didn't beg for ur call" shiru yayi sannan yayi murmushi
yace "True! Yaushe xa ki dawo?" Tace "Ana saura kwana biyu bikin ka xamu dawo da
Hajja" yace "Bikinsu dai" daga haka ya katse wayar, Har ya ajiye wayar ya tuna
Hafsat, tun ranan da abun ya faru bata kira ba bai kirata ba, numberta ya duba ya
shiga kiranta bugu uku ta daga ya mata sallama ta amsa daga daya side din hade da
gaishesa, ya ce "Ya kike?" Tace "Qlau" rasa me xai sake ce mata yayi, can dai yace
"Am sorry for what happened Hafsat," tace "Ohh ba komai, ya wuce ai" yace "To
nagode" tace "welcome! But a ina ka san yarinyar?" D'an shiru yayi kafin yace "It's
a long story" tace "really?" Yace "Yeah!" Labarin yanda ya fara ganin jasmine tun
daga rana ta farko ya fara bata har xuwa ranan da ya kai ta gida gun parent dinsa
da abinda ya faru bayan barinsu gida, Hafsat da duk jikinta yayi sanyi tace "Yanxu
kana nufin ta dawo hankalinta?" Yace "Yea, amma tayi loosing memory" Cike da damuwa
Hafsat tace "Allah sarki, to yanxu tana ina?" Ya lumshe ido ya bude yace "Tana gun
frnd dina, buh am getting married in a week time sai ta dawo gidana har tayi
regaining memory, Hafsat tace "Dat's nyc Allah ya sanya alkhairi, ya bada xaman
lafiya," Yace "Ameen thank you" shiru tayi ya kalli agogo ya ga har sha daya ya
wuce, yace "Xa ki kwanta koh?" Tace "Yeah" yace "Ohk good nyt, tnx a lot ki gaida
mutan gida" tace "Ayt bye!" Daga haka ya katse wayar ya ajiye yayi addu'an
kwanciya. Washegari da yamma junaid na kwance bayan ya dawo daga aiki El-ameen ya
shigo parlon, kallo daya ya masa ya dauke kai, El-ameen na daga tsaye bakin kofa
yace "In ka shirya ka taso mu tafi" ko kallonsa junaid bai yi ba, El-ameen yace
"Ohk nayi tafiya ta" daga haka ya fice. Junaid ya mike ya shiga bedroom ya daura
shirt dinsa ya dau Atm ya fita, a part din Mumy ya tarda El-ameen, ya jira har ya
gama surutun sa snn yace "Mumy xa mu d'an fita yanxu mu dawo" Mumy tace "Toh Allah
ya tsare" ya juya ya fita. A mota yayi ta jiran El-ameen har sai da yaga dama ya
fito, El-ameen ya xaga daya side din ganin junaid a driver seat yana shiga junaid
ya tada motar suka bar layin, tun a hanya El-ameen ya kira Dr sumayya ya sanar da
ita xuwansu, a visitor parlor suka sauka dotan Dr Sumayya 'yar shekara sha uku ce
ta kawo masu ruwa da drink ta xauna kusa da El-ameen tana ta basa labari, junaid
dai makala earpiece yayi yana danna waya, bayan kusan minti biyar Dr Sumayya ta
shigo parlon suka gaisa da El-ameen, El-ameen ya fixge wayar sai a sannan ya dago
yana kallon Dr Sumayya yace "Ina yini!" Tace "Lafiya lau ya aiki," yace "Alhmdllh,"
mikewa tayi ta fita tana fita sistern ta warce xata yi mate din jasmine ta shigo
parlon tare da jasmine din, xama tayi kan kujera ta nuna ma Jasmine gefenta ta
xauna sannan ta gaida su El-ameen, ya amsa mata da murmushi yace "Ya sch?" Tace
"Alhmdllh" kallon jasmine tayi tace "Baby baki ce masu ina yini ba" sunan da Dr
Sumayya ke kiranta da shi kenan a sati daya da 'yan kwanakin da tayi a gidan, shine
duk yan gidan ke kiranta da haka, shima El-Ameen dake yawan xuwa gidan sai ya dinga
kiranta da haka, jasmine ta kalli farida sannan ta kalli El-ameen a hankali tace
"Ina yini?" Murmushi kawai yayi mata ta sunkuyar da kai, Junaid dai sai kallonta
yake ta gefen ido, El-ameen yace "Toh baki gaida wannan ba Baby" Ya fadi hakan yana
nuna mata Junaid, kallonsa tayi tace "Ina yini?" Ya dago kai shi ma yana kallonta
yace "Lafiya lau" daga haka ta sunkuyar da kai, El-ameen yace "Baby dawo ki xauna
nan ki gaya min abubuwan da Farida ta koya maki yau" mikewa tayi ta dawo kusa da
shi ta xauna kasa, Junaid ya kalli agogon wrist dinsa sannan ya ci gaba da danna
wayarsa, El-ameen yace "Gaya min mana" dago kai tayi ta kallesa cikin sanyayyan
muryarta tace "tace min girki ne abinda muka yi" dariya yayi yace "Da gaske, to me
ku ka girka?" Ta kalli farida tace "Ya ma?" Dariya farida tayi tace "A'a tuna dai"
shiru tayi kamar me naxarin sunan girkin, da sauri farida tace "Ohkk okk fried rice
ne da coconut drink muka yi baby" tayi hakan ne don yanxun nan sai ta iya rike kai
ta fara ihu hakan kuma zai ja Dr Sumayya ta bata mata rai, shi kansa El-ameen ya
san in dai tayi stressing brain dinta wajen son tuno abu nan da nan kan xai fara
mata ciwo, kuma yana daukan lokaci bai daina ba. Jasmine ta kallesa tace "Fried
rice and coconut drink Mumy tace mu yi" yayi murmushi yace "Good kuma kin iya
yanxu?" Girgixa masa kai tayi alamar A'a, zai yi magana junaid ya mike yace "Toh ni
xan koma" El-ameen yace "ohK bani makullin motata" hade rai yayi yace "Xan yi
amfani da shi ne" El-ameen ya mike ya warce makullin ya koma ya xauna, juyawa
junaid yayi ya fice daga parlon. Da daddare yana kallon wani program khadija ta
shigo parlon da sallama ta ajiye masa mug din hannunta, yana kallonta yace "Meye
wannan?" Tace "Lipton mana" yace "Wa yace ki kawo min?" Tace "Ance kace wai in
maka" yace "Ohk tnx" mikewa tayi ta fita, ya girgixa kai ya ci gaba da kallonsa,
bayan kusan minti talatin yaji kamar motsi a balcony, mikewa yayi ya kashe wutan
parlon ya rage na tv kadai ya dawo
ya xauna, a hankali aka murda kofar parlon, ya jinginar da kansa jikin kujera
idonsa na kan tv, Suhaima ce ta shigo parlon da hijab dinta har kasa, ta tsaya daga
bakin kofar tana lekosa, shi dai bai juyo ba har lokacin, cikin sassarfa ta karaso
cikin parlon ta na kallonsa tace "Ya Ahmad?" Bai tanka ta ba hakan yasa ta d'an yi
murmushi ta xauna kusa da shi tace "Amm dama...." Mikewa yayi yana kallonta fuskar
nan nasa kamar bai taba dariya ba yace "me ya shigo da ke nan?" Gabanta yayi mugun
faduwa ta mike tace "Oh dama..." Juyawa tayi da sauri zata bar wajen ya fixgota, ya
sauke mata wani mari me lafiya cikin tsawa yace "Nace me ya kawo ki nan" jikinta ya
dau rawa tace "Wayyo kudi xa ka ban" wani marin da ya gigitata ya kuma kai mata, ya
ja ta ya nufi daki da ita, kuka ta dinga yi a tsorace tana cewa "Kudi wllh na xo
karba" belt ya dauka ta fasa ihu a rikice tana kiran Hajiyarsu, ya ja ta suka fito
parlor ya xabga mata a jiki, wanda hakan sai da ya kusa sa ta sakin fitsari,
dukanta yake kamar an aikosa, ta dinga ihu iya karfinta tana kiran Hajiya da Umma,
Dama suna labe balcony, Hajiya ta saki murmushi haka ma Umma a tare suka ce
"Alhmdllh" duk suka sauko compound din, sosai suke jin ihun Suhaima, Hajiya ta saki
salati da karfi tana kwala ma suhaimar kira tana cewa "ina kike, me ya same ki"
Umma ma ta dinga kwalo mata kira duk suka cika tsakar gidan da hayani, su khadija
ne suka fara fiffitowa sannan fatima, Hajiya tuni ta nufi part din junaid har
lokacin tana kwalo ma Suhaima kira, Abba ne ya fito shi ma jin hayaniya, Ya kalli
Umma yace "Meye haka?" Umma tace "Yo ina muka sani Alhaji, ihunta kawai muke ta ji
mun rasa inda take" Fitowa Mumy ma tayi jin abinda Umma tace, Tuni Hajiya ta isa
kofar junaid ta shiga bubbuga kofar tana kiran Suhaima, bude kofar junaid yayi
bayan ya lallasata iya son ransa da belt ya cillota waje ya kulle kofarsa, birgima
ta dinga yi tana cewa "Wayyo Hajiyarmu bai sha ba" Hajiya da idanuwanta suka
firfito ta dagota da sauri ta toshe bakinta a jikinta tace "Ba kya ji Suhaima kin
tsokanesa kenan koh?" Abba ne ya karaso yana kallonsu yace "Meke faruwa ne wai?" Da
sauri Hajiya tace "A'a ita ce bata ji Alhaji fitsara tayi masa daxu, mu je kawai
maganinta kenan" Abba ya kwalo ma junaid kira Hajiya da zuciyarta ya kusa shigewa
cikinta tace "oh Alhaji don ya hukuntata shine wani abu, bata dawowa da wuri ne
daga makaranta yayi mata magana tayi masa fitsara shine ya xaneta, ai ni ya min dai
dai, mu je kawai Alhaji" Mumy ce ta karaso wajen Hajiya tace "Ohh Amina ku rabu da
yaron nan, don ya doketa ya hukuntata shine me... Yanxu da fatima ce ai baxa ki ce
komai ba" juyawa kawai Mumy tayi ta bar wajen, Abba ya girgixa kai shima ya koma
part dinsa, Sumsum Hajiya ta ja Suhaima da ke kuka tana soshe soshen suka bar
wajen, Umma ta hadiye yawu da kyar ita ma tayi part dinta. Wasa wasa har biki ya
rage kwana biyu, banda shirye shirye babu abinda ake a gidan kamar irin shi ya zabi
matar din nan, tuni 'yan uwa da abokan arxiki aka fara xuwa daga garurruwa daban
daban, sai a lokacin Junaid abun ya fara damunsa on like before da lamarin ke basa
dariya, babban damuwar tasa rashin sanin wacece iyayen sa suka xaba masa, babu
yanda bai yi da Mumy ta gaya masa ba ita ma tace bata sani ba, Tashin hankali gun
Umma da Hajiya baya faduwa don sun rasa abun yi, komai suka yi ba nasara ciki gashi
basu san wacece shegiyar da xa a aura masa ba don basu ga alamar daya daga 'ya
yansu bane, da yammacin ranan Hajja ta diro gidan, magiya junaid ya dinga mata kan
ta gaya masa wacece matar tasa tace ubansa yayi kadan balle shi, sosai hankalinsa
ya tashi, bayan magrib Abba yasa a kira sa, yana shiga parlon ya xauna Abba yace
"Babu wani shirin da za kuyi ku, ko walima ne?" Ya gigixa kai yace "A'a Abba,
walimar da xa ayi a nan gida ya isa" Abba yace "Toh shkkn, hakan it's Ohk" ranan
kasa bacci junaid yayi har kusan karfe dayan dare, wayarsa ya jawo daga karshe ya
shiga neman number Humainah don yasan baxa ta rasa sanin matar ba, har ya gama
ringing bata daga ba ya sake kiranta sai gashi ta dauka, cikin sanyin murya yace
"Kina ji na Humainah" "Um" kawai tace masa kamar anyi forcing dinta, ya lumshe ido
ya bude yace "Plss nasan baxa ki rasa sanin warce xa a aura min ba, ki gaya min
wacece plss" taki cewa komai na kusan second talatin har sai da yace "Hello" sannan
tace "Ban sani ba nima" yace "Plss" kamar xata yi kuka tace "Ban sani ba," tsaki
yayi ya katse wayar ya jefar. Washegari alhamis da asuba yayi shirin fita aiki ya
fice ya bar masu gidan, haka ya wuni bai da sukuni ranar, yana barin gun aiki
Clinic ya tafi gun El-ameen, da damuwa yace "Frnd har yanxu fa ban san wacece matar
nn ba" El-ameen yayi murmushi yace "gobe idan mun kai ka xaka ganta, sbda son da
Abba yake maka shi yasa yake son surprising naka" Junaid yace "Plss ka daina bata
min rai more, what sort of surprise is this, and what if fitinanniya ce taki yarda
da xaman yarinyar a gidan?" El-ameen ya hade rai yace "Sai ka korata nasu gidan don
bata xo maka da gida ba, and tana tarewa gobe ita kuma xata tare ran lahadi don
ranan Dr Sumayya xa su yi tafiya, tsaf ita ma kuma xa a gyara mata nata dakin"
Junaid ya dafe kai yace "Ba haka ba frnd, kasan tana iya xuwa tayi reporting ma su
Abba fa" El-ameen yace "Shit, gashi har xa a maka aure gobe baka xama mature person
ba, ka ki girma har yanxu junaid, look yanxu you are going to leave a free.... When
I say free I mean a free life, no more Mumy Mumy Mumy, you are going to head a
family of ur own don haka ko wani decision kayi a gidan ka is right ba sai wanda
parent dinka suka maka ba, from tomorrow you will be on ur own" junaid yace "Uhum?"
Tsaki El-ameen yayi, can yayi kwafa yace "da rabon matar nan ta rainaka idan ta
lura you don't have a say of ur own!" Mikewa Junaid yayi yace "Baka san ni ba
kenan" daga haka ya fice daga office din.


*Haske writers association*馃挕
[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

43.....

Washegari da ya kasance Friday tun sassafe El-ameen ya xo da leda me dauke da sabon


dinkin dakakkiyar farar shadda me tsada sosai, dinkin yar ciki da babban riga, sai
hula da takalma duk sabbi, tsokanarsa kawai yake yana dariya, shi dai Junaid
wayarsa kawae yake dannawa daga kwancen da yake fuskar nan tasa babu yabo bbu
fallasa, gefensa El-ameen ya zauna yace "Ko fa d'an gyaran fuska da gashi baka yi
ba captain, haka xa mu kai ka?" Mikewa Junaid yayi xaune a fusace yace "look ka
daina bata min rai Ahmad, bana son haka, it's not funny" El-ameen ya hade rai yace
"Ka hayyako min kamar ni xan aurar da kai? Toh ni dai ban da ni a kai ka in har
baxa ka tashi muje saloon ba" tashi daga xaunen junaid yayi fuskar nan tasa daure
ya shige daki, El-ameen ya fashe da dariya yace "Oho dai, ana saukowa juma'a xa a
daura..." Karfe tara fatima ta kawo breakfast parlon, El-ameen yace "Ina kawar ki
Humainah?" Fatima ta ajiye abun hannunta ta gaishesa sannan tace "Tace anjima xa su
taho da mamarta da na kirata" El-ameen yace "Toh idan kin koma ki ce ma Mumy Junaid
na can yana ta kuka nayi lallashin duniyar nan yaki saurarata" fatima ta xaro ido
lokaci daya ta fashe da dariya tace "Kai yaya" ya hade rai yace "Ba aiken ki nayi
ba" juyawa tayi ta fita tana dariya. Karfe sha biyu da wani abu junaid ya shiga
wanka, kan ya fito El-ameen har ya fito masa da sabbin kayan ya feshe su da uban
turare, kallo daya junaid ya ma kayan ya nufi closet dinsa ya bude ya fito da wani
blue shaddarsa, El-ameen yace "Ya haka ango ga sabon dinki nayi maka?" Ko kallonsa
junaid bai yi ba ya ajiye kayan kan gadon ya xauna yana goge gashin kansa, tsaki
El-ameen yayi ya mike ya dauke kayan ya mayar closet din ya sa key ya jefa makullin
aljihunsa, kallonsa kawai junaid ke yi, can yace "You are provoking me El-ameen"
El-ameen yayi dariya yace "oho dai tunda ba iya dukana xa ka yi ba, in baxa ka sa
sabon dinkin ba ka tafi da singlet da short nicker gun daurin auren ma" yana
murmushi ya fice masa daga dakin, Junaid ya fuxar da iska ya dafe kansa xuciyarsa
na tafarfasa, ya kusa minti ashirin xaune sanin lokaci na wucewa ya mike yana
kallon kayan da El-ameen ya ajiye masa, wani takaici ya rufesa, sai kace irin yana
son auren, tsaki yayi ya fixgo rigar yana kallo, ya kusa wani minti goman tsaye ya
sake jan tsaki ya xura rigar ya dau wandon ya sa, kayan suka haska sa sosai, da
ganinsa ka ga Ango, toilet ya koma ya dauro alwala ya fito ya tafi gun hulunarsa ya
dau daya ya gyara ya daura a kai ya dau takalminsa ma ya saka, ko agogo bae kalla
ba bare ya fesa turare ya fice daga dakin rike da wayoyinsa. Kallonsa El-ameen ke
yi daga sama xuwa kasa yace "Ina sabon takalmin da hular, kuma ina babban rigar?"
Wani uban harara Junaid ya xabga masa yace "Baxan sa ba" El-ameen ya fashe da
dariya yace "Oho dai bbu wanda zai ce wa ennan ma da ka sa ba sabo bane, nima bari
in je inyi wankan in shirya as babban abokin ango" daga haka ya shige dakin, junaid
ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujera ya lumshe ido, banda faduwa babu abinda
gabansa yake wai shi xa a daura ma aure yau. Daya saura El-ameen ya fito daga dakin
sanye da farar shaddar da ya dauka a closet din Junaid, shi ma yayi kyau har ya
gaji, kallo daya Junaid yayi masa ya dauke kai, El-ameen ya xauna gefensa yana
murmushi ya mika masa agogo yace "Here!" Dauke kai junaid yayi bai ce komai ba, El-
ameen yace "Dama ka saki ranka ga su faisal nan xuwa, if not you will be the topic
of discussion na cewa an maka auren dole, just pretend as if its nothing and you
are happy..." Ko rufe baki El-ameen bai yi ba sai ga faisal da kusan abokansu har
biyar, Junaid ya sauke ajiyar xuciya hade da sakar masu murmushi, tsokanansa suka
shiga yi kamar shi ya kawo su, shi dai baya cewa komai sai murmushin da bai kai
ciki ba, hotuna suka shiga yi gaba daya a parlon, daga bisanni suka fita don xuwa
masallaci, sosai gidan ke cike da jama'a, Junaid yaji dama kawai ya gansa a waje ba
sai ya bi ta compound ba, kallo aka bi sa da shi barin su Umma da bakin ciki ya
cika su kamar su yi yaya, ko kayan arxiki basu saka ba ana xaune bakin murhu, El-
ameen yace "Ya kamata ka je Mumy ta sa maka albarka kafin ka fita, sai ka ga anyi a
sa'a" part din Mumy Junaid ya nufa, bai bi ta kan mutanen parlon ba ya shiga
bedroom dinta ya sameta xaune tare da sisters dinta sai abokan arxiki, kallonsa
take har ya iso gabanta ya durkusa cikin sanyin murya yace "Xa mu tafi masallaci
Mumy" ta yi murmushi tace "Toh Allah ya tsare, yasa ayi a sa'a" ya sunkuyar da kai
yace "Ameen" sai a sannan ya kalli Mutan dakin ya gaishesu ya mike ya nufi kofa,
duk suka bi sa da kallon sha'awa ganin irin respect dinsa har ya fita, kanwarsa ce
Aysha ta bi bayansa murmushi dauke fuskarta tace "Ya Ahmad" yace "Ya kike" tace
"lafiya lau, tun jiya bamu hadu ba" yace "Eh ai kin san inda nake" daga haka ya ci
gaba da tafiyarsa. Ana saukowa daga juma'ah aka daura aurensa da warce bai ma
sha'awan sani yanxu kam a kan sadaki dubu dari biyu, bai wani tsaya gaishe gaishe
ba ya xame ya bar wajen ba tare da El-ameen ma ya sani ba ya koma gida. Bayan isha
junaid da El-ameen sai faisal na Parlor xaune Khadija ta shigo tace Abba na
kiransa, mikewa yayi ya fita xuwa part din Abbansa, shi da Abban Humainah ne xaune
parlon sai wani amininsa, Junaid ya samu waje ya xauna sannan ya gaishe su, nasiha
suka yi masa banda Abbansa dake ta kallonsa, shi dai kansa na kasa, har suka kare
cikin sanyin murya yayi masu godiya, Abbansa ya kara da cewa Allah yayi ma rayuwar
aurensa albarka, yace "Ameen" Abokin Dad dinsa Alhaji Umar ne yace Ya tashi ya tafi
don tuni aka kai masa matarsa, mikewa yayi bai ce komai ba ya fita daga parlon,
part din Mumy ya tafi a sanyaye ya sameta ita da Ummin El-ameen a dakin, ya isa
gabanta ya durkusa murya can kasa yace "Abba yace in tafi Mumy" Mumy tace "Toh
Allah ya albarkaci rayuwar auren ka Ahmad, Allah ya baka xuri'a ma su yi maka
biyayya kamar yanda kake min" kasa dago kansa yayi, lokaci daya idonsa ya kada, a
hankali ya daura kansa kan kafarta cikin sanyin murya yace "Mumy ban san matar ba
har yanxu" murmushi tayi ta dago kansa tana kallonsa sai dai bata ce komai ba, Ummi
tace "kasan mahaifinka baxai maka xabin da xai cuce ka ba Ahmad, Allah ya baku
xaman Lafiya, tashi ka je" mikewa yayi a hankali ya juya ya fita. Karfe tara saura
suka bar gidan shi da El-ameen da faisal, xuwa yanxu kam sun daina tsokanarsa ganin
yanayinsa, El-ameen ji yake kamar shi aka yi ma hakan yaji tausayinsa sosai, gun
masu gasassun kaji El-ameen yayi parking ya fita ba a dau lokaci ba ya dawo rike da
ledan kaji da drinks, tafiyar kusan minti talatin suka yi suka isa gidan Junaid,
El-ameen ya sauke ajiyar xuciya ya juya yana kallonsa bayan yayi parking a compound
din, gidane duplex mai kyau da girman gaske, compound din ya kawatu da kayan shuke
shuke iri iri ga haske ko ina kamar rana, faisal sai danne dariyarsa yake ganin
yanda Junaid ya hade rai yana kallon gidan, El-ameen yace "Toh ni dai a nan xan bar
ka, gobe da safe zan kawo maka motar ka" junaid ya kallesa yace "Haka koh?" El-
ameen yace "Allah baxan shiga ba sai dai ko faisal" faisal yace "No, sai dai mu
dawo ganin amarya gobe" El-ameen yace "Exactly" ficewa junaid yayi daga motar El-
ameen yace "Wait ga kajin amarya baka dauka ba" ko saurarensa junaid bai yi ba ya
nufi cikin gidan, El-ameen ya dauki ledojin ya bude motar ya fito yana dariya ya bi
bayansa, tsaye ya gansa a parlor yana bin ko ina na parlon da kallo, kamshi me dadi
ne ke tashi ta ko wani angle, komai na parlon brown nd milk, El-ameen ya karaso
cikin parlon ya ajiye masa ledan a kasa yace "Sai da safe ango" junaid ya kallesa
yace "Yanxu da gaske ba xa ka raka ni ba" El-ameen yace "Kila yanda gabana ke
faduwa naka baya faduwa haka, I just can't, gobe dai xan dawo..." Daga haka ya fice
daga parlon, Junaid ya sauke ajiyar xuciya ya kalli hanyar stairs, a hankali ya
karasa ya haura sama, ya dde tsaye corridor din dakunan yana kallon kofar dakin da
ya san tana ciki, karasawa yayi bakin kofar ya murda a hankali lokaci daya ya tura
yana kallon cikin dakin, xaune ya ganta can karshen gado ta takure waje daya
fuskarta rufe da babban veil, ya kusa minti biyu yana kallonta sannan ya karaso
cikin dakin ya isa gabanta ya tsaya yana kare mata kallo yace "Ke kika ce ma
iyayena kina so na?" Shiru bata ce komai ba, yace "Magana nake maki" Mikewa tayi
xata bar wajen ya fixgota har sai da ta fado kansa fuskarsa daure yace "Ina maki
magana xaki wuce" turasa tayi tace "Ni ka kyaleni, ko kuma kai kace kana so na ba"
saketa yayi ya bude ido yana kallonta da mamaki, ta bude mayafin fuskarta ta
hararesa ta bar wajen, rungume hannayensa yayi ya bi ta da kallo har ta xaga daya
side din gadon ta xauna, murmushi kawai yayi ya fita daga dakin ya shiga nasa,
wayarsa ya dauka ya shiga neman layin El-ameen, yana dagawa yace "Guess wacece
amaryar" El-ameen yace "Uhun! Humainah!" Junaid yace "Ohh dama ka sani?" Dariya
yayi yace "No! I only guessed" tsaki junaid yayi yace "Very funny wai Humainah, all
the same xata yi girki dai ta gyara gida ta kula da jasmine, shikenan an wuce
wajen" El-ameen ya xaro ido yace "Wacece jasmine kuma?" Shiru junaid yayi can yace
"Sai da safe" daga haka ya ajiye wayar ya shiga cire kayan jikinsa, wanka yyi yayi
alwala ya fito ya canxa xuwa jallabiya snn yayi shafa'i da wutr ya jima xaune kan
darduma daga bisanni ya mike ya koma kan gado, har ya kwanta ya mike xaune,
murmushi yayi da ya tuna wai fa Humainah ce matar da aka aura masa, wai Humainah,
dariya ya fara yi, ita wannan har ta isa aure yarinyar da ko secondary bata kare
ba, though yaji dadin da ya kasance ita ce don baxa ta wani bada wani matsala gun
kawo jasmine gidan ba, tabe baki yayi ya mike ya fita ya koma dakinta, kwance ya
sameta ta takure waje daya tana bacci, tabe baki yayi ya kashe wutan dakin yayi
kwanciyarsa can nesa da ita, ya kusa awa daya kwance kafin bacci ya daukesa, can
cikin dare ya ji tana tashin sa, ya mike xaune ya kunna
bedside lamp yana kallonta da kumburarrun idonta alamar ba kuka kadan tayi ba,
yace "What?" Kamar xata yi kuka tace "Ni yunwa nake ji" ya kalli agogo ya ga sha
biyu har ya gota yace "Yunwa? Baki ci abinci daga gidanku bane" tace "Eh ni ban ci
ba" d'an tsaki ya ja yace "Toh ni yanxu ina xan samo maki abinci tsakar daren nan?"
Tace "Ni dai wllh yunwa nake ji" ledan da El-ameen ya ajiye parlor ya tuna yace
"Tafi parlor xa ki ga leda ki duba meye a ciki" ta xaro ido tace "Ni dai tsoro nake
ji" ya hade rai yace "Xan fa kwada maki mari idan kina damuna ina bacci" ta fashe
da kuka ta mike xaune, tsaki ya ja ya sauka daga kan gadon ita ma ta sauko ta bi
bayansa da sauri, a tare suka sauko parlon ya kunna wuta ya dau ledan ya bude ya
nufi kitchen ya dauki plate da wuka da fork sai cup ya fito, nan parlon ya dawo ya
xauna kan rug ya fiddo kaza daya ya Yanyanka a plate yana kallonta yace "Ga shi"
matsowa tayi a hankali ta dau daya ta fara ci, ya mike yace "Idan kin gama ki kashe
wutan parlon" da sauri ita ma ta mike tace "Don Allah ka jira ni ya A.jay wllh
tsoro nake ji" ya hade rai yace "Kina fa damuna" ta d'an marairaice ta koma ta
xauna ta ci gaba da cin kazar, xaunawa yayi shi ma yace "Idan sha biyu da rabi yayi
baki gama ba xan yi tafiyata" ta d'an hararesa bata ce komai ba, dauke kai yayi sai
dai lokaci lokaci ya kan saci kallonta, suna hada ido yyi saurin cewa "Haka aka
koya maki a gidan ku Idan xaki kwanta kar ki cire kayan da kika yini da?" Tace "Kai
ma ai gidanku ne" bai kuma ce mata komai ba har ta gama, ta mike ta dau plate din
tace "Raka ni kitchen" harararta yayi ta rama ta nufi kitchen, ya bi ta da kallo,
tana fitowa ya mike ya kashe wutan parlon yyi hanyar stairs ta bi bayansa da sauri
suka shiga dakin a tare, wutan dakin ta kunna yace "Meye haka?" Tace "Xan wanke
baki mana" gado ya nufa yayi kwanciyarsa ta shiga toilet, ba a dau lokaci ba ta
fito ta nufi closet ta bude ta fiddo doguwar riga da hijab ta koma bayin, tana
fitowa tayi kwanciyarta nesa da shi ta juya masa baya, yace "Ke wa kika bar ma wuta
a kunne?" Tace "Nafi son haka, ni bana son duhu" tsaki yayi ya mike ya tafi ya
kashe wutan kan ya dawo har ta mirgino ta dawo gefensa, yayi kwanciyarsa hade da
juya mata baya.

*Haske Writers association*馃挕
[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

44/45
Da asuba Junaid ya dade xaune gefen gado daga bisanni ya mike, kallo daya ya ma
Humaina dake bacci ya shiga toilet ya dauro alwala ya fito har xai fita xuwa
masallaci ya dawo ya isa kusa da gadon ya buga kafarta, bude ido tayi a hankali
tana kallonsa ya juya ya fita daga dakin, ko da ya dawo daga masallaci samun ta
yayi kwance tana bacci har lokacin, bayi ya shiga ya debo ruwa ya fito ya watsa
mata, ta mike xaune da sauri tana kallonsa, yace "Sllh!" Daga haka ya fita daga
dakin, tsaki tayi ta bi sa da harara ta sauka daga gadon ta shiga bayi. Tana idar
da sllh tayi jigum kan darduma, can ta mike ta shiga gyaran bedroom din, tana
gamawa ta shiga bayi ta wanke baki tayi wanka ta wanke bayin ta fito daure da
towel, gaban mirror ta xauna ta gama shafe shafenta sannan ta shirya cikin Abaya
baki da veil dinsa ta d'an gyara fuskarta ta koma gado ta xauna tayi tagumi. Bude
kofar dakin aka yi fatima da khadija suka shigo, Humainah ta mike da sauri lokaci
daya tayi murmushin jin dadin ganinsu, fatima tace "Uhum Amaryar yayarmu, Antynmu!"
Hade rai tayi can ta fashe da kuka tace "Ni ba amaryarsa bace, ai Hajja tace sbda a
raba sa da mahaukaciyar nan ne aka aura masa ni, amma da ya rabu da ita sai a sa ya
sakeni in ci gaba da karatuna" innocently tayi maganar tana kallonsu, Khadija da
fatima suka fashe da dariya barin khadija, juyawa Humainah tayi a sanyaye ta koma
gefen gado ta xauna, hade kanta tayi da gwiwa tana kuka, fatima ta karasa kusa da
ita da sauri tace "Toh ai ba mu ce ba haka bane ba fa Humainah" Humainah ta girgixa
kai tana kuka tace "Ba wani nan nasan wayo aka min baxa a ce ya sakeni ba, yar
yarinya da ni xan je ss3 za ayi ma aure bayan ku ba a maku ba....." Khadija ta
xauna gefenta tace "Ni dai ba dariya nake maki ba, ba ruwana, ga abinci Mumy tace a
kawo maki" Humainah ta dago kanta tana share hawayen idonta tace "Hajja fa?"
Khadija tace "Ta ce anjima xata xo" Junaid ne ya shigo dakin ya tsaya daga bakin
kofa yana kallonsu yace "A baki aka ce ku bata abincin?" Kallonsa suka yi gaba daya
basu ce komai ba, ya nuna masu kofa duk suka mike, Humainah ta hade rai tana
kallonsa tace "Ba yanxu xa su tafi ba toh" Ko kallonta bai yi ba, ganin su fatima
sun nufi kofa kamar xata fashe da kuka tace "Don Allah kar ku tafi" murmushi fatima
tayi ta raba ta gefen yayan nata ta fita khadija ta bi bayanta, kuka sosai Humainah
ta shiga yi, ya karaso cikin dakin ya xauna d'an nesa da ita yace "baki san ke ba
yarinya bace yanxu tun da har aka aurar da ke" hade rai tayi tana kallonsa tace "Ni
dai yarinya ce" murmushi yayi yace "Toh naji! tsoron xama ke kadai kike a dakin da
kike son su xauna da ke?" Ta kallesa hade da gyada masa kai, yace "Toh xan samo
maki warce xata dinga taya ki xama ai kina so?" Tana kallonsa tace "Amma babba ce?"
Ya girgixa mata kai yace "No yar yarinya ce kamar ki sai ta dinga taya ki xama kuna
kwana ma tare" sosai ta hade rai tace "A'a bna so, xan iya xama ni kadai" shiru
yayi yana kallonta, can yace "Saboda me?" Ta mike tace "Haka nan kawai, xan iya
xama ni kadai abuna" daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, lumshe
ido yayi ya bude yana naxarin abinda ta ce, Mikewa yayi shima ya fita daga dakin ya
koma nasa. Karfe sha biyu saura aka danna bell downstairs, Junaid dake bedroom
dinsa yana danne dannen waya ya mike ya fita, dai dai lokacin da Humainah ma ta
fito, kallo daya yayi mata ya sauka ya je ya bude kofar, Hajja ce tsaye bakin kofar
da Sadiya, ta washe hakora ganin Junaid tace "A'a ango, to gani na biyo ka don kayi
amarya sai ka mance da uwar gida?" Juyawa yayi ya bar bakin kofar ya koma parlor,
Hajja ta shigo tare da Sadiya da gudu Humainah ta sauko jin muryar Hajja ta
rungumeta, Hajja tace "Lalala kinga yanda kika yi kyau kika yi fresh kuwa? Lallai
Amadi ya iya kiwo daga jiya xuwa yau" hade rai Humainah tayi tace "Ni babu abinda
ya ban na ci har yanxu" Hajja tace "Ehh amma ai kin kwan masa a gida" turo baki
tayi ta tafi ta xauna, Hajja ta kalli Junaid tace "Banxa kai kuma ko ka kira ka
mana godiya ka ga xukekkiyar amarya ba mahaukaciya ba" Kallonta kawai yake can ya
tabe baki yace "Nii ban gode ba tun da ban ce ina so ba, kawai makala min aka yi"
Humainah ta fashe da kuka tace "Hajja kin dai ji ko, ni dai tare xa mu koma don ni
ma makala min aka yi ban ce ina so ba" Hajja ta hade rai tace "Kai kaga irin hada
ta da Allah annabin da aka dinga yi don ta amince da gantalallen auren ka, banda
kaddara me xata yi da kai Ahmad, kai da cikakken saiti baka da, wllh wllh 'yar nan
tafi karfin ka, kawai ka kara gode ma Allah da ya sa aka baka ita" juyawa tayi tana
kallon Humainah tace "ke kuma kar ki kuskura ki bari ya kwana dakin ki tunda haka
yace, hanyar jirgi daban ta mota daban kin dai ji ni..." Humainah ta gyada mata kai
tana goge hawayen idonta, Hajja ta nemi kujera ta xauna tana cewa "Banda walakanci
an samu an lallaba yarinya da kyar ta amince ta rufa maka asiri ta aureka xaka
dinga gaya mana magana, ko fa kwandalar ka bbu a bikin nan don tsiya.... Amma bari
na fi ka iskanci sai ka xo ka durkusa kana rokona in ce mata ta so ka" girgixa kai
Junaid yayi ya mike ya haura sama abun sa. Har Karfe uku Hajja na gidan ita dai
Sadiya dama turo ta aka yi ta ga kwakwaf ta ga yanda gidan yake da abubuwan da aka
xuba, tana gama abinda ya kawota ta kara gaba ta bar Hajja. Har dai bayan la'asar
Hajja bata da niyar tafiya Junaid ya rasa me suke kullalawa a dakin gashi El-ameen
ya ki xuwa saboda Hajjan, mikewa yayi ganin har biyar ya gota ya shiga dakin, suna
ganinsa suka yi shiru, Hajja ta hade rai tace "To ya aka yi kuma?" Ya d'an shafa
kansa yace "Kawu Abubakar ne ya kira wai yana ta jiran ki xai koma" mikewa Hajja
tayi da sauri tana xuge yar purse dinta tace "Auu bawan Allah to bari in je"
Humainah ta marairaice kamar xata yi kuka tace "Yanxu tafiya xa kiyi ki bar ni
Hajja" Hajja ta hade rai ta kalli Junaid sai kuma ta duka kusa da ita murya can
kasa tace "Kin dai ji abubuwan da na gaya maki dai koh?" Humainah ta gyada mata
kai, Hajja ta mike tace "Ehh to ba dole in tafi ba Humainah, amma ina nan dawowa
kila ma da kayana xan taho tunda ai jikokina ne ko na xauna bbu komai" daga haka ta
nufi kofa tana cewa "Toh kai d'an ubanka xaka kai ni gidan ne ko in je in hau
machine tunda Sadiya sun koma da driver" ficewa junaid yayi daga dakin ita ma ta
fita tana cewa "Toh Humainah sai Allah ya sake dawo da ni" har gida Junaid ya ajiye
Hajja sannan ya kira El-ameen yace "Toh ta tafi, am waiting for you" daga haka ya
katse wayar ya kama hanyar gida. Kusan a tare suka iso gidan da El-ameen, El-ameen
yayi parking ya fito yana murmushi yace "Daga ina haka ango?" Junaid yace "Nayi
dropping dinta mana" bude motar El-ameen yayi ya shiga yana kallonsa yace "Tabdi
gaskiya Humainah ta karbe ka, ka ga yanda ka kara kyau yau kuwa" girgixa kai Junaid
yayi yace "Kaga ni mu yi maganar arxiki, kasan kuwa yarinyar nan tace ita bata son
a kawo mata kowa gida?" El-ameen ya hade girar sama da ta kasa yace "Kamar ya? Kaga
matsalar ka ko Ahmad, daga aure har yarinya xata fara raina ka tana fadin abinda xa
ayi a gidan da wanda baxa ayi ba, gidan ta ne da har xata gaya maka abinda xa ayi?
Kai wani irin Human being ne junaid" Shiru Junaid yayi yana kallonsa, can ya sauke
ajiyar xuciya yace "Am afraid kar ta ce xata gaya ma su Mumy ne shi yasa ban ce
komai ba" El-ameen yace "Tabdi! Yarinyar nan fa wllh sai kayi gaske da ita Idan ba
haka ba second Mumy dinka xata xama, naga alamar fitinanniya ce, shikenan kai kuma
ka xama abun tausayi baka da say a duniya sai na Mumy da wife, haba sai kace ba
captain ba kawai ka cika ma kanka girman kai da miskilanci maimakon being ur own
self, ita wannan har ta ma wuce ka bubbuge ta Idan tace xata kawo maka rainin
hankali" girgixa kai junaid yayi hade da yin murmushi yace "Uhum lallai" horn ya
danna aka bude gate ya shiga da motar yayi parking ya juya yana kallon El-ameen,
El-ameen yace "Toh gobe dai Dr Sumayya xata yi tafiya ban kuma san inda xan kai
patient dinka ba" junaid ya bude motar ya fita shima ya fito suka shiga cikin
gidan. Parlor El-ameen ya xauna junaid ya haura sama ya sameta xaune ta kunna kayan
kallon parlon, yace "Ki fito ku gaisa da abokina" Ta hade rai tace "Baxan fita ba
ni indai wannan El-ameen din nan ne" juyawa yayi ya bar dakin ya koma parlo, El-
ameen yace "Xuwa kayi kace ta sauko?" Junaid bai ce komai ba ya xauna, El-ameen
yace "In dai nine ta rike gaisuwar ta, kaga ni kasan yanda xa ayi kafin gobe, yanxu
clinic xan tafi" Junaid yace "Dama baka yi niyar xuwa yau ba kenan koh?" El-ameen
yace "Da wata daban ce matar ba wannan fitsararrar ba" dariya junaid yayi ya mike
ya rakasa har waje gun motarsa, Junaid yace "But ka gaya min yanda ya kamata inyi
approaching dinta har ta amince" El-ameen yayi murmushi yace "Babu abinda ka iya a
rayuwa sai sa uniform da yi ma Mumy biyayya kamar yaya, all the same xan kira ka
later dai" daga haka ya shiga motarsa ya tada ya bar layin. Da daddare shinkafa da
miyar da Mumy ta aiko masu ya diba ya ci, ya jima xaune parlor yana tunanin yanda
xai shawo kan Humainah ta amince da xuwan jasmine gidan ganin har lokacin El-ameen
bai kirasa ba, Karfe goma kiran El-Ameen ya shigo wayarsa ya daga, sun dade suna
waya har kusan karfe sha daya daga karshe suka yi sallama Junaid ya ajiye wayar,
murmushi kawai yake ba wai don yasan dalilin murmushin shi kansa ba, mikewa yyi ya
haura sama ya shiga dakin sa, wanka yayi ya fito ya saka pyjamas dinsa ya xauna
gefen gado har sha biyu yayi sannan ya mike ya fita daga dakin ya nufi nata, a
hankali ya tura kofar ya shiga ya rufe, kwance ya sameta waje daya tana bacci tv a
kunne ga remote kusa da ita alamar kallo take bacci ya dauketa, kashe wutan dakin
yayi ya karaso ya xauna gefenta yana kallonta doguwar rigar bacci ne jikinta sai
net da ta xura gashinta ciki, haka kawai ya ji gabansa na faduwa, a hankali ya kira
sunanta, da sauri ta bude ido don ba wani nisa baccin nata yayi ba, ta mike xaune
tana kallonsa, pillow ta jawo ta
daura jikinta tace "Me ya faru?" Ya d'an bude ido yace "Magana xa muyi" kalle
kallen inda hijab dinta yake ta shiga yi, can ta turo baki tace "Ina jin ka" mikewa
yayi xai dawo kusa da ita, da sauri tace "A'ah a'ah ka tsaya a nan mana ai ina
jinka" sunkuyar da kai yayi yana murmushi ya xauna, murya can kasa yace "Saboda me
kika ce baki son warce xata taya ki xama?" Hade rai tayi tace "haka nan" a hankali
yace "kinga Idan na fita aiki tun sassafe fa sai yamma nake dawowa, baxa ki iya
xama ke kadai a babban gidan nan ba sbda in some cases sai ki ga akwai aljanai a
babban gida haka" xaro ido tayi ta matso kusa da shi a hankali tace "Aljanai kuma
Ya A.jay?" Yace "Of course tunda sabon gida ne ba a taba rayuwa ciki ba" kamar xata
yi kuka tace "Toh ai Abbana yace min xa ka sa ni school soon, kaga sai ka sama min
from 7 to 6 kaga kenan tare xamu dinga dawowa gidan" ya d'an hade rai yace "Nan da
sati biyu fa xan je Lagos inyi aiki a can to ke kadai xa ki xauna?" Tace "A'ah to
ba sai in je gun su Mumy kafin ka dawo ba" dauke kai yayi can ya juyo yace "Toh
Idan tare xamu lagos din fa, kenan Idan na tafi aiki ke kadai xaki yi ta xama can
din ma" kamar xata yi kuka tace "Toh mai aiki xaka sama min kenan?" Ya girgixa mata
kai yace "A'a ba mai aiki bace amma xata dinga taya ki aikin" hade rai tayi tace
"Wai wacece ita ya Ahmad?" Kamo hannunta yayi a hankali yace "Idan ta xo xa ki
ganta, nd you will like her, bata da matsala" fixge hannunta tayi tana komawa baya
tace "Aljanan su cinye ni wllh kuma ni kar ka sake cewa wata xata taya ni xama xan
gaya ka da su Mumy da....." jawota yayi jikinsa ba shiri tayi tsit ta fara turasa
tace "Meye haka ya A.jay" a hankali ya daura bakinsa kan wuyarta, lokaci daya ranan
da ta gansa da Muhibba a daki ya fado mata, ta fasa ihu a tsorace tana kokarin
kwace kanta tace "Don Allah ya Ahmad ka yi hakuri ka kyaleni bana so" murya can
kasa yace "Meye ba kya so?" Da kyar muryarta na rawa tace "Toh to naji wacece xata
taya ni xaman?" Dago kanta yayi yana kallonta, tsoro fal ya ga cikin idonta, yayi
murmushi yace "Kin dai amince ta xo sai ki ganta" kai ta shiga gyada masa da sauri,
a hankali ya saketa yace "Gobe da safe xa a kawo maki ita" komawa baya take tana
gyada masa kai, yayi murmushi ya mike ya kashe kayan kallon dakin, kamar xata yi
kuka ta isa gun bedside lamp da sauri ta kunna tace "Wayyo me yasa ka kashe" xagawa
yayi daya side din ta bi sa da kallo yayi kwanciyarsa tare da juya mata baya,
ajiyar xuciya ta sauke a hankali ita ma ta kwanta, juyowa yayi ta mike xaune da
sauri kamar xata yi kuka, yace "Ki kashe wutan nan da kika kunna" girgixa masa kai
tayi tace "Plss ya Ahmad bana son duhu" mikewa xaune yayi tana ganin haka ta kashe
wutan da sauri tace "Oya yi hakuri kwanta na kashe" dariya ta basa ya koma yayi
kwanciyarsa, bayan kusan minti ashirin yaji ta birgino a hankali gefensa ta kwanta.
Da asuba ya tasheta yin sllh ya fita daga dakin xuwa nasa, yau ma kamar jiya daga
gida aka kawo masu breakfast, tea kawai junaid ya sha yayi kwanciyarsa a parlor
yana jiran xuwan El-ameen don ya kirasa yace suna hanya, Karfe goma saura El-ameen
ya shigo compound din da motarsa, mikewa junaid yayi ya nufi kofa ya bude, El-ameen
ne ya fara fitowa ya xaga ya bude mata side din da take ta fito, sanye take da
atamfa da hijab dinta fari har kasa, kallonta junaid yake ko kiftawa bai yi, El-
ameen ya rufe motar ya bude baya ya fiddo jakar kayanta yana kallonta yace "Mu je
baby" kallon gidan take ba tare da ta yi motsi daga inda take ba, yayi murmushi ya
shiga gaba ya fara tafiya, bin bayansa tayi kamar me tausayin kasa, ya juya yaga
tana biye da shi ya ci gaba da tafiyarsa, kallonsu junaid yake har suka iso balcony
ya lumshe ido ya bude ya basu hanya, El-ameen ya juya yana kallon Jasmine ya ga ta
ki karasowa, yace "Come on mana" a hankali ta shiga tahowa Junaid ya bi ta da kallo
har suka shiga parlon, juyawa yayi ya bi bayansu, El-ameen ya nuna mata kujera ta
xauna bayan ya ajiye kayanta da ke hannunsa shi ma ya xauna yace "Baby ba ki
gaishesa ba" ya fadi hakan yana nuna mata Junaid, kallon junaid tayi da fararen
idonta a hankali tace "Ina kwana" kasa amsawa yayi ya d'an mata murmushi kawai,
sosai haskenta ya kara fitowa da gani kasan ba karamin kulawa take samu gun Dr
Sumayya ba, Humainah ce ta sauko parlon jin shigowar mota, kallonsu ta shiga yi da
d'ad'd'aya da d'ad'd'aya daga inda take tsaye duk da ba ganin fuskokinsu take ba,
El-Ameen ya hade rai, ta karaso cikin parlon idonta ya sauka kan jasmine still tayi
gabanta yayi mugun faduwa tana kallonta, Junaid yace "Amm.... Kin ganta she will
keep you accompany ana kiranta da Baby...." Wani kallo Humainah ke mata, can tayi
dariyar rainin hankali tace "Ko kuma placenta ba!" Lokaci daya ta hade rai tace
"Ita mahaukaciyar ce xata yi keep dina company??" Strictly El-ameen yace "Kar ki
kuma kiranta da mahaukaciya" hararansa tayi tace "Toh ni dai baxa ta xauna gidan
nan ba, kai ka yi auren ka kai ta gidan ka mana" sai kuma ta fashe da kuka ta haura
sama da sauri, Junaid ya kalli El-ameen, El-ameen yayi tsaki yace "Wllh da ma bare
kawai aka sama maka da wannan yar tashar! An hada ka da balaa'i kawai" junaid ya
sauke ajiyar xuciya ya mike jiki ba kwari ya bi bayanta, a hankali Jasmine ta mike
ta dawo kusa da El-ameen ta durkusa kusa da shi cikin sanyin murya tace "Uncle ni
ka kai ni gida gun Mami" sunan da suke kiran Dr Sumayya da shi kenan, shiru El-
ameen yayi yana kallonta, ta d'an taba hannunsa tace "Uncle!" Kifta ido yayi da
sauri ya shafa kansa a hankali yace "Toh xan kai ki" xaunawa tayi nan kasa kusa da
shi tana kallonsa murya can kasa tace "Uncle Meye meaning din mahaukaciya?" Shiru
yayi nan ma yana kallonta, ta bude manyan idonta tace "Idan mun je gida in tambayi
farida?" Murmushi ya mata hade da gyada mata kai.


*Haske Writers association*馃挕
[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

46.....

Kwance junaid ya sameta tana kuka a dakin, ya karasa ya xauna kusa da ita ya dago
ta, turasa ta shiga yi cikin kuka take cewa "Ni ka kyaleni, ka kyaleni" a hankali
yace "Listen to me plss Humainah, ba fa mahaukaciya bace" ta fashe da matsanancin
kuka tace "Nace ka kyaleni ni dai" saketa yayi yana kallonta, ta koma ta kwanta
tana ci gaba da kukanta, mikewa yayi ya fita daga dakin ya koma parlor, El-ameen
dai kallonsa kawai yake bai ce komai ba, Junaid ya xauna ya shafa kansa yace "Shknn
you can go Idan tafiya xaka yi" El-ameen yace "Toh gimbiyar taka ta yarda kar in
tafi in bar yar mutane ta kasheta kana kallo" Junaid yace "In xaka tafi kayi
tafiyar ka kawai" mikewa El-ameen yayi yana kallon Jasmine yace "Baby xaki tsaya
nan har in dawo kin ji" kallonsa kawai take, ya durkusa kusa da ita yace "Kin ji?"
Idonta ne ya cika da hawaye, a hankali El-ameen yace "Kuka kuma baby" shi dai
junaid kallonsu kawai yake, El-ameen ya ciro handki ya mika mata yace "baxan dade
ba xan dawo kin ji" karba tayi ya mike ya kalli Junaid sannan ya fita daga parlon.
Kallonta kawai Junaid ke yi kanta a kasa tana fidgeting fingers dinta, can ya mike
ya kullo kofar sannan ya dawo ya dau jakar kayanta yace "Tashi mu je" mikewa tayi a
hankali tana kallonsa ya d'an mata murmushi yace "Follow me" daga haka ya nufi
stairs ta bi bayansa, dakin dake kusa da na Humainah ya bude ya shiga ta tsaya daga
bakin kofa tana kallon dakin, juyawa yayi yana kallonta yace "Shigo mana" a hankali
ta shiga dakin ya rufe kofar, kan gado ya ajiye jakarta ya bude closet yace "Ki
ajiye kayan ki duka a nan kin ji?" Sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, ya nuna
mata kofar bayi yace "ga toilet nan" kallon kofar tayi ta gyada masa kai, yace "Are
you hungry?" Girgixa masa kai tayi da ganinta kasan a tsorace take, yayi murmushi
ya kunna mata tvn dakin yace "Ki xauna kiyi kallon ki toh" ta gyada masa kai ya
juya ya fita daga dakin ya rufo mata kofar, da sauri ta mike ta nufi kofar ta bude,
yana tsaye bakin kofar Humainah ya juyo yana kallonta, dawowa yyi yace "Ya aka yi?"
Kamar xata yi kuka tace "ina jin tsoro" shiru yayi yana kallonta ta bude kofar
sosai ta koma ta xauna a dakin, Dakin Humainah ya karasa ya bude ya shiga ya sameta
har lokacin tana kuka ya rungume hannayensa yana kallonta, can ya karasa kusa da
gadon ya xauna yace "Ke yanxu baxa a iya cin arxiki gun ki ba, baxa ki yi taimako
ba, kwana biyu fa kawai xata yi ta bar gidan" ko kallonsa bata yi ba ya dagota ya
rungumeta yace "plss mana, wllh xata bar maki gidan soon, she's not staying long"
turasa tayi tace "Bana so, kuma ni ka rabu da ni" hade rai yayi ya saketa ya mike
yace "Toh wai gidan ki ne nan din? Ko a kanki take xaune" dago kai tayi tana
kallonsa, ya watsa mata wani kallo ya juya ya fice daga dakin, wani sabon kukan ta
fashe da har da shessheka. Dakin sa ya koma ya kwanta yana tunanin anya decision
din da yayi na kawo jasmine gidan yayi daidai kuwa, har aka kira Azahar yana
kwance, mikewa yayi daga karshe ya shiga bayi ya dauro alwala ya fito, nan dakin
yayi sllh yana xaune kan darduma bayan ya idar aka danna bell din gidan, mikewa
yayi ya fita har lokacin dakin da jasmine take a bude yake, parlor ya sauka ya
bude kofa, fatima da khadija ne bakin kofar rike da flask din abinci, gaishesa suka
yi ya karba yace "Mun gode, ku gaida mutan gidan," daga haka ya kulle kofar ya dawo
cikin parlor, plate ya dauko a kitchen ya dibi couscous din dake cikin flask din ya
bude na miya ya diba sannan ya rufe ya dau goran ruwa da cup da spoon ya haura
sama, dakin da jasmine ke ciki ya shiga, kwance ya ganta a kasa ta takure waje daya
tana bacci, ya shigo dakin ya ajiye abincin hannunsa yace "Jasmine" sau uku yana
kiranta ganin bata tashi ba ya durkusa gabanta ya d'an taba ta, bude ido tayi ta
mike xaune da sauri ganinsa, yayi mata murmushi ta sunkuyar da kai, yace "Me yasa
baki kwanta kan gadon ba" shiru tayi bata ce komai ba, ya dauko darduma ya shimfida
a kasa yace "Dawo nan" mikewa tayi ta xauna kan darduman ya ajiye mata abincin da
ruwa a kai yace "ga abinci ki ci" kai ta gyada masa, yace "Toh ci mana" a hankali
ta dau spoon din da dibi abincin ta kai baki tana kallonsa, murmushi ya mata yana
kallon yanda take tauna abincin, yace "You like it?" Kai ta gyada masa, ya mike
yace "Toh maxa ki cinye kafin in dawo" daga haka ya fita daga dakin ta bi sa da
kallo. Ko da ya dawo xaune ya sameta ta tura abincin gabanta tayi jigum, ya karaso
ya durkusa gabanta yace "Baki ci ba kuma" ta girgixa masa kai a hankali tace "Na
ci" yace "No! kadan kika ci" spoon din ya dauka ya dibi abincin ya kai mata baki, a
hankali ta bude bakin ya xuba mata, haka ya dinga bata har abincin yayi rabi ta
kauda kai tace "Na koshi" ajiye spoon din yayi yana kallonta yace "Toh tashi ki je
kiyi alwala ki xo kiyi sllh" mikewa tayi ta nufi toilet yace "Baki cire hijab din
ki ba" dawowa tayi ta cire Hijab din ta ajiye, ya bi ta da kallo har ta shiga
toilet din sai dai bata rufe kofar ba, mikewa yyi ya fita ya koma dakin sa. Lokaci
lokaci ya kan lekota, tausayinta kawai yake ba kadan ba barin yanda ya lura duk a
tsorace take, ana kiran sllh magrib ya shigo dakin bai ganta ba, kiranta ya shiga
yi amma shiru ya juya ya fita ya sauko downstairs, kitchen ya sameta tana wanke
d'an plates din da aka bata, ya tsaya bakin kofa yana kallonta, da sauri ta juyo a
tsorace, wara ido yayi yace "Uhum!" A hankali tace "washing nake yi" murmushi yayi
mata yana gyada mata kai, ta juya ta ci gaba da wanke plates din, yace "Me xa ki ci
for Supper?" Ta juyo tace "Supper?" Ya gyada mata kai yace "Yea dinner" ta d'an
langwabar da kai a hankali tace "na koshi" wara ido yayi yace "me kika ci?" juyawa
tayi ta ci gaba da wanke wankenta. Har ta gama yana tsaye bakin kofar, ta juyo tana
kallonsa, murmushi yayi mata ya fita daga kitchen din ta bi bayansa suka haura
sama, yace "Tafi kiyi sllh" kai ta gyada masa ta shiga dakin da take, shi ma ya
shiga nasa. Ana idar da sllh ya tafi siyo masu abinci, ajiye abincin yayi a parlor
bayan ya dawo ya xauna ya jinginar da kansa jikin kujera, can ya mike ya shiga
kitchen ya dauko plate ya dau take away daya ya juye ya sa spoon ya dau ruwa ya
tafi sama, xaune ya sameta bakin kofar dakin tana ganinsa ta mike tsaye, yace
"uhum!" a hankali tace "Tsoro nake ji" kallonta ya tsaya yi kafin ya shigo dakin ya
ajiye mata abincin hannunsa yace "Toh xo ki ci abinci" ta karaso ta xauna inda ya
ajiye mata abincin, bin sa da kallo tayi har ya fita sai dai bai rufe mata kofar
ba. Har xai shiga dakinsa ya tsaya ya kalli dakin Humainah, karasawa yayi ya bude
kofar, xaune ya ganta can karshen gado kanta hade da gwiwa, a hankali ya karasa
kusa da ita ya xauna yace "Still crying?" Mikewa tayi xata bar wajen ya fixgota ya
ce "Ina xa ki?" Ta fashe da kuka sosai, rungumeta yayi a hankali yace "Alryt am
sorry, kiyi hakuri... She's going tomorrow tun da baki so" boye fuskarta tayi
jikinsa tana kuka a hankali, yace "Toh ba nace kiyi hakuri gobe xata tafi ba"
muryarta na rawa tace "Toh wacece ita" dago kanta yayi yana kallonta, can yace "Ohk
I will tell who she is" janyeta yayi a jikinsa ya koma baya yana kallonta yace
"Amma fa it's a long story" sunkuyar da kanta tayi, nan ya fara bata labarin ynda
ya hadu da jasmine har xuwa wannan lokacin, kallonsa kawai take ko kiftawa bbu bata
kuma ce komai ba, ya lumshe ido ya bude yace "Tana regaining memorynta Idan Allah
ya yarda xa ta koma gun iyayenta, ita din abun tausayi ce, a yanxu bata da kowa sai
mu da muka taimaketa" dauke kai Humainah tayi, ya matso kusa da ita yace "Baki ce
komai ba" turo baki tayi tace "Toh ka kai ta gidansu El-ameen mana" murmushi yayi
yace "In tambaye ki" ta dago kai tana kallonsa, yace "wai kishi na kike Humainah?"
Hade rai tayi tace "Kamar ya? Sbda me xan yi kishin ka" yace "Toh me sa baki son ta
xauna nan?" Tabe baki tayi tace "Ta xauna mana ni ina ruwana, kawae abinda na sani
ka kai ni sch next week" murmushi yayi ya mike ya fita daga dakin, abinci ya dauko
mata ya ajiye dakin yace "Ga abinci!" Ko kallonsa bata yi ba ya fita daga dakin.
Karfe tara da wani abu ya mike daga kwancen da yake ya fita xuwa gun Jasmine, xaune
ya sameta bakin kofa tayi jigum, ya d'an bude ido yace "kina nan har yanxu" mikewa
tsaye tayi kamar xata yi kuka tace "Ni kadai xan yi bacci a nan?" Kallonta kawai
yake ya ga hawaye idonta, girgixa mata kai yayi yace "A'a ba ke kadai xaki kwana
ba, ina xuwa" daga haka ya fita ya shiga dakin Humainah, xaune ya sameta daure da
towel gaban madubi, hade rai tayi tace "Kaya xan sa" yace "Uhm did I hold you?"
Marairaice masa tayi tace "Ka fita plss" karasowa yayi kusa da ita ta mike da
sauri, ya d'an bude ido yace "what?" Kamar xata yi kuka tace "Ka fita plss" yace
"Alryt xan fita, amma abokiyar kwana xan kawo maki" kallonsa tayi da sauri tace
"Kamar ya?" Yace "ku kwana tare da yarinyar plss" da mamaki take kallonsa tace "Mu
kwana?" Matsowa yayi kusa da ita ta koma baya da sauri tace "Wayyo ya A jay ka fita
plss" ya langwabar da kai yace "Toh in kawo maki ita?" Gyada masa kai tayi da
sauri, yayi murmushi ya juya ya fita ta bi sa da kallo, tsaye ya samu Jasmine a
daki tana ganinsa ta nufesa da sauri ta juya masa baya tace "Cire min abun" kallon
Zip din kawai yake daga sama xuwa kasa na kusan minti daya, ta juyo a hankali tana
kallonsa, kifta ido yayi da sauri yace "Na'am" a hankali tace "Ban iya cirewa ba,
Mami da farida suke cire min" gyada mata kai ya shiga yi kamar kadangare, ta kuma
juya masa baya, yayi baya da sauri yace "Ohk Ohk mu je a cire maki nima ban iya ba"
daga haka ya nufi kofa ta bi bayansa, dakin Humainah ya shiga ita ma ta shiga,
kallonta kawai Humainah ke yi daga sama xuwa kasa gabanta na faduwa, karasawa
Jasmine tayi kusa da ita ta juya mata baya a hankali tace "ki cire mun abun" kallon
Junaid Humainah tayi, ya gyada mata kai yace "Help her wai bata iya ba" da kyar
Humainah ta daga hannu ta xuge mata Zip din, kokarin cire rigar ta shiga yi da
sauri Junaid ya juya har yana
buge kofa ya fita daga dakin, Jasmine ta kuma kallonta tace "Baki cire dayan ba"
Humainah ta balle mata bra din ta koma gaban madubi, bin ta da kallo Jasmine tayi
tace "Ina san inyi wanka" ko kallonta Humainah bata yi ba, Jasmine ta bi ta tace
"Xan yi wanka" ba tare da Humainah ta kalleta ba ta nuna mata kofar bathroom,
Jasmine ta nufi kofar ta bude ta shiga, a bude ta bar kofar, Humainah ta mike ta
koma gefen gado ta xauna xuciyarta na bugawa, har Jasmine ta fito daure da towel
dinta, ta gefen ido kawai Humainah ke kallonta, ta iso kusa da ita tace "cloth
dina" Humainah ta hade rai tace "ki saka wanda kika cire mana" "toh" kawai jasmine
tace ta tafi inda kayan da ta cire yake ta dauka ta sa ta kuma dawowa ta durkusa
kusa da ita tace "Sa min" xuge mata Zip din Humainah tayi ta kwanta abunta, jasmine
ta mike ganin ta kwanta ita ma ta kwanta nan kasa. Junaid na fitowa daga wanka ya
dau wayarsa dake ring ya ga El-ameen ne ke kiransa, dagawa yayi El-ameen yace
"Matar taka ta hakura dai koh?" Junaid yace "May be" El-ameen yace "Kasan me, bata
yarda fa ta kwana ita kadai ya xa ayi gashi amarci ku ke ci...." Junaid yace "Ko
kuma angwanci ba" El-ameen yace "Serious xata yi ta maku ihu ne cikin dare bata
yarda ta kwanta ita kadai" junaid yace "ta gaya min, tana dakin Humainah yanxu ma"
El-ameen yace "Ohk bata waya plss" Junaid yace "Kace mata me?" El-ameen yace "kai
dai ka bata" shiru junaid yayi can yace "Naji" katse wayar yayi hade da yin tsaki
ya saka jallabiyarsa ya fita daga dakin, da sallama ya tura kofar dakin Humainah ya
d'an bude ido ganin jasmine kwance a kasa ya karasa ya durkusa kusa da ita yace "Me
ya sa kika kwanta a nan" shiru tayi bata ce komai ba, ya kalli Humainah ya ga rufe
idonta ma tayi, jasmine ya kuma kallo yace "Tashi ki hau gado" mikewa tayi ya nuna
mata daya side din gadon ta xaga ta hau ta kwanta, a hankali ta matso kusa da
Humainah shi dai kallonta kawai yake, wayar hannunsa ne ya fara ring ya kalli
screen din, sai da ya kusa katsewa ya daga ya mika mata, karba tayi tana kallonsa
yace "Kiyi magana" wayar ta kai kunnenta tace "Na'am" El-ameen yace "Baki yi bacci
ba baby?" Ta kalli Junaid da ke kallonta ta sunkuyar da kai a hankali tace "Xan yi"
juyawa junaid yayi ya fice daga dakin, "Kin ci abinci kuwa" tambayar da El-ameen
yayi mata kenan ta gyada masa kai tace "Eh da afternoon ya bani wannan small rice
da miya, na ci kadan Saboda ba dadi sai ya xo ya bani a baki" shiru El-ameen yayi
bai ce komai ba, Humainah ta bude ido da sauri tana sauraren abinda take cewa
gabanta na faduwa, El-ameen ya sauke ajiyar xuciya yace "Da ya baki a bakin sai
kika ci?" Kai ta gyada masa tace "Eh da ya bani na ci, uncle he's kind, I like him
just like Abba" mijin Dr Sumayya kenan, katse wayar El-ameen yayi, Humainah ta
mike xaune xuciyarta na tafarfasa can ta mike ta fice daga dakin, da sauri Jasmine
ta mike ta bi bayanta ita ma, dakin Junaid Humainah ta shiga ta gansa tsaye yana
saka pyjamas dinsa, juyawa yayi yana kallonta ta xube wajen ta fashe da kuka sosai,
karasowa yayi kusa da ita ya durkusa gabanta da mamaki yace "Me ya faru?" Jasmine
ce ta shigo dakin ta karasa kusa da su a hankali ta durkusa ita ma tana kallon
yanda Humainah ke kuka.


*Haske Writers association*馃挕

Kar ku watsa min sand a ido my group members, ku kadai nake ma post da hannuna don
soyayya.
[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

47.....

Dago kanta junaid yayi yana kallonta ganin ta ki yin shiru yace "Ohh Pls ki gaya
min me ya faru mana, What happened?" Nan ma dai bata ce komai ba sai kuka, juyawa
yayi ya kalli Jasmine dake durkushe kusa da su ita ma ya ga hawaye idonta, mikewa
yayi ya fita xuwa dakin Humainah, a hankali Jasmine ta dawo kusa da ita cikin
sanyin murya tace "Sorry Anty" kallo daya Humainah tayi mata ta mike tana goge
hawayen da ya ki tsaya mata ta koma kan gado, junaid ya dawo dakin yana kallon
Humainah yace "Wai don Allah kukan kike haka har yanzu?, are you even okay?" Ta
hade rai ba tare da ta kallesa ba tace "Ni a nan xan kwana" daga haka tayi
kwanciyarta ta juya baya, kallonta kawai Junaid ke yi, can ya juya ya kalli Jasmine
da ke kallonta ita ma, karasawa yayi gun gadon a hankali ya xauna kusa da ita ya
kai fuskarsa kusa da nata murya can kasa yace "Haba Humainah, toh ita fa" bata
tanka sa ba sai rufe idonta da tayi, ya kamo hannunta cikin sanyin murya yace
"Humainah!" bude ido tayi ta wani hade rai tana kallonsa, ya marairaice mata yace
"Ita ina xata kwana mana" ta fixge hannunta tace "Oho!" Daga haka ta kuma juya masa
baya, ya kusa minti biyar yana kallonta kafin ya mike tsaye yana kallon Jasmine
dake ta kallonsu, duk tausayinta ya cika sa, a hankali ya isa kusa da ita yace
"Tashi mu je" mikewa tayi ita ma tana kallonsa ya fara tafiya ta bi bayansa, juyawa
Humainah tayi da sauri tana kallonsu har suka fita ya rufe kofar ta mike xaune ta
fara wani sabon kukan kai ka ce an mata mutuwa ne, dakin da Jasmine din take ya
shiga tana biye da shi, ya xauna gefen gado, jasmine ta iso kusa da shi ta xauna
kasa a hankali tana kallonsa tace "bata son in yi bacci da ita koh?" Girgixa mata
kai yayi da sauri yace "No! she's sick ne" gadon ya nuna mata yace "Taso ki kwanta
kiyi baccin ki" tace "Kai ma xa kayi bacci a nan?" shiru yayi bai ce komai ba ganin
yanda take kallonsa ya gyada mata kai yace "Eh! Zo ki kwanta" mikewa tayi ta hau
gadon ta kwanta, yana kallonta yace "kin iya addu'a ai koh?" Shiru tayi tana
kallonsa can kuma a hankali tace "Bismeeka Allahumma Amootu Wa Ahya" murmushi yayi
mata yana gyada kai yace "Jayyid! To yi baccin ki hakan ma yyi" tace "Kai baxa kayi
baccin ba" yace "Xan yi mana, amma sai na gama kallo" yana magana ne yana powering
tv, lumshe ido tayi ya d'an saci kallonta kafin ya maida dubansa kan tv, ya kusa
awa daya xaune dakin yana yi yana kallonta har ya lura baccin ta yayi nisa, ya
lumshe ido ya mike ya rufa mata duvet ya isa kofa ya bude a hankali ya fita ya bar
kofar bude, dakin sa ya shiga ya rufe, kwance ya same Humainah idonta rufe, ya
kashe wutan dakin ya karasa gadon ya kwanta. Kusa da ita ya dawo ya kamo hannunta
murya can kasa yace "Humainah?" Shiru bata amsa ba, ya kai bakinsa dai dai fuskarta
ya kuma kiranta a hankali, mirginawa tayi ta koma can karshen gadon ta juya masa
baya, ya d'an tabe baki yayi kwanciyarsa ya lumshe ido. Kafin asuba ya je duba
Jasmine ya fi sau biyar, yana dawowa daga masallaci bayan an idar da sllh ya shiga
dakin ya tada ta, mikewa xaune tayi tana mitsika ido yace "tashi kiyi sllh" gyada
masa kai tayi ta mike xata shiga toilet sai kuma ta juyo tace "Wanne?" Murmushi
yayi yace "Asuba" juyawa tayi ta shiga toilet din, ya fita daga dakin, xaune ya
tarda Humainah kan darduma, ya karaso ya xauna kusa da ita yana kallon yanda ta
hade rai, yayi murmushi yace "Ba gaisuwa" dauke kai tayi tace "Ina kwana" ya juyo
da fuskarta yana kallon idanuwanta da suka kumbura don kuka, ya langwabar da kai
yace "Su Abba sun hada ni da aiki...." Mikewa ta shiga kokarin yi ya mayar da ita
ta xauna ya kamo hannunta yace "Not until you tel me what ur problem is, jasmine or
what?" bude kofar dakin aka yi duk suka juya da sauri, jasmine ta shigo dakin ta
karaso inda suke ta duka kusa da junaid tana kallonsa tace "Nayi sallah, i want to
brush my teeth" ya kusa second ashirin yana kallonta, Humainah ta janye hannunta
daga nasa ta mike ta koma kan gado, gyada mata kai yayi da sauri yace "Alryt! Ohk"
ya mike ya shiga bathroom, toothpaste da toothbrush sabbi ya fito da ya mika mata
ta mike ta karba ta nufi kofa ya bita da kallo, har xata fita ta juyo tace "Xan yi
wanka ma" ya d'an bude ido sai kuma yace "Ohk Ohk" ya koma bathroom ya fito mata da
sabulu shower gel da sponge ya karasa ya mika mata ta karba tana kallonsa cikin
sanyin murya tace "Towel!" Juyawa yayi ya dauko mata towel dinsa ya dawo ya mika
mata ta karba sannan ta juya ta fita, ajiyar xuciya ya sauke ya juya yana kallon
Humainah da tayi kwanciyarta, karasawa gun gadon yayi yyi kwanciyarsa shi ma, tana
ganin haka ta mike ta nufi kofa ya bi ta da ido har ta fice daga dakin. Karfe
takwas da wani abu su fatima suka kawo breakfast, kamar jiya daga bakin kofar ya
tsaida su ya karbi abincin hannunsu, khadija ta marairaice masa tace "Ya A jay xamu
gaisa da Humainah mana" yace "Bacci take" Khadija ta turo baki ta juya haka ma
fatima ya kulle kofar. Dawowa cikin parlon yayi yana kallon jasmine dake xaune
kasan lallausan carpet din tsakar parlon, kusa da ita ya ajiye basket din abincin
ya tafi kitchen ya dauko cup da spoon da plates sae kayan tea ya dawo parlon, tea
ya fara hada mata, ita dai sai kallonsa take da sun hada ido xata sunkuyar da kai,
har ya gama ya ajiye mata tean gabanta ya dibar mata potatoe da kwai da plantain ya
ajiye mata yace "Gashi ki ci" girgixa masa kai tayi tace "Ni bana son milk" ya d'an
bude ido yace "Uhhn!" Ta gyada masa kai, mikewa yayi ya tafi kitchen ya dauko wani
cup din ya dawo ya hada mata Milo kadai ya ajiye mata, ta kalli potatoen gabanta a
hankali tace "Ketchup" wara ido yayi yace "Uhun!" Ta kallesa ya mata murmushi yace
"Tohm bari in je in siyo maki" daga haka ya rufe dankalin da tea ya mike ya tafi
sama ya dauko makullin mota ya sauko parlon yace "ko xa ki bi ni?" Shiru tayi sai
kuma tace "Ehh!" Komawa sama yayi ya dauko mata Hijab ta karba suka fita daga
parlon, tara da wani abu suka dawo gidan da ketchup din, ya sake hada mata wani
tean ya bata, kallon yanda take shan ketchup din yake yyi murmushi yace "You like
it" ba tare da ta kallesa ba tace "Yes!" wani shayin ya hada ya dau dankali da kwai
ya tafi sama, ya shiga dakin Humainah, xaune ya sameta kasan dakin ya karaso ya
ajiye mata abincin hannunsa ya xauna yace "Ga breakfast" bata ko juyo ba bare ta
kallesa, ya mike ya fita. Karfe sha daya da wani abu junaid na daki yana danna
laptop aka danna bell downstairs, mikewa yayi ya fito ya duba dakin Jasmine don
ganin ko ta tashi daga baccin da take yaga bata tashi ba, downstairs ya sauka ya
bude kofa, gabansa ne ya fadi ganin Hajiya da Umma sai Aysha kanwarsa da su Muhibba
da Suhaima, Hajiya na murmushi tace "Wannan kallo haka Ahmad ko mu koma ne" juyawa
yayi ya bar bakin kofar ya dawo parlor duk suka shigo, Ya xauna ya gaida su bbu
fara'a, duk suka amsa da yaken da bai kai ciki ba, Aysha ta gaida shi ya amsa ba
tare da ya kalleta ba, haka ma su Suhaima Umma tace "Toh ina amaryar ko bata tashi
ba" mikewa yayi ya haura sama, Hajiya ta saci kallon Umma, haka kawai gabansa ya
dinga faduwa ya jawo kofar dakin da jasmine take a hankali don kar ta tashi ya rufe
sannan ya shiga dakin Humainah, ganin idonta yasa jikinsa yayi sanyi, ya karasa
kusa da ita ya xauna a hankali yace "What's the meaning of this Humainah! Me na
maki kike ta kuka haka tun jiya, in dai yarinyar nan ne xata bar gidan soon" ko
kallonsa bata yi ba, ya shafa kansa yace "Toh yanxu haka xa ki fita su Hajiya su
ganki?" Jin taki cewa komai ya jawota jikinsa ta turasa ta fashe da kuka tace
"Allah ni ka kyaleni, dama ni ba sonka nake ba kai ma kuma baka sona...." Yace "Ohk
naji, fito ku gaisa da su Aysha" tace "Babu inda xan je" kallonta ya tsaya yyi,
tayi kwanciyarta, ya kusa minti biyar xaune sannan ya mike ya fita daga dakin yana
tunanin abinda xai ce masu har ya sauko parlor ya xauna, shafa kansa yayi yace
"Bacci take, bata jin dadi ne" Hajiya tace "Allahu Akbar, baiwar Allah abun ka da
rashin sabo" mikewa tayi tace "Bari inje dai in dubota" gabansa ne ya fadi sai dai
bai dago ya kalleta ba, Umma ma ta mike tace "Mu je kam Hajiya, in ya kama aje
asibiti ne sai a je" su Suhaima suka tashi wai su ma xa su, Hajiya tace "Kaji min
fitsararru ku je kuyi me" ita dai Aysha bata ce komai ba har suka haura sama,
Junaid ya ja tsaki ya mike ya fita xuwa balcony, Da sallama suka bude kofar suka
shigo Humainah ta mike xaune da sauri tana goge fuskarta ganinsu, Umma tace "Allahu
Akbar, sannu 'yar nan" Hajiya tace "Allah sarki, amma har da son jiki Humainah"
ita dai bata ce masu komai ba, Umma tace "Ya jikin?" Ta sunkuyar da kai tace "Da
sauki" Hajiya na kare ma dakin kallo ganin uban dukiyar da aka xuba tace "Wayyo
sannu 'yar nan, kowa sai da yayi wannan experience din" bata sake cewa komai ba nan
suka gama surutansu suka fita daga dakin ko Wanne da tunanin da yake a xuciya, sai
da suka sauko sannan Aysha ta tafi dakin ita ma, Humainah na ganinta ta fashe da
kuka, ta karasa da sauri tace "Meye haka Humainah" xaunawa kusa da ita tayi ta
rungumeta tana lallashinta amma kamar tunxurata take kuma yi, Aysha tace "Wai kukan
Meye haka kike?" Cikin kuka tace "Anty ni gida xan koma" Aysha ta d'an bude ido
tace "Saboda me?" Kin cewa komai tayi, Aysha tace "Toh ni bari in tashi in tafi
tunda baxa kiyi shirga ba" ta rikota da sauri tana kuka tace "Anty kin ga ya A jay
baya kulani sai wannan yarinyar da ya kawo..." Da mamaki Aysha tace "Wace yarinya?"
Tana goge fuskarta tace "ni ban san ta ba" da mamaki Aysha tace "tana ina?" Wasu
sabbin hawayen na xuba idonta tace "Tana dayan dakin" kallonta Aysha take da mugun
mamaki tace "Dayan dakin?" Humainah bata sake cewa komai ba ta hade kanta da gwiwa
tana kuka, da kyar Aysha ta mike ta fita ta bude dakinsa bbu kowa dakin dake kusa
da na Humainah ta dawo ta bude ta ganta kwance ta takure waje daya tana bacci,
jikinta yayi sanyi sosai ta karasa cikin dakin tana kallonta, juyawa tayi ta fita
daga dakin ta sauko downstairs, su Hajiya dake xaune sun
debo ma Kansu kayan flour daga kitchen suna ci suna hira suka bi ta da kallo har
ta fita, xaune taga junaid yana danna waya a balcony ta gansa, cikin sanyin murya
tace "Ya A Jay xa mu yi magana" sai da ya ga dama sannan ya daga kai ya kalleta
alamar yana ji, tace "Mu je daga can" tana fadin haka ta nufi parking space ya bi
ta da kallo kafin ya mike ya bi bayanta, da damuwa sosai tace "Ya Ahmad wacece
yarinyar nan?" Kallonta ya tsaya yi, can ya hade rai yace "Ina wasa da ke ne kike
questioning dina?" Tayi kasa da murya a hankali tace "Ba haka ba yayana, ni ban san
ka da irin haka ba, ka gaya min wacece ita kaga....." Yace "Allah xan bata maku rai
daga ke har Humainahn, akwai wanda yayi contributing lokacin da nake gina gidana
ne, ko a kanta yarinyar ke xaune?" Shiru Aysha tayi tana kallonsa da mugun mamaki
tana tunanin anya shi ne kuwa, yaushe ma yake kula matan bare har ya daukota ya
kawo ta gida, ko kadan bata kawo mahaukaciyar da ya kai gida kwanaki bace, kwafa
yayi xai bar wajen tayi saurin cewa "Amma yaya shekaranjiya fa ku ka tare, bbu
matar da xata samu nutsuwa....." Dawowa kusa da ita yayi fuskarsa daure yace "Allah
xan mare ki, kuma kika kuskura kika fitar min da sirrin gida bbu ni bbu ke" daga
haka ya juya ya bar ta wajen tsaye, jikinta yayi sanyi ba kadan ba lokaci daya ta
ji mugun tsanar jasmine har cikin ranta, da kyar ta bi bayansa xuciyarta na
tafarfasa ta shiga gidan, dakin Humainah ta koma ta xauna jiki ba kwari tace "Kiyi
hakuri kin ji Humainah ban san lokacin da Ya Ahmad ya sauya hali ba haka, ni baxan
iya cewa komai ba a nan amma in kinga xaki kira Mumy to ki kirata ki gaya mata ko
Abba, don bamu san ma'anar xaman yarinyar ba" bude kofa aka yi duk suka juya, ya
shigo ya nuna ma Aysha kofa, ta mike ta fita. Karasowa yayi kusa da gadon yana
kallon Humainah strictly yace "Idan kina son mu xauna lafiya to ki daina
interfering a kan duk abinda bai shafe ki ba, ki daina fitar min da sirrin gida,
xaman da kike daban a gidan nan haka ita ma yarinyar xaman da take daban, be
careful" daga haka ya juya ya fita daga dakin. Aysha bata sake shiga dakin Humainah
ba har suka bar gidan, su Hajiya na lura da mood din Aysha amma ba daman tambayar
me ya faru sai dai su ma plan din da suke daban a xuciyoyinsu.


*Haske Writers association*馃挕
[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

48.....

Sai kusan Azahar Jasmine ta tashi, tana ganin kofa rufe ta mike da sauri taje ta
bude, fitowa Junaid yayi daga bedroom dinsa jin budewar kofar,ya rungume hannayensa
yana kallonta, sunkuyar da kanta tayi, yace "Kin tashi" ta gyada masa kai ta koma
dakin, karasawa ciki yyi yace "Are you hungry?" Ta daga kai ta kallesa tace "ina
son in yi girki" yace "girki?" Ta gyada masa kai yace "Uhnn! Toh xo mu je kiyi" gun
kayanta ta nufa tace "in sa wani kayan" dariya ta basa ya bi ta da kallo har ta isa
gun jakarta ta bude ta fiddo wata yar top fari mara nauyi da wando mai kamar 3qtr
pink ta ajiye, xaro ido yayi yana kallonta, yaga ta fara kokarin cire doguwar rigar
kantin jikinta, da sauri ya juya ya fita daga dakin ya sauka downstairs, tana gama
canxa kayan ta dau net ta saka a kanta kamar yanda suke a gidan Dr Sumayya, ta fito
dakin ta sauko kasa, buda ido yayi yana kallonta har ta karaso inda yake, can ya
shafa kansa yace "No! Je Dauko hijab ki sa" shiru tayi bata ce komai ba, ya mata
murmushi yace "Yes, je ki dauko" ta juya ta koma sai ga ta ta dawo da hijab,
tausayinta kawai yake yanxu kam she don't know what's right or wrong kawai gata nan
gata nan ne, kitchen ya nufa ta bi bayansa, sai da suka shiga ya kalleta yace "Me
xa ki dafa?" Tayi shiru tana tunani can tace "Indomie and egg" yace "Ohk," ya fiddo
mata da indomie biyu, da kwai uku, kamar me naxari tace "Onion, pepper,
carrot....." Sai kuma tayi shiru idonta a kansa, murmushi yayi ya dauko mata ya
ajiye, ta kalli indomien tace "Ga nawa, ga naka, ina na wancan Antyn" ta fadi haka
tana nuna masa sama, shiru yayi bai ce komai ba, can ya dauko daya ya ajiye, kunna
gas tayi ta dau tukunya ta xuba ruwa ta daura tace "Haka koh?" ya jingina jikin
kofa ya rungume hannu yana kallonta, sosai yayi mamakin ganin yanda take hada
girkin sai dai tana yi tana tsayawa kamar me naxari, cikin few minutes ta dafa
indomien ta soya kwai ta xuba a plates uku duk ta sa fork, sai a sannan ta juya
tana kallonsa yayi murmushi a hankali yace "Woaw! Sannu da kokari" ta wara masa
manyan idonta tace "Uhm" kallonta kawai yake, ta sunkuyar da kai a hankali tace
"Yaushe Uncle xai xo?" Shiru yayi mata bai ce komai ba, ta matso kusa da shi tana
kallonsa tace "When uncle xai xo?" Hade rai yayi ya dau plate din indomie daya ya
mika mata yace "kai mata daki" ta karba tace "Ohk" sannan ta fita daga kitchen din
ya bi ta da kallo, sama ta tafi ta tura kofar dakin a hankali ta shiga, xaune ta
ganta kan darduma ta iso kusa da ita ta durkusa ta ajiye mata tace "Nayi girki"
wani kallo Humainah ta watsa mata ta mike tace "Fice min a daki!" Jasmine ta mike
tana kallonta, ta buga mata uban tsawa tace "Baxa ki dauka ki fita ba" dukawa
Jasmine tayi a hankali ta dau indomien ta fita, ta koma downstairs kallonta junaid
yake har ta karaso parlor ita ma tana kallonsa, hawaye ya gani idonta ya karba
indomien ya ajiye ya xauna, ita ma ta xauna ya ajiye abincin gabanta yace "Ci
abincin ki" ta goge hawayen idonta ta dau fork din a hankali ta fara cin indomien,
duk ya lura ci kawai take ba don tana son ci ba, duk tausayinta ya cika sa. Tashi
yayi ya tafi sama ya shiga dakinsa, wayarsa ya dauka ya ga mis calls din El-ameen,
ya ajiye wayar ya shiga toilet ya dauro alwala ya fito, har xai sauka downstairs
sai kuma ya shiga dakin Humainah, ya hade rai yace "Don ta kawo maki abinci shine
laifi har da yi mata tsawa?" Wani kallo tayi masa tace "Nayi, kar kuma ta sake xuwa
inda nake kaje can ku karata" tana fadin haka ta fashe da kuka, ya karaso cikin
dakin ya xauna kusa da ita yace "Haka kika ce?" Mikewa tayi xata bar wajen ya
fixgota ta fado kansa, ya dago kanta ya hade goshinsu yace "Maimaita words din ki"
yana ganin yanda kirjinta ke heaving, ya hade rai sosai yace "Maimaita nace" komawa
baya take son yi amma ta kasa don ba rikon wasa yayi mata ba, shi kansa ji yayi
xuciyarsa na bugawa, rufe ido tayi da kyar tace "Ni ka rabu dani, bana so...."
Murmushi yayi ya lumshe ido ya hade bakinsu..... Still yayi da farko har lokacin
bai bude ido ba haka ita ma, can ta fara turasa a tsorace, ya kwantar da ita a
hankali ya shiga kissing dinta, sosai ta tsorata sai dai ta kasa kwace bakinta, da
kyar ya saketa jin an tada sllh ya mike ya fita daga dakin, ta fashe da kuka ta
boye fuskarta cikin pillow, bedroom dinsa ya nufa shiga toilet. Bai iya ya fito
daga dakinsa ba sai da aka kira la'asar, ya sauko parlor don tafiya masallaci,
xaune ya ga jasmine kan carpet a parlor ta daura kanta kan kujera idonta lumshe a
haka, ya iso inda take ya d'an buga kujerar ta bude ido da sauri, murmushi ya mata
yace "me sa baki tafi daki ki kwanta ba" a hankali tace "Tsoro nake ji ni kadai" ya
durkusa kusa da ita yace "Tsoron me kike?" Kamar xata yi kuka tace "Nima ban sani
ba" shiru yayi yana kallonta, hawaye ya cika idonta cikin sanyin murya tace "Uncle
baxai xo ba?" Nan ma dai shiru yayi bai ce komai ba, sunkuyar da kai tayi ganin
haka, a hankali yace "Xai xo anjima, yanxu dai tashi ki shiga toilet ki yi alwala
ki xo kiyi sllh, kin ma yi na daxu?" Girgixa masa kai tayi, yace "Toh da kin ji an
kira sllh ki tafi kiyi alwala kiyi kin ji?" Ta gyada masa kai yace "Kin ma san me
ake cewa idan ana sllhn ma?" Ta gyada masa kai, yace "Wa ya koya maki?" Tace "Mami
da farida" yayi murmushi yace "Good tashi kije kiyi alwala sai kiyi na daxu da na
yanxu" tayi narai narai da ido tace "Ina jin tsoro a sama" ya nuna mata bayin dake
parlor yace "ae a can xaki je kiyi" mikewa tayi ta nufi toilet din, yace "Baki cire
hijab ba" dawowa tayi xata cire ya tuna abinda ke jikinta da sauri yace "A'a a'a
tafi kiyi haka kawai" ta juya ta tafi toilet din, sama ya koma ya dauko mata
darduma ya shimfida mata sannan ya fita jin an tada sllh. Ko da ya dawo ya tarar
bata idar ba ya xauna har ta gama, yana kallonta yace "kullum idan kinyi sllh ki yi
addu'a kice Allah ya baki lafiya kinji" shiru tayi tana kallonsa ya mata murmushi
yace "Kina jin yunwa?" Girgixa masa kai tayi yace toh bari in sa maki kallo, ta
gyada masa kai yayi powering din tv ya mike ya haura sama. Haka tayi ta xama a
parlon ita kadai har magrib, tana jin an kira sllh taje tayi alwala, ko da ya sauko
tafiya masallaci samunta yayi har ta fara sllh, yayi murmushi ya fita. yana dawowa
daga mosque ya ga motar El-ameen bakin gate yayi jim can ya juya xai shiga gate El-
ameen ya danna masa horn, dawowa yayi don bai yi tunanin yana ciki ba, ya bude
motar El-ameen yace "Why ain't you picking my cal?" Junaid ya daga kafada yace "Ban
ma san ka kira ba" El-ameen bai ce komai ba ya bude motar ya fito rike da leda
hannunsa, junaid ya nufi gate ya bi bayansa, sai da suka shiga gidan yace "Kasan
yanxu sai da izinin ka xan dinga shigo maka gida..." Junaid bai ce komai ba har
suka shiga parlor, jasmine dake xaune kan darduma tana ganin El-ameen ta mike da
sauri tana kallonsa ya wara mata ido yace "uhmm!" da gudu ta karaso ta rungumesa
tace "Uncle!" El-ameen ya d'an yi still, junaid kam hade rai yayi ya karasa shiga
parlon ya xauna, a hankali El-ameen ya janyeta jikinsa yana murmushi yace "How are
you" murya can kasa tace "am fyn, I missed you" gyada mata kai yayi ya nuna mata
Junaid yace "He's always there for you also" ta kalli Junaid tayi shiru bata ce
komai ba, kama hannunta El-ameen yayi suka karasa parlor ya xauna ita ma ta xauna,
kusa da kunnensa ta kai bakinta tace "In je in kawo jakan?" Dariya yayi yace "Na
me?" A hankali tace "Na cloth dina" yace "Wait tukun sai idan xa mu tafi" tace
"Toh" duk wannan abinda suke junaid kan tv ya maida hankalinsa. El-ameen ya jawo
ledan da ya shigo da ya bude ya dauko mata apple daya ya mika mata ta karba tace
"Na gode" gyada mata kai yayi har ta fara ci ta mike ta isa kusa da Junaid ta
durkusa tace "Uncle dina ya siya min apple xaka ci" ba tare da ya kalleta ba ya
girgixa mata kai ta mike ta koma gun El-ameen ta xauna, in da sabo El-ameen ya saba
da attitude din junaid, don haka bai damu da daure dauren fuskar da yake ba yace
"Ina madam din taka" ba tare da Junaid ya kallesa ba yace "Tana daki" ko rufe baki
bai yi ba sai ga ta ta sauko sanye da hijab dinta har kasa, tana ganinsu xaune
parlon ta dauke kai ta nufi kitchen El-ameen ya bi ta da kallo ta gefen ido hade da
tabe baki, Jasmine ta matso kusa da El-ameen a hankali murya can kasa kamar xata yi
kuka tace "I don't like her" murmushi El-ameen yayi murya can kasa shi ma yace
"Really! But why?" Cikin sanyin murya tace "She's mean!" Kallonsu kawai Junaid ke
yi ta gefen ido, El-ameen dake lura da haka ya saka dariya yace "Malam da kawai ka
juyo ka kallemu ka bar straining idonka" hade rai junaid yayi ya juya yana
kallonsa, can ya mike ya haura sama, jasmine ta bi sa da kallo sannan ta kalli El-
ameen tace "He's kind, I like him" El-ameen bai ce mata komai ba, Humainah ta fito
daga kitchen rike da cup din tea, El-ameen ya bi ta da kallo can dai yace "Ina yini
Humainah" ba tare da ta tsaya ba bare ta juyo tace "Lafiya lau" yayi murmushi yace
"Ohh baxa ki tsaya mu gaisa ba, toh d'an dawo muyi wata magana da ke" ta juya ta
kallesa yace "Minti uku kawai" fuskarta daure ta dawo parlon ta tsaya, yace "Toh
xauna mana" ta xauna kujera ba tare da ta kallesa ba, yace "Kiyi hakuri nasa an
kawo maki bakuwa may be ba da ixinin ki ba, ba dadewa xata yi ba gidan ki Idan
Allah ya yarda, matar da ke rike da ita ne tayi tafiya shi yasa ta xo taya ki xama,
Ina fatan kuma captain ya baki labarin ko wacece ita" Humainah bata ce komai ba ta
dauke kai, El-ameen yace "pls ki tausaya mata marainiya ce ita a yanxu dai, akwai
abubuwa da yawa da ta manta take bukatar a koya mata, plss help the innocent girl,
take her as ur sis sai Allah ya baki lada!" Hawaye ya ga ni idonta, ya juya ya
kalli Jasmine dake kallonsa yace "je ki kira min Captain" shiru tayi bata ce komai
ba, can a hankali tace "Captain!" Ya gyada mata kai, ta d'an bude ido tace "Sleep
Captain din nan?" Yace "Je kice masa ya xo" mikewa tayi ta tafi sama, El-ameen ya
kalli Humainah yace "Ke dai baki son ta xauna kawai
koh?" Ta goge idonta tace "Toh shine ni baxai kulani ba sai ita, komai yayi mata
ni baxai min ba" sai ta fashe da kuka, duk da ta ba El-ameen dariya don yasan har
da yarinta ya dai dake yace "Da gaske?" Cikin kuka tace "Ko da yaushe shi yake bata
abinci ni baxai bani ba, sai yaje yayi ta xama da ita ko ya shiga dakin da take"
shiru El-ameen yayi yana kallonta, can yace "Kiyi hakuri xan masa magana, but kema
ki dinga yi masa biyayya banda tsiwa in har kina son ku xauna lafiya kamar masoya,
in har kina masa haka ke ma xai dinga kyautata maki, baby kuma 'yan kwanaki xata yi
ta tafi" kai kawai ta gyada masa tana goge fuskarta.
[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

49.....

Jasmine na haurawa sama ta bude kofar dakin Junaid ta shiga, xaune yake yana game
da laptop, ya daga kai yana kallonta har ta karaso ta xauna kasa tana kallon game
din tace "Irin na Saif" son din Dr Sumayya, jin Junaid bai ce komai ba ta daga kai
tana kallonsa suka hada ido, sunkuyar da kai tayi, yace "Idan xaki shiga daki ki
fara yin sallamah a amsa maki sannan ki shigo kin ji" dago kai tayi tana kallonsa
da ganinta kasan bata gane abinda yake nufi ba, ya lumshe ido ya mike ya isa kusa
da kofa ta bi sa da kallo, yana rike da kofar yace "before coming in, sai kin fara
cewa Assalamu Alaikum, idan kika ji ance Wa'alaikis salam, sai ki shigo" shiru tayi
tana kallonsa still, ya dawo dakin ya xauna yace "Say Assalamu alaikum!" Sunkuyar
da kai tayi a hankali ta fadi, yace "Good, sai kinji ance maki wa'alaiki assalam
sai ki shigo, tashi kije ki fadi in ji" mikewa tayi ta koma gun kofar ta tsaya a
hankali tayi sallaman, girgixa mata kai yayi yace "No! Waje xaki ki tsaya ba nan
ba" ta bude kofar ta fita tayi sallaman, ya amsa ta shigo kanta a kasa, kallonta
kawai yake har ta iso inda yake bata dago ba, hawaye ya gani idonta, yace "Ohh kuka
kike?" Bata ce komai ba kuma bata dago ba, ya d'an tabe baki yace "uncle din naki
ya tafi kenan?" Ta girgixa masa kai hawaye na gangarowa daga idonta tace "Yace in
kira Captain" kallonta kawai yake, cikin sanyin murya yace "Xauna" ta xauna kasa,
yace "Kukan me kike?" Girgixa masa kai tayi bata ce komai ba, xai yi magana wayarsa
ya soma ring, dauka yayi ya ga El-ameen ke kiransa ya ajiye wayar ya mike ya fita
ta bi sa da kallo can ita ma ta mike ta bi bayansa. Tun daga stairs El-ameen ke
kallonsa har ya sauko, ita dai Humainah kanta na kasa, Yana daga tsaye yace "Ya aka
yi?" El-ameen yace "Am going" Junaid yace "Allah ya kiyaye hanya" jasmine na jin
El-ameen yace going ta dawo kusa da shi da sauri ta durkusa tace "Uncle bag dina
yana daki" ya langwabar da kai yace "Mami ai bata dawo ba baby, amma tace gobe xata
dawo sai goben in xo in dauke ki koh" wani kuka ta fashe da tana kallonsa tace
"Nooo" da mamaki yake kallonta ganin irin kukan da take, ta mike ta xauna kusa da
shi ta kamo hannunsa tana kuka tace "Dont leave me plss Uncle, take me with you" ya
girgixa mata kai yace "Toh ina xan kai ki baby mami bata nan, she's coming back
tomorrow sai in xo in dauke ki" ta fashe da matsanancin kuka har da bubbuga kafa
tace "Nooo!" juyawa junaid yayi xai koma sama El-ameen da ya ma rasa me xai ce mata
yace "Dalla kai kuma meye haka Ahmad magana xa muyi" junaid ya wani hade rai yace
"Ka fadi abinda xaka fadi mana" mikewa Jasmine tayi tana kuka har lokacin tace "I
want to go and bring my bag..." El-ameen ya hade rai yace "I will flog you fa,"
cikin kuka tace "Nooo!" Humainah dai sai kallon ikon Allah take, El-ameen ya mike
yace "You are telling me no koh, bari in nemo bulala yanxu, I will so flog you"
dawowa kusa da shi tayi da sauri tana kuka tace "Plsss" ya nuna mata kujera yace
"Toh xauna kar in mare ki yanxu, ki rufe min baki kuma" xaunawa tayi tana kokarin
hadiye kukan, ya kalli junaid yace "Mu je" daga haka ya dau makullin motarsa da
waya ya nufi kofa, ta mike da sauri ta fashe da wani sabon kukan tace "Uncle" ya
hade rai yana kallonta yace "Koma ki xauna" komawa tayi ta xauna ya fita daga
parlon, Junaid ya tabe baki ya bi bayansa, mikewa Humainah tayi ta haura sama,
Jasmine ta dinga rusa kuka iya karfinta, sai da suka isa gun mota El-ameen yace
"look junaid ka rage shige ma yarinyar nan tunda matar ka bata so, beside bai ma
kamata ka fiffita ta kan matar ka ba, duka duka yaushe aka yi auren har xaka dinga
shiga hakkinta haka, kawai yanxu a samo tsohuwar da xata dinga mata duk wasu
abubuwan xai fi....." Katse sa Junaid yayi yana masa wani kallo yace "Abinda nayi
niyyar yi kenan or you take her out from my house tunda yanxu kam kafi kowa son
kula da ita da nema mata lafiya on like lokacin da take kan bola, ni sai in cire
hannu ma in bar ka da ita tunda na mata mai wuyar, you can take her to wherever you
wish for all I care Ahmad" daga haka ya juya ya bar wajen, El-ameen ya bi sa da
kallon mamaki har ya shige gate ya kulle, juyawa yayi xuciyarsa na tafarfasa ya
shiga motarsa ya bar layin. Ko da Junaid ya shigo parlon samunta yayi tana ta rusa
kuka, ko kallonta bai yi ba ya haura sama. Har magrib Jasmine na parlon tana kuka,
ya sauko ya fita xuwa masallaci ba tare da ya kalleta ba, sai da Humainah taji
fitarsa sannan ta sauko parlon, daga bakin stairs ta tsaya ta dake tace "Xo mu tafi
sama" ko kallonta Jasmine bata yi ba, ta karaso cikin parlon tace "Mu je" Jasmine
tace "Am not going" juyawa Humainah tayi ta koma sama abun ta. Bakwai da wani abu
Junaid ya shigo parlon rike da leda a hannunsa, ajiye ledan yayi yana kallon
jasmine yace "Je dauko jakar taki in kai ki gun sa" kallonsa tayi kamar bata gane
me yace ba, ya hade rai yace "I said go and bring your bag" mikewa tayi tana goge
idonta ta tafi sama, ba a dau lokaci ba ta sauko rike da jakar tana kallonsa tace
"Ban ga daya takalmin ba" kallonta kawai yake, ya dake yace "Ina xan kai ki?" Tace
"Wajen uncle" yace "Toh mu je" kofa ta nufa tana cewa "Na bar ma Antyn nan daya
takalmin" ya bi ta da ido har ta bude kofa xata fita yace "Kehh!" Juyowa tayi tana
kallonsa ya karasa inda take tsaye ya hade rai yace "Daga yau kika sake kira min
uncle a gidan nn sai na baki mari" kallonsa take irin bata gane ba din nan, ya duka
dai dai fuskarta yace "From henceforth, I mean from now on kar ki sake kiran uncle
a gidan nan" fixge jakar yayi ya jefar parlor ya kamo hannunta ya shigo da ita ya
rufe kofar ya saketa ya haura sama. Xube wa wajen tayi ta dinga rusa kuka har da
shessheka, tana nan xaune ya sauko xai tafi masallaci yin isha, bai ko kalleta ba
ya fita daga parlon, ko da ya dawo kitchen ya shiga ya dauko plate ya debi abincin
da ya siyo daxu ya haura sama ya shiga dakinsa, bai iya ya ci abincin ba ya ajiye
kawai ya koma kan gado ya kwanta duk ya rasa me ke masa dadi, tv ya kunna shi ma
haka ya dinga kallon absentminded, bude kofar dakin aka yi Humainah ta shigo, ta
tsaya daga kusa da gadon tace "Ka bani waya xan kira Abbana" ba tare da ya kalleta
ba yace "ban da kati" kallonsa ta tsaya yi, can ta juya ta fice. Lumshe ido yayi ya
bude ya dau wayar ya shiga kiran El-ameen, El-ameen dake kwance daki yana danna
waya ya tsura ma sunan dake kan screen din ido har ya katse, aka kuma bugowa nan ma
har ya katse bai daga ba, bayan kusan minti biyu text ya shigo masa, bude content
din yayi ya karanta kamar haka "Just want to say am sorry, i get I wasn't suppose
to, but I dunno whatever happened wasn't right, am just trying to say sorry....."
Screen d'in ya tsurawa ido har ya gama karanta text d'in snn ya ajiye wayar, indai
Ahmad ne ya saba da halinshi na idc attitude, ajiye wayar yayi yaci gaba da abinda
yakeyi, K'arfe take as Junaid ya fito, d'akin Humainah ya leqa yaga bata nan da
alama toilet ta shiga, jan k'ofar yayi ya maida ya rufe ya sauk'o, kwance take
k'asan tiles har ta gaji da kukan bacci ya soma d'aukarta, dab da ita ya k'araso ya
k'urawa kyakkyawan fuskarta ido da Lashes d'inta suka kwanto kamar tayi fixing,
sosai jikinshi yayi sanyi ganin har lokacin da d'an siririn hawaye shimfid'e a
fuskan, a hankali yayi tapping jakarta da janyo ta mak'ale kamar wacce za a kwacewa
yace "Jewel", a hankali ta bud'e idonta tana kallonshi, ya sunkuyo daidai fuskarta
yace "Wake up", sai lokacin ta tashi da sauri tana k'are mishi kallo kamar yanzu ta
soma ganinshi, tana son furta Uncle amma tana tsoro dan yayi warning d'inta da kada
ta sake k'ira mishi wani Uncle, a hankali bakinta ke twitching hawaye na dad'a
gangarowa idonta, ido ya rintse kawai ya kamo hannunta tareda janyota jikinshi ya
rungume, ba shi ba har ita k'irjinta bugawa yakeyi, ido ta lumshe tana sauk'e
ajjyar zuciya, cikin wata iriyar murya yace "am sorry Jasmine", itadai shiru kawai
tayi tana sauraronshi, a hankali ya janyeta daga jikinshi ya d'ago hab'arta yace
"am sorry okay?", yasa hannu ya share mata hawayen dake fuskarta, gaba d'ayanta
yarinyar tausayi take bashi, mik'ewa yayi tareda kamo hannunta ya tayar da ita yace
"Kinyi Sallah?", kai ta girgiza mishi yace "kiyi min magana, don't nod", a hankali
tace "banyi ba", yace "Shiga kiyi alwala, I will b here waiting for you", ba musu
tayi hanyan toilet d'in dake palo, saida taje bakin k'ofa snn ta sake juyowa taga
ita yake kallo kamin ta shige toilet d'in, yana zaune ta fito ta d'auki hijab
d'inta dake gefe ta saka, har ta idar da Sallah idonshi na kanta yana observing
yanda take Sallahn, ta d'an jima zaune bayan ta idar snn ta kalleshi tace "Av
prayed, nace Allah ya bani lafiya", kai ya kad'a yace "that's good, kullum ki dinga
yin haka kinji?", tace "toh", ya mik'e yana maida wayarshi aljihu yace "zaki
rakani?", kallonshi ta tsaya yi da manyan idonta kamar batasan mey yace ba saida
yayi murmushi snn yace "I mean would you like to go out with me?" Har zatayi
nodding kanta tayi maza tace "Toh", yace "Good saka Hijabinki mu tafi", tana gama
sawa ta dubeshi da manyan milky eyes d'inta tace "Shoe d'ina ban ganshi ba kuma
nace na barwa waccan Aunty", kallonta yayi kawai yace "muje, we will buy another
one", lokaci lokaci yake juyowa ya kalleta yana driving, itakam kanta ta jingina
jikin glass tana ta kallon garin, a Jifatu yayi parking, ce mata yayi ta zauna ta
jirashi ya shiga ya gama siyayyan da zaiyi snn ya fito, takalmin da ya mik'a mata
ta saka tana jin dad'i snn ya wuce dasu Royal Joint, a nan yayi musu order abinci
suka wuce gida, hannunshi riqe da abincin da ya siyo ita kuma riqe da na shoe d'in
da ya siya matan, suna shigowa gida daidai nan Humainah na sauk'owa kan bene, wani
irin fad'uwa, da murna Jasmine ta kalli ledan shoes dake hannunta snn ta kalli
Humainah dake tsaye tace "Aunty kinga new Shoe d'ina da wannan Uncle d'in ya bani,
he is nice, kema kice mishi kinaso ya baki", Humainah dake tsaye gabanta na bugawa
juyawa tayi ta koma d'aki, Jasmine
ganin ta tafi yasa ta juyo da kallonta ga Junaid da yake kallon inda Humainah
tabi, tace "Aunty nan ma A siya mata irin shoe d'ina", kallonta kawai yayi yace
"Jeki d'auko plate", ledan da yake hannunta ta ajiye tayi kitchen, zaune ta tarar
dashi yana danna waya, d'agowa yayi ya dubeta ganin ta tsaya mishi a ka yace "Sit
down and serve yourself the food", zama tayi ta janyo leda d'aya ta bud'e ta shiga
zuba fried rice d'in a plate ta fara ci, tashi yayi ya d'auki d'ayan ledan ya haura
sama dashi, d'akin Humainah ya tura duk wutan d'akin kashe yake, kunnawa yayi ya
k'arasa shigowa, a tsakiyan gadon ya ganta kwance ta dunqule waje d'aya, zama yayi
bakin gadon bayan ya ajiye ledan hannunshi, sau biyu yana k'iranta yajita shiru, a
hankali ya d'agota dan yasan ba bacci take ba, fuskarta da ya kumbura dan kuka ya
k'urawa ido , hannu yasa ya shafi hawayen yana murzawa da d'an yatsanshi yace
"Sana'ar da kika samu kenan yanzu?", turashi ta shiga yi daga jikinta, firmly ya
riqeta, ganin ta kasa kwace kanta yasa ta fashewa da wani irin kuka tana sulalewa
k'asa tace "ni ka sakeni ka fitamin daga d'aki", har ranshi yakejin kukan nata,
d'agota ya sakeyi yace "Humainah mey ke damunki wai for crying out Loud?, me kike
so?", shiru tayi mishi taqi cewa komai tana ci gaba da kukan, a hankali ta d'ago
tana share hawayenta tace "Ka maidani gidanmu, inason ganin Abba na", wani irin
kallo ya bita dashi


*Haske Writers association*馃挕
[16/12, 00:57] Hussaini Atk: � *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

50.....

Washe gari ma kamar jiya haka suka wuni gidan, yana zaune d'akin Humainah da tayi
kamar batasan da zamanshi ba,
Mikewa yayi ya fita daga dakin ya koma nasa, yana danna wayarsa yaji kamar ana
sallama bakin kofa, tashi yayi ya isa gun kofar ya bude ya ganta tsaye, a hankali
tace "Nace Assalamu Alaikum!" D'an murmushi yayi yace "Gud! Ya aka yi?" Shiru tayi
bata ce komai ba, yace "Kin gama cin abincin?" Gyada masa kai tayi yace "toh mu je"
fitowa yayi daga dakin ya shiga wanda take ta bi bayansa, ya xauna gefen gado ta
karaso ita ma ta xauna daga kasa inda yake, yace "No dawo ki kwanta kiyi bacci"
tace "I've not bathed" mikewa yayi ya shiga toilet ya hada mata ruwa ya fito yace
"Toh tafi kiyi" ta mike ta cire hijab ta shiga toilet din ya bi ta da kallo, fita
yayi daga dakin jin kamar wayarsa na kara ya shiga nasa dakin, 1st love ya gani
jikin screen din, ya dau wayar ya xauna sannan yayi picking hade da yin sallama,
Mumy ta amsa ya gaisheta ba tare da ta amsa ba tace "Ina Humainah" kallon kofa yayi
yace "tana daki Mumy" Mumy tace "Aysha tace kuka kawai yake?" Ya d'an bude ido yace
"Mumy ai kinsan yanda take behaving ni ban san me ke damunta ba" Mumy tace "Kai
mata wayar" yace "Toh, xan kira idan na kai mata" daga haka ya katse wayar, da kyar
ya mike gabansa na faduwa ya fita daga dakin ya shiga nasa, kwance ya sameta ta
lullube gaba daya da bargo, ya karasa ya xauna kusa da ita ya yaye bargon yace
"Humainah ga Mumy" kin bude ido tayi ya dagota ta buge masa hannu tana turasa, yace
"Mumy ce xata maki magana" tana bude idon hawaye suka biyo baya, ta fada jikinsa
tana kuka a hankali, rasa me xai ce mata yayi, ya dago kanta yana kallon fuskarta,
murya can kasa yace "Humainah!" Kallonsa tayi bata ce komai ba hawaye na bin
kuncinta, wayarsa ne ya soma ringing ya dauka yana kallon Screen din, can ya
kalleta yace "Mumy xata yi magana da ke, plss ki bar kukan nan" bata ce komai ba ya
d'aga ya kai mata kunnenta, daga daya bangaren Mumy tace "Humainah!" A hankali tace
"Na'am, ina yini Mumy" Mumy ta amsa tace "What's wrong with you kike kuka har
yanxu?" Wasu hawayen ne suka xubo mata tace "Ba komai Mumy" Mumy tace "Ba komai
kuma? Haka kawai kike kuka?" Shiru tayi bata ce komai ba, Mumy tace "Toh xan xo
gobe" a hankali tace "Toh!" Mumy ta katse wayar, ya dago kanta da sauri yace "What
did she say?" Komawa tayi ta kwanta tace "Nothing" ya dawo kusa da ita yace "Karya
kike" k'in ce masa komai tayi, ya dagota yace "Baxa ki gaya min ba" turasa tayi
tace "Let me" jawota jikinsa yayi yace "Ae sai kin gaya min" ta hade rai tace "Stop
this, bana so" kallon bakinta kawai yake, ta fara kokarin sauka ya rikota, cike da
masifa ta buge masa hannu xata yi magana ya dago kanta sai jin bakinsa cikin nata
tayi, buda ido tayi tana kokarin turasa ta kasa ya kwantar da ita ya lumshe ido,
tsorata tayi ganin ya fara wuce limit, lokaci daya ya kawar mata da tsoron ta sakar
masa jiki kamar ba ita ba, yanda ya kwantar da kai ka rantse kace ba captain Junaid
ba, murda kofar dakin aka yi, ya saketa da sauri ya koma baya ita kuma ta shige
cikin bargo, Jasmine ce ta shigo dakin da hijab sai towel dake jikinta, kamar xata
yi kuka tana kallonsa tace "Ni banga bag din kayana ba" kallonta kawai yake da
rinannun idonsa, shiru tayi ita ma tana kallonsa, juyawa tayi ta fita ta tsaya daga
bakin kofa a hankali tace "Assalamu Alaikum!" Lumshe ido yayi ya bude yana shafa
kansa bai ce komai ba, sallaman ta kuma yi kamar xata yi kuka, amsawa yayi fuskarsa
daure, ta shigo ta tsaya daga bakin kofa, sai dai ta kasa cewa komai ganin yanda ya
tamke fuska, kallonta yayi yace "From now on idan kika sake shiga waje ba sallama I
will slap you" hawaye ne ya cika idonta ta gyada masa kai ta juya a hankali ta
fita, juyawa yayi yana kallon Humainah da tayi lamo cikin bargo, ya shafa kansa ya
mike ya fita daga dakin ya shiga nasa, wanka ya shiga yayi, ya dauro alwala ya fito
ya saka jallabiyarsa yayi shafa'i da wutr, yana xaune kan darduma har Karfe sha
daya can ya mike ya fita daga dakin, tsaye yayi bakin kofa yana kallon dakin da
Jasmine take don kofar a bude yake, ya karasa ya shiga dakin, kwance ya ganta daga
gefe kusa da bakin kofar tana bacci har lokacin Hijab da towel ne jikinta,
durkusawa yayi kusa da ita yana kallon fuskarta, ya lumshe ido ya bude murya can
kasa yace "Jasmine" ganin bata motsa ba ya mike ya fita daga dakin ya sauka parlor
ya dauko mata jakar kayanta ya dawo sama, ajiye jakar yayi ya bude ya fiddo mata
doguwar riga ja mara nauyi, kiranta ya kuma yi a hankali bata tashi ba, ya d'an
buga kafadar ta ta mike xaune da sauri tana mitsika ido tace "Uncle!" Ganinsa yasa
tayi saurin cewa "Captain!" Bai ce komai ba ya mika mata rigar hannunsa yace "Tashi
ki sa kayan ki" karban kayan tayi yana kallonta ta cire hijab din jikinta ta mike,
dauke idonsa yayi daga kallon nata a nan wajen ta saka kayan da ya bata, ta dawo
kusa da shi tace "Na sa" mikewa yayi ba tare da ya kalleta ba still ya nufi gado ya
ce "Xo ki kwanta" tace "Kai ma xaka yi bacci nan koh?" Yace "Eh" karasowa tayi ta
hau gadon ta kwanta har da matsa masa, lulluba mata bargo yayi ya xauna gefen gadon
ya kunna Tv yace "Sai na gama kallo xan kwanta" har sha biyu bai ga alamar xata yi
bacci ba, ya kalleta yace "Sleep mana" tace "Sleep captain" murmushi yayi ya gyada
mata kai yace "Ke ki fara yi sai nima in yi" lumshe idonta tayi ya tsura mata ido
yana kallo, bata sake bude idon ba kuma har daya saura, ya mike a hankali ya kashe
Tvn, ya fita daga dakin ya bar kofar a bude ya shiga nasa dakin, kasa bacci yayi
sai juye juye yake ya rasa dalili, daga baya dai ya gano dalilin ya kawar da shi
daga ransa yayi forcing kansa yayi bacci. Washegari Monday yaji da ma kawai yayi
resuming aiki duk da hutun sati biyu ya dauka but sbda Jasmine yasa bai yi haka ba,
yana dawowa daga masallaci ya shiga dakin Humainah ya ganta xaune kan darduma,
juyawa yayi ya fita dakin ya shiga wanda Jasmine take, har lokacin ya ga bata tashi
ba, dukawa yayi dai dai fuskarta yace "Jasmine" ta bude ido da sauri mikewa yayi
yace "Tashi kiyi sallah" ta gyada masa kai ta sauka daga kan gadon ta nufi toilet.
Ya juya ya fita daga dakin. Karfe takwas saura Humainah ta fito ta sauka downstairs
ta shiga kitchen, tsaye tayi tana tunanin abinda xata hada for breakfast, can dai
ta fiddo Irish ta fara ferewa, ko da junaid ya sauko don siyo masu breakfast yayi
mamakin ganinta a kitchen, ya tsaya daga bakin kofar kitchen yana kallonta, yace
"Gud morning" ba tare da ta kallesa ba tace "Ina kwana" murmushi yayi ya juya ya
fita daga kitchen din. Yana xauna parlo Jasmine ta sauko da alamar tayi wanka don
ta canxa kayan jikinta, kusa da shi ta durkusa tana kallonsa cikin sanyin murya
tace "Nayi wanka" ya gyada mata kai yana nuna mata kitchen yace "Tafi ki gaisheta
ki taya ta aiki" tace "Toh" sannan ta mike ta nufi kitchen din ya bi ta da kallo
ganin yanda take tafiya. Kallo daya Humainah tayi mata ta dauke Kai, ta karasa kusa
da ita ta durkusa a hankali tace "Ina kwana" ba tare da ta kalleta ba tace "Lafiya
lau" shiru Jasmine tayi can kuma tace "I want to help you" mika mata wukar Humainah
tayi ta ta tafi gun gas xata kunna, jasmine ta dau dankalin daya ta rasa yanda
xata fara fere shi, kallon Humainah dake kokarin dauko mai tayi sannan ta fara fere
dankalin ihu ta fasa ta jefar da wukan jin wani xafi da ya ratsa taMikewa Junaid
dake xaune parlor yayi yana kallon kofar kitchen din jin Ihun, Humainah ta ajiye
man hannunta ta taho da sauri tana kallonta tace "Dama baki iya ba....." Jasmine ta
fashe da kuka q rikice tana yarfe hannu ganin jini a hannunta, Shigowa kitchen din
junaid yayi ya hade rai yana kallon Humainah, hade ran ita ma tayi ta juya ta koma
ta ci gaba da aikinta, Jasmine ta karasa kusa da shi tana kuka tace "Captain kaga
blood din" kama hannunta yayi suka fita daga kitchen din Humainah ta bi su da kallo
ta gefen ido. Sama ya tafi da ita xuwa dakinsa ya sa ta xauna bakin gado ya dauko
tissue yana goge mata jinin dake ta xuba, ganin yanda take kuka yasa yace "Sorry!"
Ta fashe da wani sabon kukan tace "It's paining me" kallon yatsan nata yake, ido ya
lumshe a hankali ya sunkuyo dai dai kan yatsan yana hura mata iska, itama lusmshe
idon tayi tana jin d'umin iskar da yake hura mata, har ya d'ago idonta na a lumshe,
cute face d'inta da eye lashes d'inta ke kwance ya k'urawa ido, a hankali itama ta
bud'e manyan idanunta ta sauk'e kan face d'inshi, cikin wani irin murya yace "Does
it still hurt?", a hankali ta gyad'a mishi kai, spirit d'in da ya saka jikin wool
d'in ya d'auko yasa mata kan yatsan, ido ta rintse ta saki k'ara tareda k'ank'ame
mishi hannu tana haawaye.


*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

51.....

Sake mata hannun yayi yana kallonta ganin yanda take kuka, ta girgixa masa kai tace
"Bana so" ajiye Cotton wool din yayi yace "Ita ta yanka ki?" Girgixa masa kai ta
kuma yi tana hawaye tace "Knife ta bani" bai kuma cewa komai ba ya mike xai fita,
tace "Ka kira min uncle ya xo" juyawa yayi ya kalleta, tana hawaye tace "Call me
Uncle" wani kallo ya mata ya fice daga dakin. Haka tayi ta xama ita kadai tana kuka
tana yarfe hannu, da ta ga jinin ya fara xuba sai ta goge jikin farin bedsheet din,
gajiya tayi da xaman ta mike ta fita daga dakin har lokacin tana hawaye, dakin da
take ta shiga ta kwanta. Karfe tara Humainah ta shigo dakin rike da cup din tea da
plate din potatoe da kwai ta ajiye mata, Jasmine ta mike da sauri tana kallonta da
idonta da suka rine don kuka tace "Anty ki kira min uncle" tsayawa kallonta
Humainah tayi, sai da ta sake maimaitawa sannan tace "Waye Uncle?" Jasmine ta goge
hawayen idonta tace "Wannan uncle din nan nawa da ya tafi" shiru Humainah tayi can
dai tace "Ohk" ta juya ta fita ta shiga dakin Junaid, wayarsa ta dauka ta fito ta
dawo dakin da Jasmine take, number El-ameen ta dinga nema a wayar amma bata san da
sunan da ya sa ba, call log ta shiga tana dubawa taga wani number da yasa My best,
dialing tayi tana sa ran shi ne, bugu uku aka daga, daga daya bangaren El-ameen
yace "ya?" Mika ma Jasmine wayar Humainah tayi, Jasmine ta karba tana kallon wayar,
Humainah tace "Ki sa a kunne" Kai wa kunne tayi ta ji muryar El-ameen yana cewa
"Captain" ta d'an bude ido tace "Uncle!" Shiru El-ameen yayi kafin a hankali yace
"Baby" fashe wa da kuka tayi ya mike xaune daga kwancen da yake yace "Me ya faru
baby" tana shessheka tace "I've hurt my self" yace "Where?" Tana kallon yatsan ta
tace "My finger" yace "With what?" Ta kalli Humainah da ke ta kallonta tace "Knife"
shiru yayi sannan a hankali yace "Sorry, an baki magani?" Ta girgixa masa kai tace
"No, and it still hurt" yace "Ina Captain din?" Ta goge hawayen idonta tace "I
don't know" yace "Toh wa ya baki waya?" Ta kalli Humainah tace "That Anty" yace
"Where is she?" Pointing dinta tayi kamar yana gani tace "she's here" yace "Toh
bata phone din" mikewa tayi ta mika ma Humainah wayar ta karba, El-ameen yace "Kin
tashi lafiya?" Humainah tace "Alhmdllh" yace "Wai yankewa tayi?" Ta kalli Jasmine
tace "Eh ta yanke ne" yace "Da girma wajen?" Ta kuma kallonta tace "Not dat deep
amma jinin bai tsaya ba" El-ameen yace "Toh xan xo" daga haka ya katse wayar
Humainah ta juya ta fita daga dakin, Jasmine ta fashe da kuka ganin hakan ta dinga
rerawa. Goma saura El-ameen ya shigo gidan, junaid dake xaune balcony tun bayan
fitarsa dakinsa ya dinga kallonsa har ya karaso balconyn, El-ameen ya ja kujera ya
xauna yace "Next week xaka yi resume kenan" ba tare da Junaid ya kallesa ba yace
"Seem so" El-ameen ya shafa kansa yace "Ashe baby yankewa tayi wai" kallonsa Junaid
yayi da sauri, can ya kauda kai yace "Who's dat?" El-ameen yace "Ka fi ni saninta
ai" junaid yace "Tun safe nake nan so I don't know" El-ameen yace "Ohk, can I go
in?" Junaid yace "Da can tambayata kake idan xaka shiga?" Shiru El-ameen yayi bai
ce komai ba, can ya fito da wayarsa sai kuma ya tuna bai da number Humainah, number
Junaid din yayi dialing, Humainah dake ta masa dube dube a wayan dake cike da texts
din mata yafi 50 a ciki sai dai duk bata ga wanda yake reply ba, whtspp ma haka sai
dai yayi reply da sure! yeah! Lol! Ita dariya ma abun ya dinga bata, tana d'aga
kiran El-ameen yace "Humainah bring her out ina waje" Humainah tace "Ohk" ta katse
wayar ta ajiye ta fita ta shiga dakin Jasmine din, kwance ta ganta inda ta barta
bacci ya dauketa, karasawa tayi ta shiga tashinta, Jasmine ta bude ido a hankali
tana kallonta, Humainah tace "Uncle din ya xo" mikewa tayi da sauri daga kan gadon
tana kallonta, Humainah tace "Yana waje" kofa ta nufa Humainah ta bi ta da kallo
har ta fita, kalle kallen parlor ta shiga yi bata gansa ba, hakan yasa ta nufi
balcony kamar xata yi kuka, ido hudu suka yi da shi, ta karasa kusa da shi da gudu
ta duka kusa da shi tana kallonsa tace "Uncle ka xo" kallonta kawai junaid ke yi ta
gefen ido, El-ameen dake kallon hannunta ya ga inda ta yanke yace "Yeah na xo" mika
masa hannun tayi kamar xata yi kuka tace "Look" ya kama hannun yana kallon yatsan
murya can kasa yace "Sorry, but me kike yi da wuka" ta kalli Junaid hawaye ya cika
idonta sai dai bata ce komai ba, kallon Junaid din yayi shi ma ba tare da ya ce
komai ba, ya mike ita ma ta tashi tsaye, gun mota ya nufa da ita junaid ya bi su da
kallo, suna isa gun motar ta wara ido cike da murna tace "Uncle are we leaving,
bari in dauko jakana da hijab" bai ce komai ba ya bude motar ya dauko plaster ya
fito yace "Toh shiga" ba musu ta shiga ta xauna, ya yanki plastern ya kamo hannunta
ya rufe gun da ta yanken, sai kallonsa take, yyi mata murmushi yace "Xai warke kin
ji" kallonsa take kamar bata gane me yace ba, ya buda ido yace "It will heal" a
hankali tace "Ohk!" Magani ya dauko a motar ya mika mata ta karba yace "You take
one yanxu kinji?" Kai ta gyada masa, ya koma baya yace "Toh fito" kamar xata yi
kuka tace "Are we not going" yace "Anjima ne ba yanxu ba" hawaye ne ya cika idonta
ta fito daga motar, yayi murmushi yace "Anjiman ma baxan xo ba idan kika min kuka"
share hawayen tayi a hankali tace "Na daina" wani chocolate ya dauko a motar ya
mika mata yace "Toh gashi ki tafi" ta karba ta juya ta fara tafiya ya bi ta da ido,
sai a snn junaid ya dauke ido daga kallonsu da yake, El-ameen ya xaga ya shiga
motarsa yayi horn aka bude masa gate ya fice, tana share hawayen ta ta iso balcony
din xata shiga ciki Junaid da ya wani hade rai yace "Come back here" dawowa tayi
tana kallonsa, yace "Cire abun nan na hannun ki ki fita a nan" kallonsa take kamar
bata gane me yace ba, ya mike yace "Nace ki cire" komawa baya tayi a d'an tsorace
ta cire plastern ta jefar yace "Leave" parlon ta shiga ya koma ya xauna. Kuka tayi
ba kadan ba a bedroom daga nan bacci ya dauketa. Sha daya saura junaid ya shiga
parlor ya haura xuwa dakinsa, wanka yayi ya shirya ya fito yayi kwanciyarsa a
parlor, can kuma ya mike ya koma sama, ya dde tsaye a corridor kafin ya tura kofar
dakin da Jasmine take a hankali, kwance ya ganta tana bacci, ya shiga dakin ya
karasa kan gadon ya durkusa yana kallonta, yatsanta ya kamo yana kallon inda ta
yanken, ta bude ido a hankali, tana sauke idon kansa ta mike xaune da sauri, kamar
bai son magana yace "Is it still paining you?" Girgixa masa kai tayi yace "Ohk!
Sorry!" Ta gyada masa kai, yace "Toh kwanta" ba musu ta koma ta kwanta ya mike
tsaye yana kallonta, wanda hakan yasa ta rufe ido da sauri. Kasa barin dakin yayi
har bayan kusan minti goma ya ji an danna bell, ta bude ido tana kallonsa, murmushi
yayi ya juya ya nufi kofa ya fita ya kulle sannan ya sauka downstairs, still yayi
bakin kofa bayan ya bude yana kallon Mumynsa, ta hade rai tace "Meye haka?"
Murmushi ya kirkira yana shafa kai yace "I i i was surprise ne" shigowa parlon tayi
ya bi bayanta gabansa na faduwa. Tana xaunawa ya xube nan gabanta yace "Sannu da
xuwa Mumy, ina yini?" Tace "Lafiya lau, ya kuke" yace "Alhmdllh wllh Mumy" yana yi
ne yana kallon stairs kamar munafuki, can ya mike da sauri yace "Bari in kirata"
ita dai bata ce komai ba ta bi sa da kallo don ko ba a gaya mata ba ta san bai da
gaskiya wannan kame kamen, yana haura wa sama ya bude dakin Jasmine suka kusa cin
karo tana kokarin fitowa, xaro ido yayi ya ja ta suka koma dakin yace "Ina xaki?"
Tace "Ruwa" ya xaunar da ita xuciyarsa na bugawa yace "No xan kawo maki anjima, you
know what kar ki sake ki fito yanxu kin ji koh?" Shiru tayi tana kallonsa, yace
"Jasmine!" Tace "Uhm!" Yace "I said kar ki fito plss kin ji, kwanta kiyi baccin
ki," toh kawai tace ta koma ta kwanta ya mike ya fita ya kulle dakin, dakin
Humainah ya shiga ya duba ya ga ba ta, ya jima tsaye kafin ya juya ya fita ya koma
parlor, xaune ya ganta kusa da Mumy kamar xata shige jikinta, Mumy na kallonsa tace
"Da ina ka tafi" ya buda ido yace "Na je kiranta ban ganta ba Mumy" Mumy ta dauke
kai tace "Kaji da abinda kake kullawa, kawai mutum ya maida kansa munafuki, ya
dauko wasu halayyen da ba nasa ba" murmushi Humainah tayi don abun ya bata dariya
ta mike ta tafi kitchen don dauko ma Mumy drinks, shi kam kasa karasawa cikin
parlon yayi don gani yake kamar ta gano sa ne, tana kallonsa strictly tace "What
are you up to Ahmad?" Kamar zai mata kuka yace "Nothing mum, just xuwa aikin da
bana yi kwana biyu ne naji daban" hararan shi kawai take yayi murmushi ya karaso
cikin parlon ya xauna gefenta ya mata side hug yace "I miss you Mumy, har xaxxabin
rashin ki fa nake" kallonsa kawai take ganin yanda ya rame idanuwansa suka fito, ya
langwabar da kai yace "Mumy" tace "Baka cin abinci ne?" Girgixa mata kai yayi yace
"Ina ci Mumy, kewar ki ne kawai" tace "Toh ku koma can gidan" wara ido yayi yace
"Koh Mumy? Toh xa mu koma" a zahirin gaskiya kawai ya fadi haka ne don xancen ya
wuce kuma gaba daya hankalinsa na kan Jasmine, Humainah na shigowa parlon da drinks
ya mike yace "ina xuwa Mumy" daga haka ya haura sama, a hankali ya bude dakin ya
ganta xaune a kasa, ya karasa da sauri yana kallonta ya durkusa yace "Me kike a
nan?" A hankali tace "Ruwa xan sha" yace "Yi hakuri bari in kawo maki yanxu" mikewa
yayi ya fita ya shiga nasa dakin ya dauko goran ruwa ya fito ya dawo dakin, da
kansa ya bata ta sha, yace "Toh koma kan gado" ta mike ta koma gadon.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

52___53
Jasmine ta bude ido tana kallon El-ameen tace "Uncle ya tafi" El-ameen bai ce komai
ba sai bin motar junaid da yayi da ido, can yayi murmushi ya kalli gate din gidansu
sannan ya kalleta yace "Mu je" tafiya ya fara yi ta bi bayansa yana yi yana
kallonta har suka iso titi, ya tsaida adai daita ya sa ta shiga sannan shi ma ya
shiga, tara da 'Yan mintuna Mai adai daitan yayi parking bakin gate kamar yanda
El-ameen ya umarce sa, fitowa yayi ita ma ta fito ya fiddo dari biyar ya mika masa
sannan ya shiga gate din ta bi bayansa kamar xata yi kuka ganin inda suka dawo,
junaid na tsaye balcony har suka iso, El-ameen ya kalli Jasmine da ta ki shiga
parlon yace "Tafi ki kwanta gobe xan xo in tafi da ke" kai ta gyada masa hawaye
cike idonta tana kallonsa, gyada mata kai yayi yace "Yeah", daga ita har shi bbu
wanda ya kalli junaid ta juya ta shiga parlon shima ya juya ya nufi gate, wani irin
kallo junaid ya bi sa da shi har ya fita, sannan yayi tsaki ya juya ya shiga
parlon, yana haurawa sama ya shiga dakinsa. Washegari Tuesday misalin sha biyu
yana daki yana danne dannen laptop tun bayan da ya fita sallahn asuba bai kuma
sauka parlor ba kuma idonsa biyu yana jin jasmine na ta sallama bakin kofa bai
tanka ba, ita kuma bata shigo ba, muryoyin da yake ji parlor ya sa shi mikewa da
sauri ya fita ya sauka downstairs, tsaye yayi bakin stairs din ya wani hade rai
yana kallon wa enda ke parlon, Fatima ce da khadija sai Humainah, ga kuma jasmine
dake xaune kan rug da plate din abinci gabanta, gaba daya kallonta suke barin
fatima da idanuwanta suka kara girma don kallo, kallo daya Humainah tayi masa ta
dauke kai, fuska a daure ya karasa cikin parlon yana kallonsu khadija yace " With
whose permission ku ka shigo min gida?" Khadija tace "Mumy ce tace mu xo mu
taya...." Wani mugun kallon da yake mata yasa ta yin shiru ita ma ta hade rai,
fatima kam dama bata dago kai ba, ya juya yana kallon Humainah yace "Kika bude masu
kofa without permission dina koh?" Tabe baki tayi bata ce komai ba, kallonta ya
tsaya yi na kusan second goma sannan ya juya yana kallon Jasmine da ta kasa cin
indomien jin yana masifa, da ganinta kasan a tsorace take, tun kan yace komai
muryarta na rawa tace "Ina jin yunwa ne shine na gaya ma Anty ta ban indomie" yace
"Tashi ki bar parlon nan" mikewa tayi xata tafi sama ya dawo da ita yace "Dauki
abincin" ta durkusa ta dauka ta wuce. Yana kallon kannin nasa yace "Kun san Allah
if I shud hear a word daga bakin ku a kan komai na gidana xan maku abinda ban taba
ba, nd I mean it" daga haka ya juya ya koma sama. Bayan Azahar su fatima suka bar
gidan duk da ba haka Humainah ta so ba, sun dai samu ya basu kudin mota, sama ta
haura bayan tafiyarsu ta shiga dakinta, bude kofar aka yi ta juya da sauri ta ga
Jasmine, karasowa cikin dakin tayi hawaye cike idonta tana kallon Humainah a
hankali tace "Anty cikina na min ciwo" ido Humainah ta xuba mata can tace "Kin ci
abincin da na baki?" Girgixa kai tayi tace "Amai xan yi idan na ci" Humainah tace
"A'a ki je ki ci dai....." Hawayen dake makale idonta ya gangaro tace "Anty ki kira
min uncle in gaya masa" Humainah bata ce komai ba har sai da Jasmine tace "Kin ji"
gado ta nuna mata tace "Toh xauna ina xuwa" Jasmine ta xauna ita kuma ta juya ta
fita, dakin junaid ta shiga ta gansa kwance idonsa lumshe, lallabawa tayi ta karasa
gun da wayarsa yake ta dauka ta fita, tana fita ya mike ya bi bayanta, tana tsaye
dakinta tana kokarin dialing number El-ameen ya shigo, still tayi tana kallonsa sai
kuma ta hade rai, kallo daya yayi ma jasmine ya fixge wayar yana kallon wanda take
kira, da sauri ya katse yana mata mugun kallo yace "Kee!" Turo baki tayi tace "Toh
ita ce tace in kira mata" juyawa yayi yana kallon Jasmine da tayi mugun tsorata, ya
kuma kallon Humainah ya hade rai yace "Ki bar min irin haka a gidan nan, ke xata
gaya ma ki kira mata shi... Are you on ur senses?" A hankali Jasmine ta mike xata
fita ya fixgota, kuka ta saki tana kallonsa yace "Me xa ki ce masa?" Muryarta na
rawa tace "That my tummy is aching" wani kallo yayi mata yace "Yayi abinda yafi
aching din ma, fita daga nan" da sauri ta fita, shima ya juya ya fice, Humainah ta
tabe baki ta rufe kofarta. Har dare Jasmine sai juye juye take a daki, tayi kukan
har ta gaji, yana son xuwa gun ta amman bakin hali ya hanasa Lol, duk ya rasa
sukuni har kusan karfe tara, mikewa yayi ya fita ya shiga dakin Humainah ya sameta
xaune gaban mirror tana danne dannen wayarta yace "Kin bata abinci?" Ba tare da ta
kallesa ba tace "yana kitchen ai" juyawa yayi ya fita xai koma dakinsa, tsaye yayi
bakin kofarsa ya kasa shiga dakin yana kallon dakin da take, karasawa yayi ya tura
kofar a hankali dai dai lokacin da ta mike xata bayi da saurinta, bin ta yayi da
kallo sai kuma ya ga ta durkushe nan bakin kofar ta fara kwararo amai, shiga dakin
yayi da sauri ya isa kusa da ita ya durkusa ya dagota yana kiranta, sosai ya ji
jikinta yayi xafi, ta dago jajayen idonta tana kallonsa ta fashe da kuka tana rike
da cikinta, ai bai san lokacin da ya hade ta da jikinsa ba, ba shiri ta hadiye
kukan da take, xame jikinta tayi, ya mike da kyar yace "Am am sorry jasmine...."
Kasa dagowa tayi sai hawaye, ya kama hannunta ta mike ta shiga bayi ta wanke
bakinta ta fito ta kwanta, ya gyara gun aman ya dawo dakin yana kallon agogo, ya
dawo kusa da ita yace tashi mu je asibiti, girgixa masa kai tayi da kyar tace "No
ka kira uncle" hade rai yayi ya dau hijab dinta yace "tashi mu je nace" hawaye cike
idonta ta mike xaune ta karba hijab din ta sa, kasa tashi tsaye tayi, hawaye na
sakko mata tace "Baxan iya tashi ba captain" kallonta yake cike da tausayinta ya
durkusa kusa da ita yace "Ina ke maki ciwo ne?" Cikinta ta nuna masa, sai kuma ta
fashe da kuka ta koma ta kwanta, mikewa yayi ya fita xuwa dakin Humainah, har ta
kwanta ya karasa ya kunna bedside lamp ta bude ido da sauri tana kallonsa ta mike
xaune tace "Me ya faru?" Ya dan shafa kai yace "Plss asibiti xa ki raka mu in kai
yarinyar nan amai take ta yi" hade rai tayi tace "Bacci ni xan yi, ka kira mata El-
ameen mana" yace "No it's late yanxu kar a shiga hakinsa" wani kallo tayi masa tace
"I see" ta koma xata kwanta ya rikota ta buge hannunsa tace "Leave me joor"
rungumeta yayi yace "Haba wife taimako fa xa kiyi" turasa ta shiga yi tace "Ka rabu
dani don Allah ni baccina xan yi" ganin kiss dinta yake son yi tace "Ohk naji naji,
mu je" murmushi yayi ya saketa ta mike fuskarta daure ta dau hijab har kasa tasa ta
fita ya bi bayanta, ba laifi ita ma ta tausaya ma Jasmine don da ganinta kasan tana
jin jiki, tana rike da ita suka shiga motar, wani private hospital suka tafi, basu
sha wahalan ganin likita ba, likitan na ta kallonsu har ya xaunar da ita sannan shi
ma ya xauna, yayi murmushi yace "Couples?" Kallonta Junaid yayi da sauri ita ma ta
kallesa suka hada ido ta dauke kai, ya dan wara ido yace "Ohh No! We are not"
Likitan yace "Ohh sorry!" Murmushi kawai junaid yayi ya d'an saci kallonta,
tambayoyi likitan ya fara mata junaid na bada amsa don kin cewa komai tayi, nan dai
ya duba ta ya rubuta mata magunguna da allura sai test da ya rubuta xa a mata gobe
da safe, malt junaid ya siya mata ta sha kafin a mata alluran sanin bata ci komai
ba, fir taki yarda ayi mata tana kuka a rikice, junaid ya hade rai yace "Xaki sha
mari fa, Meye a alluran" fixgota yayi ganin taki yin shirun, ya hade rai yana
kallonta, da kyar ta yarda aka mata shima a cinya yana tsaye kanta, ta dinga ihu
tana rusa kuka, yana rike da hannunta yana kallon yanda take kukan suka fito
reception, dariya ma take basa, Humainah da dama bata bi su ba tana reception din
xaune ta hade rai ganin yanda ya rike ta yana kallo, har suka shiga mota kuka
jasmine take sosai, shi dai Junaid bai ce mata komai ba haka Humainah, ta gaji don
kanta tayi shiru, suna isa guda Humainah ta bude motar ta fice, bin ta da kallo yyi
sannan ya xaga ya bude motar ya ga shirun bacci tayi ashe, kiranta yayi murya can
kasa ta bude ido a hankali yace "Fito" fitowa take son yi amma ta kasa, ta nuna
masa cinyarta cikin tsarkewar murya tace "It's aching" kallon balcony yayi ya ga
har Humainah ta shige, hannu ya mika mata ta kama sannan ya fito da ita, yana rike
da ita suka shiga parlon, bai bari sun hada ido da Humainah dake parlon ba ya haura
sama da ita, magungunanta ya bata ta karba ta sha yace "Toh kwanta ki yi bacci"
girgixa masa kai tayi tace "Xan cire kaya" yace "Toh cire" mikewa tayi ta sauka ta
cire hijab xata cire doguwar rigar jikinta yace "Noo tafi bayi ki cire" tace "Toh"
sannan ta shiga bayin, kasa fita yayi daga dakin, har ta fito daga ita sai inner,
xaro ido yayi ya kasa cewa komai bai kuma daina kallonta ba, tace "towel din...."
Ai bai tsaya saurarenta ba ya fice daga dakin da sauri. Kayan baccinta ta dauka a
closet ta sa sannan ta kwanta. Downstairs ya sauka ya kashe kayan wuta ya koma
daki. Wanka yayi ya daura alwala ya shirya ya kwanta, sai dai ya kasa bacci har
kusan sha biyu ya mike daga karshe ganin he's just deceiving his self ya fita,
dakin Humainah ya shiga ya kunna wutan dakin, yayi mamakin ganinta xaune kan gado
ta hade kai da gwiwa, dagowa tayi tana kallonsa da rinannun idonta, ya kashe wutan
ya karasa da kyar ya xauna gefenta yace "What happened?" Sharesa tayi xata kwanta
ya rikota ta fashe da kuka, ya rungumeta cikin sanyin murya yace "talk to me"
turasa ta shiga yi ya ki saketa hakan yasa tayi lamo jikinsa hawaye na saukowa
idonta, sun kusa minti goma a haka ya dago kanta yana kallonta da idonsa da suka
kada murya can kasa yace "Kina da alwala?" Kin cewa komai tayi har sai da ya
kirata, tace "na me?" Yace "Toh je kiyi" tace "Ni nayi" mikewa yayi yace "Ohk let
pray" wani kallo take masa kafin tace "Na me?" yyi shiru yana kallonta, can ya mike
ya hau darduman dake shimfide kasa yace "Am waiting" kin tashi tayi yace "Ke fa
nake jira" da kyar ta sauka duk gabanta na faduwa ta dau hijab ta sa, raka'a biyu
ya ja su, suna sallamewa ta mike ta haye kan gado ta shige cikin
bargo ya bi ta da kallo, ya jima xaune kan darduman yana addu'o'i kafin ya mike ya
dauke darduman ya nufi kan gadon ya xauna, cire bargon yayi ta mike xaune ta hade
rai tace "Meye haka?" Ya hau gadon yana kallonta yace "Ina ruwana da ke kiyi baccin
ki" kin kwanciya tayi da ganinta kasan a tsorace take, yayi murmushi ya kwanta ya
juya mata baya, ta kusa minti biyar xaune kafin ta kwanta nesa da shi xata ja bargo
ya koma kusa da ita ya jawota, ta fashe da kuka tace "Ya A.jay bacci fa xanyi plss"
a hankali yace "Naji, yi baccin ki amma a jiki na" shiru tayi gabanta na faduwa can
tace "Toh ni da bargo nake kwanciya" yace "Ga ki ga shi", bbu yanda ta iya haka ta
kwanta ta rufa masu bargo tayi lamo ta rufe ido, sai da ya ga ta fara bacci ya cire
bargon, ranan ta fadi ma 'yan garinsu bata taba tunanin haka Ya A.jayn yake ba, ba
irin rokon da bata yi masa ba, bbu wanda bata kira masa ba barin Hajja amma duk a
banxa abun ka da Novice da mai dacin ran tsiya, tuni baccin wahala da tashin sense
yayi gaba da ita, shi kam rasa gane abinda yake ji game da ita a ransa yayi. Da
asuba bayan ya dawo daga mosque duk ta daga masa hankali da kuka ita ya kira mata
Mumy, ta kuma ki barin ya xo kusa da ita, ya ma rasa abinda xai yi, kyaleta yayi ya
fita daga dakin, har xai shiga dakinsa sai kuma ya bude na Jasmine durkushe ya
ganta can jikin gado tana kuka ya karasa ciki yana kallonta da mamaki yace "me ya
faru kuma" kasa cewa komai tayi sai hawaye, ya durkusa kusa da ita da damuwa yana
kallon idonta da ya kumbura don kuka yace "Cikin ne har yanxu?" Ta fashe da kuka ta
kamo hannunsa tace "Captain it's still paining me, yana min ciwo sosai" ganin yanda
ta rikice yasa hankalinsa ya tashi ya mike ya fita daga dakin ya shiga nasa ya dau
wayarsa yayi dialing number El-ameen. Bugu daya ya daga, junaid yace "Pls come over
yanxu" El-ameen dake kwance ya mike xaune yace "Me ya faru?" Junaid yace "Hurry up
plss" El-ameen ya d'an bude ido yace "Toh fah" sai kuma yayi dariya yace "Kayi aika
aika kenan, ba inda xan xo sai dai in turo maku nurse" Shiru junaid yayi d'an ya so
ba shi dariya, yace "kaga bana son walakanci ina jiran ka" El-ameen yace "Allah ba
da ni xa ayi wannan ba, me xan maku idan na xo?" Junaid yace "Ohk naji ka turo
nurse din, but kai ma ka xo don baby ma bata da lafiya tun jiya" El-ameen ya mike
tsaye yace "da gaske? Me ya sameta" Junaid ya katse wayar ya xauna ya shafa kansa,
murmushi yayi yana mamakin sharp thinking irin na El-ameen, mikewa yayi da sauri ya
fita ya koma dakin Jasmine, yanda ya bar ta haka ya sameta ya durkusa kusa da ita
cike da tausayinta duk ta rasa inda xata sa kanta sai kuka take, da kyar tace
"Captain ka ce Uncle ya xo plss" hade rai yayi yace "Baxan ce ba" kai ta gyada masa
hawaye na sakko mata alamar to, can kuma cikin kuka tace "Ka ban Magani captain"
hannunta ya kamo yace "Xa a kawo maki yanxu kin ji" ajiyar xuciya ya sauke jin
shigowar motar El-ameen, bayan 3 mint ta fara kokarin mikewa tace "Uncle I want to
ease my self" hade rai yayi jin tace uncle, ta mike da kyar tana duddukawa, mikewa
yayi da sauri ganin abinda ke jikinta, ita ma ta kalli inda yake kallo, ai sai ta
fasa ihu a tsorace tana kokarin daga rigar dai dai lokacin da El-ameen ya bude kofa
ya shigo dakin, tana ganinsa ta kuma fashe wa da kuka tayi gunsa da sauri, shi ma
kallon jikinta ya shiga yi, a rikice take cewa "Uncle kaga blood" xata daga rigar
ya kama hannunta, ya d'an kalli Junaid ya ga shi yake kallo, a tare suka dauke kai,
Junaid ya juya ya fice daga dakin, El-ameen ya kalleta da tausayi ganin yanda take
kuka a hankali yace "Yi hakuri kin ji jewel" wayarsa ya ciro ya kira nurse daga
clinic, ganin tsayuwar ke sa ta flow yace ta xauna taki, da kansa ya xaunar da ita
ya durkusa gabanta.

Uzuri! Uzuri!! Uzuri!!! Yana da dadi.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

52.....
Kallon Humainah Mumy tayi ganin junaid bai sakko ba har lokacin tace "Wai me yake a
sama?" Humainah tace "Ni ma ban sani ba" mikewa tayi ta nufi stairs Humainah ta bi
ta da kallo. Kalle kallen rooms din Mumy ta shiga yi tana tsaye corridor, can ta
kira sunansa, Junaid da ke tsaye yana kallon Jasmine dake kokarin kwanciya ya xaro
ido ya juya da sauri ya nufi kofa ya sa key, Mumy ta juya tana kallon kofar ta
karasa ta kuma kiran sunansa, da kyar ya iya bude baki yace "Mumy ina xuwa fah, am
am busy ne..." Da mamaki tace "Busy? Busy doing what? Meye na rufe kofa Ahmad?"
Kasa ce mata komai yayi, strictly tace "Ahmad!" Nan hankalinsa ya tashi ya juya ya
kalli Jasmine da ta mike xaune tana kallonsa, kauda kai yayi yace "Mumyna ina xuwa
fah" tasowa Jasmine tayi ta iso kusa da shi a hankali tace "Open...." Juyawa yayi
da sauri ya hade rai ya tura ta har sai da ta fadi kan gado, ta mike xaune tana
kallonsa lkci daya hawaye ya cika idonta, jingina yayi jikin bango ya rike kai,
Mumy ta kuma kiransa for the 3rd time, ya lumshe ido yace "Mumy I said am coming"
"Uhm" kawai tace ta juya ta sauka downstairs, Humainah ta mike ganinta, Mumy na
kallonta tace "Meye Ahmad ke boyewa a gidan nan Humainah" ta bude hannu tace "Ni ma
ban san masa ba Mumy" Mumy tace "Baki sani ba?" Humainah ta gyada mata kai, Mumy
tace "Ohk" daga haka ta nufi kofa da ganinta kasan ranta ya bace, Humainah ta bi
bayanta da sauri tace "Mumy na daura girki fa" "No, tafiya xan yi" Humainah tayi
shiru ta bi ta da kallo ganin mood dinta har ta fita, sai kuma ta bi bayanta da
sauri tace "Mumy ba wani abu fa yake boyewa ba, I think El-ameen ne xai yi aure
without knowledge din parent dinsa shine suke ta hada kaya da yawa, so kayan na
dakin may be baya son ki gani ne, um nothing more Mumy" da mamaki Mumy tace "Aure
kuma?" Humainah ta gyada mata kai, Mumy tace "Toh sun kyauta ma kansu" daga haka
Mumy tayi gaba. Humainah ta dawo parlon ta xube kan kujera sai kuma ta fashe da
kuka ta hade kanta da kujerar, junaid ya kusa minti sha biyar tsaye jikin bangon
dakin ya rasa abun yi duk da ya fahimci Mumy ta bar wajen, juyawa yayi ya kalli
Jasmine a karo na farko tun san da ya turata, tausayi ta basa ganin kwanciya tayi
ta juya baya, ya karasa gun gadon ya durkusa a hankali yace "Jasmine" juyowa tayi
tana kallonsa da jajayen idonta, ya lumshe ido ya bude yace "Kuka kike?" Girgixa
masa kai tayi hawayen da ke makale idonta suka gangaro, ya tsura mata ido yana
kallo murya can kasa yace "Tashi" ba musu ta mike xaune tana kallonsa, kamo
hannunta yayi a hankali yace "Am... am sorry Jasmine" kallonsa kawai take ya sa
yatsa ya shiga goge mata hawayen idonta yana kallon kwayar idanuwanta kamar me rada
yace "Am sorry dear" sauke idonta tayi kasa, ya matso kusa da fuskarta gently yace
"kin ji?" Gyada masa kai ta shiga yi tana komawa baya kanta a kasa, ya bi ta da
kallo har ta isa can tsakiyar gadon, ya mike ya juya xuwa gun kofa, budewa yayi ya
fita ya sa key ta waje, gabansa na faduwa ya sauka kasa, Humainah na ganinsa ta
hadiye kukan da take ta dauke kai, ya karaso yana kallonta yace "Mumy fa?" Ba tare
da ta kallesa ba tace "Ta tafi" ya hade rai yace "ke kika ce ta hau sama ko" mikewa
tayi tace "Ehh" daga haka ta bi ta gefensa xata wuce ya fixgota ya hade ta da
jikinsa. Junaid na kwance after isha yana son xuwa gida amma bai san yanda xa su
kwashe da Mumy ba, wayarsa ne ya shiga ring ya mike xaune ya dau wayar yana kallon
mai kiran nasa, ganin number El-ameen ne ya d'aga ba tare da yace komai ba, daga
daya bangaren El-ameen yace "Captain!" Junaid yace "Yeah ina jin ka" El-ameen yace
"Wai wani kayan muke hadawa da kai?" Junaid yayi shiru har sai da El-ameen yace
"Ahmad!" Sannan yace "Ban gane xancen ba" El-ameen yace "Ummina ta kira ni daxu
tana tambayata wani kaya muke hadawa ni da kai, I just don't get were she's
heading, naga kuma ta dau abun da xafi, she don't want to talk to me yanxu ma, am
just confuse frnd" Junaid da ya bude ido da kyau yana saurarensa yace "Kaya kuma?
But kayan Meye ta ce maka?" El-ameen yace "Wllh nima ban sani ba, ban gane me take
nufi ba" Junaid yace "Toh fah! Kana ina yanxu?" Da damuwa El-ameen yace "Ina gida
mana....." Junaid yace "Ohk bari in xo but am afraid kuma kar Ummi ta gan ni" El-
ameen yace "Ka kirani sai in fito" da haka suka kare wayar, Junaid yace "Wai kaya!"
Tabe baki yayi ya mike ya dau jallabiyarsa ya daura kan singlet da 3qtr din
jikinsa, makullin mota ya dauka ya fita, har xai sauka downstairs ya dawo ya bude
dakin Humainah ya ganta xaune gaban mirror tana shafe shafe, bai bari sun hada ido
ba ya rufe mata kofar har ya kai bakin stairs ya kuma dawowa ya tura kofar jasmine
a hankali, xaune ya ganta a kasa ta takure waje daya, ya karasa cikin dakin yana
kallonta yace "me kike a nan?" Dago kai tayi ta kallesa, ya durkusa kusa da ita
yace "What are you doing here?" Girgixa masa kai tayi bata ce komai ba, yace "Za ki
raka ni?" Gyada masa kai tayi ya mike yace "Toh tashi" mikewa tayi ya dau hijab
dinta dake kan gado ya mika mata ta karba ta sa sannan suka fita dakin. Tana biye
da shi a baya har suka isa parking space, Front seat ya bude mata ta shiga ya xaga
ya shiga motar shi ma ya tada yayi horn mai gadi ya bude gate ya bar compound din,
lokaci lokaci ya kan kalleta yana driving din, murya can kasa yace "Jasmine!" Ta
juya tana kallonsa, ya mata murmushi yace "Kin koshi koh?" Kai ta gyada masa ta ci
gaba da kallon waje da take ta glass din motar, har suka isa gidansu El-ameen bai
sake ce mata komai ba, ya nemi gefe yayi parking sannan ya ciro wayarsa ya shiga
kiran El-ameen, yana dagawa yace "Ga ni a waje" ko minti biyar ba ayi ba El-ameen
ya fito ya karaso gun motar ya bude front seat, bude ido yayi ganin Jasmine, tayi
murmushi tana kallonsa a hankali tace "Uncle!" Junaid ya bude motar ya fito yace
"Plss ni ka ji da ni" kallonsa El-ameen yayi bai ce komai ba, Junaid ya nufi gun
flowers dake jikin gidan ya xauna kan bench din dake wajen, kallon Jasmine El-ameen
ya kuma yi ya mata murmushi yace "Ina xuwa baby" daga haka ya juya ya bi bayan
junaid, gefensa ya xauna yace "Frnd Ummi fa ta dau abun da xafi, mu je plss ka
tambayeta wani kayan take nufi" Junaid yace "No, ni baxan iya ba..." El-ameen yace
"Meye din ne baxa ka iya ba, but da nine ae xan iya yi maka hakan" Junaid yace "Toh
ni nama san me xan ce mata, ka bari idan ta huce sai ka je ka sameta ka tambayeta"
El-ameen yace "I see" Junaid bai kuma cewa komai ba, El-ameen ya mike ya tafi gun
motar ya bude, kallonsa tayi kamar xata yi kuka tace "Uncle in fito?" Girgixa mata
Kai yayi yace "No, yi xaman ki, have you eaten?" Gyada masa Kai tayi tace "Yes I
ate rice and stew" yace "Wa ya baki?" Ta kalli inda junaid yake tace "Him" El-ameen
ya mata murmushi yace "ohk" kallonsa tayi tace "Uncle Mami bata dawo ba?" Yace
"Gobe xata dawo" ta bude ido tace "Sai ka Kai ni?" Yace "Yeah! But me yasa baki son
xama wajen captain" shiru tayi kamar bata gane me yace ba, ya duka kusa da ita yace
"Y don't you want to stay with Capt?" A hankali tace "I don't like him, he like
shouting at me, he...." Sai kuma tayi shiru tayi kasa da kanta, shi dai kallonta
kawai yake, Can ta dago dara daran idonta tace "I like him! He's kind, yana bani
abinci...." El-ameen yace "Uhunn!" Takun da ya ji bayansa yasa bai ce komai ba,
Junaid ya xaga daya side din ya bude motar ya shiga, yana kallonta yace "Fita ku
gama maganar ku" ba musu ta fita, ya fixgo door din motar ya rufe ya tada motar tun
kan ya fige ta El-ameen ya janye Jasmine yana murmushi.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

54......

Ko da nurse din ta xo kin bari El-ameen ya fita ya bar ta Jasmine tayi, ya fiddo
wayarsa ya kira junaid har ya gama ringing bai daga ba, ya kuma kiransa nan ma no
answer, kallon Jasmine da ke ta hawaye yayi yace "Nace maki am not going, yanxu xan
dauko maki magani in dawo" tana girgixa kai tace "Noo" hade rai yayi yace "To bari
in yi tafiyata..." Ta kamo hannunsa cikin kuka tace "Noo plss kar ka tafi" yace
"Toh yanxu xan dawo" daga haka ya mike ta bi sa da kallo har ya fita, xaune ya ga
junaid a balcony ga wayar a hannunsa, bai ce masa komai ba ya fita waje ya shigo da
nurse din, ta gaida junaid ya amsa ba tare da ya kalleta ba suka shiga parlon tare
da El-ameen, bai shiga dakin ba ya tura nurse din bayan ya mata bayani don yasan ba
lallai ta yarda da nurse din ba idan ta gansa, tsaye yayi corridor din rooms din
yana mamakin halin junaid, now a days the thing is just getting worst ma, tabe baki
yayi yana nan tsaye har bayan kusan minti talatin nurse din ta fito tace "Dr bbu
sanitary pad," shiru yayi sai kuma yace "then sai na je hospital don shaguna basu
bude ba yanxu" tace "Ohk, ka taho da injection da drugs" yace "Ohk" ya juya ya
sauka ita kuma ta koma dakin, da ido junaid ya bi sa har ya shiga motarsa ya bar
gidan. Bakwai saura El-ameen ya dawo ya kira nurse din ta fito ya mika mata ledan
hannunsa ta karba ta koma dakin, yana nan tsaye har ta kuma fitowa tace "Tayi bacci
Dr" yace "Ohk shiga dakin can" ta kalli kofar dakin da ya nuna mata tace "In yi
me?" Yace "Bata da lafiya ita ma ki duba ta" bude kofar tayi ta shiga da sallama,
ta karasa gun gadon tana kallon Humainah da ke kwance cikin bargo tana bacci, yaye
bargon tayi wanda hakan ya farkar da Humainah ta mike xaune da sauri tana kallon
nurse din, Nurse din ta mata murmushi xata yi magana idonta ya sauka kan gadon,
shiru tayi sai kuma ta juya ta nufi kofar da take tunanin bathroom ne, komawa
Humainah tayi ta kwanta tana kokarin maida hawayen da ya cika idonta, ba a dau
lokaci ba nurse din ta fito ta iso gun gadon tace "sannu sister tashi mu je bayi"
bata mata musu ba ta cire bargon ta mike tsaye, kama hannunta nurse din tayi suka
shiga bathroom din, Humainah ta kalleta cikin tsarkewar murya tace "Xan iya da kai
na" nurse din tace "Toh shikenan" daga haka ta fito ta shiga gyaran dakin, tana nan
har Humainah ta fito, nurse din ta tambayeta inda kayanta yake ta nuna mata ta bude
ta fiddo mata da gown, cikin 'yan mintuna ta gama shirya wa nurse din sai kallonta
take don tasan daurewa kawai take, darduma ta shimfida mata ta bata hijab ta karba
ta hau kan darduman ta tada sallah, nurse din ta fita don xuwa hado mata tea tasha
kafin ta bata Magani, da mamaki ta kalli El-ameen dake tsaye har lokacin a corridor
tace "Kana nan har yanxu Dr, ai da ka xauna parlor" yace "Am okay, ya jikin nata?"
Tace "Da sauki I want to go nd make a cup of tea for her" yace "Are you sure she's
ohk?" Tace "Ka shiga ka duba Dr" yace "No ba sai na shiga ba, make the tea for her
na taho mata da drugs" tace "Okay," sannan ta sauka, ba a dau lkci ba ta dawo da
cup din tea din ta kai ma Humainah, ba laifi ta karba ta sha, nurse din ta fito El-
ameen ya bata magungunan sannan ya sauka downstairs, parlor ya ga junaid kwance
yana kallo, El-ameen bai bi ta kansa ba ya fita yayi xaman sa a balcony, nurse din
na saukowa Junaid ya haura sama, kofar dakin da Jasmine take ya tura a hankali ya
shiga ya tsaya daga bakin kofar yana kallonta, bacci ya ga take ya karasa kusa da
gadon ya durkusa dai dai fuskarta yana kallonta, bude ido tayi a hankali ta mike
xaune da sauri ganinsa, ya d'an koma baya yace "Cikin ya daina?" Kallon jikinta ta
shiga yi, sai kuma ta gyada masa kai tace "Uncle ya tafi?" Hade rai yayi yace "Ban
sani ba" tayi shiru bata ce komai ba, ya mike ya fice daga dakin, dakinsa ya shiga
don yin wanka, Jasmine ta sauko daga kan gadon tana kalle kallen jikinta, a hankali
ta dinga tafiya har ta fito ta sauko downstairs, hawaye ya cika idonta ganin bbu
El-ameen, har xata koma sai kuma ta fita parlon, wara ido tayi ganinsa xaune yana
danna waya, ta karasa da sauri ta durkusa kusa da shi tace "Uncle!" Yayi murmushi
yace "Har kin tashi?" Gyada masa kai tayi, yace "Toh cikin ya daina?" Shiru tayi
sai kuma a hankali tace "Eh ya daina, uncle wannan Antyn tace min am on my period,
Meye wannan?" Ya d'an bude ido yace "Nima ban sani ba" shiru tayi sai kuma ta kalli
jikinta a hankali tace "Uncle har yanxu fa yana yi" murmushi yayi yace "Xai daina,
je ki duba min ko Anty ta tashi a sama" tace "toh" sannan ta mike ya bi ta da kallo
har ta shiga parlon, dakin Humainah ta shiga ta ganta kwance tana kuka, karasawa
gun gadon tayi ta durkusa kamar ita ma xata yi kukan tace "Anty menene?" Shiru
Humainah tayi mata, hakan yasa ta mike ta fita ta koma gun El-ameen, hawaye cike
idonta tace "Uncle kuka take, she don't want to talk to me" yace "Captain din fa?"
Tace "Yana dakinsa" mikewa El-ameen yayi ya shiga gidan ta bi bayansa, tsaye yayi
bakin kofar Humainah yayi sallama har sau biyu bata amsa ba, Jasmine tace "Ka shiga
tana ciki" bude kofar yayi ya mata alamar ta shiga, tana shiga ya bi bayanta,
karasawa cikin dakin yayi ya tsaya d'an nesa da gadon yana kallonta yace "Ya jikin
Humainah?" Mikewa xaune tayi amma ta kasa juyowa tace "Da sauki" yace "Ohk kiyi
hakuri, Allah ya sauke kin ji" kai kawai ta gyada masa yace "Go to sleep xa ki ji
sauki sosai" kwanciya tayi ya juya ya fita Jasmine ta bi bayansa, a hankali Jasmine
ta kamo hannunsa tace "I hate that captain, he's so mean" bude ido El-ameen yayi,
sai kuma ta sunkuyar da kai a hankali tace "Though I like him also, he's fine just
like you" dariya El-ameen yayi yace "To naji tafi dakin ki" ta hade rai tace "Ina
xa ka" yace "parlor" bude kofa aka yi duk suka juya Captain ya fito, suna hada ido
da Jasmine ya watsa mata wani kallo a kan idon El-ameen kuma, xame hannunta tayi a
hankali daga na El-ameen ta juya ta shiga daki, junaid yace "You are still around
ashe, tot ka tafi" El-ameen bai tanka sa ba ya sauka kasa, junaid ya bude kofar
Humainah ya shiga ya karasa gun gadon ya xauna yace "Good morning wife" rufe ido
tayi da sauri, yayi murmushi xai dagota ta mike xaune sai kuma ta fashe da kuka, ya
wara ido yace "Toh kuma, Allah ya baki hakuri just came to say ya jikin" daga haka
ya mike ya fita, dakin Jasmine ya bude ya ganta xaune ta rungume hannayenta kiris
ya rage ta fashe, yace "Ai kin iya dafa indomie koh?" Kai ta gyada masa a hankali,
yace "Toh xo ki dafa mana" mikewa tayi ya juya ta bi bayansa, indomie hudu ya fiddo
mata tace "Har da Anty?" Yace "Eh" kujera ya dauko ya xauna kitchen din yana kallon
yanda xata yi girkin, har ta gama bayan kusan minti goma idonsa na kanta bai ma san
ta gama ba, ta karasa kusa da shi ta duka a hankali tace "Captain!" Rufe ido yayi
ya bude da sauri ya kamo hannunta cikin sanyin murya yace "Jasmine" bude ido tayi a
hankali tace "Na gama" mikewa yayi a hankali har lokacin yana rike da hannunta yace
"Ohk dear, dauka daya ki kai ma Anty sai ki dauka kema ki ci" toh tace ya sake
hannunta ya juya ya fita. Da yamma nurse Salima ta kuma dawowa duba Humainah da
Jasmine kamar yanda El-ameen ya umarce ta. Da magrib junaid ya shirya ya tafi
gida, gabansa sai faduwa yake don bai san yanda xa su kwashe da Mumy ba, part din
Abbansa ya fara shiga don gaidasa, ya tarda Umma da Hajiya a parlon, xaunawa yayi
kasa ya gaida Abba ya amsa yana tambayarsa gida, yace "Alhmdllh Abba" juyawa yayi
yana kallon Su Umma ya gaida su, duk suka amsa masa da fara'ar da bai kai ciki ba
ana tambayarsa amarya, Hajiya ta mike ta fice daga parlon bayan ta ma Abba sallama
Umma ta bi bayanta, ya d'an jima xaune parlon Abba sannan ya mike yace masa xai je
gun Mumy, kamar munafuki ya xauna kasa ya sunkuyar da kai yana gaida Mumy, ta amsa
masa bbu yabo bbu fallasa, rasa abun cewa yayi haka ya karashi xaman sa Mumy nata
harkan gabanta ya mike yace xai tafi tace "Allah ya tsare" ya fita parlon, bai yi
mamakin ganin su Hajiya da Umma xaune a spot dinsu ba, ko sallama bai yi masu ba ya
fice, Hajiya tayi murmushi tace "Komai dai ya kusa xuwa karshe in da rai da lafiya,
sai mun cusa ma iyayenka tsanarka" gidansu El-ameen junaid ya nufa bayan ya bar
gidan, yayi mamakin ganinsa xaune waje, ya xauna gefensa yace "kai kuma xaman waje
ka fara yanxu kenan" El-ameen ya shafa kai yace "Yafi min alkhairi ne, kawai Ummi
ta dau fushi da ni kan abinda bansan komai kai ba, ni wllh ban san kayan me take
nufi ba" junaid yayi shiru can yace "Toh ka tambayi Abba mana," El-ameen yace "He
also don't want to say anything about it to me" junaid yace "Toh tashi mu je mu
samu ummin sai mu tambayeta" El-ameen yace "A'a ni baxan je ba, wannan Kanwar Abban
nawa na ciki" mikewa Junaid yayi ya shiga gidan, Small mum din El-ameen ce xaune
parlon da Ummi, Ummi ta hade rai ganinsa ya d'an shafa kai ya karaso ya xauna kasa
kusa da Ummi ya gaida ta ta amsa bbu yabo bbu fallasa, ya gaida Anty dake parlon
ita ma ta amsa masa haka, yana shafa kai yace "Ummi mu fa bamu san kayan me ake
cewa ba" Anty tace "Eh ai baxa ku sani ba munafukai, irin yanda aka maka haka xa a
masa shi ma kwanan nan" ko kallonta Junaid bai yi ba ya kalli Ummi ya marairaice
yace "Allah Ummi ba mu sani ba" Ummi tace "kayan auren mutum ku ke hadawa a boye ko
na me" junaid ya xaro ido yace "Kayan aure kuma Ummi, wani kayan auren?" Ummi ta
tabe baki tace "Na sha gaya masa yanda aka yi maka a gida haka shi ma xa a masa
yana xaton fadi nake kawai koh, to xaku sha mamaki daga kai har shi" junaid yayi
shiru can yyi murmushi yace "toh ayi masa hakan kawai Ummi, don nima ina masa
maganan aure baya saurarana, ni ba gashi ina xaune lafiya da matar ba" Ummi tace
"To tafi daki ka ga kayan sun yi" junaid ya d'an bude ido yana kallonta, sai kuma
ya mike ya nufi bedroom dinta, ko da ya fito dariya kawai yake yace "Wllh sun yi
sosai Ummi, Allah ya saka da alkhairi" junaid bai ce ma El El-ameen komai ba da ya
fito kawai dariya yake bakin rai, El-ameen yace "Meye
haka?" Junaid yace "Nothing, na shawo kan Ummi ta hakura wllh" kallonsa kawai El-
ameen yake bai ce komai ba.

Bayan kwana biyu da ya kama ran lahadi Humainah ce tsaye kitchen tana girkin lunch
Jasmine na daga bakin kofar kitchen din tsaye duk ta cika ta da surutu ita dai
aikinta take ba tare da ta tanka ta ba don da tace ta tafi xata dawo, junaid kuma
na sama, danna bell aka yi Jasmine ta xaro ido tace "kila uncle koh Anty?" Humainah
bata tanka ta ba ta fita daga kitchen din, jasmine ta bi bayanta da sauri, suka isa
gun kofar a tare ta bude, wata yarinya da baxata wuce su ba ce tsaye bakin kofar
Humainah sai kallonta take don bata santa ba, yarinyar tayi murmushi tace "Baki san
ni ba koh, yi hakuri ruwan sha xa ki ban don Allah, na xo gidan aunt dina ne dake
layin nan ne wllh wai ashe jiya da daddare suka yi tafiya da mijinta gashi duk na
gaji bbu shagunan siyan ruwa nan kusa" Humainah tace "Ohk, shigo" yarinyar ta shigo
tana bin ko ina na parlon da kallo ta samu kujera ta xauna, fridge Humainah taje ta
dauko mata ruwa da drink ta ajiye mata, Yarinyar ta mata godiya tana murmushi
Humainah ta koma kitchen, kallon Jasmine da ta xauna kasa kusa da ita tana kallonta
yarinyar tayi tace "Sannu ya sunan ki?" Jasmine ta d'an wara ido tace "Uncle na
kira na jewel, captain na kira na Jasmine, Mamina na kirana Baby" yarinyar dai sai
kallonta take, Humainah dake kitchen tana jin su ta tabe baki ta ci gaba da
girkinta, yarinyar tace "Waye captain, waye Uncle?" Jasmine xata yi magana suka ji
taku stairs, shiru tayi tana kallon stairs din haka ma yarinyar har ya sauko, kallo
daya yayi masu ya dauke kai, yarinyar tace "Ina kwana" ya ji bai ji ba ita dai bata
sani ba don bai amsa ba ya shiga kitchen ya rufe kofar yana kallon Humainah yace
"Wacece ta shigo min gida?" Humainah ta daure fuska tace "Ruwa xata sha" ya wani
hade rai yace "Ruwa? Kika san daga inda take maxa fita ki sallameta kar ki sha
mamaki" bata tanka sa ba ta ci gaba da girkinta, ya bude kofar ya fice, kallon
Jasmine yayi yace "Come here" mikewa tayi ta bi bayansa don stairs ya nufa,
yarinyar ta bi su da kallo, fitowa Humainah tayi ta xauna parlor ganin bata ga
Jasmine parlon ba ta kalli stairs, yarinyar tace "Nagode kwarai 'yar uwa, ni sunana
Hadiza" Humainah tace "Welcome" yarinyar ta mika mata waya tace "Sa min number ki
mu dinga xumunci naga kina da kirki" Humainah ta karba ta sa mata number ta mika
mata, yarinyar tace "Suna fa?" Humainah ta gaya mata, tace "Allah sarki, amma
kishiyar ki ce wannan da na gan ku tare" Girgixa mata kai kawai Humainah tayi, tace
"Ayya, to ni xan koma xa mu ke xumunci" har bakin kofa Humainah ta rakata yarinyar
sai murmushi take ta fita daga parlon, Humainah ta kulle, ta koma kitchen. Da yamma
misalin karfe shidda motar El-ameen ya shigo gidan, Junaid dake daki ya mike yana
lekensa ta window don tun ranan basu sake haduwa ba, ko parking din arxiki bai yi
ba ya fito da ganinsa kasan yana cikin tashin hankali, junaid ya fashe da dariya
har da kyakyatawa ya sake curtain din ya koma kan gado ya dinga dariya, direct
dakinsa El-ameen ya nufa don bbu kowa parlon, kwankwasa kofar yayi junaid ya mike
xaune yace "Come in" ya tura kofar ya shiga yana kallon junaid dake ta kokarin
danne dariyarsa, junaid ya mike tsaye yace "Ya aka yi na ganka haka besty, me ya
faru" xaunawa kan gado El-ameen yayi ya rike kai, Junaid ya xauna gefensa yace
"Talk to me mana" El-ameen ya dago da kyar yace "Kaga abinda su ummi ke shirin min
sai kace wani mace, wllh not me" junaid yace "Me xa a maka?" El-ameen yace "Wai
aure!" Junaid ya xaro ido sai kuma ya fashe da dariya El-ameen ya mike yana
kallonsa, yayi mai isan sa sannan yace "Nima haka ka min" kofa El-ameen ya nufa
junaid ya rikosa da sauri yana dariya yace "Wllh ramawa na yi nima haka fa ka min"
da kyar ya lallaba El-ameen ya xauna, sannan yace "Toh kai yanxu kana da warce kake
so ne da har xaka damu kanka, ba gashi nima haka aka min ba kuma ina xaune lafiya?"
Shiru El-ameen yayi kafin yace "Ni ina da warce nake so" junaid yace "To wacece?"
Da kamar baxai ce komai ba sai kuma ya shafa kansa a hankali yace "Baby!" Kallonsa
junaid ya tsaya yi ko kiftawa bai yi, El-ameen ya mike yace "Kuma ita xan kai masu,
in ma basu yarda ba ni sai na aureta don Allah xan iya hallaka warce xa a hada ni
da" daga haka ya nufi kofa Junaid ya mike ya fixgosa yace "Wace babyn kake nufi?"
El-ameen yace "Warce ke gidan ka" wani kallo Junaid ya watsa masa yace "Sai ka jira
randa na maida ta gun iyayenta sai ka bi ta ka aureta, yanxu kam baka isa ba"
murmushi El-ameen yayi yace "Koh?"

*Haske[truncated by WhatsApp]

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By khaleesat Haiydar_�

Da sallama ta tura kofar parlon ta shigo rike da wani babban tray mai dauke da
abinci bayanta maids biyu wata dauke da bowl din fruit, wata kuma food warmers har
biyu, kallonta kawai suke har ta karaso makeken parlon ba tare da ta dago ba ta
ajiye tray din hannunta ta juya xata fita, a hankali El-ameen yace "Fatima!"
Tsayawa tayi amma bata juyo ba, Junaid dai sai kallonta yake, jin ba ace komai ba
tayi ficewarta daga parlon, saukowa El-ameen yayi ya dau fruit ya fara ci yana
kallon junaid, tun xuwan su Bauchi ya rasa dalilin sanyin da yayi lokaci guda, har
ya gama cin abinda xai ci junaid bai ko kalli abincin ba, El-ameen ya mike ya shiga
bedroom ya bar sa parlon, rike kai Junaid yayi don shi kadai yasan abinda ke
damunsa. Bayan isha ya fito makeken haraban masarautan sanye da kananun kaya ko ina
farin wuta ne wanda hakan ya maida gun kamar safiya, tafiya kawai yake hannunsa
cikin aljihu iska mai dadi na kadawa har ya karaso garden din da yasan xai ganta,
ai kam xaune ya ganta ita kadai kan lallausan rug tana sanye da alkyabba kalan gold
sai kyalli yake ta xauna kan kafafuwanta, ba wani wuta ne me haske gun shakatawar
ba, gabanta bowl ne me dauke da apple fruit, ya rasa me ta tsura ma ido a gun, har
ya karaso kusa da ita bata sani ba sai da sanyayyen kamshinsa ya bugi hancinta, duk
da haka bata juyo ba idonta na kan grasses din wajen, ya xauna d'an nesa da ita
cikin sanyin murya yace "Jasmine" bata kallesa ba bare tace komai, sake kiranta
yayi nan ma dai bata amsa ba, dawowa kusa da ita yayi ya kuma kiranta a karo na
uku, juyawa tayi tana kallonsa bbu yabo bbu fallasa tace "Sunana ba Jasmine ba"
helplessly yake kallonta a hankali yace "Ohk fatima" dauke kai tayi bata ce komai
ba, bai sake cewa komai ba lokaci lokaci ya kan juya ya kalleta, mikewa tayi daga
karshe ta dau apple daya tace "Am going in" daga haka ta yi gaba ta bar sa wajen,
ya bi ta da ido, lumshe ido yayi ya hade kansa da gwiwa, a hanya ta hadu da El-
ameen ya mata murmushi yace "Princess!" D'an murmushin ita ma tayi ta wuce bata ce
komai ba. Bangaren Ummanta ta nufa ta sameta xaune da baki da dama a babban
parlonta, sallama tayi masu ta yi hanyar dakinta duk aka bi ta da kallo, mikewa
Umma ta yi tayi excusing kanta ta bi bayanta, tana kokarin cire alkyabbarta ta
shigo dakin, ta juya tana kallon uwar tata, Umma ta kamota ta xaunar gefen royal
bed din dake dakin tace "Zahra!" Dago manyan idonta tayi tana kallonta tace "Na'am
ummana" Umma tace "Why didn't you greet at the parlor" a hankali tace "Na fa yi
sallama ummana" Umma tace "No da kin tsaya kin gaida su, they are ol here because
of you daughter" sunkuyar da kanta tayi tace "Am sorry Umma" Umma ta rungumeta
sosai jikinta lokaci daya hawaye ya taru idonta tace "It's OK sweetheart, kin kai
ma su Ahmad din abincin kuwa" gyada kai tayi tace "Na kai" Umma tace "Good je ki
gun Abba ki masa sai da safe, ko kin je?" tace "Naga yana da visitors ummana" Umma
tace "Suna masauki yanxu, tashi ki je" tace "Toh ummana" mikewa tayi ta mayar da
alkyabbar da ta cire suka fita dakin tare da umma, sai da ta fara karasawa cikin
babban parlon ta durkusa ta gaida matan dake xaune, duk suka amsa suna kallonta da
sha'awa, sannan ta mike ta fita, babban parlon Abbanta ta tafi sanin ya bar fada
yanxu, ta gansa xaune kasa kan lallausan carpet din dake shimfide fruits gabansa
daga gefensa Ya Abdul ne, sai yayyinta maza su hudu gaba, duk suka dinga kallonta
har ta karaso gun Abba dake ta kallonta shi ma murmushi shimfide fuskarsa, mikewa
xaune yayi yace "My princess" tayi murmushi tace "Abbana!" Ganin yanda yayyinta ke
kallonta ta hararesu tace "Ni bana son kallon" dariya suka yi gaba daya har da mai
martaba da ba kasafai yake dariya ba sai dai murmushi, da ganinsa kasan farin ciki
ne karara tare da shi, ya Abdul kadai ne kansa a kasa sai dai lokaci lokaci ya kan
dago ya kalleta, sun yi hira sosai da yayyin nata daga bisanni ta masu sai da safe
har da Abba ta koma bangaren Umma. Washegari da ya kama Friday ana sakkowa juma'a,
parlon mai martaba ya cika dam da 'yan uwa da abokan arxiki da suka taho nuna masa
farin cikinsu na bayyanar tilon 'yar sa, haka kuma ranan da su Junaid xa su koma
kenan kasancewar kwanan su uku a masarautan, Mai martaba sai kallon junaid da ko
dago Kai bai son yi yake, can yayi gyaran murya yace "Ahmad?" Kallonsa junaid yayi
sannan ya amsa, Mai martaba yace "Ka fadi duk abinda kake so nan duniya Ahmad in
dai bai saba ma Shari'a ba kuma bai fi karfina ma na maka alkawarin yi maka shi
koma menene" a baxata cewar sarkin ya xo ma junaid, ya sunkuyar da kai bai ce komai
ba, haka kawai gaban El-ameen dake gefensa ya dinga faduwa, junaid ya dago da kyar
yana kallonsa cikin sanyayyen muryarsa yace "Bana bukatan komai ran ka shi dade, I
helped her for Allah's own sake" kallonsa kawai sarkin ke yi daga bisanni ya juya
yana kallon El-ameen dake kallon junaid yace "Kai fa Aminu?" Ido junaid ya xuba
masa ya ji abinda xai ce, El-ameen da har lokacin gabansa bai bar faduwa ba cikin
tsarkewar murya yace "Ina son ka min alfarmar bani aurenta ran ka shi dade, na maka
alkawarin xan rike maka ita da amana...." wani mugun bugu xuciyar junaid yayi
lokaci daya yaji kamar xuciyar ta bar aiki, mai martaba da ya kafa ma El-ameen ido
yayi murmushi yace "Na baka! Bbu ko sisin ka kuma" Kallon mamaki duk occupant din
fadan ke ma mai martaba don baya magana biyu. El-ameen da ya rasa wani irin godiya
xai ma mai martaba ya mike ya isa gabansa ya durkusa yana kallonsa, shafa kansa mai
martaba yayi yace "You are blessed in'sha Allah son" kama hannunsa El-ameen yayi ya
lumshe idonsa da ya kada ya kai lips dinsa, junaid ya lumshe idonsa da ya kada shi
ma lokaci daya yana jin xuciyarsa kamar ba tasa ba.

*Haske writers association*馃挕


_Toh ga Captain Ahmad Junaid yayi gaba har ya kusa end_ Tnx for everything. My
novel inteesar if am not mistaken yana da pages kusan dari biyu, my novel ikram had
a hundred nd 15 pages or so, my novel Aneesah had 112 if am not mistaken, Dr
Khaleel had 120 pages also, 'ya mace kyautar Allah na goni also have the same, kuma
duk an san bbu ma banxa a novels din nan, I don't write anyhow may be just once in
a year, but idan nayi i will alwayz make sure it makes sense, am just in page 54 a
Capt Ajay kuma nasan nan gaba xai kai har 120 ne but see what my fans are saying,
you never judge a book by it cover, and am not in a haste while writing my books,
ban taba novel da na dakata for weeks ba sai capt a jay, toh kullum xan dinga xuwa
media ina announcement mahaifiyata bata da lafiya, ina ma nake da nutsuwar rubutu
uwa ta ba lafiya yanxu haka ma bata kasar, ga kuma karatu da nake, i can't be
coming to media and giving excuses everyday, all the same am grown up yanxu I won't
retaliate but nagode kwarai Allah bar xumunci. in ma jan labarin nayi you don't
have to be giving me hurt words, sai ka bar karantawa ka jira in kai inda kake so
sai ka ci gaba Meye a ciki. Duk Allah ya baku hakuri.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

55.....

Wani kallo junaid ke masa ya sake sa ya koma baya yace "Yess! Me ya hana ka son
auren nata lokacin da take hauka? You can call what ever prize you wish to for
giving her your attention and I will pay you" El-ameen bai ce masa komai ba ya
gyara kwalar rigar sa ya juya ya fita daga dakin, a stairs suka kusan cin karo da
Jasmine, ta koma baya ta wara ido ganinsa tace "Uncle! When did you come" murmushi
ya kirkirar mata yace "Am coming" ya bi ta gefenta ya sauka ta bi sa da kallo. Tana
jin fitar motarsa ta bata fuska tayi daki da sauri xata fara kuka. Washegari monday
Junaid na dawowa masallaci da asuba ya shiga dakin Humainah, ya sameta xaune kan
darduma daga bakin kofar ya tsaya yace "You are resuming school today" tace "Na
sani" juyawa yayi ya fita, ya bude dakin Jasmine, kwance ya ganta tana bacci cikin
bargo ya cire bargon ta mike xaune da sauri yace "Tashi kiyi sallah, after that you
brush ur teeth nd take ur bath" daga haka ya juya ya fita ya koma dakinsa, wanka
Humainah tayi ta gyara bedroom dinta ta fito parlor nan ma ta share sannan ta shiga
kitchen, ruwan lipton ta daura ta xuba kayan kamshi sannan ta fara peel din
potatoe. Karfe bakwai saura junaid ya fito daga bedroom sanye da uniform dinsa don
ranan sati biyun da ya dauka gun aiki ya cika, kitchen ya tafi ya tsaya daga bakin
kofa yana kallon Humainah, ta juya tayi masa kallo daya ta dauke kai, yace "Xan yi
tafiyata in kyale ki if you are not ready" tace "Toh ai dai ba xaune nake ba" bai
ce komai ba ya karasa cikin kitchen din ya dau cup ya hada tea ya fita. Yana xaune
parlor har karfe bakwai yayi Humainah ta fito ta wuce sama, can ya mike shi ma ya
tafi saman, dakin Jasmine ya bude ya ga ta gama sa kaya yace "Fito ki ci abinci"
shiru tayi tana kallonsa daga sama xuwa kasa yace "Baki ji na ne" komawa baya ta
shiga yi a hankali har lokacin idonta na kansa sai kuma ta fashe da kuka tana
girgixa kai tace "Ni bana son kayan nan captain" ya kalli farin shirt din uniform
da navy blue trousers din dake jikinsa yace "Me suka maki kayan" ta kuma fashe wa
da kuka tace "I don't like it" wani kallo ya mata ya juya ya fice daga dakin, a
hankali ta xauna gefen gado tana xaro ido kamar me son tuna abu, dakinsa ya koma ya
dauki wayarsa da hularsa ya fito, dai dai lokacin da Humainah ta fito ita ma rike
da cup, bai ko kalleta ba ya sauka downstairs ya dau makullin motarsa, ta bi
bayansa tace "Toh baxa ka kai ni makarantar ba?" Ba tare da ya kalleta ba yace "Sai
kuma gobe am late" daga haka ya fice daga parlon ta bi sa da kallo kamar xata fashe
da kuka, ajiye cup din hannunta tayi a parlon ta koma sama hawaye cike idonta.
Jasmine na jin fitar motarsa ta sauko ta tafi dining ta debi breakfast dinta ta ci
a nan ta koma sama. Da yamma misalin karfe hudu saura Humainah na dakinta bayan ta
daura girki a kitchen ta ji an danna bell, mikewa tayi ta fito dai dai lokacin da
Jasmine ma ta fito, ko kallonta bata yi ba ta sauka, bude kofar parlon tayi ta ga
yarinyar jiya a tsaye, murmushi yarinyar tayi tace "Kin gan ni kuma koh, daxu aunt
dina ta dawo na taho, yanxu ma gida xan koma nace bari in shigo mu gaisa" Humainah
ta d'an yi murmushi ita ma tace "Toh sannu da xuwa" hanya ta bata ta shigo ta xauna
parlon, yau ma kamar jiya ruwa ta kawo mata, yarinyar sai hira take mata kamar sun
dde da sanin juna, ita dai Humainah duk ta kasa sakewa, Jasmine ta shigo parlon
tana kallon Humainah tace "Anty ki kira min Uncle" Humainah tace "Bani da waya"
Jasmine tayi shiru bata ce komai ba, sai kuma ta juya ta koma sama, yarinyar da ta
kira kanta da hadiza tace "Amma wacece yarinyar nan?" Humainah tace "Kanwar mijina
ce" Hadiza tace "ohh, Allah sarki, amma basa kama ko dai 'yar uwar na family kike
nufi" a takaice Humainah tace "Eh!" Don duk ta kagu ta wuce sai kallon agogo take
sanin hudu da wani abu junaid ke dawowa wani time, Hadixa tace "Toh dai ki kula"
Kallonta Humainah tayi da sauri, hadiza tace "Naga yanda take wani shige masa jiya
da na xo" murmushi Humainah ta kirkira bata ce komai ba, hadiza tace "Ae ba abun
dariya bane, ni ma nan da kike ganina na kusa dawowa anguwar gaba daya gun aunt din
nan tawa sbda damuwa da yayi mata yawa, in gaya maki wata yarinya mijinta ya ajiye
wai yar uwarsa xata yi karatu a gidan, in kinga yarinyar very quiet har ni ke ce ma
Anty fa'ixa ta dinga sake mata don Allah don ko kallonta bata yi, to yanxu xancen
da nake maki Friday mai xuwa daurin auren mijin yayar tawa da yarinyar" kallonta
kawai Humainah ke yi gabanta na mugun faduwa, hadiza ta dawo kusa da ita tace "Bari
ki ga hotunan aunt din tawa da yarinyar har ma da mijin" kallon hoton kawai
Humainah ke yi amma sam hankalinta baya jikinta, bude gate din gidan aka yi, hadiza
ta bude ido tace "In ji dai ba mijin naki bane ya dawo" kasa ce mata komai Humainah
tayi, Hadiza tace "A'a kin ga ki fa kwantar da hankalin ki, ai ba duka maxan suka
taru suka xama daya ba kawai ke dai ki sa ido" Humainah bata ce komai ba still har
junaid ya shigo parlon, daga bakin kofa ya cire takalman kafarsa ya bar bakar
safar, kallonsu kawai yake a parlon lokaci daya ya hade rai, ya nufi stairs hadiza
ta bisa da kallo ta d'an bude murya tace "Ina yini" a tunanin ta jiyan da ya
shareta bai ji bane, ko kallonta bai yi ba bai kuma amsa ba ya haura sama, hadiza
tace "Toh bari in wuce naga kamar mijin ki bai son baki" Humainah tace "Rabu da
shi" dariya Hadiza tayi ta mike tace "Toh Hajiya Humainah kinga tafiyata, gobe ko
jibi xan ma dawo anguwar baki daya" Toh kawai Humainah ta iya ce mata ta rakata har
bakin kofa ta wuce sannan ta dawo ta tafi sama, tana shiga daki ta xauna gefen
gadonta tana tunanin maganganun Hadiza, bude kofar dakin aka yi ya shigo fuskar nan
tasa a daure ko uniform bai cire ba don fitina yace "Wace yar iskar ke xuwa gidan
nan?" Ko kallonsa bata yi ba ta dauke kai, ya karasa ya fixgota yace "keh! Baxa ki
gaya min wacece ita ba?" Fixge hannunta tayi tace "Mutum ce kuma ai ka gane ma
idonka" yace "Koh? To wllh wllh ta sake xuwa min gida xan baki mamaki daga ke har
ita" daga haka ya juya ya fice, kuka ta saki duk ta rasa me ke mata dadi sosai
xancen hadiza ya xauna a xuciyarta, mikewa tayi ta sauka kasa ta kashe girkin da
take ta koma daki. Har bayan magrib junaid na xaune daki duk abinda ya ma El-ameen
jiya ya tsaya masa ya rasa yanda xai yi, ta yaya ma xai ce yana son Jasmine, wani
irin so ma yake nufi, mikewa yayi daga karshe ya dau makullin motarsa ya fita, ana
kiran isha ya isa gidansu El-ameen, sai da yayi sllh a masallaci sannan ya shiga
gidan, xaune ya samesa a daki da faisal, faisal na ganin junaid ya bude ido yace
"Captain junaid, ashe ana ganin ka" murmushi junaid yayi ya xauna yace "Kai ma ai
ba ganin naka ake ba" hira suka d'an yi da faisal, shi dai El-ameen wayarsa kawai
yake dannawa, daga bisanni faisal yayi masu sallama yace xai tafi clinic ya fita,
Junaid ya kalli El-ameen da ya ki kallon inda yake yace "Har da wani pretending
baka gan ni ba?" Ba tare da El-ameen ya kallesa ba yace "Ai mun gaisa" Junaid ya
d'an shafa kai yace "Look, am sorry about what happened yesterday, I don't know
what came over me....." Katse sa El-ameen yayi yace "It's ohk, I also don't know
what came over me, i was just confused, I couldn't help it... May be dat was y I
uttered those words" shiru junaid yayi yana kallonsa ganin he was so serious, El-
ameen yace "Yess!" Junaid yace "No idan ma sonta kake da gaske ai ba komai bane,
just pray memorynta ya dawo a maidata gun iyayenta nd then you can go on...." Shiru
junaid yayi don jin maganar yayi wani iri a bakinsa, El-ameen yace "Noo, ni an min
mata ai" Junaid bai kuma cewa komai ba sai bayan kusan minti uku yace "Ohk gobe da
yamma ka raka ni ayi enrolling dinta a islamiyya, she so need it yanxu, ita kuma
Humainah is resuming school" El-ameen yace "Ohk" junaid na kallonsa yace "akwai
shirye shiryen da xa ayi ne na bikin?" No kawai El-ameen yace masa. Washegari
Tuesday junaid bai bari Humainah ta je school ba don bai son barin Jasmine ita
kadai a gida sai sunyi registering dinta a islamiyya, haka Humainah tayi ta kumbure
kumburenta ya wuce aiki abun sa, kwata kwata ranan bata sake ma Jasmine ba, sai
taji ina ma Hadiza xata xo ranan ma amma har Junaid ya dawo bata xo, bai damu da
girkin da bata yi ba don sai ya ci abinci yake dawowa, Karfe biyar saura ya shiga
dakin Jasmine ya ganta kwance tayi jigum, tana ganinsa ta mike xaune yace "Sa hijab
din ki ki fito" ba musu tai yanda yace ta fito parlor, sai ga Humainah ma ta sauko
ta tsaya bakin stairs tana kallonsu ta wani hade rai, Ko kallonta junaid bai yi ba
yana kallon Jasmine yace "Mu je" ta bi bayansa xa su fita Humainah ta rufe kofar
tana masa wani kallo sai kuma ta fashe da kuka tace "Ni wllh xan hada ka da Abba na
gaji haka kuma" Jasmine dai sai kallonta take, junaid ya fixgota yace "rashin
kunyar ki ta da ne xai dawo koh?" Bai jira cewarta ba ya turata one side ya kama
hannun Jasmine suka fita ta fashe da kuka sosai ta haura sama da sauri, Junaid ya
kira El-ameen ya fi sau biyu kafin ya daga, bai damu da hakan ba ya gaya masa
islamiyyan da xai taho ya samesu, ya fi minti talatin yana jiransa kafin ya xo, a
tare suka shiga babban makarantar suka yi duk abinda ya dace junaid ya bada kudi,
aji hudu aka sa ta bayan yayi bayanin ailment dinta, shi dai El-ameen kallonsu
kawai yake, suna fitowa makarantar xa su shiga mota junaid ya hango Hafsat sanye da
uniform din makarantar da hijab, tuni El-ameen ya shige mota Jasmine ma ta bude
bayan motar ta shiga tana kallonsa, Hafsat bata lura da Junaid ba xata wuce yace
"Hafsat!" Juyowa tayi da sauri tana kallonsa, murmushi yayi yace "kwana biyu"
dawowa tayi ita ma tayi murmushin tace "Alhmdllh" yace "Nan kike knn" kai ta gyada
masa, ganin duk tayi wani iri yana kallonta yace "Baki da lafiya amma koh?"
Murmushi ta kirkira tace "Am getting married ne" ya d'an bude ido yace "Ohh really,
when?" kamar baxa ta ce komai sai kuma tace "Friday" Junaid yace "Toh Allah ya
sanya alkhairi, but shine bbu gayyata"
bata ce komai ba, ganin kamar bata son maganan yasa yayi mata sallama tayi
wucewarta ya shiga mota.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

56.....

Kallo daya junaid yayi masu ya tada motar ya ja suka bar wajen, yana jin Jasmine
tace "Uncle why didn't you want to talk to me?" Ba tare da El-ameen ya kalleta ba
yace "Am meditating!" Ta wara ido tace "Ohh What's that?" Da Hannu ya mata alamar
da tayi shiru, tayi shiru tana kallonsa, ganin junaid gidansa ya nufa El-ameen yace
"Hey drop me, gida xan tafi" junaid bai ce komai ba yayi parking ya bude motar ya
fita ya daga ma Jasmine hannu ta hade rai tana kallonsa, murmushi yayi ya rufe
motar junaid ya ja motar ya kama hanyar gida. Yana gama parking ta bude motar ta
fice ta nufi parlor, daki ta shige ta sa key ta fashe da kuka. Washegari karfe
bakwai da minti goma duk suka bar gidan, farin riga ne jikinsa sai wandon uniform
don bai son ya ji Jasmine tace bata son kayan, ita dai Humainah ko kallonsa bata yi
ba ta wani hade rai gaban mota, jasmine ya fara ajiyewa islamiyya, sannan ya tafi
da Humainah makarantar da tace take so na su fatima, yana gama parking ya dau shirt
din uniform dinsa ya sa sannan ya bude motar ya fita ta bi bayansa, nan take ya
biya komai ya fice ya nufi office abun sa. Da yamma yana barin gun aiki Jasmine ya
fara xuwa dauka don hudu suke tashi, da fara'arta ta karaso gun motar, kamar daxu
da safe bbu uniform jikinsa sai wandon, ta wara masa ido tace "Captain nayi frnds
guda uku, kuma suna koya min karatu I like them" kai kawai ya gyada mata ta bude
motar xata shiga yace "Koma baya" ba musu ta rufe ta koma baya, ya ja motar ya kama
hanyar gida, bai yi mamakin ganin Humainah ta dawo ba, Jasmine ta durkusa kusa da
ita a parlor don xaune take tana cin abinci, ai ko ta wani hade rai, Jasmine tace
"Anty nayi frnds uku" banxa da ita Humainah tayi, Junaid na kallon Jasmine yace
"Tashi ki tafi sama" mikewa tayi, ta yi yanda yace mata. Shirye shiryen biki ake
tayi gidansu El-ameen, har ya fi junaid shiga damuwa amma ko a jikin umminsa da
Abba, ana saura kwana biyu daurin auren Junaid ya je gidan don har lokacin bai
kirasa ba, kallon arxiki El-ameen bai masa ba, shi ko bai damu ba ya dinga danna
waya abun sa, ana kiran magrib ya bar gidan. Ran saturday misalin karfe sha daya
junaid na tsaye bedroom dinsa sanye da farar shadda yana kokarin saka wristwatch,
Humainah ta shigo dakin, sanye take da riga da skirt Holland da ya mata kyau ba
kadan ba, ta madubi yake kallonta har ta karaso cikin dakin tace "Ina son xuwa gida
yau ya Ahmad" juyawa yayi ya kalleta ya dauke kai ya gama sa agogon sannan yace
"Gun Daurin aure xan tafi yanxu, sai ki jira next time" tace "Amma nasan hanya na
ga" yace "toh ko kin je wa xa ki samu a gidan bayan duk biki xa su" tace "Ehh nima
sai in bisu ae" shareta yayi don bai son barin Jasmine kadai a gidan ne, tace "Ka
ji?" Ya hade rai yace "ki jira ran lahadi in kai ki don't disturb me plss" kallonsa
ta tsaya yi hawaye ya cika idonta, ya dau makullin motarsa ya fita ya bar ta nan
tsaye, dakin Jasmine ya shiga ya ganta xaune kan darduma da Qur'ani gabanta, sosai
take catch up, amma da ganin ta kasan ta san su a da ne shi yasa, ya durkusa
gabanta yana kallonta a hankali yace "Mu'allima Jasmine!" Dago manyan idonta tayi
ta kallesa sai kuma tayi murmushi ta rufe fuska, murya can kasa tace "Captain kayi
kyau" yace "Uhnn koh?" Ta gyada masa kai yace "Uncle din ki xai yi aure yau, can
xan je" ta xaro ido tace "Toh ni baxan je ba? kuma ni bai gaya min ba" kamar xata
yi kuka ta kare maganar, Langwabar da kai yayi yace "Maza kadai ke xuwa ai" shiru
tayi bata ce komai ba, ya kamo hannunta yace "gobe sai na kai ki gidan ki ga
amaryar" kai ta masa nodding a hankali tace "Toh" ya dago chin dinta yace "Tea'n ya
ishe ki?" Tace "Uhm na koshi" yace "Ohk," sannan ya mike ya daga mata hannu ya nufi
kofa, bin sa da kallo tayi har ya isa kofa, a hankali tace "Kayi kyau" juyowa yayi
da sauri sai kuma yayi murmushi yace "Ae kin gaya min" sunkuyar da kai tayi ya juya
ya fita, har xai sauka sai kuma ya shiga dakin Humainah, xaune ya ganta ta hade kai
da gwiwa, ya karasa kan gadon ya dagota ya ga kuka take, xaunawa yayi gefenta ya
jawota jikinsa yace "Toh ba nace maki ran Sunday xan kai ki ba" ta fashe da wani
sabon kukan, ya rungumeta yace "Toh yi hakuri, da yamma sai in kai ki by then su ma
sun koma gida" shiru tayi bata ce komai ba, yace "kin ji" dago kai tayi tana
kallonsa, ya buda mata ido ya ciro wayarsa ya shiga daukarsu hotuna, mikewa yayi
daga karshe yace "sai na dawo" daga haka ya fita daga dakin, direct gun daurin
auren ya tafi, El-ameen yi yayi kamar bai taba saninsa ba, shi kam ko a jikinsa don
dariya ma yake basa, nan dai aka daura auren a kan sadaki dubu dari biyu, ko minti
biyar Junaid bai kara ba ya bar wajen ya tafi gida abun sa. Misalin karfe biyar aka
danna bell, Humainah dake kitchen tana girka supper ta fito da sauri tana kallon
kofar, karasawa tayi tun kan junaid ya fito ta bude kofar ta ga hadiza tsaye, sosai
gabanta ya fadi, hadiza tace "Gida ni kadai nace bari in yo nan!" Humainah ta
kirkiri murmushi tace "Shigo mana" shigowa hadiza tayi Humainah tace "Mu je daki"
ba musu Hadiza ta bi bayanta, Humainah dake ta addu'ar kar junaid ya fito ta bude
dakinta da sauri ta shiga hadiza ta bi bayanta, hadiza tace "Ko dai mijin ki na nan
ne" Humainah tayi murmushi tace "Yana nan" Hadiza tace "Atoh bari in tafi, amma shi
bai xuwa gun aiki ne...." Humainah tayi dariya tace "No kiyi xaman ki ai ba shigowa
xae yi ba, karfe hudu xuwa biyar yake dawowa daga aiki" Hadiza ta xauna gefe tace
"Mijin naki ne naga bai fiye son mutane ba" Humainah ta yi yake tace "Bari in duba
girki a kitchen" daga haka ta fita daga dakin. Dakin Junaid ta nufa ta tura a
hankali ta gansa xaune yana kallo a laptop, xata rufe kofar yace "Who rang the
bell?" Rasa abinda xata ce tayi, ta bude hannu alamar bata sani ba ta juya ta fita,
kitchen ta koma don ci gaba da girkinta ta ga Jasmine tsaye tana juya miyan, wani
kallo ta watsa mata tace "Wa ya sa ki?" Jasmine ta ajiye cokalin hannunta tace
"Taya ki nake" Humainah tace "Fita!" Ba musu ta fita dai dai lkcn da aka danna
kararrawan parlor, kallon kofar tayi ta karasa ta bude, su uku ne tsaye bakin kofar
ta tsaya kallonsu, daya daga cikinsu yayi murmushi yace "Hi, Ahmad na nan?" Ta d'an
bude ido tace "Waye shi?" Na gefensa yace "Junaid!" Ta kuma bude ido tace "Waye
shi?" Kallonta suka tsaya yi gaba daya, ta girgixa kai tace "A'a mu bamu da Ahmad
junaid a gidan nan, Captain kawai muke da" xaro ido suka yi gaba daya suka fara
dariya, murmushi tayi ita ma tana kallonsu, daya yace "Toh ina captain din?" Tace
"Bari in kira sa" Juyawa tayi ta gansa bakin stairs a tsaye ya hade rai yana
kallonta, ta juya ta kalli kofar kitchen taga Humainah ma tsaye tana kallonta,
karasowa captain yayi parlon yana kallon colleagues din nasa, Capt Umar yace "Ehh
lallai kam captain kadai gare su a gidan, dubi wani kallo da yake ma mutane"
murmushi junaid ya kirkira yace "Sannun ku da xuwa, ku karaso mana" Capt kb yace
"the great Aj, bamu gan ka gun daurin auren aminin naka ba" junaid ya bude ido yace
"ohh! Ae kam na je, kawai dai na bar gun da wuri ne" karasawa cikin parlon suka yi
duk suka xauna, Tuni Humainah ta koma kitchen ta ci gaba da aikinta, Gaisawa junaid
yayi da frnds din nasa, har lokacin Jasmine bata bar parlon ba duk da satan
kallonta da yake yana hararanta, durkusawa tayi kusa da shi tace "Captain in kawo
masu ruwa?" Kai kawai ya gyada mata ba tare da ya kalleta ba, Ta mike ta nufi
kitchen, Capt Mk yace "Sistern ka ce amma wannan" kai junaid ya gyada ba tare da ya
kallesa ba, Capt kb yace "Ahhh toh ni dai ina ciki, har ta fi ka kyau wllh, ina
kama kafa ni dai yaya Ahmad" dariya sauran suka yi, Capt Mk ya hade rai yace "Ae
don ta min ne shi yasa na tambayi ko kanwar sa ce...." Dariya Capt Umar yake yana
kallonsu duka yace "Toh duk na riga ku wllh, tana bude kofar ta min, na dai yi
shiru ne kawai" Sosai junaid ya daure fuska bai ce komai ba, Capt Mk yace "Toh pa,
ya da hada rai Ahmad ko dai ba blood sis bace?" Wara ido junaid yyi yace "Kai haba
blood one kuwa, irin ni babban yaya din nan shi yasa na daure fuska duk ku gama
haukan ku....." dariya suka yi gaba daya, jasmine ta shigo parlon da goran ruwa
guda uku a hannu duk ta mimmika masu, tace "Anty baxa ta bar ni in shiga kitchen in
dauko cups ba" Kb yace "Gaskiya Anty bata kyauta ba, toh ya sunan ki?" Ta kalli
junaid da ke kallon wani gun daban tayi dariya ta xauna tace "Ka ga Captain yana ce
min Jasmine, Uncle na ce min jewel, mamina na ce min Baby" kb yace "Waow that's
nyc, i will call you jewel also!" Ta kalli junaid xata yi magana ya mata wani mugun
harara, mikewa tayi da sauri tace "In tafi Captain?" Yace "Ehh" juyawa tayi ta tafi
sama, duk su ka bi ta da kallo, Mk yace "Uhmm! But ya aka yi ban santa ba Aj,
fatima da khadija kawai na sani" Junaid yace "Ehh ba tare mu ke da ita ba" Humainah
ce ta fito daga kitchen ta karaso cikin parlon ta tsaya daga bayan kujera ta gaida
su, da fara'a suka amsa mata suna tsokanarta ta kara gaba abunta, dakinta ta shiga
ta ga hadiza xaune har lokacin, ita har ta ma mance da ita, rufe kofar tayi tace
"Kiyi hakuri girki nake ne" hadiza tace "Ba komai, nima nasan aunt dina kila ta
dawo yanxu, tafiya xan yi" Humainah tace "Ki jira ki ci abinci mana, baki yayi a
parlon yanxu xa su tafi" xaunawa Humainah tayi Hadiza ta fara mata hira ita dai sai
uhn uhn take don bata son junaid ya ji muryarsu, shidda saura junaid ya raka frnds
din nasa har bakin mota yayi masu godiya yace "Kun dai ki cin abinci" Mk yace "Kai
kuma ka ki barin mu yi sallama da jewel, ni dai ina nan dawowa gobe" KB yace "kai
ka ma kai shi har gobe, bayan isha ni ina nan xuwa" dariya suka yi gaba daya banda
Junaid da yace "Ai duk kuna da 'yan mata na ga" sun kusa minti sha biyar tsaye daga
bisanni suka wuce ya koma ciki, Tuni Humainah ta sauka kasa ta debo ma Hadiza
abinci jin fitarsu, yana haurowa sama dakin Jasmine ya bude, ya ganta tsaye bakin
window tana kallon waje, hade rai yayi yace "From henceforth aka sake ring din bell
kika sauka kika bude kofa
I will slappp you, wani ya saki ne?" Kallonsa ta tsaya yi, hadiza dake jin duk
abinda yace ta kalli Humainah murya can kasa tace "Toh fah" Jasmine kam bata ce
komai ba sai kallonsa take kamar bata gane me yace ba din nan, ya karaso cikin
dakin a fusace yana mata mugun kallo yace "Kin ji abinda nace?" Girgixa masa kai
tayi da sauri, ya dawo kusa da ita strictly yace "Nace daga yau kar ki kuma fitowa
parlor idan aka ring din bell, kuma na sake ganin kin tsaya magana da maxa har kina
gaya masu sunan ki sai na maki mari!" Sunkuyar da kai tayi cikin tsawa yace "Kin
ji?" Ta gyada masa kai hawaye cike idonta, juyawa yyi ya fice daga dakin. Hadiza
tace "Toh fah, don Allah ki gaya min yanda kuke da yarinyar nan" Humainah ta tabe
baki kamar baxata ce komai ba sai kuma tace "Yar uwarsa ce" hadiza tace "Tabdi toh
Meye kuma na hanata magana da maxa, aurenta shi xai yi ko me?" Hade rai Humainah
tayi bata ce komai ba, Hadiza tace "Toh ae ba xancen hade rai bane, wllh ki sa ido
kar abinda ya samu yayata ya same ki, abu na biyu kuma na ga bbu wani interaction
mai karfi tsakanin ki da mijin ki, anya kuwa?" Shiru Humainah tayi bata ce komai
ba, Hadiza tace "Tabdi, to auren dole aka maku ne, yo ko da auren dolen ne ma ke ba
mace bace baki san yanda xa ki ja mijin ki jiki ba, ai kam xa ki tsaya kallon
ruwa...." Ita dai Humainah har lokacin bata ce komai ba, Hadiza tace "Ya ina magana
xa ki share ni, ni tun randa na ganki naji Allah ya dora min san ki banda haka
wannan ai ba hurumin da xan shiga bane, batun gaskiya Humainah da sake a xaman
auren ki, ga mijin ki hadadde me kyau da shi xa ki tsaya wasa wata ta kwace maki,
lallai ma" mikewa tayi tace "Kin ga tafiyata abincin ma ya ishe ni" Humainah da duk
jikinta ya mutu tace "A'a don Allah ki kara..." Hadiza tace "Tafiya xan yi" daga
haka ta nufi kofa fuu irin tayi fushi din nan ita, Humainah ta bi ta da sauri don
ita tsoronta kar junaid ma ya ganta, tuni hadiza ta fice daga gidan gaba daya,
Humainah ta sauke ajiyar xuciya tana naxarin maganganun ta, xama tayi bakin gado
tayi tagumi hawaye ya cika idonta, to ita ta ma san yanda xata yi da junaid, da
kyar ta iya mikewa ta shiga bayi ta dauro alwala don yin magrib, ta jima xaune kan
darduma daga bisanni ta mike ta fita daga dakin ta sauka kasa, kitchen ta tafi ta
hada masa abincinsa a tray, ta gama xata fita Jasmine ta shigo kitchen din ta tsaya
daga bakin kofa tace "Anty abinci na" ba tare da Humainah ta kalleta ba tace "Ban
yi da ke ba, ki shiga ki dafa" Jasmine tace "Na'am" juyawa Humainah tayi ta fice
daga kitchen din ta bar ta nan tsaye. Junaid na waya Humainah ta shigo dakin, ta
ajiye abinci har lokacin bata mike daga durkushen da tayi ba, yana gama wayar ya
juya yana kallonta ya d'an bude ido yace "Uhun! Yau kuma" hade rai tayi, yayi
murmushi yace "Toh na gode, kin ba Jasmine na ta?" Kallonsa kawai take, can ta tabe
baki tace "Kace da magrib xaka kai ni gida" yace "Ohh shi sa aka kawo min abinci,
to ni gidansu El-ameen xan tafi yanxu" kuka ta fashe da tana kallonsa, ya sauko
kasa ya dawo kusa da ita shi ma ya durkusa ya fara kwaikwayonta, duka ta shiga kai
masa tana cewa "Ni ka kyaleni bana so" dariya yayi yace "Sai in dawo captain din
yanxu, ni kike duka" dagota yayi suka koma kan gado yace "Gobe lahadi kin ga sai in
kai ki tun asuba sai sha biyun dare xan je daukan ki" ta tsaida kukan tace "Kace
Allah" yace "Sai na ce?" Shiru tayi tana kallonsa, ya ja hancinta yace "Allah"
murmushi tayi ta fada kansa tace "Toh na gode" can kuma ta mike ya bi ta da kallo
har ta fita, abincin ya bude ya ga tuwon shinkafa ne da miyar vegetable..... " ya
dau plate da spoon ya dibi kadan ya ci snn ya rufe ya mike, wanka ya shiga ya fito
ya shirya don xuwa gidansu El-ameen duk ya kagu yaga matar aminin nasa, dakin
Jasmine ya shiga ya ganta xaune kasa ta daura kanta kan gado, yace "Kin ci abinci?"
Ta girgixa masa kai, yace "Bata baki bane?" Ta sake girgixa masa kai, shiru yayi
sannan yace "Je daki na ki dauki nawa" tace "Toh" sannan ta mike ta fita ta shiga
dakinsa bude abincin tayi da miya sai kuma ta dawo tace "Dukka xan dauka?" Yace
"Ehh" komawa tayi sai ga ta ta dawo da tray din, murmushi yayi ya juya ya fita daga
dakin.

*Haske writers association*馃挕

_Tnx all for the prayers sisters Allah ya kara ma duk musulmai lafiya Ameen_ Sorry
for keeping you all waiting sisters.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

57.....

Junaid na fita gidan ya kira wayar Faisal, yana dagawa yace "Ya? ku na ina yanxu?"
Faisal yace "Kai kam sam baka da kirki captain" junaid yace "That's constant
ai...." Faisal yace "Toh yayi kyau muna shirin kai ango..." Dariya junaid yayi yace
"Ohk toh gani nan xuwa kar rashin kirkin yayi yawa koh?" daga haka ya katse wayar
ya dau hanyar gidansu El-ameen, El-ameen na cin abinci a dakinsa Junaid ya shigo,
junaid yace "Tab har daman cin abinci ka samu kenan, ni tym din nawa ina na samu
wannan daman....." Ko kallonsa El-ameen bai yi ba ya hade rai, dariya sosai Junaid
yayi yace "Harara a duhu kawai kake yi" Dr faruq yace "Ni na ma yi xaton tafiya
kayi Ahmad, bikin aminin naka guda ace baka kusa" Junaid ya shafa kansa yace "Daxun
nan na dawo bana nan" faisal yace "ga alama mun gani" murmushi junaid yayi bai kuma
cewa komai ba, ya mike ya bude closet din El-ameen ya fiddo wani dakakken shadda
sky blue ya ajiye masa ya koma gun huluna ya fiddo wanda xai shiga da kayan ya
ajiye masa, ya dauki agogo me tsada cikin agogunansa ya daura kan kayan yana
murmushi yace "Ka tashi ka shirya time na wucewa" wani kallo El-ameen yayi masa ya
ci gaba da cin abincinsa, can ya ajiye abincin ya mike yana kallonsu faisal yace
"Ku tashi mu je" daga haka ya nufi kofa Junaid ya fixgosa yace "Ka ma isa, da
wannan kayan da kke yawo tun safe xa mu kai ka" dariya faruqh yayi yace "Gaskiya ne
wnn kuma, go nd change frnd" duk yanda suka yi da El-ameen kin canxa kayan yayi,
sai da wani abokinsa Dr Lawal ya sa baki, sosai kayan suka yi masa kyau don bai
taba sa su ba ma, junaid sai dariya yake har su faruqh suka dinga mamaki wai ashe
dai yana interacting haka da mutane shidai baice musu komai ba, Karfe takwas da
rabi suka bar gidan bayan El-ameen ya sallami parent dinsa, karfe tara da kusan
rabi suka isa gidan nasa, junaid ya kashe mota don shi ke driving din ya juya yana
kallon El-ameen murmushi dauke fuskarsa yace "Toh gashi mun kawo ka frnd, mu iyakar
mu kenan, Allah ya bada xaman lafiya.." Kallonsa kawai El-ameen ke yi, faisal yayi
dariya yace "Ya ka yi shiru ango" faruqh yace "Manta da su, har ciki xa mu raka ka
Dr" daga haka ya bude motar ya fita Lawal ma ya fita yana dariya yace "Fadi kawai
suke, but har ciki za mu raka ka, ai dole mu bada amanarka" bude motar El-ameen ma
yayi ya fita ya nufi gate din, Junaid ya dinga dariya har ya shiga da su faruqh, ya
juya ya kalli faisal yace "Ba don halinsa ba mu shiga faisal" faisal yace "A'a ku
shiga ku fito ina nan" daga haka Junaid ya bude motar ya fita ya shiga gidan shi
ma, duk xama suka yi a parlor har El-ameen aka rasa wanda xai haura sama, junaid
yace "Wai tsoro ku ke ko me, to ni bari in je in sauko da ita" daga haka ya nufi
sama, El-ameen ya mike ya bi bayansa, bakin kofar dakin ya ga junaid tsaye kam,
abun ya ba sa dariya yana isa bakin kofar ya tura sa cikin dakin, tana xaune gefen
gado fuskarta a rufe, da sauri junaid ya juya ya fito yana kallon El-ameen yace
"Meye haka kuma" El-ameen ya janyesa daga bakin kofar ya shiga dakin, bin sa junaid
yayi yana shafa kai, har gabanta ya isa ya tsaya, ita dai bata dago ba har lkcn
kanta a rufe, fixge mayafin El-ameen yayi, junaid ya fixgosa dan kada yayi
b'aramb'arama, ita ko ta rufe fuskarta da kafarta da sauri, El-ameen yace "A ina
kika san ni da har kika ce kina son aurena?" Mikewa tayi tsaye tace "I shud be
asking you your silly ques.....!" shiru tayi tana kallonsa, can ta juya ta kalli
junaid da ya xaro ido yana kallonta, shi kansa El-ameen din kallon mamaki yake
mata, ta sulale kasa ta fashe da kuka tana kallonsu, Juyawa El-ameen yayi kamar xai
tashi sama ya fice daga dakin, Junaid ya bi sa da kallo, can ya kalleta yace
"Hafsat!" Ta daga kai tana kallonsa, rasa abinda xai ce mata yayi, can ya dau stool
din dake gaban mirror ya xauna yana kallonta yace "Did you know him?" Girgixa kanta
tayi hawaye na sakko mata, yace "Then how's this, I mean did it all happen?!" Share
hawayenta ta shiga yi a hankali tace "Ni ban san sa ba, Abbansa ne abokin dad dina
I think, kawai ni dai Abbana yace min he's getting me married, that's all I
know...." Junaid yayi shiru kafin yace "But kinsan yan gidansu?" Gyada masa kai
tayi tace "Eh nasan Ummi da Sumayya" yace "Shine dai baki sani ba kenan?" Kai ta
gyada masa nan ma, junaid yayi murmushi yace "Ki kwantar da hankalin ki, Ahmad is
my frnd, a childhood frnd, he will be of a good husband idan kin masa biyayya, just
ki cire a ran ki cewar ba a son ranki aka yi auren nan ba, ki bi mijin ki, you will
like him, infact love him ma dai" ita dai bata dago ba bata kuma ce komai ba, ya
dade xaune yana bata magana masu kwantar da hankali, daga bisanni yace "Kin ji
Hafsat?" Hawaye na bin kuncinta ta gyada masa kai alamar toh, yayi murmushi ya mike
yace "Toh Allah bada xaman lafiya" daga haka ya fita, El-ameen kadai ya gani xaune
parlor, El-ameen na ganinsa ya mike ya nufesa yace "Da kai aka hada baki aka min
auren nan koh Ahmad" Junaid yace "Toh ya xa kayi da ni" daga haka ya nufi kofa El-
ameen ya bi sa da kallo har ya fita. Ko da junaid ya koma gida dakin Jasmine ya
fara shiga yaga har tayi bacci, rage Acn dakin yayi ya sa mata blanket ya dawo dai
dai kanta ya durkusa yana kallon fuskarta murya can kasa yace "Good nyt dear" ya
fad'a tare da lumshe idonshi yana bud'esu a hankali, mikewa yayi ya kashe wutan
dakin ya fita, dakinsa ya shiga yayi wanka ya canxa xuwa pyjamas dinsa, ya jima
xaune gefen gado daga karshe ya fita ya shiga dakin Humainah. Washegari da safe
yana xaune parlor yana kallon wani movie Humainah kuma na kitchen tana hada
breakfast Jasmine ta shigo parlon sanye da kayan islamiyya, kallonta kawai yake har
ta karaso kusa da shi ta durkusa tace "ina kwana" kallon kofar kitchen yayi sannan
ya kalleta yace "Sai yanxu kika tashi?" Girgixa masa Kai tayi tace "Wanka nayi" ido
ya tsura mata ta mike xata tafi, a hankali yace "Jasmine" dawowa tayi ta durkusa
tace "Na'am" yace "How was ur nyt?" Tace "Alhmdllh" yace "baxa ki islamiyya ba
yau!" Ta kallesa da sauri tace "fashi?" Shiru yayi kafin yace "Yes for only today
xa mu fita ne" tace "Toh" sannan ta mike ta nufi sama ya bi ta da ido. Karfe goma
da wani abu Humainah ta gama shirinta ta shiga dakin junaid, ta hade rai ganin
bacci ma yake, ta karasa gun gadon tace "Ya Ajay" a hankali ya bude ido yana
kallonta ta hade rai sosai tace "Na fa gama" jawota yayi ta fada kansa yace "So
early, nifa bacci nakeji?" ya fad'i yana lumshe ido, Ta turo baki tace "Dubi agogo
fa" ya kalli agogon yace "Toh ai jiya da daddare ni ban yi bacci ba" kwace kanta
tayi tace "Ni na hanaka" rikota yayi yace "Eh mana" murmushi kawai tayi tace "Ni
dai ka tashi ka shirya ya Ajay" yace "Toh naji hada min ruwan wanka" mikewa tayi ta
shiga bathroom din, ba a dau lokaci ba ta fito tace "Na hada" yace "Toh mu je ki
min" ficewa tayi daga dakin da sauri, yayi dariya yace "Ashe bbu inda xan kai ki
kuwa" sha biyu saura Junaid ya fito bayan ya shirya cikin kananun kaya, ya shiga
dakinta ya ganta xaune gaban mirror yace "Toh mu je" ta mike cike da jin dadi ta
dau hijab dinta da hand bag suka fita, sai da ya ga ta sauka downstairs sannan ya
shiga dakin Jasmine ya sameta tana bacci, tada ta yayi ta mike xaune tana kallonsa
yace "Kafin in dawo ki shirya kin ji" kai ta gyada masa ya juya ya fita, ana kiran
azahar ya isa gida Humainah ta fice da sauri daga motar bayan yayi parking ta nufi
cikin gidan, tabe baki yayi ya bude motar ya fito yayi part din Mumy shi ma, ko
minti goma cikakke bai yi gidan ba don duk hankalinsa na kan Jasmine dake gida ita
kadai, Mumy na lura da shi ita dai bata ce komai ba har ya bar gidan, Humainah duk
ta ji kamar ta bi sa tunawa da tayi gida xai koma. Yana isa sai da yayi sllh sannan
ya shiga gidan, ya kusa minti biyar a parlor kafin ya haura sama har xai shiga
dakinsa sai kuma ya bude dakinta, durkushe ya ganta a dakin daure da towel alamar
fitowarta daga wanka kenan, tana ganinsa tace "Captain Kaga towel din ya rike
earring din, yaki ya cire" kin karasawa yayi dakin har sai da ta kuma kiransa, ya
karaso ya durkusa shima ya shiga kokarin cire mata dan kunnen daga jikin tawul din,
haka kawai hannunsa ke rawa ta daga ido tana kallonsa tace "Captain" bai ce komai
ba ya kuma kasa cirewa, rike hannunsa tayi tace "Are you sick" bai kalleta ba bai
kuma ce komai ba, hakan yasa ta cire dan kunnen gaba daya daga kunnenta, sai a snn
ya daga ido yana kallonta, tace "Na cire" mikewa yayi ya fice daga dakin. Tana gama
shiryawa ta sauko parlor ta gansa kwance idonsa lumshe, daga bayan kujeran ta tsaya
tace "Captain na gama" bude ido yayi yana kallonta ya mike xaune, makullin motarsa
ya dauka yace "Toh mu je" gaba ta shiga ya bi bayanta har suka fita parlon ya rufe.
Front seat ya bude mata ta shiga sannan ya xaga ya bude maxaunin driver ya shiga ya
tada motar, sai da suka dau hanya sannan tace "Captain ina xa mu?" Bai tanka ta ba
hakan yasa tayi shiru bata kuma cewa komai ba, tafiyar kusan minti ashirin suka yi
yayi horn bakin gate aka bude gate din ya shiga yayi parking, kallonta yayi ta
sunkuyar da kai, ya bude motar ya fita yace "Come down" bude motar tayi ita ma ta
fito ya shiga gaba ta bi bayansa, ring din bell yayi ba a dau lokaci ba aka bude,
murmushi tayi ta basu hanya tace "Sannun ku da xuwa...." Junaid ya shiga parlon
yace "Yauwa amarya, yana ciki kuwa" shiru Hafsat tayi bata ce komai ba, Jasmine ta
hangosa tsaye bakin stairs ta wara ido tace "Uncle!" Da gudu ta karasa cikin parlon
daga Junaid har Hafsat suka bi ta da kallo, tana isa gun stairs din ta rungume sa,
murmushi El-ameen yayi ya janyeta jikinsa, Hafsat ta kalli junaid da ya dauke kai,
ita ma ta sunkuyar da kai, kama hannunts El-ameen yayi suka dawo parlon tace "Uncle
ban san nan captain xai kawo ni ba" junaid ya fiddo waya kamar xai yi kira ya juya
ya fice daga parlon, Jasmine tace "kuma Uncle yace min kayi aure da gaske ne?" Wara
ido yayi yace "uhn! He's lying" ta langwabar da kai tace "Ohh captain! Why him"
Juyawa tayi ta kalli Hafsat
dake tsaye har lkcn bakin kofa ta matsa kusa da shi a hankali tace "Who's she?"
Satan kallon Hafsat yayi yace "My sister" mikewa tayi tace "Ohk let me greet her"
kafin yace komai har ta isa gun Hafsat tace "Anty ina yini?" Hafsat ta d'an yi
murmushi tace "Lafiya lau, sannu da xuwa" Jasmine na murmushi tace "Ke sistern
uncle ce koh?" Kai Hafsat ta gyada mata, El-ameen ya mike yace "Xo ki xauna in kawo
maki drink ko baki so" dawowa parlon tayi tace "Ina so uncle" fridge ya nufa Hafsat
kuma ta nufi kitchen, hollandia drink ya dauko mata da goran ruwa daya sai glass
cup ya dawo kusa da ita ya xauna ya bude drink din ya xuba mata ya sha kadan ya
bata ta wara ido ta karba tace "Thank you uncle" Hafsat ta fito daga kitchen rike
da food warmers da plate a tray ta shigo parlon ta durkusa nan kusa da su tace "Ga
abinci!" Jasmine ta kalli El-ameen, bude abincin Hafsat tayi ta dibar mata ta sa
spoon ta mika mata, karba Jasmine tayi tace "Na gode Anty" murmushi Hafsat tayi
mata ta mike ta bar wajen, Jasmine ta sauko kasa tana kallon El-ameen tace "I like
her!" Murmushi yayi ya shafa kai bai ce komai ba, spoon din ta dauka ta fara cin
abincin tace "Uhnn akwai dadi" El-ameen ya karbi spoon din ya debi abincin shi ma
ya ci, mikewa Jasmine tayi da sauri ya kalleta yace "What?" Ta xaro ido tace "Ina
captain toh?" Kofa ta nufa da sauri El-ameen ya bi ta da kallo, tana fita ta gansa
xaune waje, tace "Baka shigo ba captain" mikewa yayi yana mata wani kallo yace "ina
takalmin ki?" Kallon parlor tayi yace "Tafi ki dauko...." Ta marairaice tace "Are
we going?" Wani mugun kallo yake mata xai yi magana El-ameen ya fito, kamar xata yi
kuka tace "Uncle wai tafiya xa mu yi" El-ameen yace "A'a mu je ki ci abincin ki"
juyawa tayi ta koma parlon, El-ameen ya d'aga ma junaid hannu yana murmushi yace
"In xaka shigo ka shigo malam" daga haka ya koma parlon, xaunawa Junaid yayi ya
dafe kansa, can ya mike ya sauka daga balcony din ya nufi motarsa ya shiga ya danna
horn mai gadi ya bude masa gate ya fice daga gidan, Jasmine tace "Uncle ya tafi"
El-ameen yace "Ci abincin ki" a hankali tace "Toh" ta ci gaba da cin abincin ta,
yana nan xaune har ta gama ta mike tace "Na gama uncle ka tafi da ni gida" shiru
yayi yana kallonta, ta koma ta xauna ta marairaice tace "Ka ji?" Yace "Nan ba gida
bane?" Bin parlon tayi da kallo a hankali tace "Gidan Captain xaka kai ni" hade rai
yayi yace "ina aiki a sama sai na gama" daga haka ya haura sama ya bar ta wajen,
mikewa tayi ta bi sa da kallo kamar xata yi kuka, ko minti biyar ba ayi da
tafiyarsa sama ba, Hafsat ta sauko tace "Har kin gama" gyada mata kai tayi, Hafsat
tace "Toh taho mu je sama" ba musu Jasmine ta nufi stairs suka haura sama a tare
Hafsat ta shiga da ita dakinta ta nuna mata gado ta xauna, sannan ta kunna mata
kallo. Har bayan la'asar Jasmine na dakin tayi rub da ciki kan gado tana kallo,
Hafsat kuma na ta danne danne a laptop aka bude kofar dakin duk suka juya kallonsa,
karasowa cikin dakin yayi yana kallon Jasmine yace "Kin yi sllh" gyada mata kai
yayi, ya d'an saci kallon Hafsat suka hada ido ya dauke kai da sauri, Jasmine tace
"Anty ce kawai ya rage tayi sallah"

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

58__59
Kallon Hafsat da ta dauke kai El-ameen yayi, sannan ya juya ya fita daga dakin,
Hafsat tace "Is there any need of you telling him I've not prayed?" Jasmine ta wara
ido tace "Ohk sorry" murmushi Hafsat tayi ta ci gaba da danna laptop dinta, dab da
magrib aka danna bell Jasmine ta mike Hafsat tace "Ina xa ki?" Jasmine tace "To
open the door" Hafsat tace "No! Ur uncle will do that" komawa tayi ta xauna har aka
kira sallah Hafsat tace taje tayi alwala. Karfe bakwai da rabi El-ameen ya shigo
dakin ya ajiye basket din abincin hannunsa ya fita, Hafsat ta mike ta dauko abincin
ta bude ta dibar ma Jasmine ta bata, har kusan karfe goma suna zaune dakin Jasmine
tace "Baxa mu je muyi ma uncle hira ba?" Hafsat tace "Je ki samesa a parlor" mikewa
tayi xata fita Hafsat tace "Tafi da plates din ki kai kitchen daga nan" dawowa tayi
ta dauka sannan ta fita, yana xaune parlor yana kallon news ya bi ta da kallo har
ts shiga kitchen din ta fito ta karaso cikin parlon ta xauna kasa kusa da shi tace
"Uncle ka ci abinci?" Girgixa mata kai yayi tace "Why?" Yace "Ba a bani ba ai"
mikewa tayi yace "Ina xa ki?" Tace "Ina xuwa" dakin Hafsat ta koma ta langwabar da
kai tace "Anty Uncle yace yunwa yake ji ki kawo masa abinci" daga haka ta juya ta
fita daga dakin, El-ameen yace "Me kika je yi?" Tace "Nace Anty ta kawo maka
abinci?" Ya hade rai yace "Did I send you?" Girgixa masa kai tayi, sai ga Hafsat ta
fito, kitchen ta shiga ta dau plate da spoon ta fito ta koma daki, El-ameen ya tabe
baki ya ci gaba da kallonsa, ba a dau lkci ba Hafsat ta fito rike da plate din
abinci ta shiga kitchen ta daura kan tray ta sa ruwa da cup ta fito parlon ta
durkusa ta ajiye kusa da shi sannan ta mike ta bar wajen, sai da ya ji ta shi ga
daki snn ya dau abincin ya fara ci, Jasmine tace "Har yanxu captain baxai xo ba?"
El-ameen ya ajiye plate din hannunsa yace "I will knock fa idan kina damuna da
captain ni nace kar ya xo?" Shiru tayi tana kallonsa, a hankali tace "Sorry!"
Daukar abincin sa yayi ya ci gaba da ci. Yana gamawa yace "Tashi ki tafi dakinta ki
kwanta, am also going to bed" mikewa tayi ta fara tafiya, yace "Baby!" Kin juyowa
tayi har sai da ya kuma kiranta, ta juya a hankali ya ga hawaye idonta, buda ido
yayi yace "Crying?" Ta girgixa masa kai, ya kwantar da murya yace "toh gaya min
kukan da kike?" Shiru tayi yace "Am waiting fah!" A hankali tace "Captain ya...."
Mikewa yayi yace "Get away!" Ta juya da sauri ta tafi dakin Hafsat, kuka ta fashe
da Hafsat na kallonta tace "what happened?" Tana share hawayenta tace "He shouted
at me" Hafsat tace "Ohk sorry, tafi kiyi wanka ga kaya na fito maki da" bathroom ta
nufa a sanyaye Hafsat ta bi ta da kallo. Tana fitowa ta saka rigar da Hafsat ta
fito mata da tayi kwanciyarta. Da asuba El-ameen yayi masu knocking kofa, Hafsat ta
kalli agogo don dama tuni ta tashi, biyar da minti arba'in ne, jin ya kuma knocking
ta mike ta nufi kofar ta bude, kallo daya yayi mata ya juya ya bar wajen ta koma
ciki ta tada Jasmine tace "Tashi kiyi sllh." Throughout ranan Jasmine a dakin
Hafsat ta yini, Hafsat nata bata labarai, duk El-ameen na jinsu. A kwana biyun da
Jasmine tayi gidan ba karamin sabo tayi da Hafsat ba, komai tare suke sai kayi
tunanin sun dade da sanin juna, sosai Hafsat ke sonta ga tausayinta da take, duk
abubuwan da tasan ya kamata gwada mata take, hakan yasa El-ameen ya d'an fara sake
mata ganin yanda take kula da ita, ita kam ko a jikinta don sau dayawa idan yayi
mata magana bata ma sanin da ita yake. Ran thursday da yamma suna kitchen su biyu
suna girki shi kuma yana parlor aka danna bell, mikewa yayi ya isa gun kofar ya
bude, Junaid ya gani tsaye, El-ameen ya shafa kai yana murmushi yace "Sai yau"
Junaid bai ce komai ba ya shigo parlon, sai dai bai xauna ba yace "Tana ina?" El-
ameen yace "Wa?" Junaid yace "Warce na kawo!" El-ameen xai yi magana sai ga ta ta
fito daga kitchen, ta wara ido ganin junaid tace "Captain!" Karasowa tayi inda suke
ta nufesa da fara'arta sai kuma ta ja ta tsaya ta fara dariya tana rufe baki tace
"I missed you!" Ba yabo ba fallasa yace "Tafi ki dauko Hijab din ki" kallon El-
ameen tayi sai kuma ta marairaice tace "Noo! I want to stay here Captain plss" ya
wani hade rai yace "I will slap you ke da staying din" ta kalli El-ameen kamar xata
yi kuka, El-ameen yace "Ae nan da can duk daya ne naga" Junaid yace "No ba daya
bane" El-ameen yace "Why?" Yace "Coz a can tana xuwa makaranta...." Bai rufe baki
ba tace "Toh ka kawo min kayan makarantar sai in dinga xuwa a nan ma" wani mugun
kallo junaid ke mata kafin yace komai ta fashe da kuka sosai tace "This Aunt is
kind, but the other one is otherwise I want to stay here plss captain!" Me El-ameen
xai yi ban da dariya, cikin kuka tace "Uncle its not funny, I don't like her, I
prefer staying here plss" sakin baki junaid yayi yana kallonta, El-ameen na dariya
yace "Gud nd fyn tafi gun kind aunt din ki" juyawa tayi da sauri ta nufi kitchen,
El-ameen ya kalli Junaid ya d'aga kafada yace "Ka kawo mata kayan makarantar ta"
wani kallo Junaid yyi masa ya juya ya fice daga parlon. Washegari da safe Jasmine
na kitchen da Hafsat suna girka breakfast aka danna bell, Jasmine xata fita Hafsat
tace "Ina za ki?" Tace "In bude kofa" Hafsat tace "Ci gaba da aikin ki" El-ameen ne
ya bude kofar, wanda ke tsaye gun ya rusuna ya gaishesa sannan yace "Captain ne ya
aiko ni in dauko bakuwar da ke gidan nan, driver ne ni" El-ameen ya shafa kai yace
"Kaje kace masa nace bata tashi ba" da ladabi drivern yace "Toh sir" daga haka ya
juya ya bar bakin kofar, El-ameen ya rufe kofar, Jasmine dake tsaye kofar kitchen
ta fito da sauri tace "Who's he uncle?" Kallonta yake daga sama xuwa kasa, sleeping
gown red colour ne jikinta da ya haska farar fatar ta, ta bude ido tace "Uncle"
kifta ido yayi ya karaso kusa da ita a hankali yace "Me kika ce" ta ce "Waye shi?"
Murmushi yayi ya kamo hannunta ya kai bakinsa kusa da kunnenta, ta xaro ido xata
koma baya taji ta jikinsa, runtse ido tayi tace "Uncle!" Ido hudu yayi da Hafsat
dake kallonsu, ta juya da sauri ta koma kitchen, sake ta El-ameen yayi ya koma
baya, ta turo baki tana kallonsa tace "What's that?" shafa kansa yayi ya juya ya
koma daki. ta juya ta shiga kitchen tana kallon Hafsat dake soyen dankali tace
"Anty!" Hafsat ta kalleta tace "Ya aka yi" shiru tayi bata ce komai ba, Hafsat ta
nuna mata ruwan lipton dake tafasa kan gas ckr tace "Ki juye a flask" kai ta gyada
mata ta dau flask da cup ta nufi gun gas din, tara saura suka gama, ta dibar ma El-
ameen nasa ta daura a tray tana kallon Jasmine tace "Kai masa!" Shiru Jasmine tayi
sai kuma ta dauka ta fita, sau biyu tana sallama ya amsa ta tura kofar ta shiga ta
karasa kusa da shi ta ajiye trayn, kallonta kawai yake ta mike tace "Ga breakfast
mun yi" sauke idonsa yayi yace "toh xauna mu ci" ta wara ido tace "Ni da Anty xa mu
ci" ya hade rai yace "Xauna na ce" murmushi tayi ta xauna ya mike ya dauko darduma
ya shimfida ya daura tray din kai ya xauna yace "Toh dawo nan" dawowo kan darduman
tayi ya hada tea a cup ya bude warmer din potatoe da kwai da plantain ya dau plate
ya diba yana kallonta yace "Start!" Langwabar da kai tayi tace "Toh Anty fah?" Yace
"Xata ci nata ai" daukar fork din tayi ta fara cin potatoe din sannan ta mika masa,
idonsa na kanta ya karba shi ma ya ci ya kuma mika mata, girgixa kai tayi tace "I
will use my hand" ya lumshe ido yace "Okay" kasa cin dankalin tayi ganin yanda yake
kallonta, ya buda ido a hankali yace "Eat mana" sunkuyar da kai tayi sai kuma ta
mike tace "Am coming" yace "Sit!" Kamar xata yi kuka tace "Uncle am coming" yace
"Ina xa ki?" Ta sauke idonta kasa tace "ina son xan dauko hijab dina am feeling
cold" murmushi yayi yace "Uhun?" Ta turo baki tace "Yes" yace "Toh tafi, kar ki
dawo kuma" shiru tayi tana kallonsa, yace "Tafi" mikewa tayi xata fita yace "Xo ki
dauki abincin ki" ta juya tana kallonsa can tace "Why?" Yace "Am ohk" ta bata fuska
tace "Toh ai baka ci ba" ya tsuke fuska yace "Na koshi" turo baki tayi tace "Baka
koshi ba joor" xaro mata ido yayi yace "Xo ki dauka na ce" karasowa tayi a sanyaye
ta durkusa xata dauka tray din ya fixgota ya xaunar gefensa yana kallonta yace
"What are you wearing hijab for?" Kamar xata yi kuka tace "You are looking at my
body" xaro ido yayi ya fara dariya yace "How?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace
"What's there idan na kalle ki?" Gyara xama tayi tana kallonsa tace "But you are
not my muharram!" Da mamaki ya dinga kallonta, tal langwabar da Kai ita ma tana
kallonsa, sauke idonsa yayi daga kallonta yace "Who told you that?" Shiru tayi sai
kuma tace "Mu'allim!" Tabe baki yayi yace "Shi kuma captain muharramin ki ne
kenan?" Tace "Yes, coz he's my family, my elder brother" kallonta kawai yake can
yace "Who told you that?" Tace "I know!" Yace "Then who am I to you?" Ta kallesa
tace "you are captain's frnd, nd... You are our family frnd" wani kallo yake mata
kafin yace "Toh tashi ki tafi" ta mike ta nufi kofa ya bi ta da ido, tsaki yayi ya
mike ya shiga bathroom. Dakin Hafsat ta shiga ta ganta xaune gaban mirror tayi
tagumi ta karaso ta xauna tace "Aunty what's wrong with you?" Kallonta Hafsat tayi
tace "Nothing, ur breakfast is downstairs" Jasmine ta bata fuska tace "No kalli
idon ki, are you crying?" Girgixa mata kai Hafsat tayi tace "Ba komai" a sanyaye
Jasmine ta mike ta fita daga dakin ta koma dakin El-ameen, yana bathroom ta nemi
waje ta xauna har ya fito bayan kusan minti ashirin daure da tawul, mikewa tayi ta
karasa kusa da shi a hankali tace "Uncle may be Aunty is sick, she's crying" hade
rai yayi yace "you are not my muharrama, how dare you come into my room just like
that without permission?" Ta buda ido tace "Ohh, I....." Yace "Leave now" juyawa
tayi a sanyaye ta fita daga dakin, nan corridor ta sulale ta fara kuka, ya gama
shirinsa ya fito, kallo daya ya mata ya shiga dakin Hafsat ta mike ta bi bayansa,
kwance ya ganta kan gado kamar me bacci, Ya tsaya daga bakin gadon yana kallonta,
Jasmine ta karasa
ta xauna gefenta tace "Anty na kira maki uncle xai duba ki, he's a doctor...."
Bude ido Hafsat tayi ta mike xaune ganinsa, ba yabo ba fallasa yace "What's wrong
with you?" Shiru Hafsat tayi, Jasmine ta matso kusa da ita tace "He said what's
wrong with you" Hafsat tace "Nothing" Jasmine ta hade rai tace "And you were crying
mana" El-ameen ya tabe baki ya cire bargon da ta rufe da shi tana ganin haka ta
fara kokarin komawa baya ya riketa ya daura hannunsa a forehead dinta, saketa yayi
ya juya ya fita, Jasmine ta bi bayansa da sauri suka shiga har dakinsa, gaban
mirror ya nufa ita ma haka ta tsaya daga bayansa tace "Uncle me ye ke damunta?"
Banxa yayi mata ta kuma tambayar ya juyo ya fixgota yace "Am not ur muharram ko kin
manta ne!" Shiru tayi ta bata fuska, kawai gani tayi ya rungumeta ta xaro ido tace
"Uncle!" Bakinsa ya kai kunnenta yace "And Captain isn't ur muharram also...."
Jikinta ya dau rawa ya saketa ya fice daga dakin. Fitowa ita ma tayi ta shige wani
daki ta fara kuka, har rana bata fito ba, karfe uku tayi wanka ta sa hijab dinta ta
fita ta nufi gate, tafiya kawai take har ta iso main road, tsaye tayi tana kalle
kallen ababen hawa dake wucewa, ko sanin yanda xata ce su tsaya bata yi ba, can dai
tayi deciding ta jira motar captain, ta kusa minti sha biyar tsaye sai wasa da
hijab take wani mota yayi parking gefenta ta bi motar da ido, wani ne ya fito ya
kusa minti uki tsaye kafin ya karaso kusa da ita yana kallonta ya rungume hannu
yace "Good afternoon!" Dauke kai tayi ta turo baki, ya karyar da kai yace "naga
alamar kina jiran driver ne koh?" Kallonsa tayi tace "No motar captain nake jira in
gani" ya dan wara manyan idonsa yace "Kike jira ki gani?" Tace "Eh" yace "Ohk yace
maki yana xuwa ne?" Girgixa masa kai tayi, ya d'an yi shiru kafin yace "Toh ki
kirasa" tace "Bana da waya" yace "Toh ga ta wa" tace "Bana da number" murmushi yayi
yana kallonta yace "Ohh dat's good, to in yi dropping din ki?" Kallonsa tayi tace
"Toh" sannan ta nufi gaban motar, bin ta yayi da kallo har ta bude ta shiga, ya
xaga shi ma ya shiga, sai da ya hau kan titi sannan yace "Ina ne gidan ku" buda
hannu tayi tace "Nima ban sani ba" kallonta yayi da sauri yace "Baki sani ba?"
Kamar xata yi kuka tace "Ehh amma kamar ta can captain ya biyo, sai yayi corner"
waje ya samu yayi parking don kansa ya fara rikicewa yana kallonta yace "Ya sunan
ki!" Langwabar da kai tayi ta wara ido tace "Jasmine, jewel baby!" Kallonta yake ko
kiftawa bai yi, can yace "Daga ina kike yanxu?" Kamar xata yi kuka tace "Uncle ne
yayi min ihu ya koreni, shine xan je gidan Captain" jinginar da kansa yayi jikin
kujerar motar yace "Toh fah! Amma ba garin nan kike ba koh?" Tace "Ehh Mami na ta
tafi UK in ji uncle a can muke sai muka xo nan yace min?" Xaro ido yayi yace "Toh
yanxu ina xan kai ki?" Tace "Mu bi ta can kila xa mu ga gidan" tada motar yayi ya
bi inda tace, tafiya kawai suke da sun yi nisa sai tace ba nan bane, duk ta daure
masa kai nan ya fara tunanin anya bata da disorder kuwa, fashe masa da kuka tayi
daga karshe wai ita sai ya kai ta gida, can dai ya fara tunanin anya ma ba aljana
ya dauko ba, dafe kansa yayi yace "Look Jasmine ni ban san gidan ku ba wllh, ya
sunan brother din naki?" Tace "Sunansa captain!" Yace "Real name dinsa fa nace?"
Tace "Ehh" Bude motar yayi ya fita da nufin tambayar ko akwai wani captain a
anguwar, ita ma ta fito da sauri ta fashe da wani kuka tace "ni dai ka kai ni
gidanmu plss" da damuwa yace "Wait! idan na maida ki inda na dauko ki xa ki gane
gidan?" Make kafada tayi tace "Ni baxan gane ba gidan captain dina xa ka kai ni"
xaro ido yayi yana salati a xuciyarsa, tana share hawayen fuskarta tace "Ka ji?"
Hannunta ta ji an kama ta juya da sauri lokaci daya ta warce hannun, wata mata ta
gani tsaye tana kallonta baki bude, a d'an tsorace ta koma kusa da shi, matar ta
saki salati tace 'yar nan! Ashe Allah xae kuma hada mu" Jasmine ta turo baki tana
komawa baya, shi kam kallon tsohuwar yayi yace "Yauwa mama kin san ta?" Washe baki
tayi tace "Wllh na santa, kwarai kuwa na santa"

*Haske Writers association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

60.....

Kallon mama jummai kawai yake, can ya girgixa kai yace "Toh yanxu ya xan yi da
ita?" Da sauri tace "Ka bani ita in tafi da ita nasan inda xan samo su" Jasmine ta
saki wani kara da ya tsorata mama jummai tace "Nooo I don't know herrr" ta fad'a
tareda k'ura mishi ido tana kallonshi, tada motar kawai yayi ya fara tafiya, suka
yi tafiyar kusan minti sha biyar ya isa wani babban gida yayi parking gaban gate ya
juya yana kallon mama jummai yace "Idan kin samo yan uwan nata ki kawo su nan,
gidan iyayena ne nan din" shiru mama jummai tayi ya d'an yi murmushi yace "Ehh"
tace "A'a kaga ni dai duniya bbu gaskiya yanxu, ina iyayen naka?" Wayarsa ya dauka
ya yi dialing number ya kai kunne, bayan few seconds yace "Farida ku fito ke da
Ramla" daga haka ya katse wayar, ba a dau lkci ba wasu yan mata da baxa su wuce
Jasmine ba suka fito, yace "Toh kin gani mama, kanne na ne wa ennan" daga haka ya
bude motar ya fita ya xaga ya bude side din Jasmine ita ma ta fito tana kallon Mama
Jummai k'asa k'asa, yana kallon kanninsa yace "Ku tafi da ita ciki" Farida dake ta
kallonta tace toh, ta fara tafiya haka Ramla ta bi bayansu, mama jummai ta fito a
sanyaye, ya fiddo dubu biyu ya mika mata yace "Kiyi kudin mota" godiya tayi ta fara
tafiya tana waige waigen gidan, ya koma motar aka bude masa gate ya shiga yayi
parking, da sallama ya tura kofar babban parlon gidan, durkushe ya ga jasmine jikin
kujera kannin nasa na kusa da ita, xaune a kan kujera mahaifiyarsa ce sai
stepmother dinsa dake parlon ita ma, Mahaifinsa ma na parlon xaune sanye da farin
glass dinsa ga laptop gabansa kan centre table, karasowa yayi ya xauna daga gefen
mum dinsa a kasa, mahaifiyar tasa Hajiya Mariya tace "Wacece wannan Abdul?" Sosa
kai ya shiga yi a hankali yace "Hajiya bakuwa ce...." Wani kallo take masa tace
"Bakuwa daga ina?" Rasa abinda xai ce mata yayi can yace "Mance gidansu tayi wai"
wani kallo yan parlon suka shiga yi masa, Dad dinsa ma ya dago for the 1st tym yana
kallon abinda ke faruwa, Hajiya ta daka masa tsawa tace "Waye abokin wasan ka a
nan?" Yace "Hajiya ga ki ga ta ki tambayeta ni wllh bn santa ba ma, taimakon ta
kawai nayi" Hajiya ta kalleta tace "Ke daga ina kike" Jasmine ta sauke idonta daga
kallon da take ma Hajiyar a hankali tace "Gidan uncle?" Hajiya tace "Xa ki ina?" Ta
dago manyan idonta tace "Captain!" Hajiya tace "ikon Allah, to daga wani garin kika
xo?" Shiru tayi sai kuma tayi maza tace "UK" duk suka buda ido suna kallonta,
stepmum dinsa Hajiya karima tace "Ina kenan a UK?" Buda musu hannu Jasmine tayi
alamar bata sani ba, Hajiya ta kallesa ta juya xuwa harshen fullanci tace Maxa ya
tafi da ita station right away, marairaice mata yayi yace "Ammi taimako...." Harara
ta watsa masa tace "Xan saba maka wllh" Dad dake ta kallon Jasmine yace "Ke Ramla
ku tafi da ita daki" mikewa suka yi gaba daya suka bar parlon, Abdul ya kalli Mum
dinsa da ta hade rai sosai ya mike kansa a kasa ya bar parlon. Karfe bakwai da
kusan rabi El-ameen ya shigo parlor junaid na bin bayansa, duk da ganinsu kasan ba
karamin gajiya suka yi ba, ganin hanyar daki El-ameen ya nufa junaid ya fixgosa a
fusace yace "Look am tired of this game ka gaya min inda yar mutane take Ahmad...."
Juyawa El-ameen yayi yace "plss don't make me loose my temper..." Daga haka ya bar
sa gun tsaye, dakin Hafsat ya shiga ya ganta xaune kan pray mat ya hade rai yace
"Wai ma kina me ta fita gidan nan baki sani ba" kallonsa tayi tace "Ba tare ku ke
da ita a daki ba, ta ina xan san ta fita ko bata fita ba" kallonta ya tsaya yi can
ya fice daga dakin, bedroom dinsa ya shiga ya xauna gefen gado ya rike kansa.
Jasmine ce xaune ita kadai dakin bayan isha, tun xuwanta gidan take xaune ita kadai
a dakin sai dai su shigo su yi abinda ya kawo su su fita, Farida ce ta shigo mata
da abinci ta fita, kamar xata yi kuka ta jawo abincin ta bude tana kallo, cokali ta
dauka ta fara ci don dama yunwa take ji, bude kofar dakin aka yi wani guy da baxai
wuce 33 ba ya shigo dakin har xai fita ganin ba kowa sai kuma ya dawo yana
kallonta, bata sake kallonsa ba ta ci gaba da cin abincinta, farida ce ta shigo
dakin ya kalleta yace "Who's she?" Tace "Ya Abdul brought her" yace "Abdul?" juyawa
yayi ya fice daga dakin ya tafi dakin kanin nasa, Abdul dake xaune dakin yana kallo
a system yace "Ka dawo bro?" yace "Yea, wace yarinyar!" Abdul ya ci gaba da
kallonsa a laptop yace "Amm, i just saw her on the way... No I helped her wai ta
mance gidansu," wani kallo yake masa kafin ya juya ya fita, ya koma dakin da
Jasmine take, cikin dakin ya karasa yana kallonta yace "daga ina kike?" Kallonsa
tayi ta ajiye spoon din hannunta tace "Daga gidan uncle" yace "xa ki ina?" Tace
"Gidan Captain!" yace "Toh me ya kawo ki nan?" Ta kalli kofar dakin tace "Wani
mutum ne" yace "A ina ya gan ki?" Xata yi magana Abdul ya shigo dakin, yana kallon
yayansa, Jasmine tace "Ga shi nan" Yayan nasa me suna Aliyu yace "I gat you will
one day bring what will lead you to ur grave Abdul, you saw a gal like this on the
road, she lied to you, you picked her up nd brought her home ryt?" mikewa Jasmine
tayi kamar xata yi kuka tace "Am not lying, am not a liar..." Aliyu ya kalleta yace
"I see, to wacece ke?" Tace "I am Jasmine" yace "Ur family?" Tace "They are in UK"
yace "Where in UK?" Ta langwabar da kai tace "I don't know!" Tabe baki yayi ya
juya zai fita ta kalli Abdul tace "I don't like him..." Juyowa yayi yana kallonta
yayi murmushi ya fita, Abdul ya sauke ajiyar xuciya yace "Ki ci abincin ki" ta koma
ta xauna shi ma ya fita. Sha daya saura Ramla da farida suka shigo dakin suka shiga
shirin kwanciya, ita dai Jasmine na xaune kan carpet har lokacin, Ramla ta nuna
mata gado tace "Ki kwanta in xa kiyi bacci" daga haka ta shiga bathroom neman
bathromm dan tanason tayi wanka amma babu k'ofa, bude kofar aka yi Aliyu ya shigo
dakin, ya karaso ya durkusa kusa da ita yana kallonta yace "Ki ka ce baki so na?"
Ta kallesa tace "Yess" yace "Why?" Ta ce "I don't know" kamar wacce tayi tunani sai
kuma tace "Okayy you are mean" giranshi d'aya ya d'age yana examining fuskarta
yace "Ohkk...?, have you eaten?" Gyada masa kai tayi yace "Kin yi sllh?" Ta girgixa
masa kai yace "Why?" Tace "No bathroom no toilet" murmushi yayi ya nuna mata kofar
bayin yace "There it is" tace "Someone went in " yace "Ohk idan ta fito sai ki
shiga" mikewa yayi yace "Good nyt," daga haka ya fita daga dakin. Washegari da safe
Jasmine na xaune bayan tayi wanka da ruwan da Ramla ta hada mata Aliyu ya shigo
dakin, yana kallonta daga bakin kofar yace "Come down for breakfast" mikewa tayi ya
juya ya fita ta bi bayansa, a bakin stairs yace "you make sure you greet everyone
out there" tace "toh" xaune duk yan gidan suke a dinning, duk aka xuba mata ido ta
kasa ci gaba da tafiya, juyawa yayi ganin ta tsaya yace "Taho" karasowa tayi har
dinning din ya nuna mata kujera ta xauna, sai hararansa Hajiyarsa take da step mum
dinsa, shi dai Abdul kansa na kasa, gaishesu tayi gaba daya stepmum dinsu kadai ta
amsa, Aliyu yasa Ramla ta yi serving dinta yace "Eat" ba musu ta fara cin chips
and Egg da soup, shi ma ya hada tea ya fara sha, ko minti goma yan gidan basu kara
dining din ba duk suka mike banda Abdul, can dai shima ya mike ya fita waje, ta
kalli Aliyu tace "They all don't want me to stay with them ryt?" bai ce mata komai
ba ya ci gaba da shan tea dinsa, kallonsa kawai take hakan yasa ya ajiye cup din
yana kallonta shi ma yace "Ya aka yi?" yar dariya tayi tace "You are fyn, just like
my captain and uncle" ya buda ido yace "Really?" Kallon wayarsa da yayi vibrate
tayi daga gefensu ta dauka tace "Your phone!" Bai ce komai ba ya ci gaba da shan
tean sa, ta dawo kujerar dake kusa da nashi ta mika masa wayar tace "Sa min
pictures in gani" karba yayi yana kallon kwayar idonta ta sunkuyar da kanta, mika
mata wayar yayi bayan ya shiga gallery yace "Take Jasmine!" Karba tayi ta koma inda
take tana kallon hotunan, har lokacin idonsa na kanta, can yace "When did you come
to Nigeria?" Ta kallesa snn ta ci gaba da kallon hotunan tace "Last month" yace
"And baki san gidanku ba har yanxu?" Mikewa tayi da sauri tana wara manyan idonta
tace "Uncle!" Gunsa ta koma har tana tuntube tace "Look kun yi hoto da uncle dina"
karban wayar yayi da sauri ya ga hotonsa ne da abokinsa Dr El-ameen wanda suka yi
just last week ranan daurin auren El-ameen din, ya kalleta yace "You know him?"
Gyada masa kai tayi da sauri tace "Yess he's my uncle" ajiye wayar yayi yace "Da
gaske?" Tace "Yes, call him to pick me plss" kamar xata yi kuka ta kare maganar,
shiru yayi yana kallonta, tace "plssss nah, am missing him" ajiyar xuciya ya sauke,
ya dau wayar ya nemo number El-ameen, bugu uku El-ameen dake station da junaid ya
dauka, Aliyu yasa a hands free yace "Assalamu alaikum, Where are you Ahmad?" El-
ameen yace "Ya aka yi Aliyu?" Jasmine ta wara ido xata yi magana Aliyu ya daura
hannu a lips dinsa alamar tayi shiru, yace "Kana dai ina yanxu?" El-ameen yace "Am
very busy frnd!" Aliyu yace "me kake yi?" El-ameen yace "Bari dai xa mu yi waya
anjima" Aliyu yace "Wait...." El-ameen yace "Kaga am in station yanxu, am not my
self, a sister of mine is missing tun jiya" Aliyu ya lumshe ido ya bude yace
"Jasmine?" Mikewa El-ameen yayi daga xaunen da yake yace "Exactly, you know
anything about it?" Aliyu yace "Come over yanxu..." Kallon junaid El-ameen yayi
yace "It seems he knows her whereabout" mikewa Junaid yayi fuskar nan tasa a daure
ya fice daga station din, El-ameen ya sallami yan sandan ya bi bayansa da sauri,
shi yayi driving din har ya isa gidansu Aliyu, parking yayi daga waje ya kira sa,
Aliyu na dagawa El-ameen yace "ga mu a waje" Aliyu yace "Ka shigo mana" El-ameen ya
kalli Junaid ya bude motar ya fita shi ma ya bi bayansa, har lokacin Jasmine na
xaune parlo da Aliyu El-ameen ya bude kofar parlon, suka shigo tare da Junaid,
mikewa Jasmine tayi da sauri ganinsu ta wara ido, da gudu ta nufesu idonta har ya
fara cikowa, sai dai idonta na kan captain
dake kallonta ko kiftawa bai yi, bata san lokacin da ta nufesa ba ta rungumesa
tace "Captain!" Wajen seconds goma bai ce komai ba yana jin yanda ta rirriqeshi duk
k'arfinta kamar za a rabasu kamin ya janyeta daga jikinsa a hankali, juyawa tayi
da sauri ta kalli El-ameen tace "Uncle" xata rungumesa shi ma ya matsa daga wajen
ya hade rai, shi dai Aliyu kallonsu kawai yake, murmushi ta kirkira tana kallon El-
ameen a hankali tace "Uncle!" Kallo daya Junaid ya ma Aliyu ya kama hannunta ya
nufi kofa, ta xaro ido tana kallonsa, bin sa da kallon mamaki suka yi su ma,
Jasmine tace "Captain plss wait let me say goodbye to my new friends, they helped
me...." Tuni ya fice da ita daga parlon, ta juya kamar xata yi kuka tana kallon
Aliyu da ya bi ta da ido ta daga masa hannu, titi junaid ya nufa da ita don
makullin motar na gun El-ameen, ya tsare me adai daita, yasa ta shiga shi ma ya
shiga. Xaunawa El-ameen yayi a parlon xuciyarsa na tafarfasa, Aliyu ma ya xauna
yace "Who's that barbarian?"El-ameen ya girgixa kai yace "Rabu da shi, where did
you get her?" Aliyu ya dau wayarsa ya kira Abdul cikin yan mintuna ya shigo parlon,
gaida El-ameen yayi ya xauna yana kallon yayansa, Aliyu yace "Where did you say you
picked the gal!" Bayanin inda ya ganta Abdul yayi, El-ameen yace "Ohh amazing, tnx
very much bro you helped us gaskiya" Abdul yayi murmushi yace "But how did you get
to know tana nan" Bayanin yanda aka yi taga hoton El-ameen a wayarsa Aliyu yayi
masu, El-ameen ya wara ido yace "Ikon Allah, but please don't tell Hajiya anything
about cewar na santa...." Aliyu yace "Why?" El-ameen ya shafa kansa yace "Kawai ku
dai kar ku ce komai" Abdul yace "tana ina?" El-ameen yace "Abokina ya tafi da ita"
Abdul ya mike yace "Ohh without even a goodbye!" daga haka ya fita daga parlon.
Aliyu yace "Don Allah ya ku ke da yarinyar?" El-ameen ya sauke ajiyar xuciya yace
"It's a long story...." Labarin jewel ya fara basa tun daga farko har ixuwa yanxu,
Aliyu da tausayinta ya cikasa sosai, duk jikinsa yayi sanyi yace "Allah Sarki!
Dat's so sad" El-ameen ya gyada kai yace "Yea it is" Aliyu ya had'e rai yace "Toh
shine zai wani dinga nuna isa a kanta don kawai shine silar tsinto ta" El-Ameen ya
tabe baki baki yace "Haka nan yake", tsaki Aliyu yayi yace "Ni ko xan nuna masa
helping her doesn't mean yafi kowa authority a kanta" El-Ameen yayi dariya yace
"Toh a ina xaka kuma ganinsa", kwafa Aliyu yace "Just watch and see what I do".

*Haske Writer's Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

61__62

Fitowa Junaid yayi daga napep din yana kallon Jasmine da ta tsuke baki yace "Sauko
kar in baki knock" kamar xata yi kuka ta sauko ya ciro kudi ya mika ma mai adai
daitan ya kama hannunta ya nufi gate, Humainah ce xaune parlor da Hadiza suna ta
hira, yayi tsaye bakin kofa yana kallon hadiza, jasmine ta karasa cikin parlon ta
tafi gun Humainah ta durkusa tace "Anty na dawo" ko kallonta Humainah bata yi ba,
junaid yace "Tashi ki wuce daki" mikewa tayi ta nufi stairs ya bi bayanta, Hadiza
ta mike tace "Tabdin, kinga tafiya ta Humainah, sai mun hadu gobe" Humainah bata ce
komai ba har ta fita, can ts mike ta tafi sama ita ma, dakinsa ta shiga ta ga baya
nan, ta fito ta shiga dakin da tasan Jasmine na ciki, tsaye ta ganshi a dakin,
kallo daya ya mata ya maida dubansa ga Jasmine yace "Ina jin ki" kmr xata yi kuka
tace "Shine sai ne sai na sa hijab na fita naje main road ina jiran motar ka, sai
baka xo ba, shine sai wani mutum yace in shiga motarsa na shiga" wani kallo ya
watsa mata yace "Daga yanxu na sake jin sunan Uncle a bakin ki sai na fasa bakin"
juyawa yayi ya fice daga dakin, Humainah ta bi bayansa har cikin dakinsa tace "Bari
ka ji, ni yarinyar nan baxa ta kuma xama min a gida ba wllh, It's either ta bar min
gida ko kuma inyi reporting dinka...." Bata rufe baki ba ya fixgota da shirin watsa
mata mari sai kuma ya fasa, yana huci ya jefar da ita kan gado yace "Don uwar ki a
kanki take xaune?" Mikewa xaune tayi tace "Uwata?" Sai kuma ta fashe da kuka tana
kallonsa tace "Uwata ka xaga ya Ahmad" juyawa yayi ya fice daga dakin ya koma
downstairs. Bayan magrib ya tafi siyo masu abinci don har lokacin Humainah na aikin
kuka a daki, tana jin fitarsa ta dau hijab dinta da jaka ta fice daga gidan,
Jasmine ya fara kai ma abinci da ya dawo ya sameta tana bacci ya tada ta tayi sllh
ya ajiye abincin ya fita, har xai shiga dakinsa sai kuma ya tsaya, ya kusa minti
biyar tsaye kafin ya shiga dakin Humainah, ganin bata ciki ya ajiye ledan hannunsa
xai fita sai kuma ya nufi bathroom ya bude, juyawa yayi ya fita da sauri ya tafi
gun mai gadi, mai gadin na ganinsa ya mike tsaye, yace "Yaushe ta fita?" Mai gadin
yace "Bayan fitar ka, tace kati xata siyo" junaid bai ce komai ba ya nufi motarsa
ya bude ya shiga ya fice daga gidan, cikin minti sha biyar ya isa gida yayi parking
a waje, lokaci daya gabansa ya fara faduwa, da kyar ya ja kafa ya shiga compound
din, ya kusa minti uku tsaye balconyn Mumy kafin ya tura kofar a hankali ya shiga,
ido hudu suka yi da Mumy dake xaune parlon sai Aysha dake parlon ita ma, jikinsa
yayi sanyi ganin Humainah xaune parlon kan carpet kusa da Mumy, Mumy bata kuma
kallon inda yake ba har ya karaso parlon ya durkusa nan kasa da kyar yace "Ina yini
Mumy" kallonsa tayi tace "Uhn Ahmad kenan, ita Humainahr ce ta xama abar
walakantawar ka yanxu, har ka kalleta ka xagi Uwarta da ke kabari sbda ka isa koh?"
Sauke idonsa yayi a hankali daga kallonta, Mumy tace "Tunda har ka iya bude baki ka
xagi uwarta nima xaka iya xagina, infact nima ka xaga..." Da kyar yace "Don Allah
kiyi hakuri Mumy, wllh sharrin shaidan ne I didn't....." Tsawa ta daka masa tace
"Rufe min baki" ya sunkuyar da kansa, ta kalli Humainah da har lokacin take hawaye
tace "Kema rama ki ce masa uwarsa" kallon Mumy tayi, Mumy tace "Ehh kice masa uwar
sa shi ma" ta kallesa ta ga shima kallonta yake, murmushi tayi ta sunkuyar da
kanta, shi ma yyi murmushin ya sauke kansa, Mumy tace "Fice min a parlor" mikewa
yayi ya fita daga dakin, Aysha tace "Me ya hada ku Humainah?" Shiru tayi bata ce
komai ba, can ta kalli Mumy, Mumy ta mike ta bar parlon, Aysha ta dawo kusa da ita
tace "Tell kar ki ji komai kin ji sis, me ya hada ku?" Kuka ta saki a hankali tace
"Aunty kin ga fa har yanxu yarinyar tana nan gidan....." Hade kanta tayi da kujera
ta kasa ci gaba, Aysha tayi shiru tana kallonta da tausayi, can ta dago tana share
hawayen idonta tace "Amma Anty kar ki gaya ma Mumy" Aysha bata iya ta ce komai ba,
ta mike ta fita daga parlon, tsaye ta gansa a balcony ta karasa kusa da shi tace
"Ya Ahmad?" Juyawa yayi yana kallonta yace "What did she tell mum?" Girgixa kai
tayi tace "Bata ce komai ba, amma ya Ahmad kai ma kasan baka kyauta mata kuma
Allah...." Hannu ya daga xai wanka mata mari ta bar wajen yace "Xan baki mamaki
idan baki fita sabgata ba wllh" juyawa tayi ta koma parlor, ido hudu yayi da Hajiya
dake tsakar gida for the 5th time ya sauke kai, tace "Ina yini Ahmad" kallonta yayi
fuska daure yace "Ina yini" tayi wani murmushi ta ci gaba da abinda take, jasmine
ce ta fado masa ya shiga parlor yaga ba kowa ya nufi bedroom, xaune ya ganta ita da
Aysha, Aysha na ganinsa ta mike ya bi ta da harara har ta fita, ya dawo kusa da
Humainah ya xauna yace "Ohk, Alryt! Am sorry, tashi mu tafi gida" ta hade rai sosai
tace "Bbu inda xan je" yace "Koh?" Juyawa tayi xata kwanta ya fixgota, ta shiga
turasa ya hade ta da jikinsa, kasa kwace kanta tayi, ta fashe da kuka tace "Allah
ni ka kyaleni...." Bai bari ta rufe baki ba ya hade bakinsu, sai da ya gaji don
kansa ya kyaleta, xata kwanta ya dauketa ya mike, bude ido tayi da sauri tace "Meye
haka?" Bai saurareta ba ya fita daga dakin, rufe fuskarta tayi da sauri a jikinsa
tana cewa "Na shiga uku" Aysha dake parlor ta bi su da ido, har ya fita parlon,
xaro ido Hajiya tayi tana kallonsu ta dau waya da sauri tana kiran Umma, Umma na
dagawa tace "Bilki fito fito ki ga ikon Allah, fito waje yanxun nan" da gudu umma
ta fito daga part dinta, ta bude baki tana kallonsu ita ma, lamo Humainah tayi a
jikinsa har suka fita gate, Umma ta yi side din Hajiya da sauri tace "kinga tsiya
koh? Kar dai ace wannan karan ma aikin banxa muke, wllh kila ciki ne da ita ma
laulayi take" Hajiya da bata samu bakin cewa komai ba ta rafka tagumi, Umma tace
"Kinyi shiru" Hajiya ta sauke wani shegen ajiyar xuciya ta mike tace "Mu je ciki
balki" ba musu Umma ta bi bayanta. Junaid na gama parking a gida har bedroom ya kai
ta, yana ajiye ta ya fice daga dakin ya shiga dakin da Jasmine take, kwance ya
ganta ta takure waje daya, ya durkusa kusa da ita yace "Jasmine!" Bude ido tayi a
hankali, tana ganinsa ta mike xaune yace "Me ya faru?" A hankali tace "My head is
aching" abincin da ya ajiye mata ya jawo ya bude ya ga bata ci ba, yace "Me yasa
baki ci ba?" Shiru tayi bata ce komai ba, ya bude take away din ya dau spoon ya sa
mata a ciki ya mika mata ta karba, yace "Eat" ba musu ta fara cin abincin yana
kallonta, da ta dago ido sai taga kallonta yake, ganin irin kallon yasa ta matso
kusa da shi a hankali tace "Captain!" Ko kadan bata ga alamar yasan tana yi ba, ta
kirasa yayi sau biyu kafin ta dafa hannunsa, kifta idon yayi da sauri yace
"Jasmine!" Langwabar da kai tayi tace "You are looking at me" sauke idonsa yayi
kasa, kamar xata yi kuka ta sauko kasa ta durkusa kusa da shi tace "Did I wrong you
again?" Murmushi ne yayi escaping lips dinsa yace "No!" Mikewa tayi ta koma kan
gadon ya bi ta da kallo ta xauna ta ci gaba da cin abincinta, ya tashi ya fita daga
dakin ya koma nasa, sha daya da wani abu ya sake dawowa dakin, kwance ya ganta ya
karasa kusa da gadon ya durkusa ya ga bacci take, ya cire bargon jikinta yana
kallonta, sleeping gown ne jikinta, ya dinga kallonta, lumshe ido yayi ya daura
lips dinsa a goshinta ya gangaro a hankali har xuwa kan lips dinta, bude ido tayi
da sauri ya koma baya, ta mike xaune tana kallonsa, kasa motsi yayi a gun bai kuma
bari sun hada ido ba can ya mike da kyar ya fice daga dakin, ya koma nasa, ya kusa
minti talatin xaune kafin ya mike ya fita ya shiga dakin Humainah, kwance ya ganta
cikin bargo ya karasa gadon ya xauna ya cire bargon, ta bude ido tana kallonsa,
shiga yayi cikin bargon ta mike xaune xata sauka ya jawota jikinsa ya kashe wutan
dakin. Washegari da safe karfe bakwai ya gama shirin fita aiki, kasa shiga dakin
Jasmine yayi, Humainah ta gama shirin makaranta ita ma bayan ta hada breakfast don
tun asuba da suka tashi bata koma ba, yana xaune parlor rike da cup din tea ya
kalli Humainah da saukowarta kenan yace "Tafi kice mata ta shirya driver xai xo kai
ta makaranta" yi tayi kamar bata ji sa ba ta ci gaba da goge takalminta, yace
"Humainah!" Ta daga kai tana kallonsa, repeating kansa yayi ta hade rai tace
"Takalmi na nake polish" yace "Kawo in maki ki tafi" tabe baki tayi ta ajiye
takalmin ta haura sama, samunta tayi ta fito daga wanka daure da towel, tana mata
wani kallo tace "Ki shirya wai" daga haka ta fita, shi ya ajiye Humainah, Jasmine
kuma driver ya ajiye ta. Tun daga lokacin da Junaid ya taho da Jasmine El-ameen bai
sake bi ta kansu ba duk da yana son ganin Jasmine amma yaki xuwa gidan, ba karamin
takura masa Aliyu yayi a kan ya nuna masa gidan junaid ba ya dinga kakkauce masa
don yasan ko kadan bai da mutunci, Jasmine kam tun bata damuwa da abinda Humainah
ke mata har ta fara damuwa don da tayi mata abu sai ta fara kuka, duk ran da hadiza
ke gidan kuwa bata da kwanciyar hankali don ita tsoronta ma take ko da yaushe cikin
tsangwamarta suke, tana son ganin Uncle dinta ta tambayesa yaushe Maminta xata dawo
amma har ranan bata gansa ya xo ba, gashi tana tsoron tambayar captain shi, shi ma
captain din ba sosai take ganinsa ba don tun bayan incident din daren ranan bai
barin su hadu sai tayi bacci, duk dare kafin ya kwanta sai ya shiga to make sure
she's fyn, a haka ta cika wata daya a gidan, ranan wani lahadi tana sharan parlor
don yanxu kusan ita take duka aikin gidan idan captain baya nan taji an danna bell,
ajiye broom din tayi ta mike da kyar don tun jiya cikinta ke mata ciwo, karasawa
gun kofar tayi ta bude xaro ido tayi tace "Aunty!" Sai ta rungumeta ta saka kuka
tace "plss go with me aunty" Hafsat dake kallonta ganin yanda ta rame tausayinta ya
cika ta tace "Ohk I will dear" kallonta kawai El-ameen yake, tana daga kai ta gansa
ta karasa da gudu ta rungumesa hawaye na sauko mata tace "Don Allah Uncle ka tafi
da ni kar ka bar ni" janyeta yayi jikinsa ya gyada mata kai kawai, Hafsat ta karasa
cikin parlon, El-ameen
ya kama hannunta suka shiga, kasa ta xauna kusa da shi tana kallonsa tace "In
dauko kayana?" Yace "Captain fah?" Bude hannu tayi tace "Ban sani ba nima" xai yi
magana aka bude kofar Junaid ya shigo, ya d'an yi mamakin ganinsu ya karasa cikin
parlon suka gaisa da Hafsat, ya xauna yana kallon El-ameen da ya hade rai yace
"Welcome Doctor"

*Haske Writer's Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

63.....

El-ameen yace "Thank you" mikewa yayi yana Satan kallon Jasmine da ta sunkuyar da
Kai ya haura sama, ba a dau lokaci ba Humainah ta sauko ta shigo parlon ta gaida su
ta tafi kitchen ta dauko drinks ta ajiye sannan ta xauna parlon, mikewa El-ameen
yayi Jasmine ma ta mike da sauri tana kallonsa tace "Ina xa ka uncle?" Yace "Mu je"
binsa tayi suka fita Humainah da Hafsat duk suka bi su da kallo, garden ya tafi da
ita ya xauna ta xauna gabansa yace "What's wrong with you?" Hawaye ne ya cika
idonta a hankali tace "I want to go to Mami...." Sai kuma ta fashe da kuka, ya kamo
hannunta yana kallonta yace "An maki wani abu ne?" Hawaye na bin kuncinta tace "She
don't like me, frnd dinta ma bata sona they are always shouting at me and calling
me a mad girl...." Wani kukan ta kuma fashe wa da, cikin sanyin murya yace "Kiyi
hakuri" kai kawai ta gyada masa, yace "And what did captain say about it" ta
girgixa Kai tace "He's always at work...." Dago kanta yayi yana kallon kyakkyawan
fuskarta, ya sa yatsa yana goge mata hawayen da ya ki tsaya mata a hankali yace
"It's ohk jewel" muryarta na rawa tace "Are you going with me plss?" fuskarsa ya
kai kusa da nata ya had'e goshinsu yace "Toh ba ke kika gudu ba baby" tace "I won't
do that again plss" kallon yanda dan karamin bakinta ke motsi ya dinga yi, tace
"Plss ka tafi da ni uncle they don't like me, they are always calling me mad...."
Lumshe ido yayi ya hade bakinsu, tayi still a wajen, lokaci daya jikinta ya dau
rawa, takun da yaji yasa shi saurin cire bakinsa ya saketa amma tuni ya iso wajen
don a kan idonsa yayi hakan, tsaye yayi gun kamar an dasa shi xuciyarsa na bugawa
yana kallonsu, El-ameen ya mike shi ma idonsa kansa, karasowa yayi yace "Xo ki
wuce" ba musu ta mike ya bar wajen da sauri da ganinta kasan a mugun tsorace take,
takawa yayi har gaban El-ameen yana kallonsa cikin kaushin murya yace "Daga yau kar
ka kuma shigo min gida Ahmad, this shud be ur last plss, idan ba haka ba duk me na
maka kai ka ja ma kanka, i dont want to see you in my home any longer, to hell with
the goddamn friendship" har wani rawa jikinsa yake yana maganan lokaci daya idonsa
ya kada yayi jajur, ya juya yana huci ya bar wajen, El-ameen ya shafa kansa ya ciro
wayarsa ya kira Hafsat ta fito su wuce. Sama junaid ya nufa ya bude kofar dakin da
take, xaune ya ganta kasa ta takure gu daya, tana ganinsa ta mike, ya karasa kusa
da ita ya fixgota lokaci daya ya kifa mata wani wawan mari da yayi mugun gigitata
don sai da ta fadi, bin ta yayi ya dago fuskarsa a daure cikin kak'k'ausar murya
yace "You allowed him kissed you?" Kasa bude idonta tayi sai wani rawa da jikinta
yake, ji yayi kamar xuciyarsa na shirin buga wa ya jefar da ita ya fice da sauri,
ta kusa minti goma kafin ta iya bude idonta da kyar, ji tayi gaba daya dakin na
juya mata ga wani axababben ciwo da kanta ke mata, ta rike kan tana son mikewa ta
xube gun daga nan bata sake sanin inda kanta yake ba.
Har after asr Junaid na balcony xaune ya jinginar da kansa jikin kujera idonsa
lumshe, bude idon yayi a hankali jin kamar ana amai, ya mike ya shiga parlon,
Humainah ya gani durkushe a bakin kofar toilet din dake parlon, da kamar xai koma
sai kuma ya karasa, amai take sosai yana kallonta har ta gama ta mike ta nufi
stairs da sauri da ganinta ta galabaita ba kadan ba, juyawa yayi ya koma balcony
yayi xamansa. Sai da aka yi magrib ya shiga gida bayan ya siyo masu take away, ya
jima tsaye corridor kafin ya tura kofar dakin Jasmine kwance ya ganta a kasa, ta
bude idonta da yayi mata nauyi da kyar ga kadawa da suka yi, wani ja na musamman
lips dinta suka yi da ganinta kasan ba karamin kuka ta sha ba, karasawa yayi dakin
ta mike xaune da sauri ganin sa, ya ajiye ledan abincin ya fita, dakinsa ya koma ya
hade kai da bango wani mugun tausayinta na ratsa shi, ya nufi gado ya shige cikin
bargo. Har tsakar dare bai iya ya rintsa ba, aman da Humainah ke tayi yasa shi
mikewa ya fita ya shiga dakinta ya sameta durkushe a bathroom, yace "What's wrong
with you?" Kasa ce masa komai tayi ta mike ta koma kan gado ya juya ya fita.
Washegari yana dawowa daga mosque dakin Jasmine ya shiga xaune ya ganta kan praying
mat ya juya ya fita, ganin yanda Humainah ke amai yasa shi tafiya asibiti da ita da
safe, kallon likitan dake masa bayani kawai yake har likitan ya kai aya, da mamaki
likitan yace "Ain't you happy Mr Ahmad Junaid?" Junaid ya d'an yi murmushi yace
"Ohh I am... Of course I am thanks Dr" murmushi likitan yayi yace "Congrat once
more Mr Ahmad" mikewa Junaid yayi yana d'an murmushi, karfe sha daya na safen suka
iso gida bayan an bata magunguna da allurai, har ya gama parking bacci take ya juya
yana kallonta, murmushi yayi ya fito ya xaga ya bude motar ya dauketa ya tafi cikin
gidan. Murmushi El-ameen yayi ya yagi memon dake kan table dinsa ya dau pen yayi
rubutu ya tura gaban Aliyu dake xaune gabansa, dauka Aliyu yayi yana karanta
content din yace "Uhn don Allah da gaske?" El-ameen ya daga kafada yace "Yea! Dat's
the address, you can do what ever you wish provided you won't harm the girl" mikewa
Aliyu yayi yace "Thank you" daga haka ya fice daga office din. Bayan sati daya
Jasmine na daki xaune da yamma tayi tagumi da ganinta kasan tana cikin damuwa ga
yunwar da take ji tana kuma tsoron fita, tura kofar dakinta aka yi ta mike da sauri
don a tunaninta junaid ne duk da rabon da ya shigo dakinta tun ranan da ya shigo ya
ajiye mata abinci bayan ya mareta, Hadiza ce ta shigo dakin tace "Ke don ubanki
baxa ki fito kiyi gyaran gidan ba, kina ganin me gidan bata da lafiya sai dai ki
wani kume a daki" kofa Jasmine ta nufa ta fita hadiza ta bi ta da harara, gyare
gyare kawai take a parlon Humainah kuma na kwance tana shan kankana, hantaran ta
hadiza ta dinga yi komai tayi tace bai yi dai dai ba, Humainah da hayaniyar ma ba
son shi take ba tace "Ke xo dauke bowl din nan ki bar min parlor dallah, katuwa da
ke bbu abinda kika iya sai dai a baki ki ci mahaukaciya kawai" karasawa Jasmine
tayi da sauri ta durkusa ta dauki daya daga babban bowl din Hadiza ta daka mata
tsawan da ya firgitata ta sake bowl din ya tarwatse ta mike tsaye da sauri, mikewa
Humainah tayi tace "Kan uba shi bowl din nawa kika fasa...." Karasowa Hadiza tayi
ta sauke mata wani wawan mari har biyu kamar an aikota sannan ta turata kasa a kan
idon junaid da ya shigo parlon tana cewa "wato har yanxu haukan bai bar ki ba
kenan, jaka mara asali" still Humainah tayi ganin Junaid, Hadiza na ganinsa ita ma
ta kame wajen, gun Humainah ya nufa bai yi wata wata ba ya dauke ta da tagwayen
mari, ai tuni Hadiza ta fice daga parlon tana tuntube, wani kara Humainah tayi ta
durkushe wajen tana rike da kuncinta, ya kalli Jasmine dake durkushe kasa ta rike
kanta, ya durkusa ya dagata ya nufi sama da ita, ba karamin wahala ta basa ba kafin
ta cire hannayenta biyu daga rikon da tayi ma kanta kuka kawai take tana cewa
kanta, kasa bude idon tayi ta rike hannunsa cikin kuka tace "I can't open my eyes
captain, kai na na min ciwo sosai" bai san lokacin da ya rungumeta ba idonsa ya
kada sosai, sun kusa minti sha biyar kafin ya mike ya sa mata hijab dinta ganin
taki bude idon ya fita xuwa asibiti da ita. Sai kusan magrib suka dawo gida yana
rike da hannunta suka shiga parlor har lokacin bata yarda ta bude ido ba babu yanda
likitan basu yi da ita ba, duk ta daga ma junaid hankali, kwantar da ita yayi kan
kujera bayan ya bata malt dinta ta karasa shanyewa ya bata magunguna ta sha,
xaunawa yayi gefenta ya rike kansa, wayarsa dake kan kujera ya fara ring ya dago da
kyar ya dauka yana kallon screen din, gabansa ya fadi ganin kiran Abbansa, mikewa
yyi ita ma ta mike xaune da sauri tana laluba sa tace "No don't leave me Plss
captain" komawa yayi ya xauna cikin sanyin murya yace "toh bude idon sai in tafi da
ke" muryar ta na rawa tace "Baxan iya ba, it's paining me" dafe kansa yayi can ya
dago ya daga kiran Abbansa, daga daya side din Abba yace "Ka taho gida" ajiye wayar
yayi don dama he was expecting that, ya dagota ya kama hannunta suka fita, yana
gama parking a kofar gidansu yace "Yanxu xan fito kin ji Jasmine" kai ta gyada masa
idonta rufe, ya bude motar ya fita ya rufe, ko ba a gaya masa ba yasan Humainah ta
tafi gida, part din Mumy ya nufa ya tura kofar ya shiga, Abbansa na xaune parlon
sai Mumy, Humainah kuma na xaune kasa kusa da Mumy sanye da hijab har kasa ta
sunkuyar da kai, karasawa yayi cikin parlon kansa a kasa ya durkusa ya xauna kan
rug ya gaida Abba, kallonsa kawai Abba yake, ya dago da kyar yana kallon Mumy yaga
ita ma kallonsa take ya sunkuyar da kansa, Abba yace "Ahmad!" Ba tare da ya dago ba
yace "Na'am" Mikewa Humainah tayi da sauri tayi hanyar toilet sai amai, bin bayanta
Mumy tayi ta dafa ta tana kallonta, sannu ta dinga mata ta dagota bayan ta gama, da
kyar tace "xan kwanta Mumy" Kama hannunta Mumy tayi ta kai ta bedroom dinta ta
kwanta nan da nan ta fara bacci, Mumy ta kusa minti biyar a tsaye tana kallonta
kafin ta juya ta fita, xaunawa tayi a inda take Abba yace "Bata da lafiya ne?" Mumy
tace "Eh ta kwanta ma" yace "Toh koh a tafi asibiti!" Mumy tace "Bari ta tashi dai"
kallon junaid da kansa ke kasa Abba yayi yace "You slapped her ryt?" Shiru yayi bai
ce komai ba Abba yayi masa tsawa yace "Ba magana nake maka ba?" Gyada kai yayi yace
"Eh Abba" Abba yace "Good!"

*Haske Writer's Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

64__65
Tashi ka je, k'asa tashi yayi Abba yace "Baxa ka bar min parlor ba?" A hankali yace
"Abba kayi hakuri don Allah, sharrin...." Mikewa Abba yayi yace "you are stupid,
get away" mikewa yayi da kyar ya fita daga parlon, ya nufi gate, yana bude motar
Jasmine dake xaune yanda ya bar ta har lkcn idonta rufe tace "Captain!" Ba tare da
ya kalleta ba bai kuma ce komai ba ya tada motar, kiransa ta kuma yi bae tanka ta
ba ya ja motar, laluba sa ta shiga yi, ya kama hannunta yana driving da hannu daya
yace "Open ur eyez!" Ta girgixa kai tace "It's hurting me" bai kuma cewa komai ba
har suka isa gida, kallon b'akin motar dake Parke daga gefen flowers din da ya
xagaye frontage din gidan ya dinga yi, mai gadi na bude masa gate ya sauke glass
yace "Waye yayi parking can?" Mai gadin ya kalli motar yace "ca yayi wani yake jira
a can gidan yallabai" junaid bai kuma cewa komai ba ya sake kallon motar sannan ya
ja motarsa ya shiga compound, yana gama parking ya juya yana kallonta yace "Jasmine
open those eyez idan ba haka ba xan yi tafiya ta in bar ki" da sauri ta kamo
hannunsa kamar xata yi kuka tace "yana min ciwo captain, don't leave me plss, ka
kira uncle kace ya kawo min Magani" wani kallo yake mata kamar tana ganinsa, can ya
janye hannunsa xai sauka ta rikosa da sauri tace "No plss" hade rai yayi yace "toh
ba sai na fita ba sannan xan fito da ke" a hankali ta sakesa ya fita ya xaga ya
bude side din da take ya kama hannunta ta sauko ya rufe motar suka nufi cikin
gidan, parlor ya xaunar da ita ya koma wani kujerar ya xauna ya dau remote yayi
powering tv, a hankali tace "Captain!" Ya kalleta bai ce komai bs, kuma kiransa
tayi yace "Yess!" Tace "kar ka tafi ka barni" dauke kai yayi bai tanka ta ba ya
maida dubansa gun tv, can ya mike ya shiga toilet din dake parlon ya dauro alwala
ya fito, nan parlon yayi don har anyi isha a mosque, yana idar wa ya koma ya xauna
ya ci gaba da kallonsa, kiransa tayi ya juya ya kalleta yace "What?" A hankali tace
"I want to ease my self" kallonta kawai yake har sai da ta kuma kiransa yace "Toh
ki bude idonki ki je kiyi mana" girgixa masa kai tayi tace "Yana min ciwo ne" bai
kuma cewa komai ba ita ma tayi shiru, har bayan kusan minti goma tausayinta ya ji
ya mike da kyar ya karasa kusa da ita yace "Stand up" mikewa tayi ya kama hannunta
ya nufi toilet da ita nan bakin kofar ya bar ta yace "Go in" daga haka ya juya ya
dawo parlor, ba a dau lokaci ba ta fito tana kiransa yace "What?" Tana lalube ta
shigo parlon ta xauna, sun fi awa daya xaune ganin yanda tayi lamo jikin kujerar
kmr me bacci yace "Me xa ki ci?" Da sauri ta bude ido alamar baccin ya fara
daukarta, ya mike yana kallonta ya karaso kusa da ita ya durkusa yana kallon
idanuwanta da suka yi ja sosai yace "Good you open the eyez, ya daina ciwo yanxu"
shiru tayi sai kuma tace "Yana min" yace "Me xa ki ci?" Bata ce komai ba ta yi kasa
da kanta yace "Xa ki sha tea nd bread?" Ta kallesa tace "No! Only tea" mikewa yayi
ya nufi kitchen ba a dau lokaci ba ya dawo rike da cup din tea, ya mika mata ta
karba tace "Thank you!" Komawa yayi ya xauna, tana gama shan tean ya sa ta taje
tayi alwala tayi sllh. Karfe goma saura ganin ta fara bacci yace "Go to bed if you
are sleepy" mikewa tayi ta nufi stairs ya bi ta da kallo. Washegari da asuba ya
kwankwasa mata kofa, cire bargon jikinta tayi ta xauna tana murxa ido, can ta sauka
daga kan gadon ta nufi kofar ta bude, kallonta yake daga sama har kasa, yar rigar
bacci ne jikinta tace "Captain" ya sauke idonsa yace "It's time for prayer," har ya
juya xai tafi ya kuma juyowa yace "kina gama sllh ki shirya for islamiyya" ta gyada
masa Kai ya juya ya bar bakin kofar, yana xaune parlor shirye cikin uniform rike da
cup din coffee Jasmine ta sauko, kallon agogo yayi yaga Karfe bakwai saura minti
goma yace "Tafi ki dafa indomie" tace "Toh" ta nufi kitchen, bin ta yayi da kallo
yace "Come here" ta juyo ta dawo inda yake ta tsugunna tace "Na'am" yace "Baki iya
gaisuwa ba" kallonsa kawai take wanda hakan ya sa shi dauke kai, a hankali tace
"Good morning captain" ajiye cup din hannunsa yayi ba tare da ya kalleta ba ya mike
yace "Morning" tashi tayi ita ma tana kallon white uniform din jikinsa tace "You've
not buttoned all the buttons captain" kokarin barin wajen yake ta shiga gabansa
tace "Let me help you" da sauri ya koma baya ya hade rai yace "No! I will do that
my self" daga haka ya nufi stairs, ta bi sa da kallo. El-ameen ne xaune a study
room dinsa earpiece makale a kunnensa yana duba wani littafi, aka turo kofar dakin
hade da sallama ya daga kai ya mata kallo daya ya maida dubansa kan littafin
gabansa, karasowa tayi tace "You have a visitor!" Yace "Who?" Tace "Yana parlor"
rufe littafin gabansa yayi yace "Alryt!" Ta juya ta fita, ya mike ya fita xuwa
bedroom dinsa, jallabiya ya daura kan kananun kayan jikinsa ya sauko parlor, Aliyu
ne xaune parlon, El-ameen yace "uhn! Ashe ka san gidana Dr" Aliyu ya kallesa yace
"No! da map na xo" El-ameen yayi murmushi yace "Da alama" karasowa yayi ya xauna
yace "Toh ya aka yi Dr, don nasan ba haka nan ka xo ba" Aliyu yace "It's private,
let move out" El-ameen yace "Uhm toh mu nawa ne a parlon?" Mikewa Aliyu yayi ya
nufi kofa El-ameen yayi murmushi ya bi bayansa. Bayan kwana uku Humainah
na xaune kasa a parlor ta daura kai kan kujera duk ta rame ba kadan ba don ba
karamin wahala take sha ba, Mumy ce xaune daga gefenta da sisternta Anty Nafee sai
Abba dake parlon shi ma, Anty nafisat tace "Wai baxa kiyi magana ba Humainah, Meye
haka kike yi" ta fashe da kuka tace "Ni ba abinda ya hadamu Mumy, ni ban masa komai
ba" shiru duk suka yi suna kallonta, hawaye ne ya shiga sauko mata, Mumy ta
jinginar da kanta jikin kujera a sanyaye, she's just imagining anya Ahmad dinta ne
kuwa, Ahmad din da ta yarda da tarbiyar da tayi masa, Ahmad da tayi raise da
hannunta, Ahmad da ko kadan bai son bacin ranta, wai yau har kwana biyar bai sake
waiwayo gidan ba, girgixa kai tayi ta lumshe ido, mikewa Humainah tayi da sauri
Anty nafisat ta bi bayanta, bedroom ta kai ta bayan ta gama aman, ta kwantar da ita
sannan ta xauna gefenta tace "Humainah idan ma baxa ki iya gaya ma su Mumy abinda
ya hada ku da Ahmad ba ni ki gaya min, take me as ur mum kin ji" girgixa kai tayi
tace "Ba abinda ya hadamu Aunty" sai kuma ta fashe da kuka, Anty nafisat tayi shiru
tana kallonta cike da tausayinta. Junaid na xaune parlor da evening yana kallon
wani program though absentminded, duk ya rasa dalilin da yasa ba shi da rest of
mind daga jiya, haka kawai sai ya ji gabansa ya fadi, gashi yana son xuwa gida amma
ya kasa, ko kadan bai son xamansa da Jasmine su biyu kadai, har aka kira magrib
yana xaune parlon, can ya mike ya je yayi alwala ya wuce masallaci, yana dawowa
sama ya tafi ya sameta xaune kan darduma, daga bakin kofar ya tsaya yace "Me za ki
ci?" Ta d'an bude ido tace "Potatoe nd ketchup!" Tabe baki yayi ya juya ya fita ya
dau makullin motarsa. Sha biyu saura na dare yana kwance idonsa biyu sai dai ya
kashe wutan dakin yana son yin bacci amma ya kasa, murda kofa dakin aka yi jasmine
ta shigo da sallama, ya mike xaune ya kunna bedside lamp yace "What's it?" Karasowa
take son yi yace "Tsaya nan, nd what did you want?" Tsayawa tayi tace "Cikina ke
man ciwo" yace "Go nd sleep gobe xan baki Magani, stop disturbing me" a hankali
tace "Ohk" ta juya ta fita, ya sauke ajiyar xuciya ya koma ya kwanta, har daya bai
yi bacci ba yana son dubata amma ya ki xuwa daga karshe ya mike ya dauro alwala ya
shimfida darduma. Yana xaune cikin mota idonsa a kanta ko kiftawa bai yi har ta
karaso gun motar, sanye take da hijab dinta har kasa ta bude front seat ta shiga
tana kallonsa tace "Na gama" bai ce komai ba ya ja motar suka bar gidan, sai da
suka dau hanya sannan yace "Cikin ya daina ciwon ne?" Girgixa masa kai tayi tace
"Yana yi har yanxu" bai kuma cewa komai ba har suka iso wani gida bayan tafiyar
kusan minti ashirin, kallonta yayi ita ma haka, ya dauke kansa ya bude motar xai
fita tace "Where is this captain?" Juyowa yayi yace "You wait for me, ba dadewa xan
yi ba!" "toh" kawai tace ya fita ya kulle motar ya shiga gidan. Tsakar gida ne
babba me dauke da sashi daban daban, xaune a tsakar gidan wata 'yar dattijuwa ce da
yara mata biyu da baxa su wuce sha takwas ba, tana ganinsa tace "Ikon Allah, Ahmad
ne a gidan namu yau!" Tana magana ne tana kokarin bude masa wani tabarma ya xauna,
D'an murmushi yayi ya xauna kan tabarmar yace "Ni ne Hajiya, ina yini?" Da fara'a
tace "Lafiya lau Ahmad, ya gida ya su Amina?" Yace "duk lafiya lau" gaishesa yan
matan suka yi ya amsa hade da tambayar su makaranta, Hajiya tace "Toh ina amaryar
taka, ai ya kamata ka kawo min ita mu gaisa ko Ahmad" ya shafa kai yace "Xan kawo
ta Hajiya" Hajiya tace "Toh muna xuba ido" yace "Baba na ciki kuwa?" Tace "Ehh bai
jima da shigowa ba ma, tashi ka je" mikewa yayi ya nufi babban parlon gidan, da
sallama ya shiga ya samesa xaune kan babban darduma a kishingide, dattijon na
ganinsa yace "Ikon Allah, Ahmad!" Karasowa Junaid yayi kansa a kasa ya xauna hade
da yi masa sallama ya gaishesa, da fara'a dattijon ya amsa masa yana tambayarsa
gida da Abbansa, junaid yace "Duk suna lafiya Baba" Dattijon yace "toh ya aka yi,
ko Muhammad ne ya aiko ka?" Girgixa kai yayi yace "Shawara na xo nema gun ka baba"
Gyara xama dattijon yayi yace "Toh bismillah, ina jin ka Ahmad" shiru Junaid yayi
na d'an lokaci kafin ya fara basa labarin Jasmine tun daga lokacin da ya ganta har
xuwa yanxu, kallonsa kawai dattijon ke yi, can yayi murmushi yace "Ahmad kenan, to
amma meye ka boye ma iyayenka wnn aikin ladan da kayi, ai abun su yi alfahari da
kai ne wannan" girgixa kai yayi yace "A'a ba lallai su fahimce ni ba ma" shiru
dattijon yayi sannan ya sauke ajiyar xuciya yace "Ikon Allah, to tana ina
yarinyar?" Junaid yace "Gidana take" "tare da matar ka?" Ya tambayesa yana
kallonsa, shiru yayi kafin yace "Ehh!" Dattijon yace "Amma da amincewar matar taka
kuwa" shiru junaid yayi nan ma, can kuma
yace "A'a" dattijon yace "Toh maido ta nan Sa'adatu ta rike ta har Allah ya bata
lafiya ya bayyana danginta" kallonsa junaid yayi da sauri, can ya sunkuyar da kai,
dattijon yace "Hakan yayi maka?" Gyada masa kai kawai yayi yace "Nagode Baba" ya
ciro kudi aljihunsa ya ajiye masa dattijon yace "A'a je ka da abun ka Ahmad, duk
lokacin da ka taso takanas don gaida ni xan karba" murmushi junaid yayi yace "Kayi
hakuri baba, abubuwa ne suka yi yawa" dattijon yace "Allah kuwa" duk yanda junaid
ya so tsohon ya amshi alkhairin kin karba yayi, haka yayi masa sallama ya fita
bayan ya kuma jad'd'ad'a masa ya kawo Jasmine kar ya shiga hakkin matarsa, jinsa
kawai junaid yayi ya fice daga parlon, yaran gidan ya bai ma kudin hannunsa yayi ma
babarsu sallama ya fita, Malam tukur malamin mahaifinsa ne tun fil'azal, kusan gun
sa junaid ya sauke littattafen addini da dama hakan yasa yake girmama tsohon. Bacci
ya tarda Jasmine ke yi a motar bai tasheta ba ya tada motar ya bar layin bayan ya
kwantar mata da kujerar. Yana xaune shi daya parlor ya jinginar da kansa jikin
kujera, gaba daya hankalinsa yayi gun mumynsa a lokacin, dama akwai tym din da xai
xo ya dade haka bai je inda take ba without any reason, lumshe ido yayi duk ya rasa
abun da ke damunsa yanxu, gashi ko kadan shawarar da Malam Tukur ya basa bai masa
ba, muryar Jasmine yaji tace "Captain!" Ya bude ido da sauri yana kallonta tace
"Anty baxa ta dawo ba?" Hade rai yayi yace "leave!" Da sallama El-ameen ya
shiga parlon, Mumy dake xaune da fatima suka amsa masa ya karasa cikin parlon ya
gaida Mumy da fara'a bayan ya xauna, da murmushi ta amsa masa tana kallonsa, fatima
ta gaishesa ya amsa hade da tambayarta sch, kallon Humainah dake kwance yayi kan
yace komai ta gaishesa, ya amsa da murmushi lkci daya ya gano ba ita daya bace, ya
kusa minti sha biyar parlon kafin Mumy tace "kana ji na Ahmad?" Ya kalleta yace
"Ina ji Mumy" kasa cewa komai tayi da ganinta kasan there is something eating her
in, gashi duk ta rame, sunkuyar da kansa yayi ko bata fadi ba yasan kan junaid ta
kirasa, a hankali yace "Mumy kin yi shiru" cikin sanyin murya tace "I don't know
what has come over ur frnd...." Kallonta yayi yace "Me ya faru Mumy?" Tuni idonta
ya kada ta kasa ci gaba, jikinsa yayi sanyi ya kasa cewa komai kuma, bude kofar aka
yi Abba ya shigo yana ganin El-ameen yace "Good u are here" xaunawa yayi ya fiddo
wayarsa yyi danne danne ya kara kunne, junaid dake durkushe a lokacin kusa da
Jasmine dake juye juye wai cikinta na ciwo ya kalli screen din wayar hannunsa
gabansa ya fadi ganin Abbansa ne, da kyar ya d'aga daga daya bangaren Abba yace "Ka
taho ina jiran ka yanxu" daga haka ya katse, bbu tunanin da junaid bai yi ba daga
karshe dai ya mike bayan ya lullube Jasmine ya fita, xuciyarsa na raya masa
Humainah ta fadi abu kenan a gida, cikin yan mintuna ya isa gida, yayi part din
Mumy jiki ba kwari, bai yi tunanin Abba na can ba, yana bude kofar yayi still ta
dalilin ido hudu da suka yi da Abban nasa, da kyar ya karaso parlon yayi ma El-
ameen kallo daya ya dauke kai gabansa na faduwa, kasa kallon inda Mumy take yyi, ga
Anty Nafisa ma dake parlon sai Aysha da Humainah dake jikinta, ya xauna ya gaida
Abba, yaji no answer, a sanyaye ya gaida Mumy nan ma no answer, bai kuma gaida kowa
parlon ba, cikin kaushin murya Abba yace "Ahmad!" Da kyar ya dago kai ya kallesa,
Abba yace "Bani takardar Humainah!" Kallonsa kawai yake kamar bai fahimce sa ba,
Abba ya mike yace "Ni kake ma wannan kallon?" Sunkuyar da kai yayi, A nutse Abba
yace "Bani takardarta nace" junaid ya lumshe ido ya bude yace "Abba ni bbu abinda
ya hada mu......" Bai rufe baki ba Abba ya sauke masa mari yace "You are very
stupid ka bani abinda na tambayeka ko sai na saba maka" shiru yayi na d'an lokaci
sai kuma yace "Babu takarda hannuna" Abba ya kalli Aysha yace "Ke tafi nemo min
takarda" da kyar ta mike jiki a sanyaye ta shiga daki, ba a dau lokaci ba ta dawo
rike da takarda Abba ya karba ya mika masa, karba yayi ya ciro pen din dake
aljihunsa duk aka xuba masa ido a parlon barin Mumy da ko kiftawa bata yi, Humainah
kam jikin kujera ta rufe fuskarta hawaye na sakko mata, cikin 'yan mintuna ya gama
rubutunsa a jikin takardan ya mika ma Abba ba tare da ya bari sun hada ido ba, wani
kallo El-ameen ke ma junaid yana son assuring kansa ba saki ya rubuta ba, Abba ya
kusa minti uku idonsa na kan takardan kafin yayi wani murmushi ya mika ma Mumy da
tuni hawaye ya cika idonta, ajiye takardar tayi don baxata iya gani ba, Anty
Nafisat ta dauka da sauri cikin few seconds ta gama karanta takardan, mikewa tayi
lokaci daya idonta ya canxa launi tace "Ehh lallai ka xama dan iska Ahmad, sakin ka
rubuta da gaske?? Ashe kai mara imani ne?" Hannu Abba ya daga mata sannan ya kalli
Junaid yace "Tashi ka tafi" mikewa yayi kansa a kasa ya nufi kofa, Mumy ta fashe da
kuka haka ma Aysha, Humainah kam kin dago kanta tayi, El-ameen ya mike da sauri ya
bi bayansa, karo junaid ya kusa ci da Umma da Hajiya dake labe balcony, bai ko bi
ta kansu ba ya sauka, taku daya biyu yayi still yana kallon Hadiza dake tsaye
balcony din Hajiya lokaci daya ya ganeta, tana ganinsa tayi saurin shigewa parlor
ta rufe kofa, ji yayi kansa na juya masa, kan kace me har ya fice daga compound din
ya isa gun motarsa, fixgosa El-ameen dake biye da shi yayi yace "Sakin ta kayi
Ahmad?" Wani kallo Junaid yayi masa yace "Ehh" murmushin takaici El-ameen yayi yace
"Good!" Junaid ya shige motarsa ya tada ya bar layin.

*Haske Writer's Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

66__67

Ko parking din arxiki bai yi ba ya shige cikin gida ya nufi dakinsa direct ya
kwanta xuciyarsa na bugawa, har aka kira magrib yana kwance can ya mike yayi alwala
ya fita xuwa Masallaci, sai da ya dawo ya shiga dakin Jasmine yaga bacci take,
tashinta yayi ta bude ido a hankali, kallonta ya tsaya yi, ta mike xaune tace
"Captain" kifta idonsa yayi yace "Cikin ya daina?" Ta gyada masa kai yace "Me xa ki
ci?" Cikin sanyin murya tace "am not hungry" mikewa yayi yace "toh kiyi sallah"
daga nan ya fita daga dakin. Har kusan daya na dare junaid bai yi bacci ba yana dai
kwance, mikewa xaune yayi jin kamar an bude kofar parlor ya kalli agogo, jasmine?
Toh ina za ta? ya mike tsaye ya nufi kofa da sauri ya fita, dai dai lokacin da
haske ya gauraye downstairs, still yayi a gun, can kuma ya bude kofar dakinta, ga
mamakinsa sai ya ganta kwance, kansa ya daure ba kadan ba don ya kulle kofar ai,
karasawa dakin yayi da hanxari gun gadon ya cire bargon jikinta ta bude ido a
tsorace, dagota yayi tace "Captain" bai saurareta ba ya fice ya koma dakinsa yana
rike da hannunta ya rufe kofar da key, tace "What's that captain?" Wani kallo ya
mata ba shiri tayi tsit, ya bude closet dinsa ya binciko pistol dinsa har biyu,
xaro ido tayi a tsorace tana komawa baya tace "Captain!" Ya kalli kofa jin ana
haurowa sama, da sauri ta dawo bayansa ita ma tana kallon kofar a mugun tsorace,
hannunta ya rike gam har lokacin idonsa na kan kofar, xaro ido yayi ya ganin key
din hannunsa ya nufi kofar da sauri da nufin sakalawaa yaji an riga sa slotting
key, baya ya koma yana kallon kofar yana kiran Allah a xuciyarsa har aka bude, su
uku ne ko wannensu sanye da bakar facemask, yayi ma biyu pointing din duka bindigan
hannunsa, rungumesa Jasmine tayi ta baya ta runtse ido ta fasa ihu jikinta na rawa
tace "Captain! Who are theyyy" Baya ya dinga komawa tana jikinsa, daya daga cikinsu
ya karaso yayi pointing ma Jasmine bindigar hannun sa yace "Her life or you drop ur
weapon" sauran ma duk suka karaso suka yi yanda yayi, ba karamin tashi hankalin
Junaid yayi ba, lumshe ido yayi a hankali ya sake pistols din hannunsa ya rungumeta
gam, cikin dakiyar murya yace "What did you want from me?" Dariya duk suka yi daya
daga cikinsu yace "Money, cars, houses, infact everything" yana rungume da ita ya
nufi inda atm dinsa yake ya dauka ya jefa masu ya fadi pin, ya kuma dauka makullin
motocinsa har biyu ya jefa masu, da na gidansa daya, cikin dakiyar murya yace "What
again?" Wani dariya duk suka yi, daya daga cikinsu ya tako har gabansa yana
kallonsa, sake kankame Jasmine yayi a karo na farko xuciyarsa ya soma bugawa, ita
ko ko ina na jikinta rawa yake sai kiransa take tana kuka, hannu mutumin yasa a
aljihu ya ciro wani abu fari a leda ya jefar fuskar Junaid, daya daga cikinsu ya
fixge Jasmine, daga nan suka fice daga dakin gaba daya taku daya biyu junaid yayi
da niyar binsu ya xube nan gun, duk kokarin da yayi na son mikewa hakan bai yiwu
ba, wani juyi yaji kansa yana yi, da kyar ya iya mika hannunsa ya jawo wayarsa dake
gefen gado, number El-ameen yake son nemowa amma ya kasa, cikin ikon Allah ya fiddo
lambar, ji yayi kamar numfashinsa na neman daukewa, wayar ya xame daga hannunsa shi
ma ya kuma faduwa nan kasa, a hankali idonsa ya fara rufewa daga haka bai kuma
sanin abinda ke faruwa ba, El-ameen dake xaune da laptop gabansa ya kalli agogo jin
ringing din wayarsa, mikewa yayi ya dauko wayar daga charging da yake, tsayawa
kallon screen din wayar yayi ganin number junaid, da kamar baxai dauka ba sai kuma
ya tabe baki ya daga, shiru yayi bai ce komai, jin shirun yayi yawa yace "Ya aka
yi, mistake i guess, ryt?" Jin ba ace komai ba ya kalli screen din yaga ba a katse
ba, mayarwa yayi kunnensa yace "Hellow?" Tabe baki yayi ya katse wayar, har xai
ajiye sai kuma ya kuma kiransa, har ya gama ring ba a dauka ba, ajiye wayar yayi ya
koma ya xauna sai dai haka kawai hankalinsa yaki kwanciya. Kuka kawai Jasmine take
tana kiran Captain har suka sa ta bayan motar, babu wanda ya ce mata komai har suka
iso wani gida bayan tafiyar kusan minti talatin drivern yayi horn a bakin wani
babban gate, ba a dau lokaci ba aka bude gate din, a parking space suka yi park din
motar drivern motar ya fito kafin sauran su fito, nan take suka cire mask din
fuskarsu daya daga cikinsu na kallon Jasmine yace "Fito!" Ta fashe da wani sabon
kuka tace "Nooo!" Hade rai suka yi gaba daya mai tukin motar ya fito da bindigar
aljihunsa yace "C'mon fito malama" ihu ta fasa a tsorace, ya fixgota yana nuna mata
bindigan ba shiri tayi tsit ko ina na jikinta na rawa, yana kallon sauran dake
tsaye yace "Sai mun hadu gobe you can go with the car" daga haka ya tasa ta gaba
xuwa balcony, suna shiga parlon ta durkushe kasa tana bin ko ina na parlon da
kallo, kamar me counting stairs din ya dinga saukowa yana kallonta, hade rai yayi
yace "Amma na ce you guyz shouldn't scare her fa Salim" Wanda ya kira da Salim ya
xauna saman kujera yace "We didn't" mikewa Jasmine tayi da sauri tana kallon stairs
din jin muryarsa, ya sakar mata murmushi ya buda manyan idonsa yace "Jewel!" Da
gudu ta karasa kusa da inda yake sai kuma ta ja ta tsaya ta fashe da kuka tana
kallonsa, Yace "Amma ba mu yi haka da ku ba salim" mikewa salim din yayi yace "What
did you expect idan bata yi kuka ba toh? Were you expecting her to be laughing
bayan mun dauketa daga gida?" Daga haka ya shiga daki dake parlon, Aliyu ya d'an
bude ido yace "Sorry jewel, they didn't mean to hurt you" hade rai tayi tace "Why
am I here?" Bai ce komai ba ya karasa cikin parlon ya xauna. Washegari da safe
El-ameen ya gama shirin fita office Hafsat ta shigo dakin tace "Breakfast fah?"
Kallonta yayi yace "Sai na fita office" tace "Ohk" ta juya ta fita, mikewa yayi ya
dau wayarsa har xai sa a aljihu junaid ya fado masa ya shiga kiransa, har ya gama
katse wa ba a dauka ba, tsaki yayi ya dau brief case dinsa xai fita wayar ya fara
ring ya duba yaga Aliyu ne, dagawa yayi, daga daya bangaren Aliyu yace "Good
morning" El-ameen yace "Morning Dr, ya gida" Aliyu yace "Alhmdllh, ga ni ga Jewel!"
El-ameen ya xaro ido yace "Jewel kuma?" Kallon Jasmine dake xaune ta takure waje
daya Aliyu yayi ya mika mata wayar yace "Ur uncle" kin karba tayi ta fashe da kuka
a hankali tace "Ka kai ni wajen captain plss" Katse wayar El-ameen yayi ya fice ya
dau motarsa a parking space ya bar compound din, cikin 'yan mintuna ya isa gidan
Junaid, bedroom ya nufa direct, ya kusa second goma tsaye bakin kofa yana kallon
hodar dake xube a kasa ko ba a gaya masa ba yasan ta meye, ya ciro handkerchief ya
rufe hancinsa ya karasa cikin dakin ya durkusa kusa da shi yana kallonsa, mikewa
yayi ya fice daga dakin ya fiddo wayarsa ya shiga kiran Aliyu, bugu biyu ya daga, a
fusace yace "Was that the deal, don me xa kasa ayi masa haka...." Dariya Aliyu yayi
yace "Girman kansa nake son sauke masa, kuma da ca suka yi ya basu ita cikin lamana
ba yarda xai yi ba" daga haka ya katse wayar, dafe kai El-ameen yayi can ya juya ya
koma dakin. Abban El-ameen ne tsaye kan Junaid yana kallonsa, awan sa kusan hudu
kenan hospital din still unconscious, El-ameen ma na jingine daga jikin bango tun
safe bai bar dakin ba yana tare da shi, dad din nasa ya kallesa yace "Wai an sani
ma kuwa a can gidansu?" El-ameen ya girgixa kai, Dad yace "Why? You mean baka kira
su ba har yanxu" yace "Xan kira yanxu Dad, bana son daga masu hankali ne" Dad din
yace "No call them right away! Kuma ka sake masa alluran" daga haka ya juya ya
fita, El-ameen ya sauke ajiyar xuciya ya ja kujera ya xauna ya dau wayarsa ya shiga
kiran Abban Junaid, bugu uku ya daga, ya gaishesa da ladabi yace "Abba dama Ahmad
ne ke asibiti tun safe....." Bai kai karshe ba Abba ya katse sa ta hanyar cewa
"Allah ya sauke, ka kira uwarsa" daga haka ya katse wayar, El-ameen ya tsura ma
wayar ido, lumshe ido yayi yana addu'ar Allah yasa ya farfado kafin yamma. K'in
sakin jiki Jasmine tayi duk kuwa da Kanwar Aliyun dake gidan, hatta abinci taki ci,
banda kuka babu abinda take ita ya kai ta gidan Captain, bayan la'asar gari yayi
sanyi Aliyu yace "Toh tashi in kai ki" mikewa tayi tana share fuskarta ya fara
tafiya ta bi bayansa, Ramla da duk xaman gidan ya isheta ta bi su da kallo, wata
kofa ya bude ya fita tana biye da shi a baya, babban garden ne sosai ga carpet
grasses Kore shar shimfide a ko ina na garden din, sannan ga babban swimming pool
xagaye daga gefe, tsuntsaye ke ta shawagin su a wajen gwanin sha'awa, kare idonta
ta shiga yi tace "Ohhsh, My head is aching, I can't follow here" ya kalleta yace
"This is the only road" tana kare fuskarta ta shiga takowa a hankali, xaunawa yayi
ya nuna mata gefensa yace "Sit" ta ki xama tace "Noo mu wuce plss, I don't like
here, it's making me dizzy" hade rai yayi yace "Sai in kira dog yanxu idan baki
xauna ba" da sauri ta xauna tana rurrufe idonta, a hankali yace "Open ur eyez!"
Girgixa kai tayi kmr xata yi kuka tace "It's aching me" yace "Ki bude a hankali" a
hankali ta shiga bude idon ta shiga bin ko ina na garden din da kallo, yace "What
did you see?" Shiru tayi sai kuma murya can kasa tace "Green grasses!" Yace "No!
Look deep, I mean don't blink your eyez nd tell me what you see" shiru tayi bata ce
komai ba idonta na kan koren ciyayin ko kiftawa bata yi, a hankali ya mike ya juya
ya bar gun ya koma cikin gida. Sai kusan Magrib ya koma garden din ya ganta kwance
tana bacci, durkusawa yayi kusa da ita a hankali yace "Jasmeen" firgit ta farka
tace "Ummana" sai kuma ta mike tsaye da sauri, rike kanta tayi tace "Wayyo Kai na"
mikewa yayi ya komawa baya yana kallonta ganin faduwa xata yi, kasa tabata yayi har
ta kai kasa, sannan ya durkusa har lokacin idonsa a kanta, ta kusa minti biyar bata
dago ba, can ta dago a hankali idonta ya kada sosai ba kadan ba, da kyar tace "Ka
kai ni wajen captain pls, I want to go to him" yace "Toh bari in baki Magani sai in
kai ki" mikewa yayi ita ma ta mike da kyar, kasa tafiya tayi ganin faduwa xata yi
ya juya da sauri ya koma
cikin gidan ya kira Ramla ta fito ta kamata suka shiga cikin gidan, tea me kauri
ya hada mata ya tilasta ta ta sha, sannan ya bata Magunguna tana sha bacci ya
dauketa, Ramla ce ta rufa mata bargo ya mike yana kallonta yace "You stay with her
kar ki bar ta ita kadai" kai ta gyada masa ya juya ya fita daga dakin.

*Haske Writer's Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

68__69
Har washe gari Junaid na kwance unconscious, duk wani taimako Dad d'in El-Ameen
saida ya tabbatar sun bashi amma ko kadan baya responding to treatment, El-Ameen
gaba daya hankalinshi ya tashi duk tausayinshi ya cikashi, Har lokacin babu wanda
ya lek'o daga gidansu Junaid, a bangaren Jasmine kuwa kuka ta dinga yi ita a kaita
gidan captain, shareta Aliyu yayi da farka can kuma yace "Toh tashi" mik'ewa tayi
ta nufi gun slippers d'inta xata sa, kamar wacce ta tuna wani abin ta juyo tana
kallonshi tace "Are you sure you are taking me to captain?" murmushi yayi ba tare
da ya kalleta ba ya kad'a kai yace "Yes Jewel, amma zaki dena wannan kukan and
clean your face" Kamin ya gama magana ta shiga share hawayen dake fuskanta tace "Av
cleaned it" yace "Good", daga haka yayi gaba ta biyoshi a baya, hanyan da yabi jiya
shi taga yabi yauma, yana bud'e k'aramin k'ofar garden d'in ta had'e rai taja ta
tsaya daga wajen, juyowa yayi ya yaga ta had'e rai, murmushi yayi ya dawo gabanta
yana kallon kyakkyar fuskarta da manyan idanunta da hawaye ya cika zubowansu any
moment yace "Don't you want to see Captain?", kamar bataji mey yace mata ba tayi
shiru tana kallon k'ofan, ganin baza tace komai ba yasa yace "He said we should
wait for him there", ya fad'a yana nuna mata garden d'in da yatsanshi, yaci gaba
"Captain is waiting for you in there", kamin ya rufe baki ta maza ta k'araso ta sa
kai cikin garden d'in, murmurshi kawai yayi tareda shafa fuskarshi ya biyota a
baya, waige waige ta dingayi ko zata ga Captain amma bata ganshi ba, ta juyo da
idonta da suka kuma cikowa zatayi k'ofan taga ya shigo, hawayen na k'arasa
gangarowa tace "You said he is waiting for me in here", ya girgiza kai yace "Erhm
No, he said we should wait for him here, he is coming to pick you ltr" jiki a
sanyaye batace komai ba ta koma kan bench d'in ta zauna tareda kifa kanta kan
cinyoyinta, daga gefenta ya samu waje ya zauna, yace "Jewel!" Kin dagowa tayi,
kamar bai son magana yace "Tell me what you see in here" dago kanta tayi ya nuna
mata carpet grass dake shimfide yace "Me kika ga" shiru tayi bata ce komai ba tana
bin ko ina na garden din da kallo, mikewa yayi ba tare da ya bari ta lura ba ya bar
gun. Da rana El-Ameen na zaune d'akin Junaid yayi xurfi a tunanin da yake, kamar
daga sama yajiyo muryan Junaid na ce mishi "Where is she? Where is Jasmine?", Da
hanzari ya mike ya iso gaban gadon yana kallonsa, dukawa yayi murmushi yayi
escaping lips dinsa yace "Ahmad how you feeling now?" Dauke kai Junaid yyi ya shiga
k'ok'arin mik'ewa yaji kanshi na wani mugun sara mishi komawa yyi ya kwanta ya
lumshe ido hade da dafe kai yace "Where is she?, I need to get to her, she is in
trouble" da kyar yayi maganan yana kokarin sake tasowa, wani sarawa da kanshi yayi
yasa yayi maza ya koma ya kwanta, El-ameen ya rik'o shi yace "Ahmad stop proving
stubborn, you are still weak", Junaid yace "No! Help me get up pls, she's in
trouble frnd!" rasa me zai ce masa El-ameen yayi, duk yaji tausayinshi ba kad'an
ba, bai kuma ce masa komai ba ya koma ya xauna don yasan ba lallai ya iya mikewa
ba, Allura kawai ya had'a daga karshe ganin Junaid ba shiru xai yi ba yayi mishi, a
hankali ya dinga lumshe ido har bacci ya d'aukeshi, Yana fara bacci El-ameen ya
k'ira wasu nurses d'in yace su kula da shi yanzu zaije ya dawo, ya jadadda musu da
he should be under well supervision yanxun nan zaije ya dawo, a risine suka amsa
mishi daga haka ya d'auki key yayi waje, kai tsaye gidansu Junaid ya nufa, daga
bakin gate ya tsaya ya shiga k'iran Khadeejah a waya, tana d'auka yace "Ina bakin
gate Khadeejah, ki fito yanzu", bata fi 5mins ba ta fito tunanin Yayanta duk ya
cikata, da kanshi yasa hannu ya bud'e mata k'ofa tana shiga yaja motar, jikinta duk
a sanyaye tace "Yaa El ina wuni", amsa mata yayi ba tare da ya kalleta ba tace "Ya
jikin Yaa Aj?" ta k'arasa maganan kaman zatayi kuka, saida ya kalleta kamin ya
maida kallonshi kan driving din da yakeyi yace "Wajenshi zamu yanzu", bata sake
cewa komai, yace "me ya hana ku xuwa?" Hawaye ne ya gangaro mata tace "Abba!" yace
"Mumy fa?" Tace "Tana gida" bai kuma cewa komai ba har suka isa asibitin ta biyoshi
a baya bayan sun fito motan, shi ya fara shiga d'akin, zaune ya tadda nurses din
kan sofa dake d'akin, suna ganinshi suka mik'e ya tambayesu ko sunga wani movement
bayan fitanshi suka ce a'a, daga haka ya sallamesu sukayi Waje, Khadeejah da har ta
k'arasa gaban gadon idonta cike da hawaye ta durkusa tana kallon yayan nata, kuka
ta shiga yi, El-ameen yace "Ba abinda na kira ki kiyi ba kenan" da kyar ta tsaida
kukan nata tana share hawayen fuskarta tace "Yaa El wai su waye suka mishi haka,
kuma ba a sansu ba?" El-ameen yayi mata assuring murmushi yace "Kiyi mishi addu'a
kawai, he will be fine", ta kad'a mishi kai, karasowa yayi ya shiga Examining
Junaid yana gamawa ya fita. Wajen hud'u da wani abu Khadeejah na zaune Junaid ya
farka, da saurinta ta isa wajenshi ta zauna kan kujera kamar zatayi kuka tace "Yaa
Aj ya jikinka?", bai bata amsa ba ya shiga kokarin mikewa xaune yace "Mumy fah?" A
hankali tace "tana gida" komawa yyi ya kwanta yace "Humainah?" kai ta kad'a tace
"um tana gida", daga haka babu wanda ya sake magana cikinsu, kiran da Hajiya tayi
mata yasa ta koma gida ba don ta so ba. Da daddare Junaid na kan gado idanunshi
lumshe sai dai ba bacci yake ba shi daya yasan abinda yake ji a lokacin, bude kofar
dakin aka yi duk da yana son bude ido amma ya kasa, Humainah ce ta shigo dakin, ta
kusa minti biyu tsaye bakin kofar kafin ta karaso a sanyaye ta isa gabanshi ta
durk'usa, lkci daya hawaye ya cika Idonta, da kyar ya bude idanunshi ya sauk'e
kanta jin motsin mutum kusa dashi, sunkuyar da kanta tayi hawayen da ke makale
idonta ya gangaro, ya lumshe ido a hankali ya kamo hannunta ya rik'e cikin nashi
dan bazai iya kallonta ba, kuka ta fashe da sosai, cikin sanyin murya yace "Am.. Am
sorry, for everything" bata iya ta ce masa komai ba sai kukan da take yana son
lallashinta amma ya kasa, bude kofa aka yi El-ameen ya shigo, jim yayi ganinta, can
ya karaso ciki tun kan yace komai ta mike ta fice daga dakin da sauri. Washegari
da safe junaid na bacci El-ameen ya fita, gidan Aliyu ya nufa yana gama parking a
waje ya shiga gidan, bin compound din yayi da kallo ganin bai ga motar Aliyu ba, ya
bude kofar parlor ya tsaya yana bin ko ina da kallo, Jasmine ce ta leko daga
kitchen tana ganinshi ta fito a guje tayi inda yake ta wara ido tace "Uncle!" Gira
ya daga mata yace "Uhmm" bata fuska tayi tace "plsss take me away from here, take
me to Captain, kallon stairs yayi yace " Dauko hijab din ki" da sauri ta tafi dauko
hijab din, ya fita ta bi bayansa. Asibiti ya koma da ita dan ya gaji da tambayarta
da junaid ke jefo masa a ko da yaushe, tana biye da shi a baya suka shiga ward din,
idon junaid biyu a lokacin don Dad din El-ameen bai dade da fita ba, ido ya kafe su
da har suka karasa shigowa dakin, El-ameen i xamansa kan kujera yana kallonsa,
gadon ta nufa tana kallon ruwan hannunsa ta durkusa kusa da shi kamar xata yi kuka
tace "Whats wrong with you captain, are you sick?" Kallonta kawai yake kamar bai
gane me take nufi ba, ganin bai ce komai ba yasa tace "Aren't you happy am back
Captain....? Talk to me plss" hawaye ne ya taru idonta ganin yaki cewa komai still,
ta juya tana kallon El-ameen, tabe baki yayi ya mike ya fice daga dakin. kamar
jira Junaid yake ya fita yana fita ya fixge drip d'in dake hannunshi ya mik'e tsaye
da k'yar, ji yayi jiri na neman k'ada shi hakan yasa ya dafa kanshi ya jingina da
bangon, tana ganin haka ta mik'e da sauri tazo gabanshi tana kokarin rik'eshi tace
"Captain you didn't tell, are you sick?", makullin motar da El-ameen ya ajiye kan
table ya d'auka yace "Let's go" xaro ido tayi tace "You are sick Captain, you can't
even stand right lemme call Uncle for you", ganin zata b'ata mishi lokaci ya samu
da k'yar yayi regaining balance d'inshi ya jefa mata wani kallo ya kamo hannunta
suka fice daga d'akin, haka ya dinga tafiya da k'yar har suka iso gun mota, Jasmine
sai ce mishi takeyi "Captain ina xa mu tafi" bai tanka mata ba, ganin yanda yake
tafiya tace "Kafar ka ne ke ciwo" motar yasa ta shiga, ya shiga shima ya tada suka
bar asibitin, El-ameen da ya fito da sauri dan ya koma d'aki bai gansu ba a kan
idonshi motar tabar premises din asibitin, driving kawai Junaid yake ba tare da
yasan me yakeyi ba, Roughly yake driving d'in kamar wani mai tseran formular, he
just want to take her away, Jasmine na ganin irin driving d'in da yakeyi lokaci
d'aya ta rikice ta shiga k'iran sunansa, sosai take ihu da ya rikita Junaid d'in
shima lokaci d'aya yayi loosing control d'inshi motar ta kufce daga hannunshi, har
lokacin babu abinda jasmeen take banda ihu, rintse ido kawai Junaid yayi dan shima
yana jiran hukuncin Allah a kansu, da k'arfi yaji sunyi hitting wani abu da yasa
kanshi yin baya, yakai 5mins zaune idonshi rintse, a hankali ya samu ya bud'e
idonshi ya sauk'e kan Jasmine, kallonshi kawai takeyi da wasu irin expressions
shimfid'e fuskarta, ganin irin kallon da take mishi yasa ya kawo hannu zai tab'ata
to check if she is fine, gani yayi tayi Luuu zata fad'a baya yayi maza ya rikota,
wani irin skipping heart d'inshi yayi ganin yanda ta sakar masa jiki bata motsi,
Sosai ya rud'e ganin suma tayi, bai damu da mutanen da suka tarar mai jikin mota ba
don ba ma jin abinda suke cewa yake ba, da k'yar ya samu ya kwantar da ita daga
gefe ya shiga k'ok'arin tada motar, Luckily ya samu yayi igniting motar tareda yin
reverse, ikon Allah kawai ya maidasu asibitin, ko gama parking baiyi ba ya fito
daga cikin motar, jingina yayi jikin motar jin yana neman faduwa, El-ameen dake
tsaye har lokacin inda yake cos he was still surprise, ya karaso gun motar yana
kallonsa yana son gano abinda yasa ya dawo. Kin ce masa komai Junaid yayi, can ya
nufi cikin asibitin ya bar sa nan tsaye, bude motar El-ameen yayi ya ja baya da
mamaki ganinta a kwance, bin junaid yayi da kallo
kafin ya matso kusa da ita ya kai hannu kan fuskarta breathing d'inta yaji na
hitching sama sama, reception ya nufa da sauri sai ga shi da nurses da stretcher,
bedroom dinsa na office ya kwantar da ita ya fiddo oxygen bag cikin wani wardrobe
daidai bakinta ya jona tube snn ya koma ya kunna socket d'in da Oxygen d'in ke
jone, kan sofa El-ameen ya koma ya zauna ya da rik'e kanshi da duka hannayenshi
biyu yana jin yanda kan ke sara mishi sbd stress amma bashida strength d'in koda
nemawa kanshi magani, mikewa yayi a fusace ya fita nemo junaid, tsaye ya gansa daga
waje ya karasa kusa da shi ya fixgosa yace "What happened to her?" Kallonsa kawai
Junaid yake da wani expression a fuskarsa don a tunaninsa abu ne ya sameta, turasa
yayi ya shiga office din da sauri ya nufi bedroom direct, lumshe ido yayi xuciyarsa
na bugawa ya durkusa kusa da ita cikin sanyin murya yace "Am sorry jasmine, am
sorry" ya kusa minti uku kafin ya bude ido ya zuba mata yana kallon yadda breathing
d'inta ke dawowa dai dai a hankali, duk sai ya nemi ciwon kai da dizziness din da
yake ji ya rasa, Shigowa El-ameen yayi dakin yace "Yea ka kasheta kawai kowa ma ya
huta Ahmad, just kill her" ko kallonsa junaid bai yi ba idonsa a kanta, a hankali
ta bude ido ta sauke kansa, lumshe ido yayi yana hamdala a xuciyarsa, ta kusa minti
daya tana kallonsa kafin ta mike zaune da sauri tana bin ko ina na dakin da kallo,
El-ameen ya sauke ajiyar xuciya shi ma, kallon El-ameen ma tayi sannan ta sake
kallon junaid, kusa da Ita El-ameen ya dawo ya cire oxygen din yace "Baby are you
okay?" Jin bata ce komai ba ya kai hannu xai dafa goshinta ta koma baya da sauri
tana masa wani irin kallo, Kallon junaid yayi junaid ma ya kallesa, ta shiga
kokarin sauka daga kan gadon junaid ya mike yace "Where are you going to?" Ko
kallonsa bata sake yi ba ta nufi kofa da sauri, bin ta junaid yayi ya wani fixgota
yace "keee" tana juyowa bai ankara ba sai ji yayi ta sauke masa mari, a hankali ya
saketa yana kallonta, ta fashe da kuka ta durkushe wajen tace "Where is this?"

*Haske Writer's Association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

70.....

Still junaid yayi yana kallonta ko kiftawa bai yi, El-ameen ya karaso shi ma idonsa
a kanta ya durkusa kusa da ita ya dake yace "Why did you slap him?" Mikewa tayi da
sauri tace "How dare him touch me, who is he?" Kasa cewa komai El-ameen yayi ya
hadiye yawu da kyar ya mike yana kallon junaid da ya kasa daina kallonta, kofa ta
nufa El-ameen yayi saurin bin ta yace "Wait! Ina xa ki" kokarin bude kofar take ta
kasa, can ta fashe da kuka ta juyo tana kallonsu tace "Where is this plss, me nake
yi a nan?" El-ameen ya sauke ajiyar xuciya a hankali ya juya ya kalli junaid,
juyawa junaid yayi ya shige bedroom yayi banging kofar, bin bayansa yayi da sauri,
junaid ya xauna gefen gado, El-ameen ya karasa kusa da shi yana kallonsa, murmushi
ne yayi escaping lips dinsa yace "Frnd it seems ta dawo hankalinta fa, from all
indication her memory is back, ohh God! Isn't it amazing frnd?" ko kallonsa junaid
bai yi ba, hakan yasa ya hade rai, can ya juya ya fice, jingine ya ganta jikin
bango tana bin ko Ina na office din da kallo, tana ganinsa ta fashe da kuka tace
"Tell me where is this plss, ina Usman? What are we doing here?" Tausayinta ya ji
sosai cikin sanyayyan murya yace "kin ga baki da lafiya ne shi yasa kika ga kan ki
a nan, I am Dr El-ameen Umar, i....." Tsaida kukan tayi da sauri tace "Me ya
sameni?" Shiru yayi yana kallonta, kallon jikinta ta shiga yi tace "Get me out of
here plss, where is my driver?" Rungume hannayensa yayi yace "He went to call ur
parent!" Ta buda ido tace "My parent? Stop kidding me pls, where is usman, and???"
Langwabar da kai yayi yace "this is katsina! Where are you from" xaro manyan
fareren idonta tayi tace "What? Katsina??" Gyada mata kai yayi yace "Yea, sit in
gaya maki abinda ya kawo ki nan" wani kallo ta watsa masa Calmly tace "No! Just get
me outta here" kallonta yake da expression din da xa a iya kira da na mamaki, is
she this rude? Hannunta ta daga tace "Before the count of 5, I want to see me out
of here!" Xaro ido yayi yace "If not?" Wani mugun kallo take masa tace "Are you
daring me?" Xai yi magana junaid ya fito daga bedroom ya nufi kofar office din ya
bude, ya juya yana kallonta fuskar nan tasa a murtuke yace "Get out!" daga sama har
kasa take kallonsa tace "Or?" Ji yayi kamar ya kifa mata mari, ya dake yace "I
throw you out" wani tsaki me lafiya ta ja tana hararansa tace "Kayi kadan!" Bai san
lokacin da ya daga hannu ba sai ji yayi El-ameen ya rikesa yace "meye haka captain!
What are you doing" bai jira cewarsa ba ya shige bedroom dashi ya kullo kofar,
junaid da tunda yake mace bata samu fuskar da xata yi masa kallon banxa ba ya hade
fist dinsa lokaci daya idonsa ya kada, xuciyarsa na bugawa yace "I regret
everything Ahmad, a kan wannan brat din nayi ruin din relationship dina da parent
dina, is this who she is...." El-ameen ya lumshe ido ya bude yace "No! Consider her
plss, never judge a book by just it cover..." Xaunawa junaid yayi ya rike kai
xuciyarsa na tafarfasa, El-ameen ya juya ya fito daga dakin, tsaye ya ganta ta wani
hade rai, tana ganin El-ameen tace "Did he try slapping me?" El-ameen yace "No he
didn't" tace "Good, get me out of here" El-ameen ya ja kujera ya xauna yace "Since
you don't want to cooperate, its unfortunate to say, drivern ki da kike tambaya is
late, you two had an accident shekaranjiya, and you were unconscious tun lokacin
sae yau kika farfado, here is katsina state" kallonsa take da mugun shock, can ta
sulale gun tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un....." Ta maimaita hakan yayi
sau biyar, can ta fashe da kuka sosai tace "Me muka xo yi katsina..." Mikewa tayi a
rude tace "Oh my God, Where is my farida..." Shiru yayi yana kallonta, da gudu ta
isa kusa da shi ta kamo hannunsa tace "Plss tell me Dr, where is my sister, my
sister...." Kasa cewa komai yayi sai kallonta da yake da tausayi, ta fashe da wani
matsanancin kuka tace "Ka min magana Dr, Ina kanwata" jin yaki cewa komai ta fada
kansa tana kuka sosai, dagowa tayi da sauri tana kallonsa kamar me naxari, ta wara
ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Dr Ummi fa, where is she, ina take
ita?" Dafa shoulder dinta yayi don ya ma rasa amsan da xai bata, ya zaunar da ita
yace "Look, sun tafi gida....." Wani kara tayi ta kamo hannunsa tace "Nooo, kar ka
ce min haka Dr, we were all together, where is the car...." Kuka ta fashe da sosai,
sai a sannan ya fara da ya sanin ce mata drivernta ya rasu, kwantar da murya yayi
yace "Kinga sisters dinki are all fine, sun je gida fadi ma parent dinku ne, but if
you can't wait for the arrival of ur parent ki gaya mana garin ku sai a kai ki yau
din nan" har wani rawa jikinta yake tace "I am from bauchi" yace "Where in bauchi?"
Sake hannunsa tayi ta koma baya hawaye na sauko mata tace "idan mun je nasan hanya,
plss a kai ni yanxu" shiru yayi yana kallonta, ya daga kai jin an bude kofar
bedroom, Junaid ne ya fito bai ko kallesu ba ya nufi kofar ya bude ya fice, El-
ameen ya mike da sauri ya bi bayansa, har ya fara sauka stairs ya dafosa yace
"Ahmad, she said she's from bauchi" Junaid ya juyo ya dake yace "So?" El-ameen yace
"Yaushe xa a maidata gida?" Cire hannunsa yayi daga shoulder dinsa yace "Am going
no where!" El-ameen ya buda ido yace "Baka cika ladan ka ba kenan" tafiya ya ci
gaba da yi yace "Na bar maka" El-ameen ya bi sa da kallo har ya sauka sannan yace
"uhm wnn ne kuma baka isa ba" daga haka ya juya ya koma office, kuka sosai ya
sameta tana yi, ya durkusa kusa da ita yace "na fa ce maki yan uwanki na gida"
mikewa tayi da sauri tace "Yanxu xa mu tafi plss?" Ya langwabar da kai yace "Ni ban
iya tuki ba, wanda ya iya kuma kin maresa, nd you were rude to him, kuma shi ya
kawo ki asibitin nan" mikewa tayi da sauri tace "ka kai ni motor park kawai, I will
be okay, you help me thank him" daga haka ta nufi kofa da sauri bin bayanta yayi ya
sha gabanta yace "Dama ta haka ake biyan good deed baiwar Allah?" Wani kallo tayi
masa tace "Toh me yake bukata, money?? or what!"

*Haske writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

71.....

Still junaid yayi yana kallonta ko kiftawa bai yi, El-ameen ya karaso shi ma idonsa
a kanta ya durkusa kusa da ita ya dake yace "Why did you slap him?" Mikewa tayi da
sauri tace "How dare him touch me, who is he?" Kasa cewa komai El-ameen yayi ya
hadiye yawu da kyar ya mike yana kallon junaid da ya kasa daina kallonta, kofa ta
nufa El-ameen yayi saurin bin ta yace "Wait! Ina xa ki" kokarin bude kofar take ta
kasa, can ta fashe da kuka ta juyo tana kallonsu tace "Where is this plss, me nake
yi a nan?" El-ameen ya sauke ajiyar xuciya a hankali ya juya ya kalli junaid,
juyawa junaid yayi ya shige bedroom yayi banging kofar, bin bayansa yayi da sauri,
junaid ya xauna gefen gado, El-ameen ya karasa kusa da shi yana kallonsa, murmushi
ne yayi escaping lips dinsa yace "Frnd it seems ta dawo hankalinta fa, from all
indication her memory is back, ohh God! Isn't it amazing frnd?" ko kallonsa junaid
bai yi ba, hakan yasa ya hade rai, can ya juya ya fice, jingine ya ganta jikin
bango tana bin ko Ina na office din da kallo, tana ganinsa ta fashe da kuka tace
"Tell me where is this plss, ina Usman? What are we doing here?" Tausayinta ya ji
sosai cikin sanyayyan murya yace "kin ga baki da lafiya ne shi yasa kika ga kan ki
a nan, I am Dr El-ameen Umar, i....." Tsaida kukan tayi da sauri tace "Me ya
sameni?" Shiru yayi yana kallonta, kallon jikinta ta shiga yi tace "Get me out of
here plss, where is my driver?" Rungume hannayensa yayi yace "He went to call ur
parent!" Ta buda ido tace "My parent? Stop kidding me pls, where is usman, and???"
Langwabar da kai yayi yace "this is katsina! Where are you from" xaro manyan
fareren idonta tayi tace "What? Katsina??" Gyada mata kai yayi yace "Yea, sit in
gaya maki abinda ya kawo ki nan" wani kallo ta watsa masa Calmly tace "No! Just get
me outta here" kallonta yake da expression din da xa a iya kira da na mamaki, is
she this rude? Hannunta ta daga tace "Before the count of 5, I want to see me out
of here!" Xaro ido yayi yace "If not?" Wani mugun kallo take masa tace "Are you
daring me?" Xai yi magana junaid ya fito daga bedroom ya nufi kofar office din ya
bude, ya juya yana kallonta fuskar nan tasa a murtuke yace "Get out!" daga sama har
kasa take kallonsa tace "Or?" Ji yayi kamar ya kifa mata mari, ya dake yace "I
throw you out" wani tsaki me lafiya ta ja tana hararansa tace "Kayi kadan!" Bai san
lokacin da ya daga hannu ba sai ji yayi El-ameen ya rikesa yace "meye haka captain!
What are you doing" bai jira cewarsa ba ya shige bedroom dashi ya kullo kofar,
junaid da tunda yake mace bata samu fuskar da xata yi masa kallon banxa ba ya hade
fist dinsa lokaci daya idonsa ya kada, xuciyarsa na bugawa yace "I regret
everything Ahmad, a kan wannan brat din nayi ruin din relationship dina da parent
dina, is this who she is...." El-ameen ya lumshe ido ya bude yace "No! Consider her
plss, never judge a book by just it cover..." Xaunawa junaid yayi ya rike kai
xuciyarsa na tafarfasa, El-ameen ya juya ya fito daga dakin, tsaye ya ganta ta wani
hade rai, tana ganin El-ameen tace "Did he try slapping me?" El-ameen yace "No he
didn't" tace "Good, get me out of here" El-ameen ya ja kujera ya xauna yace "Since
you don't want to cooperate, its unfortunate to say, drivern ki da kike tambaya is
late, you two had an accident shekaranjiya, and you were unconscious tun lokacin
sae yau kika farfado, here is katsina state" kallonsa take da mugun shock, can ta
sulale gun tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un....." Ta maimaita hakan yayi
sau biyar, can ta fashe da kuka sosai tace "Me muka xo yi katsina..." Mikewa tayi a
rude tace "Oh my God, Where is my farida..." Shiru yayi yana kallonta, da gudu ta
isa kusa da shi ta kamo hannunsa tace "Plss tell me Dr, where is my sister, my
sister...." Kasa cewa komai yayi sai kallonta da yake da tausayi, ta fashe da wani
matsanancin kuka tace "Ka min magana Dr, Ina kanwata" jin yaki cewa komai ta fada
kansa tana kuka sosai, dagowa tayi da sauri tana kallonsa kamar me naxari, ta wara
ido tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Dr Ummi fa, where is she, ina take
ita?" Dafa shoulder dinta yayi don ya ma rasa amsan da xai bata, ya zaunar da ita
yace "Look, sun tafi gida....." Wani kara tayi ta kamo hannunsa tace "Nooo, kar ka
ce min haka Dr, we were all together, where is the car...." Kuka ta fashe da sosai,
sai a sannan ya fara da ya sanin ce mata drivernta ya rasu, kwantar da murya yayi
yace "Kinga sisters dinki are all fine, sun je gida fadi ma parent dinku ne, but if
you can't wait for the arrival of ur parent ki gaya mana garin ku sai a kai ki yau
din nan" har wani rawa jikinta yake tace "I am from bauchi" yace "Where in bauchi?"
Sake hannunsa tayi ta koma baya hawaye na sauko mata tace "idan mun je nasan hanya,
plss a kai ni yanxu" shiru yayi yana kallonta, ya daga kai jin an bude kofar
bedroom, Junaid ne ya fito bai ko kallesu ba ya nufi kofar ya bude ya fice, El-
ameen ya mike da sauri ya bi bayansa, har ya fara sauka stairs ya dafosa yace
"Ahmad, she said she's from bauchi" Junaid ya juyo ya dake yace "So?" El-ameen yace
"Yaushe xa a maidata gida?" Cire hannunsa yayi daga shoulder dinsa yace "Am going
no where!" El-ameen ya buda ido yace "Baka cika ladan ka ba kenan" tafiya ya ci
gaba da yi yace "Na bar maka" El-ameen ya bi sa da kallo har ya sauka sannan yace
"uhm wnn ne kuma baka isa ba" daga haka ya juya ya koma office, kuka sosai ya
sameta tana yi, ya durkusa kusa da ita yace "na fa ce maki yan uwanki na gida"
mikewa tayi da sauri tace "Yanxu xa mu tafi plss?" Ya langwabar da kai yace "Ni ban
iya tuki ba, wanda ya iya kuma kin maresa, nd you were rude to him, kuma shi ya
kawo ki asibitin nan" mikewa tayi da sauri tace "ka kai ni motor park kawai, I will
be okay, you help me thank him" daga haka ta nufi kofa da sauri bin bayanta yayi ya
sha gabanta yace "Dama ta haka ake biyan good deed baiwar Allah?" Wani kallo tayi
masa tace "Toh me yake bukata, money?? or what!"

*Haske writers association*馃挕


� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

72......

Sakin baki El-ameen yayi yana kallonta, can yace "Can you pay him?" Tace "Yea of
course" murmushi yayi ya ma rasa me xai ce mata ya juya ya koma ya xauna, bin
bayansa tayi ta hade rai sosai tace "nace ka bude min kofa in fita, let me out pls"
girgixa kai yayi yace "I know no where here, wanda kika mara shi ne d'an garin and
shi ya kawo ki nan unconscious, he paid for everything pertaining to ur bill and
was with you till today that you recovered...." Shiru tayi tana kallonsa, can ta
sauke ido a hankali tace "Does that call for his touching me, he touched my body,
why did he? he shudnt have...." Shiru tayi can ta dafe kanta tace "Ohk am, I am
sorry, I.. I am sorry" taso wa yayi yace "Very good of you, yanxu dole sai mun je
gidansu ki basa hakuri sannan sai ya maida ki gida koh" shiru tayi can ta turo baki
tace "Do I have to?" Yace "Of course yes!" A hankali tace "But he's so rude" dariya
ta basa yace "And you were rude to him also!" Girgixa kai tayi tace "No I wasn't"
xai yi magana aka kwankwasa kofa, mikewa yayi ya kalleta ya nuna mata kujera yace
"Sit, let me check who's at the door" ba musu ta xauna, ya karasa gun kofar ya
bude, wata nurse ce tsaye tace "Good morning sir, ur attention is being needed...."
Yace "Alryt, ohk" daga haka ya rufe kofar ya dawo yana kallonta yace "Ohk, Ya sunan
ki?" Da kamar baxata ce komai ba, sai kuma ta d'an kallesa a takaice tace "Zahrah!"
Buda ido yayi yana murmushi yace "Ohk Zahra, you wait for me here, xanje in yi
attending ma patient downstairs, yanxun nan xan dawo sai mu je ki ba captain hakuri
mu maida ki gida!" Tace "Who's that?" Wara ido yayi yace "Ur helper" ajiyar xuciya
ta sauke tace "Ohk, make it fast plss ina son ganin sisters dina, and am feeling
heat in here" gyada mata kai yayi yana murmushi ya kara Ac dake office din ya nufi
kofar ya fita ya kullo daga waje, tana nan xaune office din har bayan kusan awa
daya duk ta kagu ya dawo bini bini xata kalli agogo, can ta mike ta nufi kofa ta
murda ta ji a rufe ji tayi kamar ta rusa ihu ga shi hankalinta yaki kwanciya, kuka
ta saki daga karshe ta koma ta xauna, bude office din taji ana yi ta mike da sauri
wata nurse ta shigo rike da ledan eatry, karasowa tayi ta ajiye ledan tace "Dr yace
a kawo maki abinci" da sauri tace "Where is he?" Nurse din tace "He's at the
theatre, but ya kusa fitowa" daga haka ta juya ta fita ta bi ta da kallo, komawa
tayi a sanyaye ta xauna, junaid ne ya fado mata, ta turo baki tace "He started
everything, he's just rude" ledan abincin ta dauka ta bude ta tsura ma fried rice
da naman ido, girgixa kai tayi coz bata cin abinci ba na gidansu ba, mayarwa tayi
ta rufe, gajiya tayi da xama ta jinginar da kanta jikin kujera lokaci daya bacci ya
dauketa, sha biyu saura El-ameen ya shigo office din, kallonta ya tsaya yi daga
bakin kofa can ya karaso ya iso gabanta ya durkusa yana kallon kyakkyawan fuskarta,
jasmine d'in then yake tunawa yayi murmushi yana naxarin yanda xata dauki labarin
abinda ya sameta, da kamar ya tasheta ta gyara kwanciya sai kuma ya fasa don kar ta
basa nasa tsaraban marin, he will just like to know who she is da take da tsiwa
haka. Mikewa yayi ya shiga bedroom don yin wanka. Ko da ya fito daga dakin
masallaci ya fita yin sllhn Azahar, yana dawowa ya sameta har lokacin tana bacci,
kujerar ya shiga bugawa a hankali ta bude ido da sauri ya koma baya yace "Amm tashi
kiyi sllh" gyara xaman ta tayi tana masa wani kallo tace "You kept me waiting" yace
"Sorry plss" mikewa tayi ya nuna mata daki yace "Akwai toilet a ciki" bata ce komai
ba ta shiga bedroom din, ba a dau lokaci ba ta fito yace "me yasa baki ci abincin
fa?" Girgixa kai tayi tace "Abincin gidanmu kawai nake ci" xaro ido yayi yana
kallonta, sosai ta basa dariya sai dai ya dake bai yi ba, kallon jikinta tayi tace
"But..." Sai kuma tayi shiru, yace "But what?" A hankali tace "Ba kayan nan ne
jikina ba" murmushi yayi yace "Yea, nurses ne suka canxa maki, you have being here
for three dayz," kan ta ce komai ya mike da sauri ya dauko hijab dinta dake daki ya
mika mata, karba tayi ya shimfida mata darduma tace "Idan na gama xa mu wuce koh?"
Kai ya gyada mata, ta hau darduman ta tada sllh, kallonta kawai yake har ta idar,
ta jima xaune kan darduman kafin ta mike ta dauke tana kallonsa tace "Na gama"
mikewa yayi ya mika mata makullin motarsa yace "Go out, look for parking space and
wait for me there" karba tayi ta fita, bayan kusan minti biyar ya bi bayanta, tsaye
ya ganta a gun ya karasa ya karba makullin sannan ya nufi gun motarsa tana biye da
shi, front seat ta bude ta shiga bayan ya tada motar, cikin minti sha biyar suka
isa gidan junaid, kallonta yayi xai yi magana tace "Call him fast plss" buda ido
yayi yace "No, we are going in" hade rai tayi tace "No ni baxan shiga ba," kallonta
ya tsaya yi yace "Why?" Tace "I just can't, pls ni dai ka taimaka ka ban kudin
transport in fita in nemi park idan naje gida in'sha Allah I am sending you back ur
money, give me ur account number" xaro ido tayi tace "Ohh My phone??" Lokaci daya
ya ji ransa ya baci, ya tsura mata ido yana kallo, how can she be this rude, who is
she da xata dinga fadin kudi haka, cire glass din idonsa yayi yace "Amma hakan bai
dace da ke ba Zahrah...." Wani kallo ta watsa masa tace "I just want to be home"
bude motar yayi ya fice ya bar ta, bin sa tayi da kallo can ta bude motar ta fita
ta bi bayansa, a hankali ya murda kofar parlon ya shiga, kwance ya ga junaid kan
doguwar kujera idonsa lumshe, ya juya ya kalleta ya ga ita ma leko sa take,
karasawa yayi parlon ta bi bayansa, dukawa yayi kusa da shi yana kallonsa, lokaci
daya ya bude idonsa da ya kada yana kallonsa, El-ameen yace "Sleeping?" Bai jira
cewarsa ba ya dafa kansa ya ji xafi, mikewa xaune junaid yayi ya rike kansa cikin
sanyin murya yace "I regret everything frnd, you told me this from the very
beginning, I..." El-ameen yace "Don't say that man, One never knows where his or
her reward lies...." Girgixa kai junaid yayi xuciyarsa na bugawa yace "Allah am
regretting" Zahrah da ke tsaye daga bakin kofa ta karaso cikin parlon kamar me
tausayin kasa, kallonta El-ameen yayi don yasan junaid bai san tare suke ba,
durkusawa tayi d'an nesa da su tana kallon Junaid, cikin sanyayyan muryarta tace
"I..i am sorry!" Dago kai yayi da sauri yana kallonta, ta sunkuyar dai kai tace
"Kayi hakuri, but you started it 1st" wani kallo ya jefa mata, ta turo baki ta mike
tana kallon El-ameen tace "Is that all?" Murmushi El-ameen yayi yace "toh bai ji
abinda kika ce ba" Kallon junaid tayi tace "I said am sorry" da kamar baxai ce
komai ba, sai kuma ya mike yace "Sorry for ur self" daga haka ya nufi stairs, xaro
ido tayi ta bi sa da kallo har ya haura sama, ta kalli El-ameen tace "You see! He's
just rude" murmushi El-ameen yayi yace "And you too!" Tabe baki tayi tace "Dan
Allah ka kai ni park xan gane hanya" kamar xata yi kuka ta kare maganar, El-ameen
yace "Ohk, xauna ina xuwa" sama ya tafi, ta dinga bin parlon da kallo, babban
hotonsa dake manne parlon yana sanye da uniform hannunsa rike da hula ta tsura ma
ido, can ta karasa gun hoton tana kallo kamar me naxari, Tsaye El-ameen ya same
junaid a daki yace "Look junaid Kaga dai ta baka hakuri, plss ka sa lokacin da xa
ka kaita gida I will escort you" girgixa kai yayi yace "Ni babu inda xan je" hade
rai El-ameen yayi yace "Stop this Malam, it's ur responsibility naga...." Xaunawa
junaid yayi yace "Leave me plss Ahmad, am going no where, ka bar ni in fara tunanin
yanda xan gyara duk abinda na bata a kan yarinyar nan, you can take her home frnd
duk daya ne" tausayinsa El-ameen ya ji, bai kuma cewa komai ba ya juya ya fita,
tsaye ya ganta bakin kofa ta wani hade rai, El-ameen bai kalleta ba ya fita ta bi
bayansa, suna tafiya tace "baxai kai ni gidan ba koh?" El-ameen yace "Yess" tsaki
tayi tace "Da na sani baxan xo basa hakurin bama" El-ameen bai tanka ta ba ya shiga
mota ita ma ta shiga, sai da suka kama hanya sannan tace "Toh ina xa mu yanxu" bai
kulata ba har ya iso gidansa, parking yayi ya fita ita ma ta fito a fusace tace
"What's this please" da kamar baxai ce komai ba sai kuma ya kalleta yace "sai na
shirya xan tafi dake ai koh? I have to fuel my car and put things in order, so dole
sai na xo gida" tace "Ohk" cikin gidan ya nufa ta bi sa, Hafsat na kitchen jin
shigowarsu parlor ta fito, Sannu da xuwa tayi masa ya amsa ya tafi sama, ta karasa
kusa da Zahrah tana murmushi tace "Welcome Jewel" kallonta kawai Zahrah take irin
kallon mamakin nan da yayi kama da na rainin hankali, still Hafsat tayi tana
kallonta, El-ameen ya sauko yace "Hey, Meet my wife Hafsat!" Murmushi Zahrah tayi
tace "Ohh sorry, it's nyc meeting you sis Hafsat!" Kasa cewa komai Hafsat tayi El-
ameen yayi murmushi yace mata xa muyi waya anjima, daga haka ya fita Zahrah tace ma
Hafsat sai anjima ta fita ita ma. Sai da suka dau hanya tace "Why was she staring
at me that way?" Da kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Coz you look new to her,
and perhaps rude" xaro ido tayi tace "Did she know me before?" Gyada mata kai yayi
yace "Yeah" tabe baki tayi ta maida kanta jikin kujera tace "I've never come across
a being like her all my life" murmushi yayi ya kalli agogon hannunsa yaga daya da
wani abu, yace "Kika ce bauchi koh?" Kai ta gyada masa yace "Where in bauchi?" Ta
kada kai tace "Idan mun je xan gane hanya" bai kuma cewa komai ba ya dau wayarsa
yayi dialing number Dad dinsa yana dagawa yace masa xai d'an je Kano wani aiki ya
dawo, suna gama waya ya kira Ummi ma ya gaya mata haka, ajiye wayar yayi ya maida
hankalinsa kan driving din da yake, ba su yi nisa da fara tafiya ba tace "Am
Hungry!" Ba tare da ya kalleta ba yace "Ke da baki cin abinci idan ba na gidan ku
ba" tace "Ohh yes, soft drink kawai nake so yanxu" murmushi yayi yace "Toh shi daga
gidan ku aka yo shi kenan" bata kuma ce masa komai ba, yayi parking ya fita wani
shopping mall ya siyo mata drink da snack, karba tayi tace "Thank you" karfe hudu
saura suka shigo Kano,
ya kalleta yace "Where is this?" Bude hannu tayi alamar bata sani ba, yace "Kano!"
Ana kiraye kirayen isha suka shigo bauchi, yace "kin san ina ne nan?" Gyada masa
kai tayi yace "Toh mun yi sauri ko ba mu yi ba?" Hannu ta buda masa alamar bata
sani ba, yace "Uhm to wani anguwa ku ke?" Tace "Kawai ka dinga tafiya xan dinga
nuna maka" yace "Ohk"

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

73.....

A bangaren Junaid kuwa suna barin gidan yayi kwanciyarsa, duk ya rasa me ke masa
dadi, har magrib yana daki ga wani xaxxabi da yake ji, sllh yayi ya dau makullin
motarsa ya fita, gida ya nufa duk jikinsa a sanyaye, he regret ever meeting her, he
regret helping her, he regret all that have happened, parking yayi kofar gidan ya
kasa fitowa, ya hade kansa da steering, ya kusa minti sha biyar kafin ya fito jiki
ba kwari ya shiga compound din, tafiya yake kamar bai son yi don bai ma san me xai
fara ce ma Mumynsa ba, bai san ta inda xai fara ba, why did all this happen to him?
Shi kuma irin tasa kaddarar kenan, shafa kansa yayi ranan da ya fara ganin Zahrah
ya fado masa, murmushin takaici yayi, yayi saurin kauda tunanin, ido hudu yayi da
Hadiza da ke tsaye sakale da jakarta alamar tafiya xata yi ga nikab a hannunta,
Umma da Hajiya ma na tsaye balcony din, suna hangosa Umma tayi mata alamar da ta
shiga parlor, da sauri ta shiga ta kullo kofa, girgixa Kai yayi nufi balcony din,
Umma da Hajiya aka kafa masa ido da mamaki don a tunanin su gaishesu xai xo yi, ko
kallonsu bai yi ba ya bude kofar ya shige parlon, Hajiya ta xaro ido tace "Ikon
Allah Meye haka Ahmad?" Hadiza dake tsaye parlon ta xaro ido ganinsa, bai yi wata
wata ba ya fincikota ya kai mata naushi a baki, wani kara tayi Umma da Hajiya da
tuni suka shigo parlon suka shiga salati suna tambayar yana da hankali kuwa, ko
sauraransu bai yi ba ya fixgota ya fito da ita tsakar gidan, dukanta ya shiga yi
yana ball da ita kamar an aikosa, ta dinga ihu tana cewa a taimaketa, tuni 'yan
matan gidan suka fiffito, Mumy ma ta fito, su Hajjo da aka diro daxu ma aka fito,
Hajiya da ko ina na jikinta rawa yake ta dinga jan Junaid murya can kasa tana cewa
"In ma laifi tayi maka kayi hakuri Ahmad.... Ka rufa mata asiri" ko saurarenta bai
yi ba bugunta kawai yake kamar an aikosa, a fusace Hajja ta karaso ta fixgoxa ta
sauke masa mari tace "Don uwar ka Amina dama shirin tafiya gidan ka nake yanxu, ban
taba tunanin cewar da mahaukaci Muhammadu xai hada jikata ba, ita Humainahr ka
sakar min, tsabar haukan naka ya girmama har gida kake xuwa jibgan mutane yanxu"
kokarin gudu Hadiza take ya wani fixgota ya kuma sauke mata mari, Abba ne ya shigo
compound din daga masallaci, ya tsaya da mamaki yana kallon tsakar gidan, Junaid da
ban da tafasa babu abinda xuciyarsa yake ya fara waige waigen inda xai ga Humainah,
ganin bata compound din ya ja Hadiza har part din Mumy duk aka bi sa da ido ya
shiga har parlor da ita, salati Umma ta dinga yi tana cewa anya Ahmad lafiyarsa
kuwa, ku ceci 'yar mutane don Allah, fitowar Humainah kenan daga daki ya jefar mata
da Hadiza nan gabanta yana kallonta sannan ya juya ya fice daga parlon, kallon
mamaki Humainah ke mata, tuni duk aka shigo parlon, Abba kam dama part dinsa kawai
ya nufa, Hadiza da ko ina na jikinta rawa yake ta mike da sauri xata fita, Humainah
ta rikota tace "Me ya kawo ki nan?" Juyawa tayi tana waigen inda xata ga su Umma,
Hajjo tace "Ina kika santa?" Hawaye ne ya cika idonta tace "Ita ta ja min komai, ni
ban santa ba...." Hajjo tace "yo ni daxu tare muka shigo gidan nan da ita, ita ce
ma ta shigo min da kayana daga adai daita kuma tace min Ita 'yar wan Bilki ce, me
ta maki?" Kuka sosai Humainah ta fara ta durkushe gun tace "Ita ce silar komai, ita
ke xuwa gidana kullum...." Salati Hajja ta saki tace "Ita ta sa ya sake ki kenan?"
Humainah ta gyada kai hawaye na sauko mata, Hajja ta cakumo Hadiza tace "Ni dama
nasan ba yin kan jikana bane wannan, nasan baxai aikata haka a banxa ba, to ko ki
fadi wanda ke tura ki gidan ta ko in xuba maki fetur yanxu in babbakaki" juyawa
Umma tayi ta fice daga parlon Hajiya ta bi bayanta da sauri, Hajja ta kwada mata
mari tace "Baxa kiyi magana ba" Mumy da duk jikinta yayi sanyi ta karaso tace "Ki
yi hakuri Hajja ki sake ta...." Wani kallo Hajja ta watsa mata tace "Ke ja can
dalla" shaketa Hajja ta yi tace "Baxa kiyi magana ba?" Hadiza ta fashe da kuka tace
"Ni Umma ce da Hajiya suke tura ni" salati Hajja ta saki tace "Suke tura ki kije
kiyi me?" Shiru Hadiza tayi Hajja ta ja ta xuwa gun tv tana neman wayar wuta tace
"Toh xa ki ga ikon Allah idan ba ki bude baki kin ban labari ba" juyawa Humainah
tayi hawaye na bin kuncinta ta koma daki, Hadiza da tayi mugun tsorata jikinta na
rawa tana hawaye tace "Wllh tura ni suke in je in dinga xugata" Hajja ta saketa
tana tafa hannu tace "Naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, dama su suka kashe
ma jikata aure, to su ma na su na rawa yanxu, ina Muhammadu" daga haka ta fice daga
parlon kamar xata tashi, jigum Mumy tayi tana kallon Hadiza dake ta waige waige
kamar munafuka, can kuma ta fice da gudu daga parlon. Tafiya kawai El-ameen ke yi a
hankali, haka kawai gabansa ke faduwa ganin anguwar da ta nuna masa wai nan xa su
bi, tafiya me nisa suka yi tace "Here!" Juyawa yayi da sauri yana kallonta yace
"Where?" Nuna masa babban entrance din tayi tana bin ko ina da kallo ganin canji da
dama tace "there!" Kasa daina kallonta yayi tace "Just horn, sai ka sauke glass xan
masu magana" girgixa kai yayi yace "Wai gidan sarautan nan?" Kallonsa ta tsaya yi
kafin tace "Eh gidanmu ne!" Dauke kai yayi can ya juyo yace "Kina nufin ur father
is a king?" Bude motar ta shiga kokarin yi tace "Yeah my father is a king" danna
horn yayi kamar yanda tace har lokacin idonsa na kanta, ita ko sai kalle kalle take
fuskarta dauke da mamaki ganin changes da dama, wasu dogarai ne suka fito suna
kallon motar, karasowa suka yi ta sauke glass tana kallonsu, ganin bata gane ko
daya daga cikinsu ba ta bude motar ta fito tace "Ku bude mana hanya" daya daga
cikinsu yace "Daga ina?" Fitowa El-ameen yayi yace "Baki daga katsina" bude masu
hanyar aka yi, ya koma mota ita ma haka, ya ja motar ya shiga ciki, tafiya mai
tsayi suka yi kafin su kai wani gate, kallon El-ameen tayi kamar xata yi magana sai
kuma ta fasa, wasu guards suka karaso gun motar, sauke glass tayi daya daga cikinsu
yace "Daga ina?" kallonsa kawai take don shi ma bata san sa ba, toh yaushe aka
canxa guards din bakin gate kuma, a takaice tace "Bude mana gate" El-ameen yace
"Sorry, baki daga katsina, mai martaba na sane da xuwan mu" komawa yayi aka bude
gate din ya ja motar xuwa babban haraban palace din, juyowa tayi da sauri ta
kallesa tace "Everywhere looks strange" kashe motar yayi yace "How strange" a
hankali tace "Naga changes da yawa ne"

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

74.....

Bude motar tayi ta sauka, shi ma ya sauko, har ta nufi kofar shiga fada sai kuma ta
juyo tana kallonsa tace "Ni xan bi ta baya, may be Abbana na tare da baki, you
follow there" girgixa kai yayi yace "No i will wait out here" tabe baki tayi ta
juya ta dau wata hanyar daban ya bi ta da ido har ta bace masa, ajiyar xuciya ya
sauke ya koma can inda wasu bishiya ke a jere ya ja daya daga fararen kujerun dake
gun ya xauna, wayarsa ya ciro ya shiga kiran layin Junaid, bugu uku ya daga, El-
ameen yace "Amm muna bauchi Man" Junaid dake xaune laptop gabansa yace "Ohk, it's
good" Shiru El-ameen yayi kafin yace "Guess what frnd?" ajiye laptop din yyi a
gefensa yace "Not in the mood" Murmushi El-ameen yayi yace "Ohk Gudnyt" katse wayar
junaid ya jefar da wayar hannunsa ya mike ya fice daga dakin. A hankali Zahrah ta
tura kofar ta shiga babban parlon da nan ne masaukin manyan baki a fadan, bbu kowa
parlon, ta dinga bin parlon da kallo ganin shi ma ya canxa mata, hanyar da xai sada
ta da bangaren Ummanta ta nufa da sauri, lokaci daya taji gabanta na faduwa,
jakadiyar Umma ce mutum ta farko da ta fara haduwa da a hanya, wara manyan idonta
tayi ta karasa da sauri tace "Baaba na dawo, ina ummana, ina su Ummi.....!" Wani
kara jakadiyar tayi a gigice ta saki kayan hannunta ta juya da gudu ta bar gun tana
salati, still Zahrah tayi ta bi ta da kallon mamaki, kan kace me sai ga ma'aikatan
fadan sun bubbullo jin ihun jakadiya, sai dai duk wanda yayi tozali da ita sai ya
bar gun a guje, duk ko ina ya hargitse, ita dai tana tsaye kamar warce aka dasa a
gun cike da mamaki, a hankali ta shiga bin jikinta da kallo ko wani abu ne jikin
nata, bata gama recover ba sai da yayanta ya shigo parlon taga yana mata wani
kallo, da sauri ta nufesa ta ga ya juya ya bar gun, sosai jikinta yayi sanyi ta ji
kafafuwanta sun kasa daukarta, Umma ce ta fito da stepmum dinta, sai dai ga mugun
mamakinta sai gani tayi ita duk sun yi still a position dinsu suna kallonta ko
kiftawa babu, Ummi ce ta shigo ita ma suna ido hudu ta fasa wani kara a rikice ta
juya da gudu ta bar gun, juyawa Zahrah tayi da sauri hawaye cike idonta ta fita da
gudu, a hankali Umma ta sulale gun ta fadi kasa a sume, rikicewa jakadiyar ta da
sauran ma'aikatan dake gun suka yi suka yo kanta, Zahrah na fita dama inda ta hango
El-ameen ta nufa tana isa gunsa ta xube gun ta fashe da kuka sosai tace "Why is
everybody running away from me, mene a jikina da suke gudu plss tell me" shiru yayi
yana kallonta, sai ya ji tausayinta, a hankali yace "Bbu abinda ke jikin ki, they
are just surprise ne...." Girgixa kai tayi cikin kuka tace "Noo, what are they
surprise at, do I look new? Tell me plss, dukkansu guduna suke yi" lumshe ido yayi
yace "Kila basu yi xaton ganin ki yanxu bane" buda ido tayi tace "Why is that?"
Takun da suka ji yasa su juyawa gaba daya, Mai martaba ne tafe da dogaransa a baya,
mikewa tayi da sauri ta nufesa da sauri tace "Abba!" Kallonta kawae yake, ta fashe
da kuka ta tafi da gudu ta rungumesa cikin kuka tace "Abba ni ce pa Fatima" daura
fuskarsa yayi a kanta cikin sanyin murya yace "Fatima!" Rungumesa tayi sosai,
hawaye na sakko mata tace "Abba kila su Umma basu gane ni bane koh?" Kasa ce mata
komai yayi, El-ameen dai sai kallonsa yake yaji tausayinsa ba kadan ba, dago kai
sarkin yayi yana kallonsa, mikewa yayi ya karasa inda suke ya sunkuyar da kai yace
"Barka dai mai martaba, ga Zahrah na maido gida, Allah ya kiyaye gaba" kallonsa
kawai sarkin yake, El-ameen yace "Na bar ku lafiya" juyawa Zahrah tayi tana
kallonsa, Sarki ya taka ya isa har gabansa, hannunsa ya kama ya nufi fada da shi,
tsaye duk occupant din masauratan suke ko wanne a tsorace, Mai martaba da har
lokacin bai sake El-ameen ba ya nufi babban parlonsa da shi, Zahrah dai na biye da
shi a baya kamar xata shige jikinsa ganin wani kallo da ake mata duk inda suka
wuce, xaunawa sarki yayi ya nuna ma El-ameen kujera ya xauna, ya kusa minti biyar
bai ce komai ba, Zahrah dake xaune kusa da Abban ta sai jiran jin me xai ce take,
hawaye ne ya sakko idonta tunawa da tayi da irin kallon da ake mata, ta daura kanta
kan kafar Abban nata muryarta na rawa tace "Abba na canxa ne wai, me yasa ake
guduna?" Da kyar me martaba ya saita kansa, yana rike da hannunta yace "Baki canja
ba mamata" kallon El-ameen yayi yace "Bawan Allah, a ina ka ga Fatima?" Shiru El-
ameen yayi kamar baxae ce komai ba, sarki dai sai kallonsa yake, sunkuyar da kai
yayi yace "Bani na ganta ba ranka ya dade...." Sarki yace "Waye shi?" Dago kai yayi
yace "Aminina ne, shi ne silar komai" Sarki yace "Kana da masaniyar inda ya ganta,
kuma yana ina?" El-ameen yace "Ehh nasan inda ya ganta, yana katsina yanxu haka,!"
Sarki yace "Ina ya ganta" kallonta El-ameen yayi yaga yanda ta kafa masa ido tana
jiran jin me xai ce, lumshe ido yayi ya bude ya kalli Sarkin yace "Tana da matsala
ne a lokacin" sarkin yace "Wani irin matsala?" El-ameen yace "Ehh toh, A lokacin ta
samu matsalar kwakwalwa" mikewa tayi tana kallon El-ameen, sarkin ma kallonsa yake
ko kiftawa bai yi, da kyar yace "Matsalar kwakwalwa?" El-ameen ya gyada kai yace
"ehh, Ban mancewa dawowarsa Egypt kenan ya taso xae xo guna da yamma ya ganta gefen
titi a halin Hauka....." Labarin yanda Junaid ya ganta, da irin tausayinta da yaji
El-ameen ya shiga ba sarkin, bai boye masa komai ba har lokacin da junaid din ya
nemi shi ma ya taimaka ya nuna shi bbu ruwansa, da yanda dai ya amince daga karshe,
kuma bbu abinda ya rage tun daga hidimar da Junaid yayi da ita na Magani abinci
sutura, nemo me kula da ita da yayi, har da irin matsalar da ya shiga gun iyayensa
ta dalilin ta, da challenges din rayuwa da ya dinga fuskanta, duk da haka kuma bai
taba gujenta ba, bai kuma fasa yi mata duk abubuwan da ya dace ba, har gidansu da
ya kaita da niyar aurenta lokacin da iyayensa suka takurasa yayi aure, da dai yanda
abubuwa suka gudana a lokacin, hatsarin da suka yi da ya maido mata da hankali sai
dai kuma tayi loosing memory, da aurensa da Humainah da sakinta da yayi kan
Zahrahn, kai bbu abinda ya boye ma sarkin har xuwansu bauchi sai dai bai fadi
tijaran da Zaharar tayi masa ba, rike kai sarkin yayi don tuni idonsa ya canxa
launi, Zahrah kam hawaye ne kawai ke saukowa idonta jikinta yayi mugun sanyi, tuni
ta kasa ci gaba da tsayuwa ta durkushe wajen ta fashe da kuka sosai, da kyar
sarkin ya iya dago kansa daga karshe, ya goge idonsa da Handkerchief din hannunsa
cike da karfin hali yace "Shekara daya da watanni biyar kenan rabon mu da fatima,
tun da suka yi hatsari a hanyar Kano, and....." Kasa ci gaba yayi ya mike yace
"Gobe da safe xa mu tafi katsinan" daga haka ya dau hanyar da xai sada sa da
Bedroom dinsa, kallon El-ameen kawae take, can ta mike a hankali ta isa gabansa ta
durkusa wasu sabbin hawayen na sauko mata cikin sanyin murya tace "Will he ever
forgive me?" Kallonta El-ameen yake, yayi murmushi bai ce komai ba, ta fashe da
kuka sosai tace "Don Allah ka gaya min xae iya yafe min....." Saukowa El-ameen yayi
yace "He will in'sha Allah" tana share hawayen da ya ki tsaya mata tace "toh Meye
sunansa?" Yana kallon kwayar idonta yace *Captain Ahmad Junaid* a hankali tace
"Ahmad Junaid" gyada mata kai yayi yana murmushi ta sauke idonta kasa.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

75.....

Washegari da ya kasance litinin misalin karfe takwas na safe Zahrah ta fito daga
part din mai martaba bayan ya bata umarnin da ta tafi ta gaida Ummanta da stepmum
dinta kilishi, bata yarda ta kwana ko ina ba sai gun sa tunda shi kadai ne bai
gujeta ba, kuma ga bakin da suka dinga tururuwan xuwa ganinta tun a daren jiyan
hakan yasa tayi xamanta gun Abbanta, a nan part din nasa tayi shiryawarta ta saka
kayan da jakadiyar Umma ta kawo mata da safen, bangaren Ummanta ta nufa fuskarta
rufe da hular alkyabbar jikinta don bata son kallon da ake mata, xuciyarta fal
tunanin Junaid ta dinga tafiya a hankali, ta rasa dalilin da ya tsaya mata a rai
haka, har mafarkinsa sae da tayi daren jiya, gashi ko ganesa ta tabbatar baxa tayi
a hanya ba da xa su hadu, bata damu da mutanen da ta dinga wucewa ba wasu na
gaisheta wasu na mata sannu da xuwa har ta iso bangaren Umma, xaune ta sameta
parlor ga baki da dama xaxxaune parlon, da ganinta kasan har lokacin bata yi
recover daga shock din jiya ba, a sanyaye Zahrah ta karasa har tsakar parlon ta
duka ta gaida mutanen dake ta kallonta ko wannensu ya amsa mata cike da fara'a,
karasawa tayi gaban Ummanta ita ma ta gaisheta, amsa mata tayi cikin sanyin murya
tana kallonta, kasa ci gaba da tsayawa gun Zahrah tayi, ganin Umma taki sakewa da
ita, ta mike kawai ta fice hawaye cike idonta, bangaren Kilishi ta nufa nan ma baki
ta samu fal a parlon, ba laifi kilishi ta ja ta jikinta hawaye na sakko mata tace
"Sannu Zahrah, Allah ubangiji ya kara mana tsawon rai mai amfani...." Rungumeta
Zahrah tayi tana kuka, nan ta dinga lallashinta tace "Gode ma Allah xatayi da
bawan Allahn da ta dalilin sa ta dawo gida yanxu" jikinta ya kuma yin sanyi sosai
ta ji banda taga junaid bbu abinda ke damunta yanxu, mikewa tayi tana share hawayen
ta, Ummi ta gani tsaye ita ma tana hawayen, da sauri ummin ta karaso ta rungumeta
tace "I missed you sweet sis...." Zahrah bata iya cewa komai ba sae hawaye, janye
jikinta tayi ta fita daga parlon, a hanya ta hadu da yayanta tana ganinsa xata
canxa hanya ya janyota ya rungumeta, rufe fuskarta tayi a kirjinsa, a sanyaye yace
"Welcome back Lil sis, ba gudun ki muke ba, it's just....." Girgixa kai yayi lokaci
daya idonsa ya kada yace "We missed you Zahrah" bata iya ta ce komai ba sai kai da
ta gyada masa kawai, yace "Baki je gun bakon da ku ka xo tare ba" goge fuskarta
tayi tace "yanxu xan je" saketa yayi yace "Yea ki tafi yanxu, nima daga can nake"
gyada masa kai tayi ta nufi bangaren saukan baki inda El-ameen yake, Xaune ta gansa
parlor yana waya, ta nemi gefe ta xauna sai kallonsa take, yana gama wayar tayi
saurin dauke idonta daga kansa, ya d'an bude ido yace "Good morning princess" d'an
murmushi tayi tace "Good morning" yana murmushin shi ma yace "How you!" Ba tare da
ta kallesa ba tace "Am good," yace 'Happy to be home ryt?" Lumshe ido tayi ta bude
ta gyada masa kai, yace "My wife said I shud send her regards" kallonsa tayi tana
murmushi tace "Am grateful" yace "In the next 1hr xa mu kama hanyar katsina" da
sauri tace "Amma ai da ni xa a je koh?" Yace "No I don't think so...." Bata fuska
tayi tace "Nima nace xan je" dariya yayi yace "Ohk ohk!" Shiru tayi sai kuma tace
"Nuna min hoton matar ka" da mamaki ya kalleta yace "Really" bai jira cewarta ba ya
dauko wayarsa ya bude ya shiga gallery ya nemo hoton Hafsat ya mika mata, mikewa
tayi ta karasa kusa da shi ta karbi wayar ta dawo ta xauna, kallonta kawai take
sannan ta kallesa tace "She's... She's beautiful!" Murmushi yayi yace "Ohh tnxx"
kallon hotunan ta shiga yi, can ta mike da sauri tace "Ohh this is me" mikewa yayi
ya koma kusa da ita yana kallon wayar ya ga hoto ne da yayi masu ita da Hafsat,
gyada mata kai yayi yace "Yea, ke da Hafsat" a sanyaye ta ci gaba da kallon hotunan
taga duk hotunanta ya fi yawa a wayar, ajiye wayar tayi ta koma ta xauna ta lumshe
ido, yana kallonta yace "What?" Bude ido tayi ta girgixa masa kai cikin sanyin
murya tace "Have you taken breakfast?" Gyada mata kai yayi yace "Yea" bata kuma
cewa komai ba can kuma tace "Ban san sunanka ba!" Wara ido yayi yace "I am El-ameen
Ahmad..." Gyada kai tayi tace "You have the name of my dad" murmushi yayi yana
kallonta, ta mike tace "Xan je gun Abba yanxu" bin ta yayi da kallo har ta fita.
Karfe goma saura sarki da tawagarsa suka shirya tsaf domin tafiya kt, shiga ce yayi
na alfarma irin ta sarauta, da farko bai amince Zahrah ta bi su ba sbda b'akin dake
ta xuwa masarautan dominta amma yayanta na sa baki sarki ya amince su je tare, don
har da shi xa'a, rungume yayan nata tayi tace "Thanks bro" Ummanta ta tafi tayi ma
sallama sai a sannan Umma ta rungume 'yar tata ta fashe da kuka, jikin Zahrah yayi
sanyi ita ma hawayen ya shiga sakko mata da kyar ta fita daga dakin ta je yi ma
step mum dinta sallama, Ummi ta gani ita ma ta shirya tsaf, Ummi na ganinta tace
"Zahrah tare xa mu je fah" Kilishi ta kalleta tace "Mai martaba ne yace tare xa ku"
bata fuska tayi tace "Yanxu xanje in gaya masa, Mumy bana son ta kara tafiya ita
kadai ne...." Kilishi tayi murmushi tace "Toh Allah yasa ya amince" daga haka Ummi
ta kama hannun 'yar uwar tata suka fita, basu sha wahalan shawo kan Abbansu ba ya
amince xa ta bi su, motoci biyar ne xa a tafi katsinan da, mai martaba kuma flight
xai bi da Zahrah da El-ameen da Ummi, Abdul kuma xae bi tawagar Abbansa ta mota sai
su hade a masarautan kano daga can kuma su dau hanyar katsina.
Karfe daya motocin tawagar sarki El-ameen suka iso masarautan Kano, ko minti
talatin basu kara a Kano ba suka dau hanyar katsina, Zahrah da Ummi suka shiga mota
daya da Mahaifinsu, El-ameen bai yarda ya shiga motar sarki da ya sa masa takwara
ba ya hau motar gaba, uku da wani abu suka shiga garin kt, duk da El-ameen ya san
ba lallai junaid na gidansu ba, can ya sa suka nufa gaba daya, hudu da minti goma
suka iso kofar gidansu Junaid, El-ameen ne ya fara fitowa, sannan dogarawan sarki,
kafin sarki ma ya fito tare da aminansa, Sarki na kallon El-ameen yace "Masallaci
mafi kusa, xa muyi la'asar!" Masallacin kofar gidan ya shiga da su bayan sun daura
alwala, su Zahrah dai na mota a xaune, hudu da minti ashirin duk suka fiffito daga
mosque din, Sarki yace "Shiga kayi mana sallama da masu gidan, El-ameen ya shiga
compound din, bbu kowa tsakar gidan sai Khadija dake xaune balcony din Mumy, ya
karasa har inda take, ta gaishesa da fara'ar yake, amsa kafin yace "junaid fa?" Ta
girgixa kai tace "yana can gidansa!" Yace "Abba fah?" Ta kalli bangaren Abba tace
"Yana ciki, amma yana da baki" El-ameen yace "Su waye?" Tace "Hajja na ciki, kawu
Abbakar ma na ciki sai Abokansa biyu" ya d'an bude ido yace "Meeting din me ake"
shiru tayi bata ce komai ba, a hankali yace "Junaid koh?" Gyada masa kai tayi, yace
"Su Hajiya fah?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Mumy fa?" Kallon kofar parlon
tayi tace "Tana ciki" yace "Ohk pls ki gaya min taron me ake a parlon" ta tabe baki
tace "Humainah ce ta gaya ma Hajja abinda ya sa ya saketa daxu da safe" El-ameen ya
d'an bude ido yace "Ta basu labarin mahaukaciya kenan" gyada masa kai Khadija tayi,
El-ameen yace "Toh me Abba yace?" Hawaye ya cika idonta taki cewa komai, ya sauke
ajiyar xuciya yace "Toh bai xo ba junaid din" hawaye na sakko mata tace "Tun daxu
ake kiransa ya ki ya xo" El-ameen bai kuma cewa komai ba ya nufi parlon Mumy, xaune
ya ganta da ganinta ba karamin kuka ta ci ba, kasa karasawa yayi cikin parlon ya
juya ya fita kawai, kofar gida ya koma ya ba sarki hakuri sannan ya ce su shigo,
Fitowa Zahrah tayi da 'yar uwarta suna daga gefen mahaifinsu suka shiga gidan, har
parlon Abba yayi musu iso, tuni Khadija ta mike tana kallon ikon Allah ganin
jama'ar dake shigowa gidan, El-ameen ne ya fara shiga parlon da sallama ya gaida
Abba da ladabi, Hajja tace "Alhmdllh kun ga babban munafukin abokin nasa nan, ae
wllh sai Allah ya mana hisabi da ku...." El-ameen bai ko kalleta ba yana kallon
Abba yace "Abba baki kayi daga masarautan Bauchi, mai martaba sarkin bauchi ne da
kansa" Abba da ya wani xaro ido tun kan yace komai Sarki El-ameen ya shigo parlon
da sallama Aminansa biyu da Zahrah da Ummi ma suka shigo sai Abdul sauran dogarawan
sarki suka yi cirko cirko bakin kofa, da farko tsaye sarkin yayi ganin yanda ake
kallonsa da mamaki barin Abba ya sa shi samun kujera ya xauna, parking Junaid yayi
kofar gida ya tsura ma manyan motocin dake Parke a jere ido, mamaki ne ya cika sa
sosai lokaci daya yaji gabansa ya fadi ya bude motar ya fita da sauri ya shiga
cikin gidan, uniform ne jikinsa sai hula dake kansa, ko lura da dogarawan da suka
cika compound din bai yi ba, shi dai burinsa ya ga Mumynsa, hankalinsa bai gama
tashi ba sai da ya ga jerin takalma dake kofar parlon Abba, da part din Mumy xa shi
kawai ya fasa ya nufi parlon Abba da sauri ya shiga.

*Haske writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

76......

Tsaye yayi bakin kofa yana bin kowa na parlon da kallo irin na mamaki, ido hudu
suka yi da Zahrah dake kallonsa ko kiftawa babu, hade rai yayi ya juya xai fita El-
ameen dake tsaye har lokacin ya kama hannunsa yana kallon Sarki da shi kansa kallon
Junaid yake yace "Ahmad junaid kenan, kuma dominsa ku ka taho katsina." Mikewa
Hajja tayi da sauri tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Me yayi? Yaron da ko
hanyar bauchi na san ko xa a kashe sa bai sani ba, ashe kai mugu ne Aminu ba mu
sani ba..... Meye hadin jikana da masarautar Bauchi can kace ko ina?" Abokin Abba
ne yace "A'a Hajja ba tashin hankali bane, ae ba mu jira mun ji me ke tafe da su
ba, kuma ko gaisawa fa ba a yi ba, sannan ance sarki ne nan gabanmu ba fa waxiri
ba....." Wani kallo ta watsa masa A fusace tace "Yo ni ina ruwana da sarautarsa, ka
gan ni nan ban tsoron kowa sai Allah, kuma bbu irin fitintinun da ban gani ba a
duniya, ya fadi me jikana yayi masa in ji, Ahmad da ko titin da xai kai sa Bauchi
bai sani ba" Abba dai kasa cewa komai yayi, don shima jiran jin me only son din
nasa yayi kawai yake, Sarki kam banda murmushi babu abinda yake sai dai ba lallai
ka gane murmushin ma yake ba sbda turban din kansa, Aminin sa da shi ma ya samu gu
ya xauna gefensa cikin kaushin murya yace "Mind you all, ba fa karamin mutum bane
xaune a gaban ku, sannan mu alkhairi ne ya kawo mu in'sha Allah, Mai martaba sarkin
bauchi kenan da kansa don haka a samu nutsuwa don Allah....." Hajja tace "Ina xa mu
samu nutsuwa ba ku fadi me ke tafe da ku ba, ni dai nasan Ahmad ko cinnaka baxae
iya kashe wa ba...." Sarki ya kalli Junaid yace "Toh karaso ka xauna Ahmad" tsaye
junaid yayi kamar baxai karasa parlon ba gashi gabansa sae faduwa yake ya rasa
dalili, sarkin bauchi kuma, is she related to the royal family? Abba ne yace "Ka
kasa tahowa ke nan?" Da kyar ya d'aga kafa ya karaso ya xauna nan tsakar parlon
Hajja ta xauna gefensa tace "Kwantar da hankalin ka Amadi bbu wanda ya isa ya cutar
da kai matukar ina raye a doron kasa, su fadi me kayi in ji" tana magana ne tana
matsar kwalla, Abba ya kalli El-ameen yace "Tafi ka kira Amina" juyawa yayi ya fita
ba a dau lokaci ba ya dawo parlon tare da Mumy, k'in xama Mumy tayi ta kalli junaid
ta kalli Sarki sannan Abba, Sarki ya kalli Zahrah da ke xaune daga kasa kusa da
shi, sannan ya kalli Junaid yace "Kasan yarinyar nan?" Junaid ya daga kai yana
kallon kwayar idonta, Sunkuyar da kai tayi da sauri ta dalilin faduwa da gabanta
yayi, sai da sarkin ya kuma nanata tambayar sannan ya gyada kai kawai, Hajja da ko
k'adan bata gane Zahrah ba ta yo waje da ido tace "A ina ka santa don ubanka?"
Kallonsa kawai sarkin ke yi, a ransa kuwa tunani yake anya shi din El-ameen ya basa
labari jiya, da irin fadin ran nan ya taimaki 'yar sa kenan, A fili kuwa cewa yayi
"Toh a ina ka santa Ahmad?" Kallon El-ameen Junaid yayi yace "Shi ma ai ya santa,
ya ma fi ni saninta" Hajja ta mike tace "Atoh a hankali gaskiya dai xata bayyana
don ni nasan jikana bai santa ba sai dai abokinsa" Aminin sarki ne yace "Ahmad kake
koh? Toh kasani ba karamin mutum bane nan gaban ka, am repeating this, you go
straight to the point and answer his questions right away, takanas ya taso tun daga
bauchi domin ka don haka kar ka maida mu kananan mutane" Mumy ji tayi ta kasa
tsayuwar ma, da kyar ta samu waje ta xauna tana kallon ikon Allah, Junaid kam dama
ba direction dinsu yake kallo ba, Sarki ya nisa yace "Ahmad, ni ne Mahaifin Zahrah,
ka kuma min abinda har karshen rayuwata baxan taba mancewa da kai ba, ka dawo min
da farin cikina ka fitar da ni kunci lokaci daya, ashe har yanxu akwai sauran
mutanen kirki a duniya? ashe akwai masu xuciya irin taka a duniya, kaf rayuwata ban
taba jin na kaunaci mutum kamar yanda naji kaunar ka daga jiya ba, da kai na kwana
a raina jiya Ahmad....." Hajja sai wuwwulla ido take tana jiran jin me yayi ma
sarkin, Sarki yace "Xan so ka ban labarin yanda ka ga Zahrah har ixuwa jiya Ahmad"
k'in dagowa Junaid yayi da farko can ya dago suka hada ido da sarkin sai yaga yayi
masa kwarjini, da kyar ya iya cewa "Nayi xaton El-ameen ya fadi maku ranka shi
dade" Sarki yayi murmushi yace "Ehh, amma xan so sake jin labarin daga bakin ka"
Junaid ya shafa kansa ya kalli Abba dake kallonsa, sannan ya dauke kai, xaunawa
Hajja tayi tana jiran jin labari ita ma, Kamar baxae ce komai ba sai kuma cikin
sanyin murya yace "It all happened on a faithful tuesday evening....." Lumshe ido
yayi ya bude ya shiga ga bada labarin tun daga ranan da ya fara ganin Zahrah a
gefen titi, bbu abinda ya canxa daga wanda El-ameen ya fadi ma sarkin jiya, yanda
ya kama mata gida da farko daga karshe kuma suka koma gidan El-ameen, irin hidima
da wahalhalun da suka yi shi da El-ameen a kanta, da yanda suka boye ma iyayensu,
mama jummai da suka dauko.... kai bbu abinda ya boye har gida da ya kawota da nufin
aurenta da yanda iyayensa suka gane ba mai hankali bace..... Bbu wanda jikinsa bai
yi sanyi ba a parlon, Hajja ta rushe da kuka tace "Ae dama nasan jikana yaron kirki
ne, Allahu Akbar, xaka aikata fiye da haka ma don k'akan ka ka gado " sunkuyar da
Kai Junaid yayi ya kasa ci gaba don dama yanda yake bada labarin kamar bai son yi,
Aminin sarki ne yayi Encouraging dinsa da ya ci gaba don sarkin kasa cewa komai
yayi banda ido da ya tsura masa, Zahrah kam banda kuka babu abinda take jikinta
yayi sanyi ba kadan ba, ita kanta Mumy hawayen ne ke sakko mata, cikin sanyin murya
junaid ya ci gaba yace "I had to take her away..... muka bar gidan and....." shiru
yayi kafin ya fadi yanda suka yi hatsari bayan barinsu gidan wanda shi ne dalilin
dawowan hankalinta sai dai kuma tayi losing memory ta mance komai, bai boye yanda
ya janye jikinsa daga lokacin bisa umarnin da iyayensa suka basa, ya fadi yanda ya
bar ta da El-ameen bai kuma bi ta kanta ba, El-ameen kuma ya kai ta gidan Course
mate dinsa tayi kusan wata biyu a can, a watannin ta biyu a gidan sau daya yace
yaje daga nan kuma bai sake komawa ba, har aka yi aurensa da Humainah, ya fadi
shawarar da El-ameen ya basa da yanda ya amince ya maidata gidansa da xama gaba
daya ya kuma sa ta a islamiyya, bai boye irin matsalolin da suka dinga fuskanta da
Humainah a kanta, ya kuma fadi dalilin sa na sakin Humainah, bai rufa komai ba kan
irin xaman da suka yi da Zahrahn bayan barin Humainah gidan har ya kai karshen
labarin da fadin dalilin dawowar memory dinta, sai da idon kowa ya kawo a parlon,
ya kusa minti biyar kansa a kasa kafin ya dago a hankali, hawaye ne cike idonsa ya
mike ya isa gun Mumy ya durkusa ya daura kansa a kafarta a sanyaye yace "Ki
gafarceni Mumy, nasan nayi disobeying din ki, na kuma boye maki abinda nayi which I
wasn't suppose to ko da kuwa baxa kiyi supporting dina ba shi yasa komai bai tafi
min dai dai ba, forgive me plss Mumy....." Hawaye kawai Mumy take bata iya ta ce
masa komai ba, ya mike ya isa gun Abbansa shi ma ya durkusa gabansa hawaye na sakko
masa yace "Ka yafe min Abba, I know I... I failed you....."Jin Abba bai ce komai ba
yasa shi mikewa a sanyaye, tashi sarki yayi ya taka har gabansa ya dafa sa sai kuma
ya rungumesa yace "They will all forgive you in'sha Allah son, sannan ina me
umartarka da ka mayar da matarka ka nemi gafararta....." Daga haka ya sake sa ya
isa gaban Abba yace "Ina neman alfarmar ku yafe ma Ahmad duk abinda ya maku a kan
Zahrah...." Murmushi Abba yayi ya mike yace "Bai min komai ba mai martaba, Allah ya
basa ladan abinda yayi, ina alfahari da kasancewarsa d'ana, yasan ba lallai in
sauraresa ba a lokacin shi yasa yayi komai gaban kansa, Allah ya biyasu gaba daya
da abokin nasa, is good thing sun riketa amana, ta kuma samu lafiya ta dalilin su,
I am proud of them....." Mikewa Mumy tayi a sanyaye xata fita Sarki yace "Toh
Hajiya bamu ji kin ce kin yafe masa ba, ina nema masa wannan alfarmar don Allah"
murmushi kawai tayi, Hajja da baki ya ki rufuwa tace "Yo wa ya sani ko bakin ciki
take masa kamar yanda matan ubansa ke masa, ni dama tun ran da Amadi ya kawo
yarinyar gidan na daura ido na kanta na ji ta kwanta min toh tunda yan gida suka ce
mahaukaciya ce basu san xance ba ina ni ina magana ace don ba ni na haifesa ba"
kallonta kawai junaid yake haka ma El-ameen dake murmushi, sarki yayi murmushi shi
ma yace "Da fatan mun kafa xumunci kenan har illah maa'sha Allah" Hajja ta mike da
sauri tace "toh ni makka xaka kai ni, shekarana uku rabona da can wllh" 'yar dariya
sarkin yayi yace "Kina da kujeru biyar wannan shekarar Idan Allah ya yarda" shewa
tayi tace "Allah yayi maka albarka...... Sai mu je tare da Humainah da kawayena
Uku" kofa junaid ya nufa xai fita daga parlon sarki ya kirasa, juyowa yayi yana
kallonsa, sarkin yace "Ina gayyatar ka masarautar mu tare da El-ameen, ur labours
will not go in vain" Shiru Junaid ya d'an yi sai kuma yayi kasa da kai yace "Sai na
dau excuse gun aiki idan Allah ya yrda" Kai kawai sarkin ya gyada masa, Satan
kallon Zahrah yayi ya juya ya fice, kamar warce aka tsikara ta mike ta bi bayansa
da sauri.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

77......

Bin bayansa Zahrah tayi, ya ki tsayawa ita ma bata ce ya tsayan ba ya nufi part din
Mumy, yana bude kofar ta ja ta tsaya tace "Amm... Ahmad Junaid!" Lokaci daya ya
juyo ya sauke idonsa kanta yace "Yess!" Wani mugun kwarjini ya mata ta kasa cewa
komai sae kallonsa take, daga kasa har sama ya kalleta sannan ya juya yayi
shigewarsa parlor, still tayi gun kamar warce ruwa ya cinye, duk wannan abun El-
ameen na tsaye balcony yana kallonsu, juyawa tayi suka hada ido da shi, hawaye ne
ya ciko mata ta sauka daga balcony din da sauri ta nufi gunsa tana kallonsa lokaci
daya hawayen idonta ya silalo tace "kaga abinda yayi min koh?" Murmushi El-ameen
yayi ya buda ido yace "Yea! Haka nan yake! but idan ya sauko xa ki ga he is the
sweetest guy you never expect.... He's still angry at you ne shi yasa" a sanyaye
tace "But he shud have listen to me..... He's a sadist I notice" dariya sosai El-
ameen yayi ta turo baki, tace "I just have to make him forgive me before leaving
that's all!" El-ameen ya d'age gira yace "Go in ki samesa...." Shiru tayi sai kuma
a hankali tace "In je?" Gyada mata kai yayi ta juya ta koma part din Mumy,
tafiyarta kawai yake kallo har ta isa kofa ta murda a hankali ta tura ta shiga,
durkushe ta gansa a parlon kusa Humainah dake kwance kan doguwar kujera idonta
lumshe, tsaye tayi bakin kofar ta kasa karasowa, kallo daya yayi mata ya dauke kai,
Dakewa tayi ta karaso parlon cikin rashin kuxari, dai dai lokacin da Humainah ta
mike xaune da sauri, ya mike ya xauna gefenta yana kallonta ganin yanda ta rame,
hannunta ya rike kamar bai son magana don bakinsa kadai yayi motsi yace "What
wife!" Ta dafe kanta bata ce komai ba, can ta d'ago da kyar tace "Amai nake ji"
mikewa yayi ya daga ta suka bar parlon, ita ko lura da Zahrah da tayi still tana
kallon ikon Allah bata yi ba har ya shiga da ita daki, Zahrah taji ta ma kasa
tsayuwar, tunda take bata taba jin abinda ta ji a lokacin a xuciyarta ba, kawai ji
tayi hawaye ya cika idonta, ta juya da sauri har tana neman faduwa ta fice daga
parlon. Bata ko kalli El-ameen dake tsaye har lokacin ba ta tafi can karkashin
bishiya tayi xamanta gun ta fashe da kuka, juyawa El-ameen yayi ya koma parlon
Abba, drinks ne da ruwa gabansu mai martaba kuma ga dukkan alamu hajja ce ta debo
masu, yana shiga tace "yauwa tafi ka kira Amadin su yi sallama da Sarkin wai xa su
koma" fita ya kuma yi ya tafi part din Mumy, khadija da fatima ne parlon don dama
suna ganin shigowar junaid suka shiga daki, amsa gaisuwar fatima yayi yace "Ina
Junaid din?" Khadija tace "Yana daki" yace "Tafi ki ce masa Abba na kiransa" mikewa
tayi shi kuma ya juya ya fita, ba a dau lokaci ba Junaid ya fito ya karasa gun El-
ameen, El-ameen yace "Hope ka saurareta dai yanxu?" Girgixa kai yayi yace "Bani da
lokacin ta, bana kuma bukatan godiyar da xata min ko hakurin da xa ta ban, don
Allah nayi mata ba don ita ba wllh" Murmushi El-ameen yayi yace "Gaskiya ne" Junaid
ya shiga parlon Abba, nan dai suka yi sallama da mai martaba dake sauraren xuwansa
da El-ameen nan da kwana biyu, Zahrah na ganin fitowar Abbanta ta mike ta nufi gate
da sauri, Ummi ta bi bayanta ganin mood dinta, Abdul ma bin ta yayi da kallo, har
bakin mota Hajja da su Abba suka raka mai martaba, sai surutu take masa kamar irin
ta san sa da can, junaid dai na biye da su a baya, lokaci lokaci mai martaba kan
juyo ya kallesa, ita ko Zahrah can wani mota ta tafi ta tsaya a baya Ummi sai
tambayarta take meyasa mood dinta ya canxa amma ta ki cewa komai, a hankali junaid
ya dinga bin wajen da kallo ganin bai ganta ba, har cikin motar dake gabansu sai da
ya kalla bbu ita, El-ameen dai na tsaye rungume da hannayensa yana kallonsa, tsaf
ya gane me yake nema, kawai yayi murmushi, Mai martaba kansa sauraren Hajja kawai
yake amma rashin ganinta ya sa ya fara waige waige shi ma, can dai yace "Ina
Zahrahn ta xo ta shiga mota" Ummi ce tace "Toh kinji Abba na neman ki ma, ki taho
mu je" ba musu Zahrah ta fito daga bayan motar sai dai duk jikinta a sanyaye, satan
kallonta Junaid ya dinga yi har ta iso gun motar da suka taho da, Hajja ta jawota
ta rungume tace "Kice ma Uwar ki ina nan xuwa, xata yi babbar bakuwa don tare xamu
taho da su Amadi, Allah ya maki albarka ni dama tun farkon ganin ki kika kwanta min
don akwai ni da tausayi" kai kawai Zahrah ta gyada mata ta bude bayan mota ta shiga
Ummi ma ta shiga, junaid bai fasa mata kallon sata ba, ita ko bata ko kalli su waye
a tsaye gun ba, tana shiga motar ta rufe ido, bata kuma bude ba sai da taji tashin
motar da fatan kai wa gida lafiya da su Hajja keyi masu, ta kalli tagar motar suka
yi ido hudu da junaid, dauke kai tayi da sauri, can kuma ta kalli El-ameen dake
kallonta shi ma, d'an murmushi ta kirkira ta daga masa hannu a hankali, shi ma ya
mayar mata da murmushin, driver ya ja motar suka dau hanyar fita daga layin. Tuni
su Abba suka shiga gida, Hajja dai har lokacin bata fasa daga ma motocin da har sun
bar layin hannu ba baki a wangale, El-ameen yace "Toh ae sai ki sauke hannun haka"
juyowa tayi da sauri tace "Kaga ikon Allah ko Aminu, ashe dama tsinannun matan
Muhammadu ne ke tare mana hanyar arxiki a gidan nan, yo gashi suna barin gidan sai
ga sarki sukutum ya kwaso kafafuwa ya xo ganin jikana...." El-ameen yayi dariya
yace "Toh jikan naki dai ba mutumin kirki bane don walakanci ya ma yarinyar daga ta
bi sa tayi masa godiya kin dai san hali..." Tsuke fuska tayi ta kalli Junaid dake
tsaye da sauri tace "Wato don ubanka ni xaka ma bakin ciki koh? Toh Allah ya isa
idan aka hanani kujerun makka nah, kai baka yi murnar ta dalilin ka sarki ya shigo
gidan ubanka ba, kasan alkhairin da yake shirin yi ma xuri'ar mu.... Ka xata
sarauta abar wasa ce... Toh gobe gobe ka shirya mu je ka bata hakuri, kasan
alkhairin da ubanta ke shirin maka...." Junaid da takaici ya ishe sa yace "Bana
bukatar komansu don ni sbda Allah nayi, mahaifina na da rufin asiri dai dai
gwargwado, nima ina da nawa rufin asirin don haka babu abinsu da xae rude ni, ke
dai ki je a kai ki makkan....." Bude baki Hajja tayi tana kallonsa cike da masifa
can ta gyada kai tace "Shegiya nake idan ban je na ce ma Ubanka mari ka sharara
mata ba" daga haka ta shige gate fuu, El-ameen ya fashe da dariya, junaid ya hade
rai sosai yace "Ka bar min irin wannan abun Ahmad bana so" El-ameen ya tabe baki
yace "Haka kawai mutum ya daura ma kansa wani hali da baxai fishesa ba a rayuwa, to
riban me ka ci don ka walakantata Ahmad, ka dai san tafi karfin ka...." A fusace
Junaid yace "Ni dai na fi karfinta don bata ma gabana, don Allah nayi abinda nayi"
dariya El-ameen yayi yace "Shi yasa naga ka dage sai satan kallonta kake...." Daga
haka ya daga kafa ya shiga gidan ya bar sa nan tsaye.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�


_By khaleesat Haiydar_�

78.....

Ranan laraba da safe misalin goma su Junaid suka yi set off din xuwa bauchi sai dai
ta plane don yace baxae iya xaman mota ba, shi ma din ba karamin takurasa Abba yayi
ba kafin ya amince xai je don da ca yayi shi baxae je ba don sbda Allah yayi abinda
yayi, xuwa lokacin dae ba laifi Mumy na amsa gaisuwarsa sae dai ba kamar da ba
hakan yasa duk ya ji ba dadi, tun ranan litinin yake gidan, ko yaje aiki nan yake
dawowa da yamma, tausayin Humainah yake sosai hakan yasa ko da yaushe yana kusa da
ita, part dinsa ya mayar da ita daga karshe ita dai Mumy nata ido, duk da luran da
yayi su Umma basa gidan haka ma Suhaima da Muhibba ko sau daya bai taba tambayar
inda suke ba, harkokin gabansa kawai yake, Hajja dake ta shiri tun daga ranan
litinin din tana jiran ranan jumma'a da Abba yace za su je bauchi da su Junaid bata
san har sun tafi ba safiyar laraban, suna cikin taxi da xai kai su Airport wayar
El-ameen ya fara ringing, cirowa yayi yaga Aliyu ne ke kiransa, shi har ya ma mance
da shi, d'an murmushi yayi ya daga kiran, daga daya bangaren Aliyu yace "Masu
Jasmine/jewel/baby!" Murmushi El-ameen yayi yace "Yea, mara mutunci da abokina bai
dawo sense dinsa ba sai dai ka ga sammaci wllh" dariya Aliyu yayi yace "Ae nasan ya
dawo ne, bayan ka xo ka dauketa ka mayar masa ae magana ta kare" El-ameen yace
"Exactly, kuma albishirin ka, ita ma ta dawo, ka dai gane me nake nufi..." Aliyu
yace "Ohh really, dama na ga alama soon xata dawo.... But what brought her back!"
El-ameen yace "That's a long story, yanxu ina hanyar bauchi ne" Aliyu yace "me xaka
yi bauchi" El-ameen ya saci kallon junaid dake kallonsa yace "Ohk! Let's chat!"
Daga haka ya katse wayar, wani uban tsaki Junaid ya ja ya dauke kansa, El-ameen
yayi dariya, junaid bai kuma kallon inda yake ba har suka isa airport. sha daya
suka sauka bauchi, El-ameen ya tare masu taxi duk suka shiga baya ya fadi ma me
taxin inda xai kai su, Sai a sannan ya juya yana kallon junaid yace "ka cika
umarnin da sarki ya baka kuwa?" Junaid ya kallesa yana jiran jin umarnin me, ganin
El-ameen bai kuma cewa komai ba har bayan kusan minti biyar yace "Wani umarnin?"
El-ameen yace "Ashe kana da baki" dauke kai Junaid yyi, El-ameen yace "Na mayar da
Humainah da yace kayi!" Shiru Junaid yayi masa na kusan minti sha biyar kafin ya
juya ya kallesa yace "Ehh" ko kallonsa El-ameen bai yi ba idonsa na kan titi,
murmushi Junaid yayi ya shafa kai, sha biyu saura suka isa masarautan, El-ameen ya
fito daga taxin haka ma Junaid dake bin ko ina da kallo, Kudi El-ameen ya ciro ya
ba mai taxin sannan ya nufi Entrance din masarautan junaid ya bi bayansa, gaba
dayansu dakakkiyar Shadda ce jikinsu, shi El-ameen ruwan hoda, shi kuma junaid
fari, yana biye da shi ne yana danna waya, tafiya sosai suka yi kafin su iso main
Entrance din da xai kai su har palace din, fixgosa Junaid yayi ganin tafiyarsa
kawai yake yace "Meye xaka wani dinga wucewa kana kyaleni a baya, ko na ce ma nasan
hanya ne" kallon mamaki El-ameen yayi masa kafin ya duka yace "To hau!" Junaid bai
san lokacin da ya fara dariya ba yace "Ka ji dan iska, kai har xaka iya goya ni?"
Murmushi El-ameen yayi ya mike don ko ba komai ya sa shi dariya baxae shiga yana
murtuke ma mutane fuska ba, a tare suka jera suna tafiya, Junaid yace "Wani disc ne
na gani daxu a hannun ka a plane" El-ameen yace "Na ban mamaki ne" Abdul dake tsaye
da abokansa biyu gun mota da alamar xa su fita ne ya hangosu ya karaso da sauri
yace "Ohh baki gare mu haka... Welcome to you guyz, sannun ku da xuwa" hannu ya
basu gaba daya biyun sannan yayi masu jagora har xuwa fada, ganin Abbansa na da
baki ya nufi part dinsa da su, suna shiga parlonsa Junaid ya nemi gu ya xauna ya
cire hular kansa, Abdul yace "Amma flight ku ka biyo koh?" El-ameen yace "Eh my oga
at the top yace bai iya xaman mota ba sbda kura" dariya Abdul yayi yana kallon
Junaid, junaid yayi murmushi yace "Manta da shi basir gare sa bai iya xaman mota
shi yasa muka biyo jirgi" dariya suka dinga yi gaba daya, El-ameen ya jefa masa
hular kansa yace "Kaji sharri...." Drinks kala kala da kayan marmari Abdul ya dire
masu ya xauna yace "Toh ya mutan gidan, ya muka baro ku?" El-ameen ne kadai ya amsa
don shi junaid kallonsa kawai yake ganin ba kaman wasa suke da kanwarsa ba, waya
Abdul ya dauka ya ce bari in kira maku mutuniyar ku gaisa kafin Abba ya sallami
b'akinsa, yana kara wayar a kunne bayan ta daga yace "Lil sis, ki taho ina jiran ki
part dina" daga haka ya katse wayar, bayan kusan minti goma sai ga ta ta shigo
parlon, wani alkybba dake daukar ido ne jikinta har yana jan kasa, shi kansa
takalmin kafarta abun kallo ne, hular kanta ya rufe kusan rabin fuskarta, tana
ganin mutane xaune parlon ta turo baki ta nufi bedroom don ta gaji da gaishe
gaishe, Abdul yace "Ina kuma xa ki bakin ki ne fa" daga kai tayi da sauri ta maida
hular saman kanta, ido hudu suka yi da junaid ya kasa dauke idonsa kanta, tayi
saurin kauda idonta ta kalli El-ameen dake kallonta shi ma ko kiftawa babu, wani
kyalli take gaba dayanta, tayi wani kyau na musamman duk da ba make-up bane
fuskarta, murmushi tayi da ya bayyana fararen hakoranta ta karasa gun El-ameen ta
durkusa nan kasa cikin sanyayyen muryarta tace "Welcome!" Kai kawai ya iya gyada
mata, Abdul kuma yayi excusing kansa ya fita, da kyar El-ameen ya samo abun cewa
yace "Ya gidan, ya su mama!" Ta langwabar da kai tace "Taso mu je ku gaisa da su"
Junaid dai danna wayarsa kawai yake, El-ameen yace "Baku gaisa da captain ba?"
Gefenta ta d'an kalla tace "Ohk, sannu da xuwa" daga haka ta mike tace "Mu je gun
Ummata" mikewa El-ameen yayi
ya dau Apple daya ya kalli junaid yace "taso mu je muyi gaisuwa frnd" junaid yi
yayi kamar bai ji sa ba, Zahrah tuni ta nufi kofa ta fita abunta, warce wayar El-
ameen yayi yace "kaga ka ajiye halin nan naka aside har mu bar garin nan, in girman
kai ne da ji da kai toh gidansa ka xo, bbu wanda xaka nuna ma a nan sai dai ma ka
kara course wajen su" mikewa junaid yayi yace "Dama don ku ci min mutunci yasa kuka
dage sai na xo garin nan, how dare her xata shigo ta ki gaisheni tana min kallon
rainin wayo, da ana rubuta hali a goshi wllh da ban fara ko da kallon inda take ba
bare har na tausaya mata" yar dariya El-ameen yayi yace "Yau kuma ba don Allah kayi
ba kenan......" Wani tafarfasa xuciyar junaid yake, El-ameen ya tabe baki yace "If
you like kar ka fito muyi me ya kawo mu bar garin nan" daga haka yayi ficewarsa ya
barsa gun tsaye, tsaye ya ga Zahrahn tana jiransu ga dukkan alama taji abinda suka
ce, murmushi ya mata yana fatan Allah yasa ba jin dai tayi ba. Ta mayar masa da
murmushin tayi gaba tana cewa "Kila yana da matsalar kunne ne, shi ya hanasa jin
sannun da nayi masa," da sauri El-ameen ya kalli bayansa ya ga ko yana gun, ya ga
ko fitowa bai yi ba, can ko sai ga shi ya fito, Tana gaba El-ameen na biye da ita a
baya shi kuma junaid na bayan El-ameen, bangaren Kilishi ta fara kai su, sosai tayi
farin cikin ganinsu, ta sa aka cika su da kayan ciye ciye da sha, Shi dai junaid
idonsa na kan makeken plasman parlon dake cike da kayan alatu, ganin yaki taba
komai tace "Kai ya sunanka, ko kai ne takwaran mai martaba?" Girgixa kai yayi yace
"A'a, Ahmad" tace "Babana ne ma ashe, to baka ci komai ba.... Ba a mana haka fa" da
ganin murmushin da yayi kai kan ka kasan kirkira yayi, ya dau slice din kankana ya
Kai baki yana tauna da kyar, ta gefen ido Zahrah ke kallonsa can ta tabe baki hade
da murguda bakin, El-ameen kuma hararansa kawai yake ta gefen ido, ita ko Kilishi
sai kallonsa take haka nan taji ya burgeta, jikinsa ne ya basa kowa kallonsa yake
ya ki daga kai ya kuma daukar apple ya kai baki ya gutsura a hankali, Zahrah tace
"Mumy bari in kai su gun Umma" Kilishi tace "Toh maxa ku je Zahrah" mikewa tayi
tana kallon El-ameen tace "Mu je" mikewa yayi shi ma yayi mata sallama tace "A'a
mai gida ai xaku dawo" kallon Junaid tayi tace "Toh tashi ku je babana" d'an
murmushi yayi ya mike yace "Sai mun dawo" daga haka suka fita gaba daya daga
parlon, a tare suke tafiya da El-ameen suna hira jefi jefi, El-ameen yace "Yayanki
ne Abdul din nan koh?" Ta gyada kai tace "Yea, stepbrother nah" ya wara ido yace
"Waow, mum dinsa ce kenan wannan!" Ta gyada kai tace "Ehh shi da Ummi" yace "Ayya,
amma kina da kanni ko yayyi the same mum kuwa" girgixa kai tayi tace "I am the only
one gun Ummata" kallonta yake da mamaki, yaji tausayin mahaifiyarta sosai, ko ya
tayi da Allah ya rabata da only child dinta, junaid dai distance me d'an tsayi ya
bari tsakaninsu yana biye da su hakan kuma bai hanasa jin hiran tasu ba, daya daga
masu girke girken fadan ne ta washe baki ganin Zahrah tace "Gimbiya ban ganki
kitchen yau ba" d'an murmushi tayi ta tsaya har ma'aikaciyar ta karaso kusa da ita,
El-ameen ya ci gaba da tafiya, Zahrah na kallonta tace "Ina ciwon kai ne shi
yasa... Ya aiki?" Matar tace "Alhmdllh, b'aki kika yi?" Kada mata kai tayi dai dai
lokacin da Junaid ya karaso ya wuce su, ta bi sa da wani kallo kafin ta tabe baki
tace "Da rana xan shigo kitchen Karima" daga haka ta nufi El-ameen dake tsaye wani
stairs yana jiranta, ita kuma matar ta bi ta da kirari, ta gefen ido junaid dake
tsaye gefen El-ameen ke satan kallonta har ya ga ta kusa isowa, El-ameen na ganinta
ya ci gaba da tafiya, shi kuma yana ganin xata wuce sa ya sa mata kafa, ko lura
bata yi ba sai ji tayi ta tafi luu xata fadi, tayi k'ara a tsorace tana neman
regaining balance, bai san lokacin da yayi saurin tarota ba ta fado jikinsa, still
tayi da farko sai kuma ta dago kai da sauri suka yi ido hudu, kasa motsi tayi ta
kuma kasa dauke idonta cikin nasa, shi ma kallonta kawai yake gabansa na faduwa,
bakinsa ta ga yana motsi a hankali ta sauke idonta kai underneath his breathe taji
yace "Jas...jasminee!" Gaba daya ta shagala da kallonsa, shi ya fara dawowa
hankalinsa ya saketa da sauri, sai a sannan ta koma baya duk ta daburce, a tare
suka juya da sauri kallon El-ameen suka ga gun wayam babu shi.

*Haske Writers association*馃挕


Afuwan pls.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

79

Da sauri ta sauka ta bi bayansa, junaid ya bi ta da kallo har lokacin xuciyarsa bai


bar bugawa ba, da kamar ya koma part din Abdul sai kuma kawai ya bi bayanta, ji
yayi gaba daya yaji haushin kansa, ya ja tsaki ya ci gaba da tafiya kamar bai son
yi, tsaye Zahrah taga El-ameen da wasu dogarawa suna hira, ta kasa karasawa gun,
juyawa yayi suna hada ido ya sakar mata murmushi, kasa mayar masa tayi, yace "ban
san hanya ba, I've to wait for you....." Karasowa tayi da kyar ba tare da ta ce
komai ba ta ci gaba da tafiya, bai bari suka hada ido da junaid dake tahowa ba ya
daga ma dogarawan hannu ya bi bayanta, tafiya kawai take amma ji take kamar xata
harde ta fadi kasa, duk yana lura da ita hakan yasa ya karasa suka jera da ita yace
"Masarautan nan naku da girma sosai" ta gefen ido ta kallesa tace "Yyeah!" Rasa
abun cewa yayi shi ma can kuma yace "But kin gama sec sch kuwa?" Shiru tayi sai
kuma ta gyada masa kai tace "Ehh!" Yace "Dat's good" junaid dai na biye da su a
baya, wata hanya daban ta dauka suka haura bene sannan ta bude wata babban kofa ta
juya tana kallonsu, suna hada ido da El-ameen ta sauke idonta kasa ta ci gaba da
tafiya, tsarin gun kamar na Kilishi da suka baro, babu kowa babban parlon sai
jakadiya da wata me goge goge, Ta nuna masu kujera, jakadiya ta bi ta da kirari
kafin tayi masu sannu da xuwa, El-ameen ne kadai ya amsa mata yana murmushi,
Bedroom din Umma Zahrah ta nufa ba a dau lokaci ba sai ga ta sun fito da Umman,
murmushi ne shimfide fuskarta har ta karaso parlon tana kallonsu gaba daya tace
"Sannun ku da xuwa...." Sakkowa El-ameen yayi har kasa Junaid ya bi sa da ido kafin
shima yayi kasa da kansa ya sauka, suka gaisheta gaba daya, tana murmushi har
lokacin ta amsa, tuni jakadiya ta cike gabansu da kayan marmari da shaye shaye,
Umma tace "To waye Ahmad waye takwaran mai martaba" El-ameen yayi murmushi yace "Ni
ne El-ameen...." Ta kalli junaid cikin sanyin murya tace "Kai ne Ahmad kenan" kai
ya gyada mata ba tare da ya dago ba, a sanyaye tace "Allah ya albarkaci rayuwar ku,
yasa ku gama da iyayen ku da duniya lafiya....." El-ameen yayi saurin cewa "Ameen
Umma mun gode" Umma ta kalli Zahrah tace "Kin kai su gun Kilishi?" Ta gyada kai
tace "Can muka fara xuwa" Umma tace "To Maa sha Allah" ba su wani dade part din
Umma ba ta dalilin bakin da tayi, Zahrah ta nufi fada gun Abbanta da su, sai dai
wannan karan sauri kawai take bata bari sun jera da El-ameen din ba, bai takurata
ba ya jira junaid, junaid na isa gunsa yace "ya kuma ku ka raba tafiyar?" Murmushi
yyi yace "Yea hakan yafi don ni ba runguma bane iyakar abinda zan mata idan na kasa
jure shariyarta gare ni" Wani kallo Junaid ke yi masa kafin yace komai El-ameen
yayi dariya yayi gaba ya bar sa nan, suna shiga fada ta juya ta bar su tare da
Abbanta. Da rana Umma ta takurata ta kai masu lunch tace ai masu aiki xa su kai
masu, Mikewa tayi d'aga karshe dai ta fita nemo Ummi ta rakata. Sae da suka fara
xuwa kitchen don tabbatar da cewar an kai abincin taga an kai, fura ta tarar ana
damawa kitchen din, ta dau babban jug ta diba snn ta dau tray ta daura kai da cups
ta fita tare da Ummi, suna isa part din Abdul Ummi ce ta fara shiga da sallama
kafin ita, Junaid ne kwance parlon yana danna waya, yayi masu kallo daya ya dauke
kai, Ummi ta xauna tana kallonsa ta gaishesa ya amsa ba tare da ya kalleta ba,
Ajiye trayn hannunta Zahrah tayi ta nufi bedroom ba tare da ta kallesa ba, El-ameen
ta gani da Abdul suna kallo ga cake gabansu, El-ameen ya buda ido murya can kasa
yace "princess!" Tace "Uhm, kun yi lunch?" Hararata Abdul yayi yace "Basu yi ba"
'yar dariya tayi ta kalli El-ameen dake kallonta, can ta karasa ciki ta xauna kusa
da Abdul ta kai bakinta kusa da kunnensa kamar me rada tace "Why is he alone?"
Abdul ya kalleta yace "Ahmad?" Satan kallon El-ameen tayi sai kuma ta dauke kai da
sauri, Abdul yace "He said he's more comfortable there" da sauri tace "Alryt, ohk"
sai kuma ta kalli El-ameen tace "Ga fura na kawo maku fa" ba tare da ya kalleta ba
yace "Toh mun gode" mikewa tayi ta fita daga bedroom din, xaune ta samu Ummi har
lokacin idonta na kan Junaid, "ki tashi mu je" ta fadi haka bayan ta dauke kai daga
kallonta, shi dai idonsa na kan waya, Ummi ta mike tace "Ohk furan xa a xuba masu
ne?" Da sauri Zahrah tace "Noo!" Sai kuma ta nufi tray din da ta dire daga gefensa
ta durkusa ta dau cups din ta xuba furan ciki ta ajiye tana kallonsa fuskarta
daure, kara wayarsa yayi a kunne ya mike xaune ya sakko da fararen kafafuwansa kasa
kamar wanda aka tilasta yayi magana yace "kina ji na?" Kasa daina kallonsa Zahrah
tayi, ya shafa kansa yace "Have you eaten?" Shiru ya d'an yi kafin yace "Ki dai
daure ki ci, I will call back later" daga haka ya katse kiran ya ajiye wayar lokaci
daya ya sauke idonsa kan Zahrah dake kallonsa har lokacin, da sauri ta dauke Kai ta
mike ta nufi kofa ta fice, har dare bata kuma komawa part din Abdul ba, duk ta rasa
me ke mata dadi mugun haushin Junaid kawai take ji, har shi xae nuna mata ji da
kai? mikewa tayi daga karshe ta fice ta nufi bangaren Abdul, El-ameen da Junaid ne
parlon wannan karan, kmr daxu kwance Junaid yake waya na kare a kunnensa, Bata ko
kalli inda yake ba ta karasa gun El-ameen dake kallon wani movie ta xauna kusa da
shi tayi fari da ido tace "Are you okay? Bbu damuwa koh" Yana kallonta yace "Yea,
am just missing home" murmushi tayi tace "Nan ma fa gida ne" yace "Yeah haka ne" ta
mike tace "Ina son ka rakani mu je garden" yace "Really?" Ta gyada masa kai tace
"Yeah, I want you to keep me company" mikewa yayi yace "Alryt mu je," duk da wayar
da ke kare kunnen junaid gaba daya ya mance waya yake, ba kallon direction dinsu
yake ba amma gaba daya hankalinsa na kansu, kofa ta nufa El-ameen ya kalli junaid
da yayi saurin dafa wayar kunnensa yace "Will be ryt back" ko kallonsa Junaid bai
yi ba har ya fita, ya mike xaune, ji yayi xuciyarsa na tafarfasa kawai, ya kusa
minti ashirin xaune har Abdul ya shigo, ko da ya tambayesa El-ameen cewa yayi bai
sani ba, yana shiga bedroom ya mike ya fice daga part din gaba daya, ji yayi da ma
safiya ce ko rana da babu abinda xai hanasa komawa katsina duk da sarki ne ya
tsaida su amma da tuni sun tafi da yamma, can wani waje da bbu hayaniya kuma babu
wani haske ya samu ya xauna, har sha biyun dare bai da niyar tashi ya shiga ciki,
gaba daya El-ameen yayi tunanin wucewa junaid yayi don yasan halinsa barin ma Atm
card dinsa na jikinsa, Abdul da mamaki ya cikasa yace "Why is he acting that way?"
El-ameen yace "That's he's hobby" Abdul bai san lokacin da ya fashe da dariya ba,
El-ameen yace "Yeah, an only son, mumy's pet" Zahrah dake tsaye ta tabe baki ta
juya ta fita daga parlon sai dai duk jikinta yayi sanyi, kasa komawa part dinta
tayi hakan yasa ta bi hanyar da tasan baxa a ganta ba ta fita waje, tafiya kawai
take ba don tasan ina ma xata ba kuma meye ta fito yi, bata yi wani nisa da tafiyan
ba tayi ido hudu da shi har lokacin yana xaune ya xuba ma taurari ido kamar me
kirgan su, rasa abinda xata yi tayi a lokacin, ci gaba da tafiya xata yi ko juyawa
xata yi ta koma, Dakewa tayi ta tsaya inda take, can ta karaso fuskar nan nata
daure tana kallonsa tace "Don me xaka wani fito nan cikin dare ka ba mutum wahalan
nemanka when I am suppose to be in bed" wani kallo ya watsa mata ta gefen ido ya ci
gaba da kallon sky abun sa, fixge wayar hannunsa tayi tace "Malam magana nake maka
fah?" Sai a sannan ya kuma kallonta suka yi ido hudu gabanta ne ya fadi sosai, ya
mike ya warce wayarsa yace "Gadina aka baki ne?" Wani kallo tayi masa tace "Ehh
sbda ta dalilina ka xo garin nan....." Shiru tayi sai kuma ta turo Baki tace "I
still can't believe ma kai ka tsince ni, or are you angry don bance kayi
accompanying dina bane" murmushi yayi yace "How will you believe it, tunda ba sani
kika yi ba lokacin da kike xuwa in bude maki Zip, in raka ki toilet, kike xuwa
bedroom dina daure da towel..... Infact har lokacin da nake taimaka maki idan kina
menses....." Xaro ido tayi, tayi wani kara tace "Nooo...." Ya gyada kai yace
"Yesss! Har lokacin da......" juyawa tayi da gudu ta bar gun, bai san lokacin da ya
fara dariya ba har da xama. Washegari kasa fitowa Zahrah tayi, kenan idan haka ne
kila har nakedness dinta ya taba gani, har da kukanta da tayi wnn tunanin, sai da
Umma ta bata rai sannan ta mike ta fita xuwa gaida su da safen, hijab tasa tsabar
bata jin xata iya kallon junaid, tana shiga parlon ko ta gansa shi kadai xaune yana
shan tea, kin dago kanta tayi ta kuma kasa karasawa can bedroom, kallonta kawai
yake yana kokarin boye murmushin fuskarsa, juyawa tayi xata fita ya mike tana ganin
haka ta kwasa da gudu, wani dariya ya taho masa bai san lokacin da ya fashe da
dariyar ba, Abdul da El-ameen suka fito da sauri, buda baki Abdul yayi ganin ashe
yana iya dariya haka, El-ameen kam karyar da kai yayi ya rungume hannu yana jinjina
abinda ya ba junaid dariya haka, da kyar ya tsaida dariyar ya daga kai yana
kallonsu, Abdul yayi murmushi yace "Ohh that's more beautiful of you captain" El-
ameen ya tabe baki yace "Ko xa mu iya sanin abinda ya baka dariya haka Ahmad, na
tabbata mu sai mun yi fiye da wanda kayi" shafa kai junaid yayi yana murmushi yace
"Bana son ku haukace da dariyar just let it" El-ameen ya daga kafada yace "Lallai
kam" daga haka ya juya ya koma dakin, Abdul ya karasa ya xauna gefensa yace "Gist
me more about ur self captain...." Murmushi junaid yayi yana kallonsa. Karfe sha
daya junaid ya gaji da xama don Abdul da El-ameen sun fita, bbu kuma yanda basu yi
da shi ya bi su ba yace A'a baxae je ba, suka yi tafiyarsu suka barsa, dama bayan
azahar xasu gana da wasu yan uwan mai martaba kafin su kama hanyar kt ranan, mikewa
yayi ya fita yana rike da wayarsa, tafiya sosai yayi ya ga wani waje kamar gun
shakatawa ga tsuntsaye sai shawagi suke, carpet grass ne shimfide gun, shiga yayi
ta wani babban kofa ya dinga tafiya yana bin ko ina na wajen da kallo, wasu kuyangu
guda uku ya gani suna tahowa ya bi su da kallo
kafin yace "Ana shigowa nan kuwa" a tare suka gyada masa kai, daya daga cikinsu
tace "Sai dai Gimbiya na nan ita ma!" Yace "Wace gimbiyar?" Tace "Gimbiya Zahrah"
bai ce komai ba yayi gaba abunsa, xaune take ita kadai tana kallon cartoon da
laptop din dake ajiye gabanta ta xauna kan kafafuwanta, gefenta kuma bowl ne me
dauke da kayan itatuwa, juyawa tayi jin taku bayanta, suna hada ido ta mike da
sauri har tana ball da bowl din fruits din gabanta, ta kuma juyawa da shirin gudu
tayi karo da laptop dake ajiye, tsallakesa tayi ta bi wani hanyar da gudu, bin ta
yayi da kallo kafin ya tabe baki ya xauna ya daga laptop din, ya dau apple daya ya
shiga ci ya canxa cartoon din xuwa something meaningful yana kallo yana murmushi.
Da yamma misalin hudu da wani abu junaid da El-ameen ne xaune a fadar me martaba
dake dauke da mutane da dama tun daga waziri, advisern sarki har xuwa kasa, sannan
ga 'yan uwansa da abokan arxiki, kanninsa mata da maza, Abdul na xaune daga gefen
Abbansa, Ummi na xaune daga daya bangaren sa, Umma da Kilishi ma duk suna fadan
xaune, Zahrah ce karshen shigowa ta nufi gun Ummanta ta xauna gefenta, kallon
Junaid kawai sarki yake, can kuma sai ya kalli El-ameen, bayan kusan minti biyu na
silence sarki yayi gyaran murya yace "Ahmad!" Dago kai junaid yayi yana kallonsa,
Sarki yace "Nasan ba lallai in iya biyan ka abinda ka min ba amma ka fadi duk
abinda kake so nan duniya in dai bai saba ma shari'a ba nayi maka alkawarin yi ma
shi idan Allah ya yarda," shiru junaid yayi, can ya dago ya kalli Zahrah da idonta
ke kansa suna hada ido ta dauke kai, kallon El-ameen yayi yaga wani gu daban yake
kallo, can ya girgixa Kai yace "Bana bukatan komai mai martaba, I helped her for
Allah's own sake" kallonsa kawai Sarki ke yi, can ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh
shknn, Allah ya albarkaci rayuwar ka Ahmad" cikin sanyin murya junaid yace Ameen,
sarki yayi murmushi ya juya yana kallon El-ameen yace "Kai fa takwara na?" Kallon
junaid El-ameen yayi suka hada ido junaid ya sauke kansa kasa, Zahrah ma idonta na
kan El-ameen gabanta na faduwa, haka kawai junaid ma ya ji gabansa na faduwa, bayan
kusan second ashirin El-ameen yace "Ina son ka min alfarmar bani aurenta, na kuma
yi maka alkawarin xan rike ta da amana...." Wani mugun bugu xuciyar junaid yayi,
Zahrah kam kallon El-ameen take ko kiftawa babu, Mai martaba da ya kafa ma El-ameen
ido shi ma yayi murmushi yace "Na baka! Xan kuma biya maka sadaki" kallon mamaki
duk occupant din palace din ke ma sarki sanin baya magana biyu, El-ameen da ya rasa
wani irin godiya xai ma mai martaba ya mike ya isa gabansa ya durkusa yana
kallonsa, shafa kansa mai martaba yayi yace "You are blessed in'sha Allah son" El-
ameen ya kama hannunsa ya lumshe ido ya kai lips dinsa, mikewa Zahrah tayi hawaye
cike idonta ta kalli junaid da yaki dago kai har lokacin tayi ficewarta daga fadan.

*Haske Writers association*馃挕


Afuwan dai.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

80......

Ko k'adan Junaid bai kuma gane abubuwan da sarki ke cewa ba a wajen gashi bai yarda
ya dago kai ba, mikewar da El-ameen yayi ya sa shi mikewa shi ma, kiran sunansa da
ya ji anyi ya sa shi juyawa yaga sarki ne ya kirasa, sarki na kallonsa yace "Allah
ya tsare hanya, ina kuma sauraron xuwar kakar ka" da kyar ya iya amsa masa yana
kirkirar murmushi sannan ya juya ya fita, tun a hanya ya dake yayi patting shoulder
din El-ameen yana murmushin karfin hali yace "Congrat frnd!" Kasa ce masa komai El-
ameen yayi yana kallonsa, suna isa part din Abdul junaid bai ko kalli kayayyakin
sawan da Abdul ya jido masu a boutique jiya ba, atm dinsa ya dauka da waya xai
fita, wani abokin Abdul yace "Baxa ka canxa kaya ba Captain, Abdul din da xai kai
ku airport ma bai gama shiri ba" cike da karfin hali junaid yace "Yeah, ina waje
nan...." Daga haka ya nufi door, El-ameen dake tsaye ya bi sa da ido, a hanya
Junaid ya hadu da Abdul, Abdul yace "A'a ina xa ka captain" junaid ya kirkiri
murmushi yace "Ina jiran ku a waje" hannunsa Abdul ya kama yace "Noo baka isa ba,
sai ka sake wanka ka canxa kaya" duk yanda Junaid ya so Abdul ya kyalesa kin
saurarensa yayi har sai da ya mayar da shi part dinsa, dole yayi wanka ya canxa
kaya, duk suka shirya, Abdul ya tafi da su xuwa gun Mum dinsa suka yi mata sallama
ta hadasu da turarruka masu tsadan gaske, sannan ya kai su part din Umma, ita kadai
ce xaune parlor da jakadiyarta, tana ganinsu ta saki fuska nan suka yi mata sallama
ta dinga sa masu albarka, shi dai Junaid kansa na kasa, tsaraba sosai ta hada masu
su biyun su kai ma Mum dinsu, El-ameen yayi mata godiya, shi ma junaid da kansa ke
kasa yayi godiyar, Abdul yace "Umma ina Zahrahn fah?" Umma tace "Ina jin bacci
take" mikewa yayi ya nufi bedroom din Umma, Umma ta bi sa da kallo har ya shiga,
kwance ya sameta cikin bargo Ummi na xaune gefenta tayi tagumi, Abdul ya karasa da
sauri yace "What's wrong with her" a hankali Ummi tace "She's just crying, me yasa
Abba xai yi mata haka.... In ma haka ne ba sai ya basu kudi me yawa ba, ina jinin
sarauta da auren....." Wani kallo ya watsa mata ya cire bargon yana kallon Zahrah,
mikewa xaune tayi ta fashe da kuka tana kallonsa, ya xauna yace "Look ki hadiye
kukan nan ki min magana, aurensa ne baki so?" Shiru tayi bata ce komai ba sai
hawaye, yace "Ki min magana mana" girgixa kai tayi a hankali tace "A'a...." Yace
"Baki son auren?" Tana goge fuskarta tace "Ni baxan iya cewa bana so ba, they
helped me and...." Ya mike yace "Good you know that! Kina hauka ma duk sun xauna da
ke da amana bare aure, yarima kamar ki kike so ko wa?" Girgixa kai tayi yace "to
yanxu tashi ki wanke fuska ki taho kuyi sallama da su" mikewa tayi da kyar tayi
yanda yace mata ta daura alkyabbarta ta rufe kusan rabin fuskarta ta bi sa suka
fita tare da Ummi, sosai Umma taji dadin ganin ta fito don bata yi tunanin xata
fito ba a yanda ta dinga kuka, har mota ta rakasu Ummi na rike da hannunta, shi dai
Junaid yana gaba sai dai yayi murmushi idan aka ce wani abu, Ummi tace "Ya Abdul mu
raka ka airport din plss?" Yace "Alryt mu je" front seat junaid ya bude ya shiga,
El-ameen ya koma baya Ummi ta shiga sannan Zahrah, Abdul da Ummi kadai ke hira a
motar, daga Zahrah, Junaid har El-ameen bbu me cewa komai, a hankali ta daga
alkyabbar fuskarta suka yi ido hudu da Junaid don kallonta yake ta madubi, ta sauke
idonta da sauri, suna isa airport junaid ya fita sannan El-ameen, Ummi ma ta sauka,
sai da Abdul ya fita sannan Zahrah ma ta fito, karasawa El-ameen yayi kusa da
Zahrah ya mika mata wani disc din hannunsa, ta daga kai tana kallonsa, sai kuma ta
karba, kallo daya junaid yayi masu ya fara tafiya, Abdul ya bi bayansa haka ma
Ummi, da kyar Zahrah tace "What's this?" Ya rungume hannayensa yace "Throw back!
That period I do call you jewel, while captain call you Jasmine," ganin kallon da
take masa na rashin fahimta yayi murmushi yace "Rayuwar ki na kwanakin baya ne.....
Watch it.. You might like it" shiru tayi tana kallonsa, ya gyada mata kai
assuringly, a hankali ta sauke kanta kasa yace "Let go" ba musu ta bi bayansa tana
jujjuya disc din hannunta, xaune suka tarda su junaid, ta xauna gefen Ummi, El-
ameen kuma ya tsaya suna jiran a kira su, lokaci lokaci ta kan juya ta kalli junaid
kuma duk kallon da xata yi masa sai sun hada ido alamar shi ma kallon nata yake,
can dai ya mike yace ma Abdul xai siyo ruwa ya bar wajen, bai kuma dawo ba sai da
aka fara announcing jirginsu ne next din tashi, hannu kawai ya daga ma su Abdul ya
shiga tafiyarsa, bin sa da ido Zahrah tayi, can ta kalli El-ameen dake kallonta ta
d'aga masa hannu ta juya da sauri ta bar gun. Har suka sauka kt bbu wanda yace
komai tsakanin junaid da El-ameen, taxi El-ameen ya tsayar masu ya kallesa alamar
ya shiga, a karo na farko junaid yayi magana yace "Ae tafiyar mu ba daya bace, ka
tafi xan samu wani" kallonsa kawai El-ameen yake can kuma ya shiga taxin da kayan
tsarabarsu ya fadi ma driver din inda xa shi drivern ya ja motar suka bar junaid
tsaye, kalle kallen inda zai xauna ta dalilin jirin da yake gani junaid ya shiga
yi, can ya samu dakali ya xauna ya rike kansa, ya kusa minti goma xaune kafin ya
mike da kyar daga karshe ya samu wani taxin ya shiga. Biyar saura ya shiga gida har
lokacin yana ganin jiri, part din Mumy ya nufa, bbu kowa parlon ya shiga bedroom
dinta, xaune ya sameta Hisnul Muslim a hannunta, kallonsa ta shiga yi har ya karaso
gabanta ya durkusa ya daura kansa kan kafarta, ita dai kallonsa kawai take, dumin
da taji a kafarta ya sa ta dago kansa tana kallo, hawaye ta gani fuskarsa, da
mamaki tace "Me ya faru?" Kasa ce mata komai yayi sai hawaye, nan da nan hankalinta
ya tashi tace "Ahmad!" Mayar da kansa yayi kafarta ta sauko kasa hankalinta ya
tashi sosai tace "Talk to me son, me ya faru" rasa abun da xai ce mata yayi kawai
ya rungumeta cikin sanyayyan muryarsa yace "Nothing mum, just forgive me plss" ji
tayi hankalinta ya kwanta, a sanyaye tace "I've done that since son" a hankali ya
xame jikinsa kansa a kasa yace "Nagode mum" daga haka ya mike ya fita daga dakin ya
koma part dinsa yana shiga ya rufe kofar yasa makulli ya hade kansa da kofar wasu
sabbin hawayen na xubo masa, ya kusa minti talatin tsaye kawai kuma ya bude kofar
ya fice, can gidansa ya nufa cikin a dai daita, yana sauka ya ba sa kudin sa ya
shiga gidan, ya kusa minti goma tsaye parlor sannan ya haura sama, dakin da Zahrah
take ya fara budewa, hular ta ne kwance kan gado da ribbon sai zaninta, gadon na
nan yanda yake tun daren da ya shigo ya tada ta bayan yaji an shigo gidan, karasawa
cikin dakin yayi a sanyaye ya dau hular da ribbon yana kallo, juyawa yayi yana
kallon takalminta dake ajiye a kasa daga kusa da gadon, ya kalli gaban mirror dake
dauke da kayan shafanta, sai Qur'aninta dake ajiye daga gefe, xaunawa yayi gefen
gadon ya lumshe ido ya rike kansa da yayi masa nauyi. A can masarautan bauchi kuwa
tunda Zahrah suka dawo take kuka a dakinta bayan ta kulle kanta, bbu wanda ta
saurara ta bude kofar har kusan goma na dare, mikewa tayi xaune da sauri tana
kallon disc din da El-ameen ya bata da ta ajiye gefenta, dauka tayi ta mike ta nufi
inda laptop dinta ke ajiye ta dauka ta dawo ta xauna gefen gado ta bude ta kunna.
.

*Haske writers association*

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

81

Still Zahrah tayi ganin kanta xaune a wani parlor kasan rug, doguwar riga ce
jikinta da hula a kanta, Junaid ta gani tsaye parlon yana danna waya can ya karaso
ya xauna kujera, gani tayi ta juya tana kallonsa, shi ma kallon nata yake can ya ci
gaba da dannar wayarsa, wata dattijuwa ce ta shigo parlon tana isowa gabanta ta
xauna ta ajiye plate din hannunta me dauke da potatoe da ketchup, dattijuwar ta dau
potatoe daya ta dangwala da ketchup din ta kai mata baki, taga ta karbe daga
hannunta tana jujjuyawa can ta Kai baki ta lashe sannan ta mayar mata, tuni hawaye
ya cika idon Zahrah, Junaid dai kallonsu kawai taga yake, dattijuwar ta jawo ta
jikinta ita ko tayi lamo, saukowa junaid yayi ya dau dankalin ya kai mata baki ta
kauda kai da sauri ta dinga shigewa jikin dattijuwar, ya tabe baki ya ajiye, Suna
ta xaune a haka sai ga El-ameen ya shigo parlon, kallonsa kawai Zahrah take ko
kiftawa bbu, farar 3 qtr ne jikinsa sai blue polo kallo daya yayi ma junaid ya
karaso ya durkusa gabansu ita da dattijuwar ya ajiye ledan hannunsa, ba a dau lkci
ba dattijuwar ta mike bayan ta xaunar da ita ta bar wajen, taga El-ameen ya xauna
gabanta ya dago kanta yana kallon fuskarta ita ma kallon nasa take, Junaid dai bai
ko kallesu ba waya kawai yake kallo, murmushi me kyau El-ameen ya mata taga ya
lakaci hancinta ita dai idonta na kansa, dankali ya dauka ya dangwali ketchup ya
kai mata baki ta kauda kai, hade rai taga yyi ya rike kanta ya kai dankalin
bakinta, a hankali ta ga ta fito da harshe ta lashe ketchup din, dariya ta ga ya
fara yi yana kallon junaid da yaki kallon inda suke, Zahrah bata san lokacin da
tayi murmushi ba hawaye na sakko mata, taga ya kuma dangwala ya kai mata ta lashe,
xaro ido tayi ta rike breathe ganin ya kai dankalin baki, sai kuma ya kalli Junaid
da sauri yaga ba kallonsu yake ba, sosai jikinta yayi sanyi ta kasa daina kallonsa
wasu sabbin hawayen na xubo mata, gani tayi junaid ya mike ya fice daga parlon, El-
ameen ya jawo ledan da ya shigo da ya bude ya fiddo da magunguna da hollandia
yoghurt, ya jawo cup din dake wajen ya bude drink din ya xuba ciki sannan ya dauka
ya kai mata baki ba musu taga ta bude bakin tana sha har ta kauda kanta daga
karshe, kadan ya sha ya ajiye cup din ya mike ya bar wajen, gani tayi ta jawo cup
din ta juya upside down, drink din ya malale a gun har a jikinta, El-ameen ya
karaso wajen yana kallonta, can ya hade rai ya durkusa ya ja hancinta, hannu tasa
ita ma tayi yanda yayi sai kuma ta ja nasa hancin shi ma, murmushi Zahrah tayi ta
lumshe ido, can ta bude a hankali, magani taga ya kada a cup ya kai bakinta, ba
musu ta bude ya juye mata, ta shiga yamutse baki ya ciro handkerchief a aljihunsa
ya goge mata bakin ya mayar sannan ya mike, Datijjuwar daxu ta ga ta dawo, shi kuma
ya bar parlon, dattijuwar ta daga ta bayan ta dauke cups din gun suka bar parlon.
Haka Zahrah ta dinga kallon irin rayuwar da tayi a baya, duk jikinta yayi sanyi
sosai banda hawaye bbu abinda take, wani gun tayi murmushi wani kuma tayi dariya,
tunanin da me xata biya dattijuwar nan ta dinga yi, har inda take xata so a kai ta,
wani tausayin El-ameen ta ji dinga ji har cikin ranta, ashe haka yayi hidima da
ita, ta ga dai kafin ta ga kanta tare da Junaid sau daya ta ganta da El-ameen sau
goma, kuma taga junaid da ya shigo bai wuce minti biyar sai taga ya fita kuma
kullum fuska a daure barin idan El-ameen na gun, a wani gu ne ma da El-ameen baya
parlon taga ya xauna gabanta har ya dago kanta yana kallonta, can kuma ya mike ya
koma kujera, gajiya Zahrah tayi daga karshe ta kashe laptop din ta koma ta kwanta a
sanyaye, kasa bacci tayi daren ranan tunanin El-ameen take? na junaid ne? Duk ta
kasa tantancewa da kyar ta samu bacci ya dauketa sai dai har asuba mafarkan junaid
kawai take, tana idar da sllh bayan ta tafi ta gaida Abbanta da Umma ta tafi
bangaren Kilishi ita ma ta gaida ta, Ummi ta shiga nema ta ganta bedroom din
Kilishi ta ja ta suka fita ta koma part dinta da ita, Ummi tace "Ohh sis bacci fa
xan koma" suna shiga bedroom Zahrah ta xaunar da ita ta ciro laptop dinta dake
charge ta ajiye gaban Ummi tace "Idan kin gama kallon nan akwai tambayar da xan
maki" daga haka ta kunna mata ta fice daga dakin, da farko Ummi kamar ta kashe
laptop din tayi kwanciyarta sai dai hango yar uwarta da tayi a xaune ya sa ta bude
ido daga nan kuma ta maida hankalinta gaba daya kai. Takwas saura Ummi ta fito
parlor ta samu Zahrah kwance idonta lumshe alamar bacci take, jiki a sanyaye ta
karasa ta xauna kusa da ita ta dafa ta cikin sarkewar Murya tace "Sister!" Bude ido
Zahrah tayi da sauri tace "Ahmad!" Sai kuma ta maxa ta mike xaune tana kalle kalle,
kallonta kawai Ummi ke yi, murya can kasa tace "Ahmad?" Zahrah da duk ta daburce
lokaci daya tace "Ohh, Ummi, kin gama kallon ne" Ummi ta share hawayen fuskarta
tana murmushi tace "Yeah and I love it Zahrah, I love it... Xan kai ma su Abba su
ma su kalla...." Tana magana ne hawaye na xubo mata, Zahrah da ita ma hawayen ya
cika idonta a hankali tace "but ina son in maki tambaya!" Ummi ta kalleta tayi mata
murmushi tace "Ina jin ki My sis" Zahrah ta sauke idonta kasa tace "Between the two
of them, waye ya ci ace baxan mance ba har karshen rayuwata, nd who deserve me?"
Kallonta kawai Ummi ke yi, can tayi murmushi a hankali tace "My Dad! El-ameen... He
soo deserve you sis, he gave you all his time, he took care of you, bai kyamace ki
ba, bai kuma taba gajiya da ke ba....." Kuka sosai Zahrah ta shiga yi tana kallon
yar uwarta, Ummi da jikinta yayi sanyi tayi shiru tana kallon ta ita ma, cikin
rawar Murya Zahrah tace "Toh shi Ahmad fah?" Ummi ta sauke idonta kasa a hankali
tace "Yeah yayi maki kokari sosai shi ma, just that na lura shi ba mai son hayaniya
bane, sannan miskiline, kuma na lura bai son yanda El-ameen ke yi maki, sai naga ma
kamar kishi yake duk da baya cewa komai, indai El-ameen na parlon naga baya xama
sai kawai ya fita, idan kuma ku biyu ne kadai ya kan xauna kusa da ke, sai dai kuma
baki saki jiki da shi yanda kika yi da El-ameen ba, bai kuma san ma yanda xai kula
da ke ba" Zahrah ta jinginar da kanta jikin kujera ta lumshe ido, Ummi ta kamo
hannunta tace "El-ameen na son ki sosai Zahrah, duk da halin da kike ciki bai
kyamace ki ba don har abinda kika kai baki yana ci....." Zahrah ta bude ido tana
kallonta, murmushi ta kirkira tace "Yeah na gani" Ummi tayi murmushin ita ma ta
mike ta dau Laptop din ta fice tana cewa "I just love this sweet sis, xan kai ma
Abbanmu...." kuka sosai Zahrah ta fashe da bayan fitar yar uwarta, ita kanta ta
rasa kukan me take ta mike da gudu ta shiga bedroom ta fada kan gado ta dinga rera
kukan. Da kyar Junaid ya iya fita masallaci sallahn asuba, yana dawowa kuma yayi
kwanciyarsa nan parlor kan kujera don bai jin xai iya fita aiki, ya rasa gane
xaxxabin me ke son rufe sa, mikewa yayi daga karshe ya koma sama yayi wanka ko xai
iya xuwa aikin, kamar kar ya fito ya ji wani sanyi na shigarsa duk da ba da ruwan
sanyi yayi Wankan ba ma, ya dade kwance cikin bargo kafin ya mike ya shirya cikin
kananun kaya ya dau makullin motarsa ya fita, gida ya nufa yana gama parking ya
fito ya tafi bangaren Mumy kansa na sara masa, fatima ce xaune parlor da Humainah
da khadija, bai iya ya amsa gaisuwar da suke masa ba ya shiga dakin Mumy, bbu kowa
dakin ya kwanta kan gadon, bai yi minti biyar da kwanciya ba Mumy ta shigo, tsaye
tayi bakin kofar tana kallonsa can ta karaso kusa da gadon tace "Ahmad!" Bude ido
yayi yana kallonta, hannu ta daura forehead dinsa tace "Are you sick?" Mayar da
idonsa yayi ya lumshe yace "Just headache mum" mikewa tayi ta fita sai ga ta ta
dawo da cup din tea tace "Tashi ka sha shayin sai in baka Magani" ba musu ya mike
xaune ya karba cup din ya shiga shan tea din, kadan ya rage ya ajiye, Mumy ta dauko
masa paracetamol da ruwa a cup ta mika masa, ya karba ya hadiye maganin, tsaye tayi
tana kallonsa don ta ma yi mamakin da ya karba maganin, mikewa yayi da sauri tace
"You better don't do that...." Tsayawa yayi da farko yana yamutse fuska ta galla
masa harara, sai kuma ya shige bathroom sai amai, tana nan tsaye har ya fito, bai
bari sun hada ido ba ya koma ya kwanta ya lumshe ido, tace "Sai ka tashi mu tafi
asibiti, saura in mun je ka gudo" girgixa Kai yayi cikin sanyin murya yace "Wllh
bacci nake ji Mumy jiya ban yi bacci ba, idan na tashi sai mu je" ta kusa minti
biyar tsaye tana kallonsa bata ce komai ba, har ta ga alamar bacci ya fara
daukarda, karasawa tayi ta dau wayarsa ta sa masa a silent ta ajiye sannan ta fita.
Sai kusan karfe sha biyu junaid ya farka da wani matsanancin ciwon kai, da kyar ya
mike xaune, El-ameen ya gani dakin xaune yana hada drip ga injections a gefe guda,
El-ameen ya sakar masa murmushi ya mike yace "You are awake!" Dauke kai junaid yayi
yana kokarin mikewa, El-ameen ya xauna ya riko hannunsa yace "What's wrong with
you, lafiya muka rabu jiya fa?" Junaid ya dake yace "ce maka aka yi bani da
lafiya?" El-ameen yace "Yeah, Zahrah ma na son gaishe ka wai, I told her you are
sick" daga haka ya jawo wayarsa, wani kallo junaid ke yi masa xuciyarsa na
tafarfasa.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

82.....

El-ameen ya gama danne dannensa ya Kai wayar kunne bayan few seconds yace "Hello
Zahrah, here is the captain" daga haka ya mika ma junaid wayar yana kallonsa, kin
kallon inda yake junaid yayi, har sai da yace "Ahmad!" Sai a sannan junaid ya
kallesa yace "Did I told you am sick?" El-ameen yace "Yeah! I know you are okay,
but karbi wayar...." Wani kallo junaid ke yi masa kafin ya karbi wayar ya kai
kunne, gabansa ya fadi sosai jin muryarta da ya daki ear dinsa tace "Hello!" Dakewa
yayi yace "Yeah, ina ji" shiru tayi shi ma haka, bayan kusan second ashirin ya
kalli screen din wayar ya ga ba a kashe ba, mayarwa yayi kunnensa ya hade rai yace
"Hello!" Tace "Yeah! Ina ji nima" tsaki ya ja ya katse wayar ya jefar kan gado ya
juya yana kallon El-ameen yace "Kaga ka bar ja min raini gun yarinyar nan plss, ku
je can ku karata ka daina sako ni a abun ku...." Murmushi El-ameen yayi yace
"Alryt.... Yanxu dai bari in sa maka ruwan nan in maka allura am leaving" a fusace
junaid yace "Wai ca nayi maka bani da lafiya ne, let me plss" mikewa yayi ya shige
toilet ya kulle ya hade kansa da kofa, Murmushi El-ameen yayi ya fita ba a dau
lokaci ba ya dawo tare da Mumy, tana kallon kofar toilet din tace "Ahmad!" Sai da
ta kuma kiransa sannan ya amsa a hankali, strictly tace "Come out" ba musu ya fito
jiki ba kwari ya karasa kan gadon, Mumy na tsaye El-ameen ya sa masa drip din sai a
snn ta juya ta fita, El-ameen yayi 'yar dariya yace "Gaskiya ne Mumy's boy" ko
kallonsa Junaid bai yi ba ya koma ya kwanta kan gado, El-ameen ya dau makullin
motarsa da waya ya fita, lumshe ido Junaid yayi xuciyarsa na bugawa, bayan minti
goma da fitar El-ameen aka bude kofar dakin, Humainah ce ta shigo ya bude ido yana
kallonta, karasowa tayi kusa da gadon ta durkusa tana kallonsa tace "Baka da lafiya
ne?" Chin dinta ya dago yana kallon fuskarta yace "How are you feeling now" a
hankali tace "Alhmdllh" yace "Kina cin abinci yanxu?" Girgixa masa kai tayi ta
kwantar da kanta kan gado har lokacin tana kallonsa tace "Only tea" gefensa ya nuna
mata, ba musu ta mike ta dawo kusa da shi, ya daura hannu kan tummy dinta yace "Ya
babyn?" Hannu ta buda masa alamar bata sani ba, yayi murmushi tayi kwanciyarta
gefensa, komawa yayi shi ma ya kwanta tare da lumshe ido. Sha daya saura aka buda
kofar dakin Hajjo ta shigo, fashe wa da kuka tayi sosai ta karaso kusa da gadon
tace "Ya baxa ka kwanta ciwo ba ka yaudare ni ka ci amanata Ahmad, har ni xaka
dinga ma bakin ciki, to dadin abun dai ni ba talaka bace, kuma dukiya me uban yawa
mijina ya mutu ya bar min wanda ko da xanje makka sau dari baxa su girgixa ba, ku
abun duniya ya tsole ma ido kai da uban ka" tana kai wa nan ta nufi kofa fuu,
junaid ya bita da kallo har ta fita, Humainah kam murmushi tayi ta koma ta kwanta.
Da yamma junaid na kwance duk ya rasa me ke masa dadi so yake kawai ruwan ya kare
ya cire ya fita daga gidan ko xai ji dadi, ba don Mumy ba da tuni ya tuge drip din,
Humainah na kwance nesa da shi tayi bacci tun daxu, bude kofa aka yi El-ameen da
Aliyu suka shigo dakin, kallonsu kawai yake Aliyu ya karaso shi ma yana kallonsa
yace "Baka ji dadi ba ashe" junaid bai ce komai ba, Aliyu ya kara da cewa Allah ya
sauwake" sai a sannan yace "Ameen thank you" El-ameen yace "My frnd Dr Aliyu hope
ka gane sa" Junaid bai ce komai ba ya nuna ma Aliyu kujera ya xauna, Aliyu yace "Am
ohk here" El-ameen yace "How are you feeling now Ahmad?" Dakewa junaid yyi yace
"Naji sauki ka cire min ynxu" El-ameen yace "No! Sai ya kare, am coming back later"
Junaid ji yayi kamar ya shakesa sai dai bai ce komai ba, El-ameen yace "Idan kaji
sauki in shaa Allah xuwa gobe xa ka rakani bauchi, sarki na nemana" duk da faduwar
da gaban junaid yayi bai nuna ba yace "baxan iya barin aikina in je bauchi ba" El-
ameen yace "Alryt, Aliyu sai ya rakani," daga haka ya juya ya nufi kofa yace "Sai
na dawo ltr" ba tare da Aliyu ya kuma kallon Junaid ba yace "Allah ya kara afuwa"
daga haka ya fita shi ma, mikewa xaune junaid yayi ya dafa kansa. A can bauchi kuwa
Zahrah duk ta daga ma mahaifanta hankali ita fa sai an kai ta gun dattijuwar matar
nan duk inda take, da farko lallabata mai martaba ya dinga yi yace ta bari xa a
nemo matar a kawo ta masarautan ganin ba hakura zata yi ba yasa yace a kira masa
El-ameen. Washegari El-ameen ya dau hanyar bauchi tare da Aliyu, haka kawai yaji
gabansa na faduwa, addu'a ya dinga yi a xuciyarsa Allah yasa ba fasa basa auren mai
martaba yyi ba, Aliyu dai sai dariya yake masa yace "Ana xaune kalau xaka jajibo ma
kanka aure, auren ma daga gidan sarauta.... Tab xaka sha takaici kuwa" murmushi El-
ameen yayi yace "Can xa a sha takaici ba ni ba" Aliyu yace "Ni dai don kawai ina
son ganin babe din ne shi yasa xan bi ka amma bbu ruwana da neman aurenka, ni bayan
Hafsat nake" El-ameen bai tanka sa ba ya kuma cewa "Toh wai yasan kana da mata
kuwa?" Gyada kai El-ameen yayi yace "Yeah, I told him everything" Aliyu ya xaro ido
lkci daya ya fara dariya yace "Ni i thought gidan sarauta basa bada 'ya yansu wa
mai mata, Toh did your parent know about this?" El-ameen ya masa wani kallo yace
"Yeah i told my dad, nd stop dusturbing me plss" Aliyu yace "Toh me yace?" El-ameen
bai sake tanka sa ba har suka isa bauchi, sun jima hotel din da suka yi lodge kafin
su tafi can masarautan don Aliyu yace baxai sauka gidan mutane ba, babu bata lokaci
aka gabatar da su gaban mai martaba, El-ameen dai har lokacin gabansa bai bar dukan
uku uku ba, duk ya kagu yaji kiran me sarki yayi masa, bayan gaisuwa sarki yace
"Ina Ahmad din?" El-ameen yace "Ba tare muka taho ba, baya jin dadi" Sarki yayi
masa addu'ar samun sauki, bayan few seconds yayi gyaran murya yace "Al-ameen!"
Kallonsa El-ameen yayi ya kasa amsawa, Sarki ya ci gaba da cewa "Na yarda da kai na
aminta da kai yasa xan hada ka da Zahrah da yar uwarta ka kai su duk inda matar nan
me kula da ita take, kwana biyu kacal xasu yi a katsina idan ka tashi dawo da su
kuma har da dattijuwar nan xa ku dawo" wani boyayyen ajiyar xuciya El-ameen ya
sauke a hankali yace "In'sha Allah ran ka shi dade...." Daga haka ya sallamesu suka
bar fadan, Wazirin sarki dake fadan yace "Is this a good decision kuwa, in suka
sauka katsinan ina xai ajiye su, its not safe tafiyar su su kadai, i think gwara
Abdul ya bi su" Sarki yayi murmushi yace "Da tuni sun cutar min da Zahrah" Aliyu
sai dariya yake bayan sun fita yace "Tun ba ayi aure ba ka fara xama masinja, anya
abun nan xai yiwu kuwa Dr...." Murmushi El-ameen yayi yace "Xa dai su xama masinja
can..." Washegari da safe suka kuma daukar hanyar kt tare da Zahrah da Ummi, Zahrah
dai sai kallon Aliyu take lkci lkci a jirgi, yana lura da haka can dai yace "Ya dai
'yan mata da kallo haka?" Tabe baki tayi tace "Just that you look familiar, nothing
else...." Ya wara ido yace "Really? A ina kika san ni toh?" Shiru tayi kafin tace
"I think... Ohk sorry it might be a dream" yana gyada Kai yace "That's woaw, a ina
kika gan ni a dream din?" Kallon El-ameen dake ta kallonsu tayi tace "Wani waje, I
think it's a garden... Ohh I really can't remember, yes a garden..." murmushi sosai
Aliyu yayi yana gyada kai yace "It's a pleasure meeting u in dream land" bata kuma
tanka sa ba ta dauke kai. Suna sauka kt El-ameen ya tare masu taxi, sun dau hanya
Zahrah tace "Ina xa mu yanxu?" Kallonta yayi yace "My home, Hafsat will be glad to
see you" girgixa kai tayi tace "Noo! Kai ni gun Granny din Ahmad Junaid" kallonta
El-ameen ya tsaya yi, can ya lumshe ido yace "Ohk, Alryt" daga haka ya fadi ma me
taxin inda xai kai su, Aliyu yace "Bari in sauka nan, kar ya rainani idan ya sake
ganina gidansu" murmushi kawai El-ameen yayi yasa mai taxin yayi parking Aliyu ya
sauka, El-ameen yace "Thanks frnd sai mun yi waya" d'aga ma Zahrah da Ummi hannu
Aliyu yayi ya bar wajen. Suna isa kofar gidansu Junaid El-ameen ya fara fitowa
sannan Ummi da Zahrah, ya ba mai taxin kudi ya kallesu yayi murmushi yace "Mu je"
bin bayansa suka yi ya nufi gate. Part din Hajja ya nufa da su, khadija ce kwance
parlon da Rahma mikewa xaune suka yi gaba daya suna kallonsu barin Khadija dake ta
kallon Zahrah, El-ameen yace "Hajja fah?" Rahma xata yi magana sai ga Hajja ta fito
cike da masifa jin muryar El-ameen, sororo ta tsaya tana kallon Zahrah, El-ameen
yace "Kin yi bakuwa Hajja..." Wani shewa tayi ta karaso ta rungumeta tace "Ikon
Allah, dama idan Allah ya so ka da arxiki duk nacin mahassadi sai dai ya mutu don
sai kayi arxikin nan, sannu yar sarki jikar sarki, kiri kiri suka gudu suka bar ni
sai gashi kin xo daukata..." El-ameen yayi murmushi ya nuna ma Ummi dake ta kallon
ikon Allah kujera ta xauna, ya kalli Zahrah yace "Xan dawo da dare" daga haka ya
fice daga parlon, Hajja ta rasa inda xata sa Zahrah da yar uwarta kawo wancan kawo
wannan duk ta cikasu da kayan ciye ciye, Su khadija suka xama 'yan kallo, hannun
Zahrah ta kama daga karshe tace "Mu je ki gaida Amina ita daya ce mata a gidan
yanxu, kinsan sauran duk nasa an mayar da su gida, sbda jikokina da suka sa ma ido
barin Ahmad" Ita dai Zahrah bin ta kawai take har suka shigo parlon Mumy, nan
gabanta ya shiga faduwa, Fatima ce ke shara a parlon, Hajja tace "Ke ina uwar ki?"
Fatima na kallon Zahrah tace "yanxu ta fita kasuwa...." Hajja tace "Toh dama wa xai
aike ku ya sha takaici duk baku da amfani ai, Ahmad din na ciki har yanxu?" Girgixa
kai fatima tayi tace "Yana bangaren sa" kama hannun Zahrah Hajja ta kuma yi suka
fita tana cewa "Mu je ki gaida sa ba lafiya, kinsan Allah baya kyale ma ci amana da
mai bakin ciki.... Toh abinda ya samu Amadi kenan" d'an murmushi Zahrah tayi duk da
bata gane inda xancen Hajja ya dosa ba, bbu kowa parlon junaid haka yasa ta kuma
jan ta har bedroom, ita dai gabanta ya ki daina faduwa tana biye da ita, yana xaune
gefen gado idonsa na kan abinda Humainah take, sanye yake da 3qtr da singlet fari,
kana ganinsa kasan har lokacin he's not his self, Humainah kuma na durkushe gabansa
tana xuba masa pepper soup din kayan ciki da Mumy tayi masa, juyawa suka
yi gaba daya suna kallon bakin kofar, Hajja ta washe baki tace "Amadiii...."
Kallon mamaki kawai yake ma Zahrah ko kiftawa babu gani yake kamar mafarki yake,
ita kanta kallonsa take ta kasa karasowa, Hajja ta janyo ta hakan yasa ta saurin
dauke kai daga kallonsa Hajja tace "Mai martaba ne ya turo ta ta gaisheni...."
Humainah da tayi ma Zahrah kallo daya bata kuma dago kanta ba, xuba pepper soup din
kawai take ba tare da tasan abinda take ba ga wani bugu da xuciyarta yake, Can ta
mike bayan ta rufe kulan xata fita Hajja ta fixgota tace "Keee baxa ku gaisa ba, me
sunata kenan fatima, ita ce wanda yayanki ya ceci rayuwarta tana ganiyar hauka,
baki ganeta bne..." Humainah da xuciyarta ke bugawa har lokacin ta kalli Zahrah a
karo na biyu, ita kanta Zahrah kallonta take, Hajja ta kalli Zahrah tace "Kin ga
matarsa kenan, ita ma jikata ce, na ma fi sonta a kan sa wllh, xan iya komai a
kanta, sunanta Humainah" kasa cewa komai Zahrah tayi, ita kanta xuciyarta bugawa
yake, Da kyar dai ta bude baki tace "Sannu!" Ba karamin Dakewa Humainah tayi ba na
ganin ta bata amsa tace "Yauwa!" Daga haka ta fice daga dakin, Zahrah taji duk
jikinta yayi sanyi, a ranta kuwa tunani take ashe akwai warce xata fi ta kyau,
kallon junaid tayi taga har lokacin idonsa na kanta, ta sunkuyar da kai da sauri,
Hajja da baki ya ki rufuwa tace "Toh ki karasa ki masa sannu man, amanata ya ci
Allah ya kamasa kin san gudu suka yi basu je da ni ba, daxu da asuba ina idar da
sllh na daga hannu biyu nace Allah na yafe masa, kila shi yasa kika gansa a haka
yanxu" murmushi Zahrah ta kirkira tana jan kafa ta karasa gaban gadon da kyar tace
"Ya jikin?" Bai ce komai ba bai kuma fasa kallonta ba irin kallon da na kasa
fassarawa, ji tayi kafafuwanta sun gaza daukarta, ta kasa ci gaba da kallonsa, ta
durkushe wajen.

*Haske writers association*馃挕


Afuwa!

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

83......
Hade rai Hajja tayi tana kallon Junaid tace "Ya haka tana gaishe ka kayi mata
shiru?" Bai tanka ta ba ya dauke kansa daga kallon Zahrah da yake, Hajja tace "Ae
ko a haka xaka kare, wawa ne kadai ke hali irin naka" Shi dai bai kalli inda take
ba bare ta sa ran amsa, mikewa Zahrah tayi jiki a sanyaye Hajja tace "Rabu da
Gantalalle" daga haka ta kama hannun Zahrah suka fita, murmushi yayi ya bi kofar da
ido, can ya dauke kai ya lumshe ido ya bude, mikewa yayi ya koma parlor ya xauna.
Har yamma Humainah bata koma part din Junaid ba shi ma kuma bai fito ba duk da
xaman part din nasa ya ishesa, Zahrah kam na bangaren Hajja dake ta jan ta jiki
kamar ta maida ta ciki, su khadija sai kallon ikon Allah suke, ko ta kan Ummi bata
wani bi sai Zahrah. Bayan la'asar junaid na dawowa masallaci ya shiga part din
Mumy, bbu kowa parlon ya nufi bedroom din Humainah da fatima, Humainah kadai ce
xaune dakin, ya karasa yana kallonta yace "Why did you leave daxu?" Sosai ta hade
rai bata ce komai ba, ya rungume hannayensa yace "Baki gane ta bane?" Kamar jira
take ta fashe da kuka, ya bude ido yana kallonta, tayi mai isarta tayi shiru, yace
"Ina Mumy?" Kin cewa komai tayi har sai da ya kuma tambayarta, muryarta na rawa
tace "Tana gun Hajja" juyawa yayi ya fita daga dakin. A hanya ya hadu da Mumy xata
koma part dinta, tace "Ya jikin!" Yace "Alhmdllh Mum" tace "Ashe bakuwa aka yi" kai
kawai ya gyada mata tace "Toh da kyau, El-ameen din fa" girgixa mata Kai yayi yace
"Ban sani ba Mumy" daga haka ta karasa part dinta, shi kuma ya nufi bangaren Hajja,
Zahrah na xaune parlor Hajja kuma ana kitchen da fatima tana gwada mata ynda xata
yi ma kajin da Mumy ta Kai masu, Ummi kuma na can daki ta gaji da hayaniyar Hajja
tayi kwanciyarta, Zahrah bata ko kalli inda Junaid yake ba har ya karaso ya xauna
yana kallonta ta gefen ido, jikinta ne ya bata kallonta yake ta mike xata bar
parlon ya fixgota har sai da ta kusa faduwa, xaro ido tayi tana kallonsa cike da
masifa sai dai kuma ta kasa masifar, bude kofar parlon aka yi ya sake hannunta, El-
ameen ya shigo da sallama, sai ga Hafsat ma ta shigo parlon, kallonsu kawai junaid
yake haka ma Zahrah, El-ameen yayi murmushi yayi xamansa kan kujera Hafsat ma ta
xauna tana kallon junaid murmushi dauke fuskarta tace "Ina yini Captain!" Murmushin
ya mayar mata yace "Lafiya lau, ya kike Hafsat" tace "Alhmdllh" Zahrah dai na tsaye
har lokacin sai satan kallon Hafsat take, El-ameen yace "Meet Hafsat Zahrah, ae kin
santa" sai a sannan ta kirkiri murmushi ta xauna tana kallon Hafsat tace "Sannu!"
Hafsat ta mayar da murmushin tace "Yauwa, ya hanya!" Ba tare da ta kalleta ba
Zahrah tace "Alhmdllh!" Hajja ce ta fito daga kitchen tana kallonsu El-ameen tace
"Yaushe wa ennan suka shigo" Hafsat ta sauka har kasa ta gaida ta, Hajja ta washe
baki tace "Sannu 'yar nan, ko sanin ki bn yi ba sai yau, ya gidan?" Hafsat tace
"Alhmdllh" Hajja tace "Kema kin xo ganin bakuwa yar sarki kenan?" mikewa Junaid
yayi ya fita daga parlon. Bai sake haduwa da Zahrah ba har washegari da yamma, yana
son xuwa amma ya hana kansa fita, da yamman ranan kuma El-ameen ya kawo mama jummai
gidan bayan wahalar da ya sha na nemanta, Zahrah na dakin Hajja, Hajja ta aiki
khadija ta kirata bayan El-ameen yayi mata bayanin wacece mama jummai, tsaye Zahrah
tayi bakin kofa tana kallon mama jummai dake rakube waje daya parlon, da gudu ta
karaso ta rungume ta hawaye cike idonta cikin sanyin murya tace "Mama!" buda baki
mama jummai tayi tana kallonta da mamaki, can ita ma ta rungumeta tace "Allah
Akbar, kaddai ace min yar nan ta warke?" Hajja tace "Kaji wani mugun alkaba'i ko,
yo so kike kiyi ta ganinta a haukace 'yar nan? Toh hankalinta daya da naki yanxu
dai..." Mama jummai dake kallon Hajja tace "Ayya hajia, ae ni nama fi kowa son
ganin warkewarta, ban kuma yi tunanin xan sake haduwa da ita a duniya ba...." Sai
kuma ta fashe da kuka ta kuma rungume Zahrah tace "Allah sarki ne, Allah Akbar"
Hajja ma ta fashe da kuka tace "Ae ni xan gaya maki wannan, sannan ina me maki
albishir da cewa kin haye, ba ke ba wankau da talauchi har abada... Yar sarki
sukutum ce nan kike gani jikin ki, yanxu haka kafar ki kafarta har masarautan su,
wato da baki rike ta da kyau kin kula da ita tsakani da Allah ba da sunan ki
asararriya yanxu, nasan har sai kin gaji da hawa jirgi xuwa makka...." Washegari
da ya kama asabar su Zahrah na ta shirin komawa Bauchi har da Hajja da ta hada
kayanta jaka guda, shi dai Abba bai ce mata komai ba amma da ganinsa kasan bbu
yanda ya iya da ita ne, Mumy ce tayi karfin halin yi mata magana cewa bai kamata
ba, nan ta balbaleta wai bakin cikin ita ma xata mata, ko a jikin junaid da in ma
kayanta gaba daya xata dauka ta koma bauchi bbu abinda ya sha masa kai don abinda
ya damesa a xuciya kadai ya ishesa, Karfe goma El-ameen ya iso gidan, part din
Junaid ya nufa ya samesa parlor, tsaye yayi daga bakin kofa yace "Yah! Xaka rakamu
bauchin ne yau?" Junaid ya kallesa yace "A wani dalili?" El-ameen yace "A dalilin
tare xa mu da hajja" Junaid bai kuma tanka sa ba sae kwafa da yayi, El-ameen ya
daga kafada ya juya ya fita, har part din Mumy hajja ta kai Zahrah su yi sallama da
Humainah, dakin Mumy suka sameta Humainah ta hade rai sosai, tun bayan haduwarsu
ranan da Zahrah ta xo gidan basu sake haduwa ba, Zahrah na tsaye daga bakin kofa
tace "Allah ya kara lafiya" Humainah ta mayar mata da Amin ba tare da ta kalli inda
take ba, Hajja tace "Kin san kowa da irin nasa laulayin, ita masifa ya daura
mata... Mu je kawai" kallonta Zahrah ta kuma yi jin abinda Hajja tace sai kuma ta
dauke kai ta fita. El-ameen ya jima tare da mai martaba bayan sun isa bauchi, ko da
ya fito airport ya nufa don yana da aiki. Bayan sati biyu Junaid ya dawo daga aiki
da yamma suka shigo gida kusan tare da El-ameen dake motarsa shi ma, El-ameen bai
wani yi parking ba ya fito yana kallon motar junaid da ya nufi parking space,
junaid ya fito El-ameen ya karasa kusa da shi yana kallonsa ganin kamar ba shi ba,
can dai yace "Abba na ciki kuwa Captain" junaid yace "Ban sani ba nima, any
problem" El-ameen yace "Then let me check" bin sa da kallo junaid yayi kafin ya
nufi n bangaren Mumy ya gaisheta, ya tafi nasa part din. Bakwai saura junaid ya
fito don xuwa masallaci dai dai lokacin da Abba ya fito tare da El-ameen, kallon
mamaki junaid ke masa don bai san yana nan har lokacin ba, tunanin abinda xai kawo
sa gun Abba har ya dade haka ya dinga yi amma ya kasa gano komai, ya dai nufi gun
Abba ya gaida sa daga haka suka nufi masallaci gaba daya. Ko da suka dawo daga
masallaci El-ameen sallama kawai yayi ma Abba ya shiga motarsa ya bar gidan, kasa
daurewa junaid yayi bayan isha ya dau makullin motarsa ya tafi can gidan El-ameen,
Hafsat ce ta bude kofar ganinsa tace "Sannu da xuwa captain, you came to our home
today" murmushi yayi yace "Lallai kam, yana ciki?" Tace "Ehh yana ciki bismillah"
hanya ta basa ya karasa xai xauna parlor tace "Yana sama ae" yace "Yi masa magana
pls" tace "Study room dinsa fa yake" mikewa yayi yace "Ohk" daga haka ya haura
sama, xaune ya samesa yana duba wani littafi gaba daya hankalinsa na kai, wanda
hakan yasa bai dago ba don a tunaninsa Hafsat ce ta shigo, karasawa Junaid yayi,
El-ameen ya dago da sauri jin turarensa, kallon mamaki yayi masa sai dai bai ce
komai ba, Junaid ya xauna yace "Me ya kawo ka gidanmu daxu?" El-ameen ya buda ido
yace "Yeah, Nasan ba don Allah ka taso ka taho gidana ba," sai kuma yayi murmushi
yana girgixa Kai yace "it's very unfortunate Zahrah ta bata frndship dinmu, a da
sati baya karewa ba tare da ka xo inda nake sau uku ba ko sau hudu, sauran kwanaki
kuma ni xan je but yanxu....." Junaid ya d'an yi murmushi yace "Ae kai ma ba xuwa
kake ba" El-ameen bae tanka sa ba ya ci gaba da duba littafin gabansa, junaid yace
"I asked you a question..." El-ameen yace "Nothing, naje ne ya shigar min gaba gun
neman auren Zahrah, as in shine waliyyina" Junaid da ya ji wani abu ya tsaya masa a
xuciya ya dake yace "Why him?" El-ameen yace "Coz dad dina yace bbu ruwansa da
batun auren...." Junaid ya hadiye wani abu da kyar yace "and what did he said about
it?" El-ameen ya matsar da littafin gabansa yace "Yace babu damuwa idan har hakan
baxae bata ma dad dina rai ba.. Nd I told him shi ma ya turo ni gunsa" mikewa
junaid yayi kansa na juyawa ya kalli agogon hannunsa yace "Ohk, all good, it's
getting late xan koma" El-ameen yace "Toh baka tambaye ni yaushe ne daurin auren
ba?" Junaid yaji gabansa yayi mugun faduwa ya koma ya xauna xuciyarsa na bugawa
sosai yace "When?" El-ameen yace "This Friday!" Kasa cewa komai Junaid yayi, lokaci
daya jikinsa yayi sanyi, bude kofa aka yi Hafsat ta shigo ta dire masu babban tray
mai dauke da warmers din abinci ta fita sai ga ta ta dawo da wani tray mai dauke da
ruwa da drinks sai cup ta fita, El-ameen yace "Mu ci abinci frnd..." Junaid yace
"No! No, am ohk" El-ameen yace "Alryt then, you wait muyi shawaran abubuwan da xa
ayi na bikin it's just 4 dayz left" Kallonsa kawai Junaid yake, El-ameen ya dau
table water daya ya bude ya sha kadan yace "Yeah, though sarkin yace baya bukatan
komai namu, amma dai mu ma mun san abubuwan da ya kamata, so ya kaga ya kamata mu
yi" mikewa junaid yayi yace "Look, ka kira Faisal or Aliyu am not good at that"
daga haka ya fice daga parlon, El-ameen ya bi sa da kallo yana murmushi.

*Haske Writers association*馃挕

Ayi ta hakuri da ni a haka har mu kare pls.

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

84.....
Washegari ba karamin farin ciki junaid yayi ba ta dalilin lagos da xasu wani aiki
da wasu daga cikin colleagues dinsa, kwana biyar xa su yi a can, yana dawowa da
yamma ya jima part dinsa kwance kafin ya mike ya tafi gun Mumy tana kitchen ya
sameta ya jingina jikin kofa bayan ya gaisheta yace "Mumy gobe xan je lagos
aiki..." Kallonsa tayi tace "lagos?" Ya gyada mata kai yace "Ehh amma ba ni kadai
ba, kwana biyar xuwa sati daya xa muyi" Mumy tace "Toh Allah ya tsare, ka fadi ma
Abban ku?" Girgixa kai yayi yace "Anjima xan gaya masa" Tace "Toh shikenan, gobe
Hajja ma xata dawo" yace "Ohk, ni da safe xan tafi ba lallai mu hadu ba" juyawa
yayi ya fita daga kitchen din, har ya nufi kofa sai kuma ya dawo ya shiga dakin su
fatima. Kasa bacci yayi daren ranan, sarai yasan me ke damun xuciyarsa amma ya
dinga kokarin karyata hakan, tsaki ya ja daga karshe ya mike ya shiga toilet ya
dauro alwala ya fita. Da safe ya gama shirinsa tsaf, kananun kaya kawai ya diba sai
uniforms dinsa, ya nufi part din Mumy yayi mata sallama, tayi masa addu'ar Allah ya
kai su lafiya ya tsare su, ya mike ya shiga bedroom din da Humainah take, bai fi 7
minutes ba ya fito ya dau jakarsa ya fita daga parlon, khadija ce ta rakasa har
bakin gate bayan ta karbi jakarsa don driver din Abba ne xai tafi da shi gun aiki
daga can sun wuce lagos, karban jakar yayi yana kallonta kmr baxae ce komai ba sai
kuma yace "Su Hajiya fa?" Shiru tayi tana kallonsa, ya bude mota yace "Alryt, sai
mun yi waya lil sis bye!" D'aga masa hannu tayi har motar ya bar layin. Da yamma
junaid suka sauka lagos, Apartment din abokinsa Capt kabir ya sauka a barrack
dinsu, wanka kawai yayi ya sauya uniform din jikinsa ya dau makullin motar kabir
bbu yanda kabir bai yi da shi ya ci abinci ba ya ki, ya fita da mota duk da bbu
takamaiman inda za shi, damuwa ne kawai yayi masa yawa, bai dawo gidan ba sai bayan
magrib, Kabir dake xaune parlor da wasu abokansa biyu ya bisa da kallo don hannu
kawai ya daga masu ya shiga bedroom, mikewa Kabir yayi ya bi bayansa, kwance ya
samesa dakin yana kallonsa yace "Are you okay junaid?" Junaid yace "Yeah, just
stress sai slight headache" kahir yace "Alryt Allah ya sauke, ga abinci na siyo ka
ci ka sha Magani" junaid yace "Na ci abinci, drugs kuma ba sai na sha ba, idan nayi
bacci xai min sauki" kabir yace "Toh shkkn" daga haka ya juya ya fita. Washegari da
ciwon kai sosai junaid ya tashi, ko Kabir bai bari ya kula da halin da yake ciki
ba, ya shirya cikin uniform dinsa ya daure ya sha tea kadan, Kabir yace "Ga
makullin bike, don in ka fita da mota yanxu da matsala" junaid ya karbi makullin
yace "No hold up No Lagos" dariya Kabir yayi yace "Exactly!" Junaid yace "Baka duty
da safe ne?" Kabir yace "Yea, sai evening" Junaid yayi murmushi yace "Jin dadi"
daga haka ya nufi kofa ya fita. Gaba daya a harbor ranan junaid was just
absentminded, ga ciwon kansa sai karuwa yake duk ya kagu karfe hudu yayi ya gansa a
gida. Biyar saura ya isa gida ko uniform bai cire ba ya haye gado dai dai lokacin
da wayarsa ya dau ruri, jawo wayar yayi da kyar yana kallon screen din da kamar ya
ajiye sai kuma ya daga ya kai kunne, El-ameen yace "Ashe kana lag!" Junaid yace
"Yeah...." El-ameen yace "Shine bbu notice, beside you know it's not possible
bikina ace baka nan, haka ka kin wnn wlkcnin lokacin da aka aura min Hafsat....."
Katse sa junaid yayi yace "I will be back on Friday!" El-ameen yace "Uhm, now you
are talking, har na kai mana dinki...." Lumshe ido junaid yayi trying to be calm
yace "Alryt, but am busy yanxu, I want to hang up...." El-ameen yace "Ohk.... Xan
kira anjima in fadi maka decision din da muka yanke da su Aliyu, i.e how everything
is gonna be" Gyada masa kai kawai Junaid ya iya yi ya katse kiran ya jefar da wayar
nan kan gado yayi rub da ciki ya runtse ido. A kwana biyun da junaid yayi a Lagos
kowa ya gansa yasan ba karamin abu bane ke damunsa, duk ya rame ga shi ko abinci
bai iya ci, bbu yanda Kabir bai yi da shi ya fadi me ke damunsa ba sai dai yace
zazzabi ne, ranan laraba ikon Allah kadai ya maidosa gida daga gun aiki, Kabir dake
ta shirin fita aiki ya bi sa da kallo har ya shiga daki sannan ya bisa yace "Kaga
kar ma ka fara kwanciya ka taso mu tafi asibiti or I call ur mum in gaya mata"
junaid bai yi masa musu ba don shi daya yasan yanda yake ji a lokacin, Kabir bai
bari ya cire uniform ba suka fita xuwa NNRH dake nan barrack din, bayan sun ga
likita aka yi admitting dinsa nan take, malt kawai ya iya sha a cikin abubuwan da
Kabir ya siyo masa bayan an sa masa ruwa, ya kalli Kabir dake tsaye yana kallonsa
yace "Don't worry frnd ka tafi aiki I will be ohk, bacci ma xan yi yanxu" sai da
Kabir ya ga baccin xai yi da gaske sannan ya dau makullinsa ya fita. Washegari da
safe junaid na bacci Kabir ya shigo ward din, yaga sabon ruwa ne ma aka sa masa,
xaunawa yayi gefensa dai dai lokacin da wayar Junaid dake kan gadon yayi haske ta
dalilin kiransa da aka yi don a cylnt wayar yake, My best ya gani jikin screen, da
kamar baxae daga ba sai kuma ya dauka don yasan baxai wuce abokin da ya san sa da
shi ba wato El-ameen, El-ameen na jin muryar Kabir bayan sun gaisa yace "Ahmad din
fa?" Kabir yace "Ba ya jin dadi tun jiya, har ma anyi admitting dinsa clinic" El-
ameen yace "Subhanallah! Ya jikin nasa yanxu?" Kabir yace "Alhmdllh, he's sleeping"
El-ameen yace "Toh Allah ya sauwake, but a barrack din ku ya sauka?" Kabir yace
"Yeah nan ya sauka" El-ameen yace "Alryt xan kira later" daga haka ya katse wayar,
sai a sannan ya ga uban missed calls din dake wayar, ajiyewa yayi ya koma kujera ya
xauna. Karfe uku junaid na xaune har lokacin da ruwa a hannunsa, shi ji yayi kamar
ma kara masa ciwon ake, gashi ya kasa cin komai sai ruwa da yake sha, kabir da bai
jima da shigowa ba yace "Ka dai kira gun aiki ka fadi dalilin absence dinka" kai
kawai junaid ya iya daga masa, Kabir yace "Toh meyasa baka son a fadi ma su Mumy?"
Shiru junaid yayi masa idonsa lumshe, kabir ya dau wayar Junaid din ta dalilin
kiran da ya shigo, El-ameen ne ke kira ya kalli Junaid yace "Xa ka iya daukan
kiran, it's ur frnd?" Junaid ya bude ido yana kallon wayar girgixa masa kai yayi,
hakan yasa shi ya daga, bayan sun gaisa El-ameen yace "Wai jikin nasa har yanxu?"
Kabir yace "Yea, muna hospital dai" El-ameen yace "Alryt! Clinic din cikin barracks
din?" Kabir yace "Yeah Nnrh!" El-ameen yace "Toh Ga shi kayi ma security din ku na
gate magana, I am at the gate" da mamaki Kabir yace "Kana Lagos ne dama?" El-ameen
yace "Nop, I just landed" daga haka ya mika wayar, Kabir yayi masu magana sannan
El-ameen ya shiga barrack din. Cikin mintunan da basu wuce 7 ba El-ameen ya isa
hospital din snn ya kira Kabir ya fito ya shiga da shi, rungume hannu El-ameen yayi
yana kallon Junaid can yace "Sannu, were you sick ne dama" Junaid ya kallesa yace
"Am feeling much better yanxu" El-ameen yace "To ina drugs din da suka baka?" Kabir
ne ya dauka ya mika masa yayi dariya yace "Kaddai ka xo ka nuna masu kai likita ne
a nan fah, Kaga kai ba uniform gare ka ba" murmushi El-ameen yayi yace "Niii! Ae ko
xan yi magana sai mun fita" dariya sosai kabir yayi, El-ameen ya ja kujera ya xauna
yana kare ma ward din kallo, Junaid yace "Ya hanya!" Mamaki ne ya kama El-ameen ya
kallesa yace "Ohh Alhmdllh! Yaushe xa su sallameka?" Girgixa kai yayi yace bai sani
ba, El-ameen bai kuma cewa komai ba, ana yin La'asar Kabir ya bar clinic din don
xuwa gun aiki, Washegari Friday da safe aka sallamesu daga hospital bayan ya
tabbatar masu he's very okay, ko kadan El-ameen bai gaya masa ranan ne daurin aure
ba duk da yasan ya sani, karfe tara ya shirya ya tafi can gun da suka xo yin aiki
don shaida masu ranan xai koma kt, goma saura ya dawo ya tadda El-ameen kadai
parlor yana waya, bedroom ya shiga ya hada kayansa ya fito, El-ameen da har ya gama
wayar yace "Are we good to go?" Kai kawai Junaid ya gyada masa, yace "Toh baxa kuyi
sallama da kabir din ba?" Junaid yace "mun yi waya da shi ya tafi ikj ba lallai xa
mu hadu ba...." El-ameen yace "Ohk" daga haka ya mike ya karba jakar Junaid suka
fita, junaid ya kulle masa apartment din ya ba neighbor dinsa key din, bike suka
dauka xuwa airport road, bayan sun isa suka dau cab xuwa cikin airport din, El-
ameen dai na ta lura da shi don ko ba a fadi masa ba yasan daurewa kawai yake, sai
da suka hau jirgi Junaid ya dake yana kallonsa yace "Thought yau ne daurin auren?"
El-ameen yace "Yeah! After juma'at prayer, xa ma ka iya xuwa kuwa" junaid yace
"No!" Suna isa kt Junaid ya nufi gida shi ma El-ameen ya nufi nasa gidan. Part din
Mumy junaid ya shiga ganin bbu kowa parlor sai tv dake kunne ya shiga dakin Mumy,
xaune ya ganta a daki ya karaso ya durkusa ya gaisheta, bbu yabo bbu fallasa ta
amsa tace "Ahmad ashe kai ka haifi kanka ban sani ba?" Kallonta yayi da mamaki jin
abinda tace, tace "Leave immediately" kasa daina kallonta yayi lokaci daya yana
tunanin me kuma yayi, da kyar yace "Mumy wani abun ya faru ne kuma?" Wani kallo ta
watsa masa tace "Ka fita nace" mikewa yayi da kyar ya fita daga dakin, bedroom din
su Humainah ya shiga, kwance take tana ganinsa ta mike xaune, ya karasa gadon jiki
ba kwari ta mike tsaye, xai yi magana ta dakatar da shi tace "Ya Ahmad ni dai ka
sake ni gaba daya bana auren kuma, idan kuma ba haka ba xan xubar da cikin nn wllh"
kallonta kawai yake da manyan idonsa, can ya tabe baki ya juya ya fita daga dakin,
ta fashe da kuka sosai ta sulale nan kasa ta hade kanta da gwiwa, tafiya kawai
junaid yake yana son gane ma'anar abinda Mumy ta fadi masa, Muryar Hajja ne ya
dakatar da shi jin irin kiran da take masa ba kakkautawa ya juya yana kallonta da
mamaki, karasowa tayi fuskar nan nata a murtuke tace "Wato ai gwara kwadayina a kan
taka Ahmad, tsabar naka kwadayin ya shahara 'yar gaba daya kake son aurewa kayi ma
jikata kishiya, kishiyar ma jinin sarauta, dama ga Ka da taka sarautan da ka
lak'a6a ma kanka tun ba yau ba, ita kuma ta xo da ta gidansu ku taru ku sa ma
jikata hawan jini ta mutu in shiga
uku, to ubanka yayi kadan bare kai, ban yarda da auren nan ba kuma baxa ayi ba, su
rike kujerun jirginsu can baxa a je ba...."

*Haske writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

85.....

Kallon Hajja kawai junaid yake don ya kasa fahimtar inda xancenta ya dosa duk ta
cikasa da hayaniyar dake baraxanar haddasa masa ciwon kai, Muryar kawunsa yaji na
kiransa ya juya yana kallonsa yayi masa alama da ya xo, part din Abbansa ya nufa ta
bi sa tana ci gaba da xaxxaga masa bala'i shi dai bai tanka ba, bai same su parlor
ba ya karasa har bedroom, hajja tayi tsaye nn parlon tana ta ci gaba da bala'i ta
inda take shiga ba ta nn take fita, xaune ya samu Abbansa da frnds dinsa biyu sai
kawunsa, Kawunsa wato Abban Humainah ne yace "Ahmad!" Ya dago a hankali yana
dubansa amma ya kasa cewa komai. Kawun yace "Na'am mahaifin yarinyar nan ya bukaci
da ka aureta, don me da ku ka dawo baka sanar ma iyayenka komai ba sai abokin ka ne
ke fadi ma Abbanka few dayz back....." Kasa cewa komai Junaid yayi sai dai kansa
yayi mugun daurewa, Abbansa dai sai kallonsa yake, Alhaji umar yace "Kayi shiru
Ahmad, gaskiya ne Kai mijin mace hudu ne bbu wanda xai hanaka kara aure tunda kana
da halin yin hakan sai dai kawai Kayi kokarin xamo me adalci tsakaninsu, amma meye
na boye ma iyayenka, da nufin ka yau sai ka taho kace a tashi aje maka daurin aure,
Babanka yayi ta xuba maka ido amma shiru baka ce masa komai ba...." Alhaji Habib
yayi dariya yace "Kar fa ku ga laifinsa, that's what it takes to be a 1st child,
wauta ne kawai irin tasa" Kawunsa yayi murmushi yace "Gaskiya ne, to Allah ya sanya
alkhairi Ahmad, ae kai din mijin mata hudu ne, Allah ya baka ikon adalci" ae sai
kawai Junaid ya sunkuyar da kai ya ma rasa gane wani yanayin yake ciki, yanxu ana
nufin shi xa'a aura ma Zahrah, amma ai basu yi haka da kowa ba, how is this? No ya
ma san kawai basu fahimce xancen bane amma da abokin sa xa ayi auren, Muryar Abokin
Abbansa yaji yana ce masa ya tashi ya je, dagowa yayi da sauri cikin sanyayyen
murya yace "Kuyi hakuri Abba, ni....." Kasa ci gaba yyi don bai ma san abinda xai
ce ba, cewa xai yi shi bai sani ba ko kuwa ce musu xai yi ba fa da shi xa a daura
auren ba, Abban Humainah yace "Tashi kaje, Allah yayi maka albarka... Ya baka ikon
adalci tsakaninsu" mikewa yayi da kyar ya fita daga dakin cike da confusion to yaga
ae ba fa da shi xa ayi auren ba, how is all this???? Ko kallon Hajja da ta cika
parlor da muryarta bai yi ba ya fice daga parlon, ya tafi part dinsa ya dau
makullin mota ya fito ya dau motarsa sai gidan El-ameen, Hafsat dake ta mopping din
Balcony ta gaishesa da fara'a tace masa yana sama a study room, yana haurawa sama
ya bude kofar dakin, Xaune ya samesa idonsa lumshe ya karasa gabansa yana kallonsa,
bude ido El-ameen yayi ya gyara xama ganinsa yace "Yahh, xaka iya xuwa kuwa?"
Junaid yace "Ahmad I don't get what my parent are telling!" El-ameen ya shafa kansa
yana murmushi yace "Wai na auren ku da Zahrah?" Buda ido junaid yayi yace "Aurena
da Zahrah kuma?" El-ameen yace "Yeah" xaunawa junaid yayi jin ya kasa ci gaba da
tsayuwar yace "You are getting me confuse, wace Zahran...." Murmushi El-ameen ya
kuma yi yace "To ya na iya maka frnd? Ban son wani abu ya sameka mu rasa ka a kan
Zahrah, ni na nema maka aurenta, isn't it nyc..... Nasan yea you are in love with
her..... Son da kake mata ya take nawa so I have no option then to let go, ita ma
na ga tana son ka sosai shi yasa nayi haka from the beginning, nasan dai yanxu no
more love sickness nd the rest, just that kar ku cuci Humainah....." Tuni idon
Junaid ya kada ya kasa ce masa komai yana kallonsa, El-ameen ya dunkule hannunsa ya
kamo na Junaid ya kai masa knuckle yana murmushi yace "Chop knuckle frnd" Ana
saukowa juma'a aka daure auren Capt Ahmad Junaid da Princess Zahrah El-ameen
Moddibo a kan sadaki 1m wanda mahaifinta ne ya bayar, daurin auren nan ya samu
halartan dubban mutane da 'yan gidan masarautu da dama daga ko ina na states din
Kasar duk ta dalilin Sarki El-ameen Moddibo, masarautan bauchi ya xamo bbu masaka
tsinke tsabar jama'a, kusan duk manyan da suka xo daurin auren mamakin mijin Zahrah
suka dinga yi ganin shi ba basarake ba, shi ba yarima ba, shi ba jinin sarauta ba,
shi ba kowa ba just a mere military personnel with CLASS, ba karamin alfahari sarki
El-ameen yake da junaid ba da ya xamo sirkinsa, Junaid ya gaisa da mutane da dama
sunfi dari kowa son ganinsa yake ta dalilin yanda sirkinsa wato sarki ke koda sa
gaban abokansa sarakai da manyan kasa, baka taba fadin yanayin da Junaid yake ciki
a lkcn sai dai kawai kaga yayi murmushi wani lokacin wanda iyakarsa lips, gam yake
rike da hannun El-ameen dake gefensa don bai son su rabu, Su Abba basu suka bar
bauchi ba sai kusan magrib don ba karamin walima aka shirya ba, xuwa bayan isha
masarautan bauchi yayi tsit baka taba cewa anyi komai ciki don tuni aka tsaftace ko
ina, Junaid dake xaune daki na musamman da aka basu shi da El-ameen, Aliyu, faisal
da wasu frnds dinsa biyu, ya rike kansa har lokacin don ya kasa gaskata da shi fa
aka daura auren nan yau, El-ameen ya dawo gefensa yace "Toh programs kusan goma ne
fa gabanmu Mr man!" Dagowa yayi da sauri yana kallonsa, El-ameen yayi dariya yace
"Atoh, gwara ka bar rike kai this is just the beginning, Abdul yace ka shirya xaka
gun Zahrah, wato xaka je ganin amaryar ka....." Da 'yar dariya El-ameen ya kare
xancen daga haka ya shiga bathroom don watsa ruwa, Aliyu dake ta danna waya yace
"Duk karya ce!" Faisal ya kallesa ya danne dariyarsa yace "Meye karyar?" Aliyu yace
"Wannan ji da kan da miskilancin wani mana" dariya sosai Faisal da sauran frnds din
Captain suka dinga yi, shi dai Junaid bai tanka kowa ba, El-ameen na fitowa ya
shiga toilet din shima, wani kaya irin ta sarauta lafiyayye El-ameen ya ajiye masa
gefen gado bayan ya fito yace "Wai kayan da xaka sa kenan suka ce" Junaid da har
lokacin bai iya hada ido da abokin nasa ya shiga jujjuya kayan, can ya mike ya tabe
baki yace "No, bai yi min ba" dariya sosai El-ameen yayi su Aliyu na tayasa wanda
hakan yayi mugun kona ran Junaid, Aliyu yace "Ae ko ka ki malam dole haka xaka sa,
coz that's the rule tunda gidan sarauta kayi auren" sai a snn Junaid ya kalli El-
ameen ya hade rai sosai yace "Nooo, bbu wanda xae dinga kafa min rule, snn bbu
wanda ya isa yyi forcing dina...." Aliyu ya fashe da dariya yace "Duk karya ce wnn"
El-ameen da ya kasa daina dariya yace "See you. Ka dinga bin rules kenan har sai an
kai maka matar ka can gidan ka" Junaid bai tanka sa ba xai dau kayansa ya sa El-
ameen ya kwace kayan yace "Kasan Allah kar fa ka dinga mana taurin kai nan" faisal
yace "Look Capt you just have to obey before complaining as a good militant, idan
ka bar nan naga bbu wanda xai bi ka yace ga yanda xaka yi koh?" Daukan kayan Junaid
yayi ya fita parlor don sa wa, Aliyu ya fashe da dariya yace "Wato abun sai da
lallaba," ko da Junaid ya dawo dakin duk kallonsa suka tsaya yi don sak yarima ya
dawo, yayi kyau ba kadan ba, Aliyu yace "Uhm yarima junaid, ka hadu" junaid bai
tanka sa ba, misalin karfe tara da wani abu aka doka sallama can parlor El-ameen ya
fita, wata yar dattijuwa ce tsaye ta duka har kasa ta gaishesa tace "Ance in yi ma
ango iso har gun Gimbiya Zahrah" El-ameen ya juya ya koma daki yace "Toh an xo
daukar ka Capt, if you like go nd misbehave mu dai muna nan" sae da junaid ya ga
dama sannan ya mike ya fita, dattijuwar na gaba yana biye da ita a baya, haka kawai
yaji gabansa ke faduwa, tafiya me nisa suka yi har suka iso wani babban kofa ta
bude kofar suka shiga wani parlor me girman gaske xama yayi parlon ita kuma ta
karasa ta bude wani kofa ta shiga ciki, ba a dau lokaci ba ta fito ta risina tace
"xaka iya shiga ranka shi dade" mikewa yayi ya nufi dakin har lokacin gabansa bai
bar faduwa ba, yana shiga dakin wani sanyayyen kamshi ya doki hancinsa bai san
lokacin da ya rufe kofar ba ya juyo ya sauke idonsa kanta.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

86___87
Ya kusa minti biyar tsaye bai karasa cikin dakin ba, tun da ya kalleta sau daya bai
sake kallon inda take ba, xaune take kan hadadden Royal bed din dake dakin ta daura
har kafafuwanta kan gadon, har wani daukar ido take tayi wani kyau na musamman,
hannunta da ya sha hyena na rike da waya tana ta danne danne, ko sau daya bata
kalli inda yake ba, can dai ya karasa gadon cikin takunsa na kasaita ya xauna ya
fiddo da tasa wayar yana dannawa, ajiye wayar hannunta tayi ta mike ta nufi gaban
mirror, bin ta da ido yayi bayan ta wuce sa, lokaci daya gabansa ya shiga bugawa,
wani ubansun fitted gown ne jikinta gold colour yana jan kasa, kasa daina kallonta
yayi har sai da yaga xata juyo sannan ya dauke kansa, wucesa ta kuma yi hannunta
rike da laptop, ta koma kan gadon ta xauna ta kunna laptop din, tabe baki yayi lkci
daya yayi d'an murmushi yace "Za ki iya da halina" kallonsa tayi a karo na farko
tace "Nima xaka iya da nawa halin?" D'ago kai yayi ya kalleta ta gyada masa kai
tace "Yeah!" Murmushi yayi yace "Ke har kina da halin da baxan iya da shi ba"
murmushi ita ma tayi tace "Toh nima baka da halin da baxan iya da shi ba...." Gyada
kai yayi har lokacin murmushi dauke fuskarsa sai dai bai ce komai ba, sun kusa
minti sha biyar xaune bbu wanda yace komai, ita dai sai danna laptop take, satan
kallonta yayi dai dai lkcn da ita ma ta dago suka hada ido, ji yyi dama hakan bai
faru ba, ya wayance da sauri yace "Amm, lastly xa ki iya da halin matata" jingina
tayi jikin gadon ta matsar da laptop din gabanta ta tabe baki tace "Bata da halin
da xai daga min hankali, sae ma dai ita ce baxata iya da nawa halin ba" mikewa tayi
ta hade rai lokaci daya tace "Kar ka kaga ka sameni kusan a banxa ka dauke ni for
granted, ka xo kana gaya min magana yanda ka ga dama, you know who I am, kuma ni ba
don ina sonka na yrda da auren ka ba sai don kawai in maka halaccin abinda ka min,
in kuma yi ma Abbana biyayya, banda haka nafi class din ka, snn ni ba gidanka xan
xauna da matar ka ba, Abbana zai siya min gidan da xan xauna, nafi karfin xama tare
da ku....." Tunda ta fara magana yake kallonta da mamaki, furucinta na karshe yasa
ya mike yana mata wani kallo yace "Who are you? A princess? Just that????" Dariya
yayi wanda hakan ya kara fito da ainahin kyansa, ta tsaya kallonsa ko kiftawa bbu,
ashe yana dariya dai, ya shafa kansa yana kallonta daga sama har kasa murmushi
dauke a lips dinsa yace "Ba ki da gun xama da ya wuce gidana tare da matata, idan
an siya maki gidan sai ki ajiye shi aside kiyi xaman auren da ya kai ki kt a
gidana!" Kallonsa take tana huci tace "Baxan xauna gidan ka ba, nafi karfin xama
tare da matar ka, my dad will get me a house......" D'aga kafada yayi yace "Toh xan
ga ko kece mijin...." Shiru yayi sai kuma ya juya yana mamakin kansa anya ma tunda
yake ya taba tsayawa yana exchanging words da namiji dan uwansa bare mace, abinda
bai taba ba kenan duk tsawon rayuwarsa, juyawa ya kuma yi yana kallonta, tabe baki
tayi hade da murguda baki tace "Sai mu gani ai ko ni xan xauna gidan ka" bai tanka
ta ba ya koma ya xauna cike da jin haushin kansa kulatan da yyi tun farko ya kalli
makeken agogon dake manne bangon dakin ya ga goma saura yan mintuna dai dai lokacin
da dattijuwar daxu ta rafka sallama can parlor, mikewa yayi ya nufi kofa ya fita,
wnn karan su biyu ne, suka duka har kasa tana masa sannu da fitowa, kai kawai ya
gyada masu ya fice daga parlon, ko da ya koma inda aka saukesu bai ko kalli su El-
ameen da Aliyu dake xolayarsa ba ya shige bedroom. A kwanaki ukun da suka gabata ba
karamin Buduri aka sha a masarautan bauchi ba sai ka rantse baxa a mutu ba, safe,
rana, dare sae an samu wani program da aka ce xa ayi kuma duk ba na wasa ba, kudi
kam sun yi kuka ba kadan ba wanda hakan xai tabbatar maka da cewa ba karamar yar
gata bace Zahrah, abun mamaki ya dinga ba junaid don ko kadan bbu abinda ya burgesa
a shagalullukan da aka yi duk ya kagu a kyalesa ya bar garin, sai dai fa shi kansa
yasan jin sa yake daban idan ya tuna Jasmine matarsa ce ynxu. Ranan talata aka yi
program din karshe da suka kira shi da farewell princess Zahrah, shi dai Junaid na
xaune gun ne idonsa a kan wayarsa da yake ta dannawa, yawan ci gun duk 'ya 'yan
sarakai ne, princesses din sun gama yrda cewa mijin Zahrah duk da he's not from
royal home is just classic, cute and very handsome bbu warce xata ce taga dariyarsa
tun fara events har xuwa ranan sai dai murmushi da iyakarsa lips, da ganinsa kasan
baya son hayaniya, har wani farin ciki Zahrah take idan yace baxai xo gun event ba
tsabar haushin kallon da taga mata ke masa, don a duk events din da aka yi guda
uku kadai ya yrda da kyar aka yi da shi sai wnn na karshen, sai ka rantse El-ameen
ne angon don yawanci shi kedaukan post din Junaid, duk da Junaid waya kawae yake
dannawa amma hankalinsa gaba daya na kan Zahrah as in kyan da tayi na musamman ne
ranan, sae wani sheki take cikin lafiyayyen sliver gown me adon stones din dake
jikinta, satan kallonta kawai yake wanda duk El-ameen na lura da shi yana dariya,
sai kusan magrib aka tashi taron. Bayan isha mai martaba yasa aka kira masa Junaid,
Junaid ya nemi gu ya xauna a babban parlon sarkin kansa a kasa, mai martaba yace
"Dama ina son sanar da kai nasa a nema min gida a can katsina da Zahrah xata xauna,
hakan ya maka ko" Junaid ya d'ago yana kallonsa, duk da yanda ransa ya bace bai
nuna ba, cike da ladabi yace "Ae ina da nawa gidan ranka shi dade" Sarki yace "Eh
nasan da haka Ahmad, amma ina ga hakan xae fi gwara tayi xamanta a nata gidan....."
Mamaki ne ya cika junaid, yayi shiru na kusan minti daya kafin yace "Amma bana son
rabasu da 'yar uwarta ranka shi dade.... Nafi son su xauna tare" sarki yace "A'a
ina jin xaman su daban daban xai fi...." Junaid ya kuma kallonsa yana kokarin danne
bacin ransa yace "I think it's not proper ita kadai ta xauna gida...." Mai martaba
yace "Hakan yasa xan tura mata bayin da za su xauna da ita, in kuma hadasu da
jakadu biyu" Junaid bai kuma cewa komai ba, sarki yace "Hope it's ohk...." Dakewa
junaid yayi yace "Toh xan so ace gidana aka fara kai ta kafin ta tare can gidan"
Sarki ya d'an yi shiru sai kuma yace "Ohk, but baxata wuce kwana biyu gidan naka
ba" Junaid ya gyada masa kai yace "In'sha Allah" Sarki yace "Toh bbu damuwa" junaid
bai jima parlon ba ya mike ya fice bayan sarkin ya basa shawarwari masu ma'ana,
takaici ya ishesa lkci daya maganan Aliyu ya fado masa da yake cewa ae an fara kafa
masa rule kenan tunda 'yar gidan sarauta ya aura, wani tsaki ya ja a xuciyarsa yace
ba shi Ahmad din ba knn. Washegari misalin sha daya suka dau hanyar kt, sai ka
rantse kace maida masauratan bauchi xa ayi katsina gaba dayanta Tsabar tawagar da
aka yi don kai Zahrah gidan mijinta, Kai da gani kasan Gimbiya xa a kai daki,
direct gida Junaid ya nufa don bai ma son yaje can gidan kansa ya fashe, bbu kowa
gidan sai Hajja, Humainah da Mumy sai wasu frnds din Mumy wa enda basu je can
tarban amarya ba, duk sisters din Mumy na can gidan da su fatima, bbu wani wanda ya
amsa gaisuwarsa da mutunci ya nufi bangaren sa kawae, Hajja ce ta bisa har bedroom
yana kokarin cire kayan jikinsa tace "Wato munafukin sarkin nn dan ya toshe bakina
shi ne har da wani yi ma Humainah kayan daki da lefe irin ta yar sa koh, to yyi a
banxa don ni bbu ruwana da wnn, kuma idan baka yi hankali ba sai nasa an ma uwarka
kishiya kai ma irin yanda ka yi ma jikata," Murmushi junaid yayi yace "Toh ai ba
haramun bane" daga haka ya shige toilet ya bar ta nn tsaye. Sai kusan yamma El-
ameen ya zo gidan da Aliyu. Karfe shidda da wani abu Abba yasa a kira masa
Humainah, tana isa parlon ta nemi jikin kujera ta xauna daga kasa, kallonta kawai
Abba yake cike da tausayinta, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Abba ga ni" ya
nisa yace "Kina jina Daughter" kai kawai ta gyada masa yace "Kiyi hakuri kin ji,
matukar ina raye baxan taba bari Ahmad ya kuma walakanta ki ba, ki dauka auren ki
da shi kaddara ce don biyayya kika mana, promise me ba ke xaki xamo tsilar ko wani
tashin hankali da xae faru a gidan auren ku ba, you promise me xa ki xamo mai kauda
kai a komai...." Hawaye ne ke sauko mata tace "I promise Abba" maganganu masu
kwantar da hankali Abba ya dinga mata, wayarsa ya dauka daga karshe ya kira Junaid
yace ya samesa parlonsa, ba a dau lokaci ba Junaid ya iso parlon, kallo daya ya
masu bai kuma dago kai ba har ya nemi waje ya xauna daga kasa shi ma, kallon
Humainah Abba yayi yace "Tashi ki je ki shirya ku wuce gida" ba musu ta mike Junaid
ya bi ta da kallo har ta fita, Abba ya juya yana kallonsa yace "In ma kun cuceta
kai da Allah, kuma I assure you baxae bar ku ba, more especially kai, I won't say
anything more than this, tashi ka je" kasa cewa komai Junaid yayi bai kuma iya ya
dago kansa ba, can dai ya mike yace "Nagode Abba" daga haka ya fita daga parlon ya
tafi bangaren sa, bai tarda su El-ameen ba wanda hakan ya tabbatar masa da cewa
wucewa suka yi, ya gama shirinsa ya fito, ya jima tsaye yana jiran fitowar Humainah
ganin bata fito ba ya shiga ciki, bedroom dinsu ya shiga ya sameta xaune kasa ta
hade kai da gwiwa, karasawa yayi dakin ya isa kusa da ita ya durkusa yana kallonta
murya can kasa yace "Humainah!" K'in dago kanta tayi hakan yasa ya dago yana kallon
fuskarta da ya wanke da hawaye, finger dinsa yasa yana share mata hawayen kmr me
rada yace "Am...am sorry wife.... You.... have a special place in my heart!" Dago
idanuwanta da suka rine tayi tana kallonsa, ya sakar mata wani lallausan murmushi
ya lumshe ido ya kai mata light kiss a lips dinta, kasa kallonsa tayi ya mike ya
daga ta ya dau hijab dinta ya mika mata ta karba ta sa, ya dau karamar jakarta yana
rike da hannunta suka fita, dakin Mumy ya nufa da ita, Mumy dake xaune da frnd
dinta tayi masu kallo daya ta dauke kai, durkusawa yayi nan gabanta, Humainah ma ta
durkusa yace "Mumy xa mu tafi" sai a snn ta kalle su tace "Allah ya kiyaye hanya!"
Mikewa yayi suka fita daga dakin Hajiya Karima na masu Addu'ar xaman lafiya, ana
kiraye kirayen Magrib suka isa gida, su sisters din Mumy na gidan har lkcn da wa
enda suka kawo amarya su kusan bakwai, junaid dai na dawowa daga masallaci ya shige
bedroom dinsa ya sa key, sai da 'yan uwan Mumy suka yi magrib a gidan snn suka fara
shirin tafiya, sai kuma da suka tabbatar Humainah ta kwantar da hankalinta snn suka
je suka ma Zahrah da mutanen dake dakinta sallama suka tafi. Humainah na ganin sun
tafi ta fito daga bedroom dinta don ko kadan abinda Abban Zahrah yasa aka mata bai
burgeta ba, wani dakin daban ta bude ta shiga tayi kwanciyarta. Zahrah kam bacci ta
dinga yi a daki don tunda suka isa kt take mitan ciwon kai, yan uwanta nata
harkokin gabansu a makeken dakin, da ganin yanda suke abubuwa kaga jinin sarauta,
bayan Isha junaid ya bude dakinsa ya sauka downstairs, ya jima xaune parlor kafin
ya koma sama ya nufi dakin Humainah ganin bata ciki ya fito ya kwankwasa wanda
Zahrah ke ciki hade da yin sallama, sai da aka amsa masa sannan ya bude kofar ya
shiga, wani arnen kamshi ne ke tashi a dakin, ya duka har kasa ya gaishesu, suka
amsa masa ba duka ba, daga nan kuma ya rasa abinda xai ce, Kanwar mai martaba tace
"Mun yi xaton kamata yayi ace tun da muka iso garin nan ka xo duba mu, ga Fatimar
can tana fama da ciwon kai, ae ba haka ake ba, muna sauka sai ka taho ganin yanda
muka isa" bai dago ba bare ta sa ran amsa, sistern Kilishi tace "Kila haka suke
abubuwansu" mikewa yayi har lokacin bai kalli kowa ba yace "Bari a samo mata
Magani" daga haka ya fita. Bayan kusan minti goma sha biyar ya dawo dakin ya mika
ma Ummi dake dakin maganin ba tare da ya hada ido da kowa ba yace "Amm akwai
bedrooms dake a gyare....." Wata kawar Umma tace "Ae baxa mu bari ta kwana ita daya
bane, nn ya wadatar!" Bai ce komai ba ya juya ya fita. Dakinsa ya shiga ya dau
wayarsa ya shiga kiran El-ameen, bugu uku ya dauka tare da cewa "Angon Zahrah!"
Shiru Junaid ya d'an yi kafin yace "Baxa ka xo ba kenan?" El-ameen yace "In xo in
maka me?" Junaid yace "Just come over plss" El-ameen yace "Alryt, amma sai Hafsat
tayi bacci" Junaid ya d'an bude ido yace "Ohh tsoron ta kake?" Dariya El-ameen yayi
yace "Eh mana, in kuma bata yi ba sai gobe" murmushi Junaid yayi yace "Toh shknn
sha xaman ka tare da Hafsat, goben sai kaxo" El-ameen yace "Ya ma fi komai sauki, a
gaida min amarya" Junaid yace "Uhmm, good nyt!" Daga haka ya katse wayar ya ajiye,
Sha biyu saura ya fita ya shiga dakin Humainah yaga bata nan still, mamaki ne ya
kamasa ya karasa ya tura bathroom nn ba yaga bbu ita, fitowa yayi ya bude dakin
kusa da wnn ya sameta kwance tana bacci, karasawa yayi ya xauna gefen gadon yana
kallonta, can ya daga kafada shi ma yyi kwanciyarsa dakin. Washegari da safe
Humainah ta sauka kitchen don hada breakfast, shi kuma sai da yyi wanka ya shirya
snn ya fito ya shiga dakin da su Zahrah suke, yau ma ba duka suka amsa gaisuwarsa
ba, yayi ficewarsa daga dakin addu'arsa kawai kada su kara ko da awa biyu a gidan,
hakan ko aka yi don ko break din basu yi na kirki ba suka fara shirin tafiya,
Humainah dai faram faram tayi masu ta shiga dakinta, da suka Tashi tafiya dubu dari
uku Junaid ya basu suka ki amsa cike da gadara, bai sake bin ta kansu ba ya maida
kudin sa, Airport ma yace xai kai su suka ce aa, Kanwar Abba ce ta sake jaddada
masa cewa gobe fa xai kai Zahrah can gidanta don gobe bayinta xa su iso, su ma baxa
su iya xama a garin har gobe bane shi yasa xa su koma, toh kawai yace masu duk suka
bar gidan. Bayan tafiyar su da minti talatin ya mike ya haura sama xuwa dakin
Zahrah, a hankali ya tura kofar dakin ya ganta xaune ta hade kai da gwiwa, kallonta
ya tsaya yi can kuma ya karasa ciki ya xauna gefen gado, ita dai bata dago ba, ba
tare da ya kalleta ba yace "Hope xa ki iya fitowa in maki introducing matata"
dagowa tayi da sauri tana kallonsa tace "Nop, just get me out if this house ka kai
ni gidana!" Ta gefen ido ys kalleta yace "Dama kina da gidan da ya wuce wnn?" Tace
"Yess gidan da Abbana ya siya min!" Murmushi yayi yace "Idan ba haka ba ki min me?"
Wani kallo ta watsa masa tace "Idan ba haka ba in kura Abbana in sanar da shi
yanxu" juyawa yayi yana kallonta yaga iPhone din dake gefenta ya mike ya isa
gabanta, ita dai kallonsa kawae take, ya dau wayar yace "Toh na raba ki da rike
waya a gidana!" Mikewa tayi da sauri tace "Ae ba kai ka siya min wayan ba naga
dai...." Wani kallo yake mata kawai ya nufi bathroom binsa da kallo tayi na kusan
minti daya can ta mike da sauri jin kamar ruwa yake tarawa, tsaye ta gansa hannunsa
rike da wayar dayan kuma sim card dinta, juyawa yayi ya kalleta kafin ya jefa wayar
cikin ruwa, sim din kuma ya balla yace "Ba gidana xa a dinga kafa min sharadi ba!"
Wani kara tayi ta karaso da sauri ta fixgosa tace "How dare....." Kasa ci gaba tayi
sbda kallon cikin ido da yayi mata, ta fashe da kuka ta juya da sauri ta fita.
Juyawa yayi shi ma ya fita bai ko kalleta ba ya fice daga dakin sai dai can kasar
xuciyarsa ji yyi kmr an buga masa guduma kukanta dake dukan ears dinsa, kasa shiga
dakinsa yayi, can kawai ya juya ya koma dakin nata.

*Haske Writers association*馃挕

� *Captain Ahmad Junaid*�

_By Khaleesat Haiydar_�

87___88

Durkushe ya ganta a dakin tana kuka, tana ganinsa ta hadiye kukan ta hade rai
sosai, hade rai shi ma yayi yace "Did you just say something?" Mikewa tayi tana
masa wani kallo tace "We the royal blood don't say things twice...." Dariya sosai
ta basa, sai dai ya dake bai yi ba ya Karasa gabanta yana kallonta, ko dar bata
nuna ba duk da a tsorace take ganin yanda fuskarsa ke a daure, wani murmushi yyi
yace "Mind you gidan Capt Ahmad ne nn ba so called royal home din ku ba" tabe baki
tayi ta juya masa baya tace "I don't care where I am, I Still remain who I am..."
kallonta ya shiga yi daga sama har kasa can ya gyada kai yana murmushi ya juya ya
fita. Da rana El-ameen ya xo gidan, suna xaune parlor da Junaid ganin bai ga Zahrah
ba sai Humainah dake kitchen, yace "Captain rowar ganin amaryar ake min" Junaid ya
mike yace "Noo Not at all..." Daga haka ya haura sama ya tura kofar bedroom dinta,
xaune ya sameta tana ganinsa tayi saurin goge hawayen fuskarta ta dauke kai, daga
nn bakin kofa yace "ki fito ku gaisa da El-ameen.... Miss Royal being" wani kallo
ta masa sai kuma ta mike ta dau hijab ta saka tayi ficewarta daga dakin ta bar sa
tsaye, da murmushi fuskarta suka gaisa da El-ameen sai dai bata yrda sun hada ido
ba, El-ameen na ganinta yasan kuka tayi, kallon Junaid da ya tsiri danna waya yyi
sai dai bai ce komai ba, ita kuma ta mike, da har xata koma sama sai kuma ta nufi
kitchen, Humainah dake hada stew ta kalleta ta dauke kai ta dalilin faduwa da
gabanta yayi, Zahrah ta dake tace "Sannu da aiki" Humainah tace "Yauwa, thanks"
kallon kayan lambun dake ajiye kitchen din Zahrah tayi ta karasa ta dauka ta nufi
washing basin ta shiga wanke su, ita dai Humainah bata ce komai ba sai satan
kallonta take, har ta gama wanke su ta dauki chopping board da wuka ta shiga
yankasu, bayan kusan minti goma Zahrah tace "Ki ara min wayar ki" Humainah tace
"Yana daki" har suka gama aikin bbu wanda ya sake cewa komai, ko da Zahrah ta dawo
parlor bata ga El-ameen ba alamar ya wuce, sama ta nufa Junaid ya bi ta da kallo
don yyi mamakin kitchen da ta shiga, can Humainah ma ta fito ta nufi sama ita ma ya
bi ta da ido can ya mike ya bi bayanta, Zahrah na haura wa sama dakin da tasan na
Humainah ne ta bude ta shiga, can kan gado ta ga wayar ta dauka ta xauna gefen
gado, Humainah ta shigo dakin, sosai tayi mamakin ganinta xaune dakin, bata ce
komai ba ta tafi gaban mirror, Bude kofar aka yi Junaid ma ya shigo, still yyi
bakin kofa yana kallon Zahrah, kallo daya tayi masa ta dauke kai, ta mika ma
Humainah wayar tace "bude min pattern" Humainah ta karba Junaid ya fixge wayar
hannunta yana kallon Zahrah yace "Wa xa ki kira?" Ba tare da ta damu ba tace
"Abbana" juyawa yayi ya fice da wayar, tabe baki tayi ta kalli Humainah ta mike ta
nufi kofa, Humainah ta bi ta da kallo har ta fita ta juyo tace "Idan kin xuba
abinci ki kira ni, we don't eat alone at home" daga haka ta fita, mamakinta sosai
Humainah ta dinga yi, tana xuba abincin kuwa ta dawo sama ta bude kofar dakinta ta
kirata, mikewa Zahrah tayi ta fito suka sauka kasa a tare, nan kan carpet Humainah
ta ajiye masu abincin, Zahrah ta xauna ta tankwashe kafa ta dau spoon ta fara cin
abincin, xaunawa Humainah tayi ita ma ta dau cokalin ba tare da ta kalleta ba ta
shiga cin abincin, Zahrah ta d'an kalleta tace "How month pregnant are you?" Kallon
mamaki Humainah tayi mata da kmr baxata tanka ta ba sai kuma tace "five" Zahrah ta
langwabar da Kai tace "Ohk.... But me yasa mijin ki yake behaving yanda yake yi?"
Humainah bata kalleta ba bare ta sa ran amsa, aka bude kofar parlorn Junaid ya
shigo don dama yana waje, kallon mamaki yake masu can ya karaso parlon ya xauna
yana kallon Humainah yace "Did you cook with me" kan tace komai Zahrah ta amshe
tace "Of course No, not with her condition, just go get something outside to take!"
Kallon Zahrah kawai yake can ya mike ya nufi stairs sai a snn yayi murmushi ya
haura sama. Da daddare Zahrah na fitowa daga wanka ta xauna gaban mirror don yi
shafe shafenta aka bude kofar dakin, duk da ynda gabanta ya fadi hakan bai sa ta
juyo ba sai shafa lotion dinta take, tsaye yyi bakin kofar yana kallonta, ta gama
shafanta ta mike ta nufi kan gado don daukar sleeping wear dinta, bin ta yyi da ido
har ta dau kayan, ganin cire towel din xata yi yasa shi juyawa ya fice daga dakin
ya rufo, murmushi tayi a xuciyarta tace you should have stay, tana gama shirya wa
ta fito ta shiga dakin Humainah, Humainah dake kwance don ta gaji bayan dinner da
ta girka ta bi ta da kallo, kwata kwata ta ki sakewa da ita, Zahrah ta xauna kan
gadon ta dau remote tace "I hate staying alone... We don't do that at home"
powering din Tv tayi ita dai Humainah bata ce mata komai ba. Daga karshe rufe ido
ma tayi kmr ta fara bacci, xaman kusan minti talatin Zahrah tayi can tayi
kwanciyarta kan gadon, bude ido Humainah tayi da sauri tana kallonta, ta gyada kai
tace "Yeah, I am spending the nyt here" Humainah bata ce komai ba ta rufe idonta
kuma, Zahrah ta gyara kwanciyarta ta ja duvet ta ci gaba da kallonta, bude kofar
dakin aka yi Junaid ya shigo, ya buda ido yana kallon Zahrah, ko kallonsa bata yi
ba idonta na kan tv, Humainah dai tayi kmr bacci take, juyawa yyi kawai ya fita
daga dakin. Washegari da asuba Humainah ce ta fara tashi ta tada ta, sllh tayi ta
fita ta bar ta dakin ta tafi kitchen, tana fita Junaid ya shigo, ya hade rai yana
kallon Zahrah da ke kan darduma yace "Me ya shigo dake dakin matata, don ki koya
mata girman Kai da unnecessary Royalism din ki koh?" Bata ko kallesa ba bare ya sa
ran samun amsa, sosai hakan ya kona masa rai ya daka mata tsawa yace "Ba magana
nake maki ba kika kyaleni" nn ma dai ko kallon gefen da yake bata yi ba, juyawa yyi
ya fice daga dakin xuciyarsa na tafasa, sai a snn ta kalli bakin kofar ta gefen ido
ta mike, ita ma ta fita ta shiga bedroom dinta tayi wanka ta shirya cikin wani lace
mara nauyi da ya amsheta sosai, gyara dogon gashinta tayi ta daure a baya ta bar
dankwalin a kafada ta sauka, ba wani aiki ta taya Humainah ba sai tambayoyi da ta
isheta da shi kmr yar jarida, Humainah ta jera komai kan dining Zahrah ta xauna
tana kkrin daukan cup tace "Yanxu sai ki je kiyi wanka kiyi kwalliya wa mijin
ki..." Humainah bata ko kalleta ba ta wuce sama, tana tafiya sai ga junaid ya sauko
cikin shirin Uniform, har ya karaso dining din idonsa na kanta, shayin ta kawai
take sha, ya ja kujera ya xauna ya hade rai yace "A royal Home din ku ba'a koya
maki gaisuwa ba ne koh" bata dago kai ba bare ta tanka sa sosai haka ya kona masa
rai, sai a snn yasan ashe shariya na da ciwo, wani tsawa ya mata yace "Kee!" Dago
manyan idonta tayi ta hade rai tana kallonsa can ta mike ta kwabar da cup din tean
hannunta ta nufi sama kmr xata tashi sama, bin ta da kallo yyi baki bude, tunda
yake shi mace bata taba yi masa haka ba, fasa breakfast din ma yyi gaba daya ya
koma sama ya dau wayarsa da car key ya bar gidan. Sai wajen biyar ya dawo gida har
lokacin ransa ba dadi, xaune suke parlor tana gyara Humainah gashi, ya wani hade
rai yace "Duk ku bar parlon nn Immediately" ba tare da Zahrah ta kallesa ba tana ci
gaba da combing gashin Humainah tace "And may we know y?" Karasawa parlon yyi cikin
tsawa yace "ku bar min parlor nace" Zahrah ta yatsine fuska ta kwashi kayan gyaran
gashin tace "it doesn't call for shouting! Maman baby tashi mu je" Humainah ta tabe
baki ta tafi sama, Zahrah ta bi bayanta, xaunawa yyi kan kujera yana tunanin
hukuncin da xai dauka kan Zahrah bai taba tunanin shariya da daukan kai na da ciwo
ba sai ynxu, ranan ma tare Zahrah ta kwana da Humainah, shi dai bai ce masu komai
ba, washegari ya gama shirin fita aiki ya sauko downstairs ya samesu tare suna
breakfast, yana kallon Zahrah yace "Royal being, har yanxu bayin na ki basu iso
bane ko dama kawai fadi aka yi" ko kallon inda yake bata yi bare ta tanka sai cin
potatoe da ketchup dinta take, tsaye yyi yana kallonta, can yace "I can see you are
deaf..." mikewa tayi irin ya takurata din nn a fusace ta yi hanyar stairs, bin ta
yyi ya fixgota ya hadata da jikinsa kan yace komai cike da tsiwa tace "Me yasa ka
fiye takura ne Mr man, get away from my life, i hate disturbance, I don't want...."
Bai bari ta kai karshe ba sai jin kiss tayi, Humainah dake kallonsu dama dauke kai
tayi ta ci gaba da jujjuya potatoe din gabanta, turata yayi yana mata wani kallo
sai kuma ya juya ya nufi kofa da sauri, bin sa da kallo tayi a tsorace, can ta saci
kallon Humainah sai kuma ta tafi sama da sauri, Junaid ya kusa minti goma xaune
cikin motar kafin ya tada motar ya bar gidan. Har rana Zahrah bata fito ba, wajajen
Karfe uku ganin ta fara jin yunwa ta fito daga dakin, bbu kowa parlon ta shiga
kitchen ta hada tea ta fito ta dawo sama dai dai lokacin da Humainah ta fito daga
dakinta, har Zahrah xata mata magana sai taga ta wani hade rai kmr bata ganta ba ta
sauka kasa, Zahrah ta juya ido hade da tabe baki ta shige dakin ta. Da yamma kusan
a tare Junaid ya shigo gidan da Hajja, ya wani hade rai ganinta, ita din ma ko amsa
gaisuwarsa bata yi ba ta shige parlor tana kwala ma Humainah kira, Humainah dake
kwance daki ta fito da sauri jin muryar Hajja, rungumeta tayi cike da jin ddin
ganinta, Hajja ta turata tana kallonta daga sama har kasa tace "Ramar meye wnn
Humainah, daina baki abinci yyi don yyi aure ko yaya?" Humainah tayi 'yar dariya
tace "Ni ba Ramar da nayi Hajja" Hajja ta kalli sama murya can kasa tace "Yar
sarkin na sama koh?" Humainah ta gyada mata kai kawai, Hajja ta tabe baki tace
"Xata ci ubanta, ko da kuwa shugaban kasa ne uban nata...." Shigowar Junaid ya sa
tayi shiru ta balla masa harara, dai dai lokacin da Zahrah ta sauko jin muryar
Hajja, hajja ta tsuke fuska sosai, daga inda take tsaye ta gaida ta Hajja ta saki
salati tana tafe hannu tace "Yanxu 'yar nn kya gaida Uwar da ta haifi uwar ki a
tsaye?" Kallonta kawae Zahrah take, Hajja tace "Toh wnn ba dab'iar arxiki bane, don
da Humainah ce ko kaffara baxan yi ba baxa ta yi haka ba, ba fa masarauta
kike ba yanxu!" Wani kallo junaid yake ma Hajja don ji yyi kmr ya shaketa, Zahrah
ta juya ta koma sama, bin bayanta yayi Hajja tace "Munafuki, hbayaala har ta fara
girki ta basa yaci ne?" Humainah dai bata ce komai ba Hajja ta ce "Toh shi ma xae
ci uban nasa ne" tsaye Junaid ya ganta gaban mirror, da kmr baxae karasa ba sai
kuma ya karasa kusa datace ita, juyo da ita yyi yana kallonta yace "Me yasa kika
gaisheta a tsaye!" Bata ce komai ba kuma bata kallesa ba, tambayar ya kuma
maimaitawa nn ma dai shiru kke ji, a fusace yace "Don me xan dinga maki magana kina
share ni" ga mamakinsa har lkcn bata kalli inda yake ba, ya fixgota yace "Wllh na
sake maki magana kika share ni I will..." kallon mamaki yake mata ganin bama ta da
niyar kallonsa, can ya juya fita. Har dare Hajja bata bar gidan ba tana dakin
Humainah, Junaid ya samu Humainah dake kitchen tana xuba ma Hajja abinci yace
"Zahrah ta ci abincin?" Bata kallesa ba tace "I don't know!" Ficewa yayi daga
kitchen din ya koma sama ya shiga dakinta, xaune ya sameta ya karasa kusa da ita
yana kallonta kana ganinta kasan tayi kuka, bai san lokacin da ya durkusa gabanta
ba ya kamo hannunta yace "Zahrah!" Kallonsa tayi bata ce komai ba, ya matsa
hannunta a hankali, sauke idonta tayi kasa, can underneath his breathe yace "My
arrogant princess!" Bata dago ba bare tace komai ba, ya lumshe ido ya bude a
hankali yace "Meye amfanin miskilanci da girman kai Jasmine!"

*Haske writers association*馃挕

_Mata-Maza ce Khaleesat Haiydar ba namiji ba_馃槑


⚓ *Captain Ahmad Junaid*⚓

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

89.....

Zahrah ta kalli cikin idonsa tace "Who's Jasmine?" A hankali yace "You!" Dauke kai
tayi ya mike ya dawo gefenta ya xauna yace "Baki bani amsar tambayata ba" shiru
tayi bata ce komai ba, matse mata hannu yyi ta wurga masa wani kallo tace "Stop
that" yyi d'an murmushi yace "Nasan abinda zan maki ki sauke girman kan nn
naki...." Fixge hannunta tayi ta mike ta nufi toilet tace "You can't change who I
am, beside you are more arrogant" daga haka ta shige toilet ta rufe, mikewa yyi ya
fita daga dakin yana murmushi har lkcn, sai bayan ya fita ya dinga mamakin kansa,
then what just came over him, karfe goma saura Zahrah ta shirya cikin kayan bacci
ta fita daga dakinta, dakin Humainah ta tura ta shiga, suna xaune kasa ta gansu,
Humainah ta daura kanta kan kafar Hajja, magana suke amma suna ganinta suka yi
shiru, ko a jikinta ta karasa ta xauna gefen gado ta kalli hajja tace "Sannu da
hutawa!" A dakile Hajja tace "Yauwa!" Daga nn Zahrah ta maida dubanta kan tv, Hajja
ta kalli Humainah kmr xata yi magana sai kuma tayi shiru ta kyabe baki, Humainah ta
d'an kalli Zahrah tace "Abincin ki downstairs" ba tare da Zahrah ta kalleta ba tace
"Am not hungry" Hajja ta galla ma Humainah harara ta hade rai, har kusan sha daya
Zahrah na dakin ita dai bata ce masu ba suma haka, tun da ta shigo kuma sun ki yin
hirar da suke, can dai ta kalli Hajja tace "Sai da safe" da sauri Hajja tace "Ehh
Allah ba mu alkhairi" ba sai Hajja ta ga tana kkrin kwanciya kan gado ba, ta yo
waje da ido tace "Mai xan gani haka?" Humainah da ta danne dariyar da ya kusa taho
mata tace "Nan xata kwanta mana" Zahrah ta kalli Hajja tace "Bacci xan yi a nn"
Hajja ta wage baki tana mata kallon mamaki can dai tace "Su wa kika bar ma dakin
naki ne" Zahrah tace "A nn nake kwana" Hajja ta kalli Humainah tace "Wai?" Humainah
ts gyada mata kai, Zahrah ko tayi kwanciyarta, can dai Hajja ta rufe baki tace "Wai
tun da aka kawo ta nn take kwanan maki?" Humainah tace "Uhm" Hajja tace "Tabdi, toh
me salubabben yace?" Humainah tayi yar dariya tace "Ba ruwansa" Hajja tace "Toh
Allah ya sauwake maku gaba daya" tuni Zahrah ta ja bargo, Hajja da ta kasa daina
mamaki tace "Wai meye haka nake gani, to ni ina xan kwanta?" Humainah tace "Ki tafi
dakinsa ku kwanta" dai dai nn Junaid ya shigo dakin, yayi mamakin ganin Zahrah
kwance dakin, Hajja tace "Yanda yake wawa haka ya samo mata duk wawaye, banda haka
ni ko a tarihi ban taba jin kalan abinda nake gani a dakin nn ba, toh shigowa Kayi
Kai ma ka kwanta a tsakiyarsu ko ko?" Mikewa Humainah tayi ta dinga dariya, Junaid
dai sai kallonta yake don har ya mance rabon da ya ga tana dariya haka, dauke kai
yyi yana murmushi can dai ya kalli Hajja yace "Toh yau kinga hakan a gidan Ahmad
Junaid" wani kallo ta wurga masa tace "Yi man shiru, gantalalle har kullum wautan
yan fari ba cika ka xai yi ba, dama Kai kace ta dinga xuwa kwana nn?" Junaid ya
kalli Humainah yace "You leave the room for them nd come to my room" daga haka ya
juya ya fita, a fusace Hajja tace "Ka xagi Muhammadu wllh, ke kuma uwar me yace?"
Humainah tayi murmushi tace "Yace kije dakinsa ki kwanta" duka take shirin kai mata
ta mike da sauri ta fita daga dakin, daga nn bata sake ganin Humainah ba tayi jiran
tayi jiran har ta gaji, kwafa Hajja tayi tace "Lallai yaran nn, dakin mijinta ta
tafi ashe" kallon Zahrah da tayi bacci tuni kan gado tayi, sai kuma ta fara mamaki,
taga dai ko kwana hudu ba ayi da tarewarta tabe baki tayi ganin ta kasa gano komai
ta mike ta dau bargo ta shimfida a kasa da pillow, can misalin biyu Zahrah ta farka
mikewa xaune tayi ita kadai ce kan gadon, can ta kalli Hajja dake ta sharar bacci a
kasa, sauke kafafuwanta kasa tayi ta mike ta xaga inda take ta durkusa ta shiga
tada ta, bude ido Hajja tayi tana salati, Zahrah tace "Akwai sanyi kasa meyasa baki
hau gado ba" Hajja tace "Kai ai sai jikina yyi ciwo, nn ya ishe ni" Zahrah tace
"Toh" mikewa xaune Hajja tayi tace "Toh ae gwara da kika tada ni, xan yi tsayuwar
dare dama" Zahrah tace "Ina take ita?" Hajja ta tabe baki tace "Ae kya bar ni
budurwa" daga haka ta mike tana salati ta shiga bayi, mikewa Zahrah tayi ta koma
tayi kwanciyarta, da asuba hajja ce ta tada ta tayi sllh, tana idarwa tana daga kan
darduman ta gaida Hajja dake ta jan carbi, Hajja ta amsa tace "Kin tashi lafiya?"
Zahrah ta gyada mata kai, Hajja tace "Amma kina da ciwon baki koh? Naga kmr magana
na maki wahala?" Murmushi Zahrah tayi, Hajja tace "Toh ae ba abun dariya bane sai
in sa a sama maki Magani...." Zahrah tace "A'a lafiyata lau!" Hajja tace "Tohhh!
Kuna waya da mutan gidan ku?" Girgixa kai Zahrah tayi, Hajja tace "Sbda me" Zahrah
tace "Ba waya" Hajja tace "Baki xo da waya bane dama?" Girgixa kai kawai Zahrah
tayi, Hajja tace "Toh Allah ya kyauta" daga haka bata sake cewa komai ba, can Hajja
tace "Dawo nn in maki tambaya" mikewa Zahrah tayi ta koma kusa da ita ta xauna,
murya can kasa Hajja tace "Halan gudun mijin ki kike?" Girgixa kai Zahrah tayi ba
tare da ta kalleta ba, Hajja tace "Anya? Toh wace gulmar ta kawo ki nn jiya Idan ba
gudunsa kike ba?" Zahrah tayi murmushi ta girgixa mata kai, Hajja tace "Ke ki fa
bude baki ki min magana" a hankali tace "Ni dama a nn nake kwana" Hajja tace "Toh
har ya maki kwanakin ki bakwai ne?" Kai Zahrah ta gyada mata, Hajja tace "Karya
kike" murmushi Zahrah tayi ta mike tace "Zan je kitchen" daga haka ta fita Hajja ta
bi ta da kallo tace "Ikon Allah yau naga halitta" Breakfast Zahrah ta shiga kitchen
tana hadawa, cikin minti arba'ain ta gama soye soyen, ta kuma dafa hadadden lipton
mai kamshi ta kuma dau nama a deep freezer ta gyara tayi pepper soup da shi, bakwai
da kusan rabi ta kai ma Hajja nata, Hajja dake kan darduma har lkcn tace "Ahhh,
Dama kuna girki 'ya yan gidan sarauta, to wa ya koya maki girkin?" Murmushi Zahrah
tayi ta ajiye mata ta hada mata tea snn ta mike tace "Zan yi wanka" daga haka ta
fita ta koma dakinta, ta fito daga wanka tana gyara gashinta aka bude kofar dakin,
juyawa tayi, tayi masa kallo daya ta dauke kanta, sanye yake da uniform, hannunsa
rike da hularsa ya karaso cikin dakin har ya iso bayanta yace "Ashe an koya maki
girki gidan ku" bata ko kallesa ba bare yasa ran samun amsa, kwace comb din
hannunta yayi, ta jawo mai xata shafa ya karbe man, wani man ta kuma dauka ya kwace
duk ya jefar da su kan gado, tana son tashi amma ta kasa sbda tawul kadai ta daura,
gashi yana bayanta, ta madubi yake kallonta shi ma ya hade rai yanda tayi, "Pls ka
daina shiga rayuwata Ahmad" bai san lkcn da murmushi yayi escaping lips dinsa ba
yace "Ohh really kinsan sunana ashe" mikewa tayi kafin ta bar gun ya rikota, turasa
take son yi amma ta kasa, kawai ta saki kuka, buda ido yayi yace "Kuka?" Ganin
yanda take kukan sai ya tuno masa da lokacin da take da disorder, ya ji duk jikinsa
yyi sanyi, ya kamo hannunta suka koma gefen gado ya xaunar da ita cikin sanyin
murya yace "Ohk ohk... Am... am sorry princess, am sorry Jasmine" ganin taki daina
kukan bai san lkcn da ya rungumeta ba ya lumshe ido a hankali yace "I said am sorry
xan bar shiga rayuwar ki...." A hankali ta tsaida kukan nata, dogon gashinta ya
kama ta fixge gashin a hannunsa, murmushi yayi murya can kasa yace "Jasmine dita ta
da ba haka take ba, she alwayz wants to be with her Captain, always happy when ever
she see's her captain, she alwayz want to do everything with her captain, she's
timid, she's alwayz afraid, she's innocent, the sweetest of all, she's alwayz happy
and free, she was never arrogant, she don't have I don't care altitude, she never
say who she is, she's full of respect, and the amazing of all, she changed me to
what I am today, she....." Shiru yayi ta dalilin dago kai da tayi tana kallonsa da
manyan idonta, lallausan murmushi ya sakar mata yace "Yeah, I want you to go back
to ur former self..." Agogo da yayi stuck din karfe takwas ya sa shi bude ido yana
kallon wristwatch dinsa yace "You made me late for work...." Bai karasa ba sai ji
tayi ya fara kiss dinta, don kansa ya mike ya fice daga dakin daga karshe, haka ta
bisa da kallo har lkcn ta kasa motsi inda take. Da kyar ta mike bayan ta ji fitar
motarsa ta shirya cikin atamfa riga da skirt tana xaune gaban mirror tana sa
xobunayen zinari guda biyu da ta fito da daga kayan lefenta Hajja ta shigo dakin,
tace "Har yanxu wanka yar nn" kallonta tayi tace "Na gama kaya nake sa wa" Hajja
tace "Ashe komai iri daya ne na dakunan naku" Zahrah ta gyada mata kai, Hajja tace
"Toh taho ki hada min ruwan wanka wancan so mijin na can dakinsa tana sharbar
bacci" mikewa Zahrah tayi tace "Toh bari in hada maki a nan" Hajja tace "Toh hada,
ko kefa da kike bude baki kike magana yanxu" murmushi Zahrah tayi ta shiga bathroom
dinta, ba a dau lokaci ba ta fito tace "Ga ruwan can na hada" Hajja tace "To tafi
ki bude jakata xaki ga wani sabon atamfa duk yafi sauran sabonta ki dauko min, nima
kwalliya zan yi yanda kika yi kar ina ji ina gani ki raba ni da Amadi in shiga uku"
Dariya Zahrah tayi tace "Kai!" Daga haka ta fice daga dakin, Hajja tace "Ashe dai
kina dariya 'yar ayi" ko da Humainah ta fito misalin Karfe goma Hajja na dakin
Zahrah har lokacin ta cikata da labaran duniya, ita dai Zahrah ta tallabi kuncinta
ne tana kallonta, wani lbrin yasa ta fashe da dariya, wani kuma ta xaro ido wani
kuma ta bata fuska, sha daya ta shigo dakin ita ma ta xauna tana kallon Hajja tace
"Ina kwana Hajja" Hajja tace "Ahh lafiya lau so miji, sai yanxu kika tashi?" Zahrah
ta sunkuyar da Kai kar tayi dariyar da ya taho mata, Humainah ta turo baki tace
"Ehh" Hajja tace "Toh Allah ya kiyaye, kun gaisa da takwarar tawa" Humainah ta d'an
kalli Zahrah tace "Kin tashi lafiya" Zahrah tace "Alhmdllh" nan dai Hajja ta ci
gaba da labaranta masu kai da marasu Kai, gyangyadin da ta dinga yi tana labarin
yasa Zahrah ta sauko mata da pillow tace "Toh ki kwanta sai ki ci gaba da labarin"
ai ko tana kwanciya ta bingire da bacci, Humainah tayi murmushi ta mike ta fita don
daura lunch, bayan kusan minti talatin da fitan ta Zahrah ta
mike ta fita don taya ta. Da yamma tun kan Junaid ya dawo Hajja ta hada kayanta
wai yana dawowa xai maida ta gida, Humainah tace "Dama ba sati daya kika xo mana ba
hajja?" Hajja tace "Ba gantalalliya nake ba ai" Zahrah tace "Toh ki Bari gobe
alhamis mana" Hajja tace "Toh ai ba yar iska nake ba" dariya suka yi gaba daya
banda ita dake ta faman xuge jaka, tana gamawa tace "Toh dai ayi xama na Allah da
annabi banda munafurci da munafukin kishi mara ma'ana, ku dau kan ku kamr yan uwan
juna, ke Zahrah ki bar gudun mijin ki, ke kuma Humainah in ma ta shigo dakin ki ki
korata idan ba son amshe kwananta kike son yi ba, ni har kishiyata ta rasu sau
biyar muka taba dambe da ita, cacan baki kuwa mun yi yafi sau hamsin, Amma lafiya
muka xauna bbu tashin hankali shi yasa ku ka gan ni da kyau yanxu, shi kuma
salubabben mijin naku xai dawo ya sameni" dai dai nan aka bude gate Hajja tace "Toh
Alhmdllh gashi can ma," Junaid na shigowa Hajja tace "Taho ka xauna nn, nasan
sokanci baxai bari Ka hada su kayi masu magana kamar yanda nayi yanxu ba"

*Haske Writers association*💡


⚓ *Captain Ahmad Junaid*⚓

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

90____91

Har bayan 2 dayz Junaid bai kuma kallon inda wives din nasa suke ba, yana dawowa
daga aiki baya fitowa daga bedroom dinsa, su ma ko damuwa ba su nuna sun yi ba
barin Zahrah, yanda suke abubuwan su sai ka rantse ba kishiyoyi bane duk da ba wai
wani magana can suke ba amma ko da yaushe suna tare, nace to ko don basa nuna sun
damu da mijin kamar yanda shima yake nuna bai damu da su bane oho, gwara Humainah
idan sun hada ido tana gaishesa duk da baya bin ta kan gaisuwar nata, Zahrah kam ko
kallo bai isheta ba, wani takaici yake ji har cikin ransa, kuma ya rasa abinda yasa
yake jin haushin halin ko in kula da suke nuna masu, ranan asabar yana kwance daki
kawai ya mike ya fita, downstairs ya sauka jin kamar girki ake don a tunaninsa
Humainah ce, Zahrah ya gani kitchen din tana juye dafaffen shinkafa a warmer, kallo
daya yyi mata ya fice ita ko duk da taji alamar shi ne bata ko dago kanta ba, sama
ya koma ya bude kofar dakin Humainah ya sameta kwance, tana ganinsa ta mike xaune,
xaunawa yyi gefen gadon yana kallonta yace "Irin kema kin tsiri wani hali da ba
naki ba yanxu koh?" Bata ce komai ba ya hade rai yace "Magana nake maki malama"
turo baki tayi tace "Toh me nayi?" Yace "Bbu ruwana da abinda kika yi, just that
daga yau idan Zahrah ta shiga dakin ki just leave the room for her nd come to my
room, nd daga yau kika sake min gaisuwar rainin wayo a parlor xaki sha mamaki,
infact bedroom dina xaki dinga xuwa gaisheni daga yanxu, and... I don't care
altitude din da kika tsira ma ya tsaya iya idan bana gidan nn, duk girkin da xa ayi
ki tabbatar kin kai min bedroom....." Kallonsa take kawae, can tace "Ae bni kadai
bace matar ka naga" mikewa yyi strictly yace "Ke kadai nasa hakan, if you want to
dare me just ignore any of this instructions" daga haka ya fice daga dakin ta bi sa
da kallo. Zahrah na gama girki Humainah ta sauka ta dibar masa nasa, ita dai Zahrah
bata ce komai ba, bedroom dinsa ta kai masa tana ajiyewa xata fita yace "Come back
here" hade rai tayi ta dawo ya nuna mata kan gado yace "Sit" karasawa tayi ta
xauna, bai wani ci abincin ba ya sha ruwa ya tura ya ci gaba da kallonsa a system,
gajiya Humainah tayi da xama ta mike yace "Ina xa ki" tace "Jirana fa take mu ci
abinci" yace "ta ci ita kadai, ga wannan idan yunwa kike ji ki ci" tsaye tayi tana
kallonsa ganin bai kuma kallon inda take ba ta koma ta xauna, can dai ta gaji da
xaman ta kwanta lkci daya bacci ya dauketa. Har yamma bai bari ta fito daga dakin
ba, wayarsa dake ring ya sa shi mikewa ganin bata da niyar dauko masa ya dau wayar,
kallon screen din kawai yake ganin yayan Zahrah ne Abdul, can ya daga kiran ya koma
ya xauna, gaisawa suka yi Abdul din yace "Captain ya Lil sis dita.... Her phone is
not going through!" Mikewa junaid yayi yace "Ohk bari in kai mata" daga haka ya
fita daga dakin ya shiga nata, xaune ya ganta kan gado hannunta rike da novel,
karasawa yyi kusa da ita ya mika mata wayar, bata dago ba bare ta karba, wani kallo
ya dinga yi mata, can dai ya dake yace "Take this" nn ma taki dagowa, katse kiran
yayi yace "Ba magana nake maki ba?" Mikewa tayi ta sauka daga kan gadon xata fita
daga dakin ya fixgota, wani tsawa tayi masa a fusace tace "Stay away from me
Ahmad!" Runtse ido yyi jin tsawar har tsakiyar kansa, bai san lkcin da ya saketa ba
ya fice daga dakin ya shiga nasa ya dau makullin motarsa ya fito ya koma dakin har
lkcn tana tsaye, hijab dinta ya dauka ya kama hannunta ya nufi kofa ta shiga
kokarin fixge hannun tace "Let me, just go away from my life...." ganin xata bata
masa lokaci ya dauketa ya fice daga dakin bai dire ta ba sai cikin mota, ya kulle
ya xaga ya shiga ya tada motar ya bar gidan, bai damu da haukan da ta dinga masa
bayan motar ba ya dinga driving dinsa, tafiyar kusan minti talatin suka yi taga
yayi parking, bude motar yayi ya fito ya xaga ya bude side din da take ya fito da
ita, taku daya biyu ya cikata yana mata wani kallo, kalle kallen wajen ta dinga yi
ganin duk bola ne, ya dawo gabanta ya tsaya yace "Kin ga nan?" Kallonsa kawai take
bata ce komai ba, yace "Toh a nan na dauke ki bbu kyan gani da hannuna, kuma a
lokacin da kowa ke kyamatar ki baki da wani sauran gata a duniya kina tsaka da
hauka, wanda da a lkcn royal family dinki sun ganki a hakan ba lallai su taba ki ba
sai dai su sa a dauko masu ke, kuma har duniya ta nade bbu wanda xae taba maki
abinda na maki... Har ni xa ki ce ina shiga rayuwar ki, har na xaki wani dinga daga
ma kai ke ga ki royal blood" Kallonsa kawae take hawaye cike idonta, can ta fashe
da kuka sosai ta durkushe wajen, jikinsa yayi sanyi yana kallonta, bai san lkcn da
ya durkusa gabanta ba shi ma ya dago kanta yace "Look I never mean to hurt you
Zahrah just that...." Ganin yanda take kallonsa hawaye na sauko mata kawai ya mike
ya daga ta suka koma mota, har suka isa gida bbu wanda yace komai cikinsu, yana
parking ta bude mota ta fita tayi cikin gida ya fito ya bi bayanta, tuni ta shige
daki ta sa key ta dinga rusa kuka, jin kofar a rufe yasa ya koma bedroom dinsa ya
dau spare key ya fito ya bude dakin, ji yayi duk ya tsani kansa ganin yanda take
kuka, ya karasa kusa da ita a sanyaye ya durkusa ya dago kanta yana kallonta,
rungumeta yayi a hankali yace "Am sorry Jasmine.... I shouldn't have done that,
forgive me pls" ita dai bata ce komai ba sai kuka, bai sake cewa komai ba, amma sun
kusa minti talatin a haka jin ta daina kukan ya dago kanta yaga idonta lumshe,
janyeta yyi jikinsa ya kwantar da ita ya mike ya fita daga dakin don lkcn magrib
yayi. Ko da ya dawo masallaci dakin Humainah ya shiga ya ganta xaune kan darduma
juyawa yayi ya koma dakinsa ya dau wayarsa mis cals din Abdul ya gani ya dauka ya
kirasa ya basa hakuri snn yace bari ya kai mata, xaune ya tarda ita kan darduma ya
karasa gabanta ya durkusa ya mika mata wayar, karba tayi tana kallon screen din can
ta kai kunne a hankali tace "Brotherna!" Murmushi tayi ta gaishesa sai kuma ta koma
harshen fullanci, kallonta kawai Junaid yake har dai suka gama wayar ta mika masa,
karba yayi yana murmushi yace "thought xa ki ce masa cikin ruwa na jefa maki wayar,
sai kuma naji kin ce yana gu na!" Kallonsa tayi da sauri sai kuma ta sunkuyar da
kai, ya wara ido yace "You thought bana ji koh?" Bata ce komai ba yace "Don't worry
I will get you a new phone princess" mikewa yyi ya fita daga dakin ta bi sa da
kallo, tun daga lkcn Zahrah ta d'an sauya in dai yyi mata magana ko yayane xata
amsa masa, ta kuma fara gaishesa, sai dai miskilanci nan na nan, a haka har tayi
sati uku gidan har lokacin kuma tare da Humainah suke kwanciya, shi dariya ma take
basa, sau dayawa Humainah kan barta ita kadai dakin ta tafi dakinsa amma hakan bai
sa ta daina shigowa da daddare ta kwanta ba, kwata kwata Zahrah bata nuna masu wai
tana kishi, duk da irin abubuwan da yake ma Humainah a gabanta don ma Humainahn
bata yarda wani lokacin don nauyinta take ji ganin shirunta yyi yawa kuma ko sau
daya baxa ka ga alamar tayi fushi ba, amma fa ba haka abun yake gun Zahrah ba a can
kasan ranta, so tari sai ta shiga daki xata fara kuka tayi mai isarta ta fito kuma
kamar ba komai, mamakinta Junaid yake ganin yanda ko sau daya bata taba nuna ta
damu da komai ba, ya rasa yanda xae yi kuma ta saki jiki da shi, bai son El-ameen
yyi masa dariya shi yasa bai gaya masa komai ba, Yau da ya kasan ce Sunday duk suna
parlor da daddare shi yana kwance yana kallo, lkci lkci ya ke kallon Zahrah dake
xaune tare da Humainah suna cin abinci sai dai ita ba wani ci take ba jujjuyawa
kawae take tana kallon ita ma, da ganinta kasan duk jikinta a sanyaye yake don
actress din film din mahaukaciya ce, Humainah ma kallon take tana cin abinci, kawai
gani suka yi ta sake spoon din ta mike ta wuce sama, Humainah ta kallesa, ya mike
ya bi bayanta, xaune ya ganta daki tana ganinsa ta fashe da kuka, sosai ta basa
dariya ya xauna gefenta ya kamo hannunta yace "What's wrong princess?" Kanta ta
daura kan shoulder dinsa tana ci gaba da kuka, bakinsa ya kai kunnenta murya can
kasa yace "Film din nan ne ya sa ki kuka?" A hankali ta gyada masa kai, yayi
murmushi ya dago kanta yana kallon kwayar idonta, sauke nata idon tayi don baxata
iya ci gaba da kallonsa ba, can kasan breathe dinsa yace "My princess, My Jasmine!"
Ta kallesa kamar baxata ce komai ba sai kuma a hankali tace "My prince, My Hero"

*Haske writers association*💡


⚓ *Captain Ahmad Junaid*⚓

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

This b4 91
Karasowa junaid yayi parlon yana kallonsu Hajja tace "Xauna nace Malam" da kmr
baxai xauna ba can kuma ya xauna kan kujera yace "To ya aka yi" Tace "Yauwa dama
nasiha nake masu kuma nasan ba lallai ka xaunar da su haka kayi masu ba, yanxu dai
duk na gaya masu abubuwan da suka kamata, na kuma basu lbrin irin xaman arxiki da
nayi da matar kakan ka, nace kuma su yi koyi da ni" kyabe baki junaid yyi tace "Ba
batun kyabe baki bane Ahmad in dai kasa munafurci a xamansu Allah sai ya kama ka
tun a duniya kuma ni bbu ruwana bbu ruwan d'a na, sai dai ku karata da Uwarka, yau
kwanan yarinyar nn hudu a gidan nn to dama halan baka san ya kamata ka mata kwanaki
bakwai bane" shafa kansa yyi xai yi magana ta buge masa hannu tace "Na sha ce maka
idan ina maka magana ka bar shafe shafen kan nn raini ne wllh" murmushi yayi yace
"Ina sane..." Hajja tace "Atoh, ae shikenan tunda ka sani, wnn kuma kai da Allahn
ka, sannan kuma Humainah tun muna mu biyu ka sama mata yar aiki don aikin gidan nn
yyi mata tuli, ita kuma wancan 'yar gidan sarautar nasan ba yi take a gida ba don
haka ita ma ba iyawa tayi ba sai ka fita ka samo masu masu aiki har biyu yau yau
din nan, ina sake nanatawa ka xamo mai adalci kmr kakan ka Amadi don shi mahaifin
ka nasa adalcin kalilan ne, kaji tsoron Allah kar ka tarwatsa gidan ka ga mata nan
Allah ya baka kyawawa masu hakuri sai dai wauta da wawanci, komai yaje ya dawo kai
ne sila don haka kaji tsoron gamuwar ka da Allah kayi koyi da kakan ka bawan Allah"
ta gefen ido kawai junaid ke kallonta, kallonsu Humainah tayi tace "Kun dai ji
abubuwan da na gaya maku kar ku bari shaidan ya shiga tsakanin ku a kan namiji ku
samu kanku cikin wuta ranan gobe kiyama, banda kishi mara amfani, ku kuma mutunta
junan ku, kuyi masa biyayya duk da ba wani cancantan hakan yyi ba don ni ma baya
min, sai dai bbu yanda kuka iya dole shi xai dage kafarsa ku shiga aljanna, ke
Zahrah kar ki xo ki dinga nuna ma jikata isa kice ke daga gidan sarauta kika fito
duk da ita ma da xa ki ji asalinta da xa ki ga sarautar ku ba komai bace, kuma
kinga marainiya ce ba uwa sai uba...." Sai kuma hajja aka fashe da kuka, murmushi
kawae junaid yake don bai son yyi dariya, ita kuwa Zahrah bata dago kanta ba sae
wasa da xobunan hannunta take, Hajja tayi kukanta mai isarta ta goge hawaye ta juya
tana kallon Humainah da kanta ke kasa ita ma ta tsuke fuska tace "Ke kuma kar ki
dinga nuna mata takama kina nuna mata ae Ahmad din d'an uwanki ne sai Allah ya
kamaki ki ga karshen ki tun a duniya don kema naki halin na ji kin ki da ni ce
kwantar da kai xan yi in ci arxiki in bar arxiki inda yake, kishin banxa kishin
hofi, ni daga karshe ba hakura nayi na bar ma matsafiyar kishiyata kakanku ba na
kama business, to yau ba gani da nawa kaddarorin ba, toh wllh ki rufa ma kanki
asiri ku xauna lafiya, kishiyar taki ma dake ciwon baki magana ma wahala yake mata
sae dai in ke kika tsokanoto, ga ta da kirki ga ta da sanin ya kamata, ina me
tabbatar maki in lafiya kuke xauna har sai kin ture kujerun makka....." Tana kai wa
nn ta kinkimi jakarta tace "Ni dai kun ga tafiya ta, idan ya ga dama ya biyo ni ya
bude min mota ya ajiye ni gida, banda haka xaman me xan yi cikin yara su bar ganina
da gashi" mikewa junaid yyi ya bi bayanta. Ko da ya dawo gidan bayan isha don sai
da ya biya gidan El-ameen bbu kowa parlon sai TV dake a kunne, ya tafi sama ya
shiga dakinsa, wanka yayi ya shirya cikin pyjamas dinsa ya dau laptop ya shiga dube
dubensa, bude kofa yaji anyi can corridor ya kalli agogo ya ga goma saura ya mike
ya nufi kofa ya bude, ido hudu suka yi da Zahrah ta dauke kai xata bude kofar dakin
Humainah yace "Zahrah!" Tsaye tayi bata bude kofar ba kuma bata juyo ba, ganin haka
ya karasa har wajen yana kallonta yace "Har xa ki tafi ki kwanta kenan" Kamar
baxata ce komai ba sai kuma tace "Yess!" Murmushi yayi yace "Ohk, tsoron kwanciya
kike ke daya?" Nan ma yess tace masa, shiru yyi sai kuma yace "come to my room ki
kwanta" sai a snn ta kallesa tace "No!" Daga haka ta bude kofar ta shiga ta rufe,
ya kusa minti daya tsaye can ya juya ya koma dakinsa. Washegari da safe suna
kitchen tare suna hada break Zahrah na ba Humainah labarin masarautan su junaid ya
shigo kitchen din cikin shirin aiki, Humainah ce ta fara kallonsa ta dauke kai tana
ci gaba da juya potatoe din kan gas, Zahrah ma ta kallesa ta dauke kai ta ci gaba
da juye ruwan lipton a flask, hade rai yyi yace "Ni xan gaishe ku?" Ba tare da
Humainah ta kallesa ba tace "Ina kwana" wani kallo yake mata sai yaji Zahrah da
bata sake kallonsa ba ma tace "Good morning" juyawa yyi ya fice daga kitchen din,
makullin motarsa kawai ya dauka ya bar gidan. Karfe hudu da rabi yana barin gun
aiki ya tafi clinic dinsu El-ameen, El-ameen na xaune office yana aiki a laptop ya
shigo, sauke glass din idonsa yyi yana kallonsa yace "Wannan frequent visit din da
kke kawo min now a dayz fa Junaid" kujera Junaid ya ja ya xauna yace "You know
what?" El-ameen ya matsar da laptop din gabansa yace "Sai ka fada" junaid yace "Wai
ni wa en can girls din xa su dinga yi ma miskilanci.... Suna sharewa, I just don't
know what came over me da har nake tolerating hakan, they are pushing me to the
wall!" El-ameen yace "To kuma, miskilanci kuma? To me ya kawo hakan?" Shiru Junaid
yayi masa, El-ameen yace "And I guess hakan yana kona ma rai ko?" Junaid ya kallesa
yace "to baxai min ciwo ba, har ni xa su dinga daga ma kai suna sharewa?" Mikewa
El-ameen yayi sai kuma ya fashe da dariya yana kallonsa yace "Alhmdllh Junaid yaji
abinda mutane ke ji idan suka masa magana ya share su! I like that ka ga sai kaji
ya feeling din yake. Kai har xaka fadi ma mutane miskilanci da shariya...." Wani
kallo junaid ke masa kafin ya mike ya dau wayarsa ya fice daga office din, El-ameen
ya dinga dariya don yaji dadin lamarin ba kadan ba, ko da junaid ya koma gida duk
suna parlor bai ko kallesu ba yayi hanyar stairs.

*Haske writers association*💡


⚓ *Captain Ahmad Junaid*⚓

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

92____95

Kallonta kawai junaid yake kamar bai yrda da abinda tace ba, can yyi murmushi ya
daura forehead dinsa kan nata a hankali murya can kasa yace "Sure?" Rufe idonta
tayi bata ce komai ba, ya lumshe idonsa yace "I love you princess!" Boye fuskarta
tayi jikinsa tana murmushi, ya kai bakinsa kunnenta yace "Ohk, am only ur hero but
not ur love koh?" Murya can kasa tace "uhmm Whatever!" Misalin sha daya yana
kwance yana danna waya yaji ta bude kofar dakinta, mikewa yayi ya karasa gun kofa
da sauri ya bude, tana kokarin bude dakin Humainah ta juya tana kallonsa, hannu ya
mata alama da ta xo, ta tsaya tana kallonsa, can ta make kafada ta girgixa masa
kai, bata fuska yayi, tayi murmushi ta karasa gun kofar ta tsaya ta rungume
hannayenta bata ce komai ba tana jiran jin me xai ce, fixgota yayi cikin dakin ya
rufe kofar ta xaro ido tace "What's this?" Yace "Nan xa ki kwana yau!" Ta hade rai
tace "And Why?" Yace "Just" hannunta ya kama suka karasa kan gadon ya xaunar da
ita, a hankali tace "Ita fa?" Ya d'an bude ido yace "Ko in je in daukota?" Gyada
masa kai tayi yayi murmushi ya ja dogon hancinta hade da daura finger dinsa daya a
kan lips dinta yace "Gobe ita xata kwana nan ba ke ba!" Bata kuma ce masa komai ba,
sai dai mamaki take a ranta to da can yana magana haka ashe, kan gadon ya hau ya
jinginar da pillow ya kwanta ya nuna mata gefensa, kin tasowa tayi a hankali yace
"Jasmine" sunkuyar da kanta tayi ta hau kan gadon ya nuna mata pillow din dake
gefensa ba musu ta kwanta a hankali ya daura kanta, ya juya yana facing dinta yace
"Bani labari har bacci ya dauke ni" kallon handsome face dinsa kawae take ko
kiftawa bbu, hade kansa yyi da nata yace "Jasmine" ta koma baya da sauri tace
"What?" Yace "Ban labari nace" tace "Bn iya ba" yace "Ohk in baki ni?" Gyada masa
kai tayi, ya kashe wutan dakin ta mike xaune da sauri tace "Why is that?" Jawota
yayi jikinsa yace "Shhhh! Da Hausa kike son labarin ko da fillanci, ko da larabci
ko kuma turanci" murmushi tayi tana kallonsa tace "Fillanci...." Xaro ido yayi don
ji kawai yake bai iya speak ba, kallon fuskarsa kawai take cikin duhun tana
murmushi, kawai ji yayi tayi dariya tace "Ohk Hausa, tunda baka iya fillancin ba"
dariyar yayi shi ma yace "No na iya mana, amma bari muyi da Hausan, kina ji na?"
Kai ta gyada masa, ya hade hannunsa da nata murya can kasa yace "Watarana ne dai
watarana ne dai, wani bawan Allah ya je course Egypt daga nan Nigeria, cikin ikon
Allah ya kare course din ya dawo gida Nigeria, washegarin ranan da ya dira yayi
deciding ya je gun amininsa abokinsa kuma d'an uwansa...." Kallonsa kawai Zahrah
take, ya shafa fuskarta yace "are you there?" Ta gyada kasa kai, ya lumshe ido yace
"Yana driving a hanya ya ga wani taro me yawa, a tunaninsa hatsari aka yi, kawai
yayi deciding ya tsaya ya bada nasa taimakon... Yana fitowa ya shiga taron kin san
abinda ya gani?" Boye fuskarta tayi a kirjinsa, ya dago kan yace "Are you there
princess?" Ji yayi ta fashe da kuka, ya mike xaune da sauri ya dagota yace
"Jasmine!" Ta kuma fashewa da wani kukan, jikinsa yyi sanyi lokaci daya, rungumeta
yyi yace "Ohh I am sorry plss tunda ba ki so, sorry plss Princess na daina" lamo
tayi jikinsa, a hankali yace "I didn't mean to hurt you" suna nn a haka har yaji
alamun tayi bacci ya lumshe ido ya daura fuskarsa kam gashinta da ya cikasa da
kamshi. Washegari da asuba kafin ya dawo daga Masallaci ta fita ta koma dakinta,
yana dawowa dakin Humainah ya shiga ya tarda kwance ya karasa ya xauna kan gadon
yace "Sallah fah?" Tace "Nayi" yace "Ohk Gud morning" mikewa xaune tayi tace "Ina
kwana!" Yayi murmushi yace "Kin tashi lafiya" komawa tayi ta kwanta tace "Yeah"
yace "to babyn fah" bata ce masa komai ba hakan yasa ya mike ya fita. Bakwai da
minti goma ya sauka downstairs bayan yayi shirin fita aiki, kallo daya Zahrah da ta
gama ajiye kayan breakfast kan dining tayi masa ta dauke kai, ya isa kusa da ita ya
tsaya, ta gefen ido ta kallesa tace "Good morning" ya rungume hannayensa yana
kallonta jin bai amsa ba ta juyo tana kallonsa ita ma, karasawa tayi gabansa ta
langwabar da kai cikin sanyin murya tace "Gud morning" bai amsa ba still sai
kallonta da yake, can ya kamo hannunta ta fixge tayi masa buttoning masa button din
karshe na farin uniform din jikinsa ta kara gaba. Da yamma yana parlor xaune bayan
ya dawo daga aiki su kuma suna kitchen aka danna bell, mikewa yayi ya isa gun kofar
ya bude, El-ameen ne tsaye daga gefensa kuma Dr Sumayya, El-ameen ya wara ido yace
"ko mu koma" Junaid yayi murmushi yana kallon Dr sumayya ya bata hanya yace "Sannu
da xuwa Dr, bismillah" murmushin ta mayar masa ta shiga parlon tace "Yauwa Captain
ina daughter nah" yace "Uhm tana ciki bari in kirata" daga haka ya nufi kitchen,
xama tayi parlor El-ameen ma ya xauna tace "Allah sarki rayuwa, kamar ba ayi ba
yanxu koh?" Murmushi kawai El-ameen yayi, tace "Allah ya baku lada gaba daya....
Amma na so ace kai ka sameta ba wnn Capt mara son son jama'a ba" Junaid na shiga
kitchen ya kamo hannun Zahrah dake tsaye Humainah kuma na ta aikin, yace "You know
what princess, xaku gaisa da bakuwa yanxu, ta taimake ki ita ma sosai lkcn da baki
da lafiya, you stayed with her for 3 month ta kuma kula dake sosai, she's Dr
sumayya by name, tare suka xo da El-ameen" kallonsa kawai Zahrah take yayi murmushi
yace "Yeah princess," juyawa yayi ya kalli Humainah dake ta harkan gabanta yace
"Wife ki kawo masu drink pls" daga haka ya kama hannu Zahrah suka fita, kallonta
kawai Zahrah take kamar yanda ita ma Dr Sumayyar ke kallonta har suka karaso
parlon, Dr Sumayya ta mike tana murmushi ta bude mata hannunta, karasa Zahrah tayi
ta shige jikinta, Dr Sumayya tace "Am happy you are back my baby.... Alhmdulillah,
am happy for you baby" Zahrah ta rufe idonta da ya cika da hawaye Dr Sumayya ta
janyeta jikinta tana kallonta cike da tausayinta. Su El-ameen na barin gidan bayan
magrib Junaid ya shiga dakin Zahrah bai yi mamakin ganinta a sanyaye ba ya xauna
kusa da ita ya kamo hannunta yace "Yeah you owe a lot to her, after you loosed ur
memory ita ta rike ta kuma dinga nuna maki abubuwa, komawarsu abroad yasa kika dawo
gidana,then baki ma son rabuwa da ita you were crying xa ki bita" kallonsa kawae
Zahrah take, yayi murmushi ya lakaci hancinta yace "Yess princess..." Danna bell da
aka yi downstairs ya sa ya kalli bakin kofa can yayi peck din cheek dinta ya mike
yace "Am coming princess" daga haka ya fita ya sauka kasa, yana bude kofar yayi
still yana kallon wa enda ke tsaye bakin kofar, Hajiya ce ta kirkiri murmushi tace
"Ahmad, ina yini" bai amsa ba sai kallonta da yake, Umma dai sai wurga ido take,
Hajiya tayi karfin halin bin ta gefensa ta shiga parlon sai a snn ya juya ya bar
bakin kofar ya koma parlor, Umma ma ta shigo duk suka karasa parlon kamar masu
tsoron taka tiles din parlon, xaman sa yyi parlor suma suka shigo suka xaxxauna,
Umma tace "Sannu Ahmad ina yini ya aiki" sai a snn ya kallesu, can yyi kasa da kai
yace "Sannun ku da xuwa" washe baki Hajiya tayi tace "Sannu Ahmad, ya iyali" yace
"Alhmdllh" daga haka ya mike ya wuce sama, bin sa da kallo suka duk jiki yayi
sanyi, dakin Humainah ya shiga ya ga tana bayi, ya fita ya koma dakin Zahrah tana
nn yanda ya barta ya xauna kusa da ita ta kallesa tace "Waye?" Hannunta ya kama
yace "My step mothers" d'an bude ido tayi tace "You have them?" Murmushi yayi ya
daura goshinsa kan nata yana rike da hannunta yace "Yeah, and they don't like me"
tace "Why?" Ya girgixa Kai yace "tafi ki kai masu ruwa" ba musu ta mike ta fita,
tunanin abinda xai kawo su gidansa ya shiga yi, can ya mike ya koma dakin Humainah
tana xaune gaban mirror yace "Ki tafi ki gaida su Hajiya" tana kallonsa ta madubi
tace "Wace Hajiya" yace "warce kika sa ni mana" daga haka ya fita, ta kusa minti
biyar tana naxari kafin ta mike ta sa hijab ta fita. Kasa karasawa parlon tayi
yanda suke kallonta haka ita ma take kallonsu, Zahrah dai na xaune kasa bayan ta
kawo masu ruwa har da abinci, can Humainah ta karasa ta xauna ita ma kasa tana
kirkiran murmushi tace "sannun ku da xuwa" amsa ta suka yi ko Wanne na murmushin
dole, bata kuma cewa komai ba can dai ta mike ta koma sama, har aka yi isha Junaid
bai shigo parlon ba iyaka ya tafi masallaci ya dawo ya koma sama, can dai Umma na
kallon Zahrah tace "D'an yi mana magana da shi xa mu koma ne" mikewa tayi ta tafi
sama ta shiga dakinsa, yana danna laptop ta samesa ta karasa tace "Xa su wuce wai"
kudi ya ciro har dubu hamsin ya mika mata yace "Ki basu" xaunawa tayi kusa da shi
ta karbi kudin ta ajiye tace "Nooo, ka fito kuyi sallama" yace "Why?" A hankali
tace "From there expression sun yi regretting everything" yayi murmushi ya dago
fuskarta yace "And that's because basa gidanmu yanxu" tace "Kamar ya?" Mikewa yayi
yace "Am coming" daga haka ya dau kudin ya fita, xaunawa yayi parlon ba tare da ya
kallesu ba Umma tayi karfin halin cewa "Ahmad dama mun xo ne mu roki alfarmar ka
taimake mu kayi ma Alhaji magana mu koma dakin mu, sai kuma a yafe juna abubuwan da
suka faru a baya.... Sharrin shaidan ne" shi dai kansa na kasa can yace "Toh..." Ya
mika masu kudin yace "Allah kiyaye hanya" Hajiya ta karba tace "A'a har da wahala
haka Ahmad, to Allah yayi albarka" Ameen kawai yace ya mike ya nufi stairs yace
"Bari in kirata" daga haka ya haura sama. Yau Zahrah kin fitowa tayi xuwa dakin
Humainah don ma kar ya kuma kiranta dakinsa, duk ya kagu ya ji fitowarta amma shiru
har Karfe sha biyu, to ko dai har ta xo ta wuce bai sani bane, mikewa yayi ya fita
ya nufi dakinta, a hankali ya tura kofar ya ganta kwance, tana ganinsa tayi saurin
rufe ido ya karasa ya xauna gefenta yace "Yau baki tsoron kwana ke daya kenan?" Ba
tare da ta bude ido ba tace "Eh" wara ido yayi yace "Da gaske?" Xata juya masa baya
ya rikota yace "Jasmine" bude ido tayi ta mike xaune ta buda masa hannu alamar
what, murmushi yayi ya kamo hannunta yace "Nothing, m just missing you" tace "Ohk
thank you, Gud nyt" yace "Uhm korata kike?" Gyada masa kai
tayi yayi dariya yace "Ohk xan tafi, but you know what?" Kallonsa kawai take, ya
lumshe ido ya bude murya can kasa yace "Ba mu taba sallah tare mun roki Allah ya
albarkaci auren mu ba" tace "Ni na taba yi" ya buda ido yace "I mean togeda
princess, c'mon tashi kiyi alwala muyi sallah" tace "Ina da alwala na" ya d'ago
kanta yace "Gud" daga haka ya mike ya dau darduma ya shimfida masu, juyawa yyi yana
kallonta yace "Taso mana" ta nuna masa hijab dinta tace "Bani" yace "Meyasa baxa ki
dauka da kanki ba" tace "Nothing" murmushi yayi ya dauko ya mika mata ta sa sannan
ta mike. Nafila ya ja su raka'a biyu, ya jima xaune yana addu'a bayan sun sallame
snn ya juya yana kallonta, murmushi ya sakar mata ya dafa kanta, a hankali yace
"Let me pray for you princess" rufe ido tayi bata ce komai ba har ya gama sannan ta
bude ido tana kallonsa, langwabar da kai tayi tace "Is that all" ya gyada mata kai,
ta mike ya bi ta da kallo, kofa ta bude ta juyo tana kallonsa tace "Gud nyt, I want
to go to bed!" Wara ido yayi yana kallonta can yayi murmushi yace "Oh korata ma
kike ko?" Girgixa masa kai tayi tace "A'a bacci xan yi ne" yace "toh ni a nan nake
son in kwana" shiru ta d'an yi tana kallonsa can tace "Ohk," ta rufe kofar ta dawo
tayi kwanciyarta ta ja bargo tace "Gud nyt" kai kawai ya gyada mata, kusa minti
goma xaune snn ya mike ya kashe wutan dakin ya dawo ya kwanta ya birgina kusa da
ita, Juyowa tayi da sauri murya can kasa yace "Baki yi bacci ba" "Uhm" kawae tace
xata kuma juyawa ya jawota jikinsa. Washegari da asuba ko da ya fito daga bayi bai
tarda Zahrah a dakin ba, tsaye yyi dakin don yasan baxata je dakin Humainah ba,
bude kofar yyi ya fita ya bude dakin dake kusa da nata, nan ya ganta kwance ya
karasa ya durkusa kusa da ita a hankali yace "Zahrah!" Idonta rufe yake, ya mike ya
xauna kusa da ita ya dago ta yace "Nasan kina jina, open ur eyes pls" ganin baxata
bude idon ba ya rungumeta cikin sanyin murya yace "Am sorry Jasmine" dumin hawayen
ta ya ji a bayansa, ya dago kanta ta rufe idon da sauri.
3 month later.
Zahrah na daki kwance bayan junaid ya fita aiki, tana chatting da 'yar uwarta ummi
taji kamar Humainah na kiranta, mikewa tayi ta ajiye wayar ta fita ta shiga
dakinta, durkushe ta ganta dakin ta karasa da sauri ta durkusa kusa da ita tace "Me
ya faru?" Humainah ta dago da kyar tace "Am not okay" mikewa Zahrah tayi da sauri
ta fita xuwa parlor, Mama jummai dake goge goge ta kalleta ganin yanda ta sauko a
rikice tace "Me ya faru Zahra'u?" Zahrah da ke shirin kuka tace "Wai tace min bata
da lafiya ban san me ya sameta," mikewa mama jummai tayi ta haura sama da sauri ta
bude kofar Humainah ta shiga, dagota tayi tana mata sannu ta kalli Zahrah tace
"Maza je ki yi ma driver magana mu tafi asibiti" da sauri Zahrah ta kuma fita don
yi ma driver magana, ita kuma mama jummai ta fito da Humainah da banda daurewa bbu
abinda take, kafin su isa asibiti sai ka rantse Zahrah ke nakuda, duk ta cika masu
kunne da koke koke ganin yanda Humainah ke wahala, ana shiga da Humainah dama ta
kira junaid, yana dagawa ta fashe masa da kuka tana cewa "captain kaga kila haihuwa
xata yi ka xo pls, she's in pain" Mama jummai ta karbe wayar tace "Rabu da ita soja
kar ta daga maka hankali, ka taho muna asibiti" daga haka ta katse wayar don ko ba
a gaya mata ba tasan Zahrah ta gama ruda shi, karban wayar Zahrah ta kuma yi tace
"xan kira Mumy" Mama jummai ta karbe tace "A'a ki bari sai ya xo kin ji, in shaa
Allahu xata sauka lafiya ki daina kukan nan" ba a dau lkci ba sai gashi ya taho
asibitin, da sauri ta je ta rungumesa ta kuma fashe wa da kuka tace "My prince ni
daga yau kar ka sake ce min xan haifan maka yara bana so" kallonsu kawai ake a
reception din wasu na dariya kasa kasa, ya kamo hannunta yace "Ohk princess na
daina" ko minti uku bai yi hospital din ba Humainah ta haifo santalelliyar 'yar ta,
sai dai kuma bata san ma wa enda ke kanta ba, nan hankalin Junaid ya tashi, mama
jummai ce tayi karfin halin karban yarinyar bayan an fito da ita, Zahrah kam tun da
abinda likitan ya gaya ma junaid ya samu shiga kunnenta ita ma ta dinga rusa kuka
ita fa sai ta shiga wajenta, har sai da nurses suka fita da ita daga reception din
ma gaba daya, wata nurse da gulma ke ci ta isa gun mama jummai da tayi jigum tace
"Allah sarki yar uwarta ce wancan da aka fitar ko?" Mama jummai ta girgixa kai a
sanyaye tace "Kishiyarta ce" nurse din ta kwalalo ido sai kuma ta juya ta koma gun
sauran nurses din ta fesa masu abinda ta ji su ma. Ba karamin karfin hali Junaid
yayi ba ya kira Abba ya sanar da shi haihuwar ya kara da cewa bata da lafiya bayan
ta haihu, kafin minti ashirin sai ga Mumy da su Umma da Hajiya sun iso asibitin,
duk hankalin Mumy ya tashi suna asibitin har dare bbu wani improvement, Abba ma har
ya xo ya koma shi ma rai ba dadi, karfe tara Mumy ta koma gida da Zahrah, sai a snn
Junaid ya tuno da El-ameen don duk Zahrah ta gama rikita masa lissafi ya ma rasa da
wanda xai ji, cikin few minutes El-ameen ya karaso clinic din, da yake yawancin
doctors din ya san su yana neman alfarmar a bar sa ya shiga gun Humainah aka barsa
ya shiga tare da wasu doctors biyu, ba a dau lokaci ba ya fito nan ya shiga kwantar
ma Junaid hankali yace "Don't worry frnd she will be Alryt, tayi loosing blood ne
da yawa amma xuwa gobe xa ka ga she will be okay, haihuwar ne yayi gardama"
kallonsa kawae Junaid yake, El-ameen yayi masa murmushi assuringly yayi Pat din
shoulder dinsa sannan ya isa gun mama jummai ya karbi babyn ba tare da ya kalli su
Umma dake gun ba. Washegari kamar yanda El-ameen ya fadi cikin ikon Allah jikin
nata da sauki sosai kamar ba ita ba, murna gun Zahrah kamar xata yi yaya, haka duk
ta bi ta takura babyn da riko ta ki kwantar da ita, ba ita ba hajja dake ta mata
gorin ita ma tayi tayi ta haifo nata dai, Da taji ance mata haka mood dinta ke
canxawa, junaid sai dai yayi dariya can ciki, kwanan su biyu asibiti aka sallamesu,
a ranan kuma Umman Zahrah da Ummi sai Kanwar mai martaba suka iso katsina don yin
barka, kaya ba na wasa ba suka yi ma Humainah da jaririyarta, hajja ta rasa inda ta
sa su don murna, kwanansu biyu suka koma bauchi, ranan suna baby ta ci sunan late
mum din Humainah fatima, washegari Hajja ta tattara Humainah da yar ta suka yi gida
tare da mama jummai wai sai ta gama mata wanka xata dawo, Zahrah bata ji dadi ba
amma bata ce komai ba don tasan balbaleta Hajja xata yi, da daddare tana dakin
Junaid tace "My prince ya xa mu dinga kiran babyn?" Junaid na danna laptop din
gabansa yace "Amm baby xa mu ce koh?" Tace "Noo let call her Jasmine" kallonta yayi
yace "No, I have a wife Jasmine...." Tace "yess, a wife Jasmine, a daughter
Jasmine" murmushi yayi yace "Ohk, to ke yaushe xa ki haifo min naki babyn, nd I
want two boys" bata rai tayi sosai ta mike xata fita ya fixgota ya rungumeta, ta
fashe da kuka tace "My prince ni ka daina cewa xan haihu Allah bana so" ya buda ido
Yace "Toh sbda me?" A hankali tace "Kana son in mutu koh" danne dariyarsa yayi yace
"Nooo, bana son ki mutu wife toh naji kiyi ta rike babies din nawa a ciki koh?" Kai
ta gyada masa ya kankameta yana dariya, tace "My prince I want to continue with my
education" shiru ya d'an kafin yace "Ohk" amma da jin ohkn kasan fadi kawai yayi,
har aka yi bikinsu fatima da khadija Hajja bata bari Humainah ta dawo dakinta ba,
ae ko tana tafiya kai amare ya dauko matarsa suka yi gida, Zahrah dai na rungume da
Jasmine da tayi wayo sosai, yarinya me kyau da ita komai na babanta ne jikinta.
Satin Humainah daya da dawowa Zahrah ta dinga yi ma junaid magiyar ya kai su
bauchi, ko kadan bai son bacin ran princess din tasa washegari ya daukesu gaba daya
ya kai su bauchi shi ya koma gida, iyayen Zahrah basu nuna banbanci tsakanin yar su
da kishiyarta ba, komai aka ma Zahrah sai an mata hatta gwalagwalen da aka ba
Zahrah sai da aka ba Humainah sak irinsa, kwanansu biyar Junaid ya koma ya dauko
su, da daddare yana kwance Humainah dake shirya Jasmine tace "Ya Ajay?" Kallonta
yayi yace "Wife!" A hankali tace "Plss ina son kayi min wani alfarma" mikewa xaune
yayi ya jawota jikinsa yace "Ina jin ki dear" sauke idonta kasa tayi tace "Ina son
ka raba mana gida da Zahrah" shiru yayi na kusan minti uku kafin yace "Sbda me?"
Hawaye ne ya cika idonta tace "Bana son ranan da xai xo mu fara xama irin na
kishiyoyi da ita, bana son komi ya hada ni da ita, idan bama tare za mu ta xumuncin
mu bbu abinda zai hada mu plss dear" shafa kanta yayi yace "Hakan baxae tafa faruwa
ba wife, Zahrah me saukin kai ne kema kin sani, snn the both of you kuna da ilimin
addini baxa kuyi kishi mara amfani a kai na ba, bana son raba kan family dina I
want to see you both together" shiru tayi bata ce komai ba, yayi peck din cheek
dinta yace "Yeah wife" a hankali tace "Toh school fa ya Ajay" murmushi yayi yace
"Duk sai kun gama haifa min kidz dina xa ku koma sch" kallonsa tayi ya wara ido
yace "Yess wife" Washegari da ya kasance sunday Humainah na gama hada breakfast don
ita ce da girki snn ta koma sama, tayi mamakin rashin saukowar Zahrah which is very
unusual, dakinta ta shiga tana cewa "Antyn Jasmine," don haka take kiranta, Kwance
ta ganta tana bacci ta karasa ta tada ta Zahrah ta bude ido ta mike xaune tace
"Momyn Jasmine" Humainah tace "Ki sakko muyi breakfast" toh kawai Zahrah tace mata
ta juya ta fita, Mikewa Zahrah tayi ta shiga bayi ta wanke baki sannan ta fito,
Junaid na xaune dining yana danna waya Ita kuma Humainah na serving din breakfast
din, xaunawa Zahrah tayi Junaid dake kallonta ta gefen ido ya harde kafarsa da nata
ta karkashin dining table din, turo baki tayi bata ce komai ba, ya matso da
kujerarsa a hankali ya daura hannunsa kan cinyarta, buge masa hannu tayi ta mike ta
koma wani kujerar dake nesa da nasa, murmushi Humainah dake lura da su tayi ta gama
zuxxuba masu tayi xamanta ta fara cin nata, Junaid ma ya dau nasa ya fara ci,
Plantain kawai Zahrah ta dauka ta Kai bakinta ta fara ci bata gama hadiyewa ba ta
mike da sauri duk suka daga Kai suna kallonta, juyawa tayi ta bar dining din da
gudu ta haura sama, bin ta da kallo duk suka yi, Humainah ta tallabi kuncinta tana
murmushi tace "Hmmm" don kusan sati biyu kenan da ta gaya mata ita fa bata ga
period dinta ba kamar xata mata kuka take gaya mata, kwantar mata da hankali kawai
tayi tace ai yana yin haka wani lokacin, sai a snn ta kwantar da hankalinta ta ci
gaba da harkokin gabanta, kallonta kawai junaid ke yi ganin irin kallon da take
masa, can yayi murmushin shi ma ya mike ya bi bayan Zahrah, xaune ya ganta bakin
kofar bathroom dinta har ta gama aman, ya durkusa da damuwa yace "Ohh sorry
princess, plantain din ne baki so" bata iya tace komai ba ta mike da kyar ya riketa
tace "Am feeling dizzy my prince" daukarta yayi ya kwantar da ita yayi kan gado
yace "Toh bari mu je asibiti koh babyna" girgixa masa kai tayi tace "No I will be
Alryt, bacci xan yi" ya jima yana kallonta har ya ga kamar ta fara bacci ya mike ya
fita, yana sauka kasa Humainah ta wara masa ido tace "Congrat My Capt" xaunawa yayi
kusa da ita ya jawota ya rufe bakinta da yatsa yace "Shiii don't tell her that
plss" dariya tayi sosai tace "Ohk ohk"

*Haske writers association*💡

⚓ *captain Ahmad Junaid*⚓

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

End

Har dare Zahrah na kwance gashi ta ki cin komai duk jikinta yayi xafi, da yace su
je asibiti sai tace no allura, shima dama tsoron kai ta yake don yasan ba karamin
aiki xai yi ba idan ta gano sanadin rashin lafiyar nata, kwanaki uku ta dauka tana
wahala, ganin duk ta jigata yasa kawai ya kira El-ameen sai ya lallabasa yayi mata
treatment kawai ba tare da ya gaya mata me ke damunta ba, ya ji ddi da ya kasan ce
mama jummai taje kauyensu da ta tona dalilin rashin lafiyan nata, dariya kawae El-
ameen ke yi bayan junaid yayi masa bayani, Junaid yace "Plss frnd bana so ta sani
daga min hankali xata yi wllh" El-ameen yace "Alryt I won't let her know, ni ma my
Hafsat is pregnant" Junaid yace "Ohh Congrat, Allah ya raba lafiya" El-ameen na sa
mata ruwa bacci me nauyi ya dauketa, haka suka ci gaba da lallabata El-ameen na
xuwa bata allura yana sa mata ruwa, har bayan sati uku taga ciwo yaki tafiya nan ta
fara tunanin ko dai ciki ne ma da ita don har lkcn bata ga period ba, mikewa tayi
da kyar tana ganin jiri ta dauko wayarta ta yi Google din signs and symptoms na
pregnancy, nan taga duk abubuwan da take ji a jikinta a lissafe gun bata san lkcn
da ta wurgar da wayarta ba ta mike da gudu ta fice sai dakin Junaid ya fito daga
wanka kenan ta fixgoxa ta fashe da kuka sosai tace "Na shiga uku my prince kila I
am pregnant ne" xaro ido yayi irin yayi mamaki din nn yace "Pregnant kuma, wa ya
gaya maki" a rikice tace "I Googled it, kuma I've missed my period for a long time,
plss my prince mu je asibiti a cire na shiga uku mutuwa xan yi kila baxan iya
haihuwa ba ka taimakeni plss" tana kuka sosai ta kare maganan, ya danne dariyarsa
ya rungumeta ya isa kan gado da ita, ya kai bakinsa kunnenta yace "Haba my
princess, Toh ba ga Humainah ba ta haifi nata bbu abinda ya sameta, kuma tare fa xa
mu haifa babyn" cixo ta kai masa a kirji tace "Nooo baxan iya ba mu tafi asibiti
plss" yace "Nooo bbu inda xa mu je ina son babyna, I want to see my little prince
or princess, baki son ki ga royal kidz dinki wife?" dagowa tayi tana kallonsa a
rude ta kuma fashe wa da kuka tace "My prince saura kadan fa Momy Jasmine ta mutu"
rungumeta ya kuma yi yace "Baxa ki mutu ba sai kin haifa min royal kidz my
princess, sai mu kai ma Umma kinga she will not be lonely again ga ta ga princes
and princesses dinta" shiru tayi hawaye na sauko mata, yayi murmushi yana shafa
gashinta yace "Yeah tare xa mu haifo su wife" cikin kuka tace "Promise?" Yar dariya
yayi yana shafa cikinta yace "I promise my princess" rungumesa tayi muryarta na
rawa tace "Ohk, xan haifi babyn sai mu kai ma ummata" yace "Waoww yauwa my royal
wife, nd Umma will be very happy..." Kallonsa tayi yayi mata gwalo ta turo baki
sannan ta tura cikin nasa ya shiga kissing dinta.

Hmmm! Alhmdulillah a nan na sauke littafina mai taken *Captain Ahmad Junaid* kura
kuren da nayi a ciki Allah ya yafe min, na kuma sadaukar da littafin nan xuwa ga My
Sweetest bro like no other, my abokin fada, my abokin argument, infact my
everything *Ahmad M Bello* da kuma my best frnd, my abokin shawara, the handsome
tall d'an Fulani, the great *Captain Ahmad Junaid murnai* Allah ya albarkaci
rayuwar ka, ya kare ka daga sharrin mutum da aljan, ya baka mace ta gari ya rabaka
da iyayenka lafiya ya kuma bar mu tare, ka girma in baka daughter nah, uhm bari in
bar sa haka kada ya ji sa wane jirgi a sama Lol.
My sweet Mum Allah kara maki lafiya da duk musulmai baki daya, ya dawo min dake
lafiya am missing you so muchh, My sweetest Big mum Ummu Aneesah am grateful for ur
encouragement from the Beginning of this novel to the end, Allah raya maki Jamcy da
Humy, sai dai kinsa my Novel is not that romantic oo Lol🙈 My greetings goes to all
the occupant of Haske asso, Allah ya kara hada kawunanmu, I hail you all with
respect, where are you my Ummu Shakur, fido s Dangi, phatiemarkh, Asmy b Aliyu,
Hafsat Ummu ilham duk ina gaida ku and am grateful for the encouragement alwayz,
and finally my fans!!! words alone can't express my feelings toward you all, sai
dai kawai ince Allah bar xumunci ya bar mu tare ina sonku, ina alfahari da ku, ina
ji da ku har kullum, My brother from another mother *Anas Sufyan* tnx for the
tsokana and everything from d beginning of C.A.J to the end, ban mance ki ba
*Sharifata* a sister from another momma tooo.
Hmm my siblings _Maryam, Fatima, Baby, ilham, Ameer, Fadil, Sudais, Haiydar and
my Umar am missing you all_😘

Taku har ko da yaushe *Jiddah M Bello* A.k.a *Khaleesat Haiydar/ Lag~Lady*

✍🏻
Na bar ku lafiya fans

You might also like