Shalelan Baba CMPLT
Shalelan Baba CMPLT
(Romance)
She is a very very poor girl HANEEFA, who fell in love with one person, he is rich
man, nd beautiful, miskilin gaske, duk inda kake tunanin masifa tashi ta wuce nan
karku Bari abarku Abaya wajan Jin Yaya wannan story zai kasance
💕SHALELAN BABA 💕
💕SHALELAN BABA 💕
COMING SOON
✍🏻
Mrs Usman ce
[10/8, 10:31 PM] SHALELAN BABA: 💕SHALELAN BABA💕
(Romance)
Ina Fata da burin kasance war mu tare my fan's, Allah Kuma yabani ikon gama wannan
labari lafiya Kamar Yanda nafara 🙏🏻
Daga marubuciyar :
🌱DANA SANI🌱
(Ahmad&Feenah)
💞BURINAH💞
(Amal&Daddy)
💖WAZAN ZABA?💖
💕SHALELAN BABA💕
Is loading...
Bissmillahir-rahmanirraheem
1&2
Tsugunne yake agabanta,hannunsa riqe da Kambos na yara Yan makaranta fari qal dashi
Mai kyau, yayinda ita Kuma take atsaye, tayi tsananin kyau cikin uniform dinta na
makaranta,wandon dark blue ne, yayinda rigar ta kasance white blue, Dan qaramin
hijabi ne ajikinta fari wanda ya Qawata kyakkyawa fuskarta aciki
dago kansa yayi yadubeta da tsananin soyaiya da kulawa yace Shalele nah saka
takalmin naki mana banaso kiyi latti wani malamin ya tabamin lafiyarki
Bubbuga kafafunta tafara aqasa cikin shagwaba tace Allah baba ni Bansan wannan
Kambos din, baba yaufa zamu gama makaranta, nide saide ka daukomin wannan sandal
din daka siyomin jiya, wannan dinfa satinsa daya baba, taqarasa maganar tana turo
masa baki gaba
Murmushi inna Marka tayi, ta dafa kafadarta tace haba Shalele, yanzu menene laifin
wannan takalmin,?
Murmushi Baba yayi yace "Kinga Marka dauko mata wancen din saita saka"
Duban ta inna Marka tayi tace to jeki cikin kwabet Dina zaki ganshi aciki saiki
dauko
Karba tayi takai shi cikin yar qaramar barandar datake gaban dakinsu, sannan ta
nufo wajan baba da wani Kofi ahannunta
Daqyar tagano takalmin nata ta futo dashi, Kai tsaye wajan babanta ta nufa
Baba gashi
Safar tabashi, ahankali yakama farar kafarta da yatsun kafar suke dogaye Zara Zara
dasu gwanin sha'awa, saka mata safar yayi tana Daga tsayen saide ta Dora hannayen
ta akafadarsa, Saida yagama saka mata sannan yasaka mata sandal dinta
Murmushi yayi kawai, cikin ransa yana yaba tsananin hankali da nutsuwa dakuma uwa
uba kunya da Allah yabawa yartashi qwaya daya jal
Kinga Shalele karbi wannan kwastadin naki Kisha, kada kitafi da yunwa, inji inna
Marka
Babu musu tace to inna, tsugunna wa tayi, ta karbi kofin zata sha, baba yace a a
Shalele nah, kawo nabaki da kaina
Cikin nutsuwa yake Bata, Saida takusa shanyewa sannan tace baba naqoshi
A a Shalele nah, bakyason cin abinci, daure ki shanye shi duka, bazaki dawo gidaba
sai Bayan sallar zuhur
Bata musu da mahaifinta, dole haka ta karba ta shanye da kanta, domin yaji dadi,
suna gamawa, sukayi wa inna sallama tace to Maigida a dawo lafiya
Ya amsa da ameen, suka fice, suna Zuwa bakin kofar gidan, taci uban tuntube da
bakin kofar gidan, dasauri baba yace yi Ahankali Shalele
To babana muje
Kekensa yadauko yahau sannan itama tahau kan kariyar keken, yaja suka tafi, basu
zame ko'inaba sai makarantar su, dalibai dayawa atsaye afilin makarantar wasu Kuma
a zaune, Daga saman ginin makarantar Naga an rubuta Government day junior school
kuje local government
Tana sauka sukayi sallama dashi tayi wajan sauran daliban, yana tsaye yana
kallanta, tareda jiran yaga shigarta ciki sannan yajuya yatafi gida Kamar Yanda
yasaba duk ranar Allah
Tana tafiya tana waigensa ta nayi masa bye bye, mutane da yawa dasuke wajan ba
qaramin birgesu sukai ba, irin wannan soyaiya ta 'ya da uba
Saida yaga shigarta sannan yaja Kekensa yatafi gida, yana shiga gida ya ajiye
Kekensa agefe, inna Marka tana masa barka da Zuwa, ya amsa yana tambayar ta, Marka
Ina tsohon gatarin nan nawa?
Tsananin mamaki ya Kamata tace gatari Kuma Maigida? Mezakayi dashi kaida bame
faskaren itace ba?
Yana Zuwa wajan yafara saran kofar gidan nasa da gatarin, duk wani tudu da gangare
Saida ya sai tashi yabaje qasar wajan
Haba Maigida, yanzu fisabilillahi kofar gidan nan kalau da ita Amma haka kawai kasa
gatari kadinga saran kofa Kamar Allah ya aikoka?
Dagowa yayi, yana goge Dan gumin daya Tara yace, Shalele nah ce tayi tuntube da
wajan dazu, shine nake baje qasar wajan, saboda kada naje Garin shige da ficenta,
tasake wani tuntuben (😳)
Yanzu Maigida saboda Allah akan wannan shine kake ta haqilo kaida gatari?
Wato Marka Naga alama bakisan Yanda Shalele take arainaba shiyasa kike wannan
maganar, to dazu datayi wannan tuntuben jinsa nayi Har cikin Raina, abin baimin
dadiba
Wani wajan yasake kaiwa duka da gatarin yana fadin ameen Marka, batare daya kalleta
ba
** *** **
Su HANEEFA manya, wato de Har yanzu ke bazaki hutar da babanmu ba Ko? Kinsa bawan
Allah kullum saiyazo daukar ki Bayan ya kawo Ki da kansa
Wata Daga cikin qawayen ne tace majidah ba HANEEFA zaki Ceba, Shalele zakice, Wai
Shalele saikace wata yarinyar goye maishan mama
Cikin damuwa da kalaman nasu tace yau naji jaraba, babanku Ko babana, Shalele shi
nakeso danhaka dashi zaku kirani, bawani Haneefa, haka kawai ga sunan da babana
yake kirana, Shima yanajin dadin sunan ne shiyasa yake kirana dashi, ai yasan da
haeefan
Wata Daga cikin su maisuna nasiba tace, to maji magani, yarinya Gara ma kidawo da
ainahin sunanki, bawani Shalele ba, Tunda girma kike kina qara zama yanmata, inba
hakaba samarin Garin nan wallahi Raina ki zasuyi
Itama tace eh naji Shalele na nakeso, ai ni Har yanzu inde awajan babane, to a
yarinya ta nake, nida zai maidani ciki ma saboda tsabar yarinta da bazan qiba
Sabira tace wanne irin yarinya kike magana Haneefa? Ga qirgen dangi nan akirjinki
zaki dinga kawo wa kanki yarinta, to ai kuwa Ana kaiki gidan miji zama zakiyi daram
yarinya
Kafin tayi magana Taji saukar Dan karamin duka abayanta, dasauri tajuya, tana ganin
fuskar me dukan nata tace Kai Kai kai fadila sani miye Hakan?
Gani tayi duka qawayen nata Suna Daria, nasiba ce tace Rabu dasu Haneefa, Wai so
take Taji kokin fara saka breziya shine ta wayance da dukanki Abaya, ashe ke
bakisan wannan sarar tasuba
Da mamaki Shalele tace wacce irin brezia Kuma Ana zaune lafiya?
Still nasiban ce ta dubi wadda tayi dukan tace fadila to kinji de abinda Shalele
tace, babu ita ba brezia yanzu, inajin sai anyi auren mijin nata zai aunasu da
kansa, idan yaji adadin girmansu saiya siyo mata wadda zata mata
Shalele zata sake magana aka kada musu qararrawar shiga aji, danhaka Bata Cewa
nasiba da fadila komai ba sai harara data bisu dashi, suka miqe Dukansu suka shiga
aji
Suna zama malamai suka fara Raba musu questions paper, sannan aka basu umarnin
farawa, daliban na kalla Dukansu bazasu wuce 14 to 15 ba
Suna gamawa kowa yafara futowa, kowa kagani yana dauke da Murmushi a fuskarsa
Kowa nagama futowa Aka fara photuna, maza da mata wannan yakira wannan ayi musu
photo wannan ma yakira wannan
Sai can gab da la'asar suka fara watsewa, itama itada qawayenta suka futo, suna
tafiya Ahankali, yayin da suke fira cikin nutsuwa,
Sunyi Nisa sosai akafa ta hango baba yana tunkaro su, cikin Murmushi tace to nide
babana Yazo, sai anjimanku dalibai
Dukansu sukayi mata caaa kowa Yana tsokanarta, Daga me Cewa to Shalelen baba sai
munkawo Miki ziyara, sai Mai Cewa to Haneefa sai anjima, Sabira cede ta Daga murya
tace Yarinya ba sai anjima ba kihau keken nan de Ahankali wallahi kada kiyi wa
angon ki asara, Dan me rabaki dashi sai Allah ehe mude ba ruwanmu
Gaba dayansu suka kwashe da Daria, itama murgudawa Sabira baki tayi, sannan tayi
wajan babanta, ta Dane keken suka nufi gida, suna tafiya baba yace,Shalele nah ya
jarabawar?
(wannan page din na farko zan tura shi akowanne group, duk group din dasuke so naci
gaba da sambado musu, sai sumin magana 💁🏻💁🏻💁🏻💁🏻💁🏻)
✍🏻
Mrs Usman Ce
💕SHALELAN BABA💕
           (Romance)
Writing by Amnah El
3&4
Eh baba sai mun gama hutun sannan zamu shiga ss1, a lokacin exam dinmu ta futo
Hankalinsa yana kan tuqin keken dayake yace Ai jarabawarku na futowa kokari zanyi
in sauya Miki makaranta Mai kyau ta kudi, ke inda Hali ma makarantar kwana zan
kaiki
Dasauri tace a a baba, nikan banaso nayi neda dakai da inna
Murmushi yayi yace to ya zamuyi Shalele nah, neman ilimi aiya zama dole, keda
kikeso kiyi ilmi me zurfi kizama lauya, Ko bakyason ki ganki acikin wannan babbar
rigar baqa, wadda lauyoyi suke sakawa,?
Inaso baba, Amma ni Bansan yin nesa dakai Ko kadan baba, sannan baba bakada kudi,
Kawai zanci gaba dayin day din
Kiyi wa babanki Addu'ah, Allah yahore masa kinji?idan inada Hali zan Iya kaiki Har
qasar qetare, kije kiyi karatun ki, nasan bazaki bani kunya ba, saboda nasan irin
tarbiyar Dana baki
Amin Shalele nah, suna tafe Suna firar su Har   suka je gida
Suna Zuwa gidan tashige da gudunta ta rungume   inna, itama cikin Daria tace oyoyo
Shalele nah, to Yaya jarabawar? Allah yasa de   kinyi da kyau
Nayi inna, yaude gashi mun gama junior, saura   Kuma senior insha Allah
Tashi tayi ta dauko mata abincin ta, ita Kuma ta shinfida tabarma a birandar tasu
ta zauna akai domin taci abincin
Baba ne yashigo ya jingine kekensa agefe, inna tace maigida ga abincin Naka fa,
abude shi yanashan iska ne?
Yace a a Marka, bani nafita dashi waje, Naga Malam yahai a zaune, saimuci tare
Dauka tayi ta meqa masa, Yadubi Shalele data bararraje atabarma tanacin abinci,
yace Shalele nah Bana hanaki cire Dan kwalin ki bane?
Banasan barin gashi awaje fa
Cikin ladabi tace to baba,Saida takama doguwar kalbar datake yawo agadon bayanta da
ribom sannan tadauki Dan kwalinta ta daure kanta dashi
Ficewa yayi daga gidan yana Cewa Marka Dan Allah kisata tashirya da wuri saboda
kada tayi lattin islamiyya, banason abinda za'a zo Ana dukan nan nata Kamar sun
sami jaka
Ta dubi Shalele tace toke kiyi ki maida hankali kiqarasa kije ki watsa ruwa kutafi
Tana gamawa tashige wanka, Bata batalokaci ba tashirya, cikin uniform dinta, wandon
ruwan toka, sai farar riga wadda tsawon ta yakai mata Har gwiwa, dakuma farin hijab
Sallama tayiwa inna tace inna natafi saina dawo, inna tace to Shalele a dawo
lafiya, ayi karatu da kyau kinji? To inna tah
Tana fita taga babanta da Malam yahai maqocinsu, Har qasa ta tsugunna tana gaida
shi, tace baba Malam Ina yini?
Yana kawo idonsa wajan kafar Tata yataka birki, lokaci daya duk ya rikice,
subhanallah, Shalele kice naji Miki ciwo, kiyi hakuri kinji yata
Ganin duk yabi ya rikice ne yasa ta boye jin zafi da radadin da kafar take mata,
tace baba babu zafi ba
Cikin ranta kuwa kukan zuci take, saboda ita Abu kadan ne zai sata kuka, babanta ya
riga daya gama shagwaba ta, gaba da baya
Haba Shalele ya zakice babu zafi Bayan ga jini yana fita Daga jikin ki, Bari muje
chemist, kinji
Kan keken sa yajuya Daga hanyar makaranta Zuwa chemist, suna Zuwa tasauko suka
shiga ciki, tana dingisa kafar
Cikin damuwa baba yayi masa bayanin komai, mai chemist din ya nuna mata kan benci
yace ta zauna
Babu musu ta zauna, shikuma baba yana tsaye, kayan aikinsa yadauko, yakama kafar
Tata zai wanke mata
Yana zuba mata hydrogen tafara yarfe hannu, tace wayyo Allah na Baba zafi, nan da
nan sai hawaye
Shi kansa baban dayaga Yanda wajan yake kumfa nan take ya runtse idonsa
Mai chemist din ya kallesu gaba dayansu, shi sai suka bashi Daria ma, wannan Dan
ciwon akewa wannan abun, ita tana kuka shi yana runtse ido, to ciwo ma akai masa
haka inaga haihuwa Kuma?
Saida yagama wanke mata kafar tass sannan yadago kansa cikin Murmushi yace Alhaji
nagama, sai a sannan baba yabude idonsa yace to nawane kudin?
Yafada masa kudin, baba yabashi kudin sa, sannan yasai mata magunguna yazuba musu
aleda, maimakon yabashi saiya miqa mata yace gashi qanwata riqe wannan kije waje
kijirashi, ta karbi ledar maganin tafice tana dingishi
Tana fita, mai shagon Yadubi baba yace baba Dan Allah a kiyaye gaba kada tasake jin
wani ciwon, kasan karfe bashida dadi, idan akwai datti tetanus zai iya shiga cikin
ciwon nata, Kuma koba haka bama ita mace ce, Yawan Hawa keken bashida amfani
Ajiyar zuciya baba yasauke yace to likita insha Allah za'a kiyaye
hannu Mai chemist din yabashi suka sake sabuwar musabaha sannan baba yafuto   Daga
shagon
                                                                         😃
Suna Zuwa wajan keken, yace Shalele nah zaki Iya Hawa kuwa kona doraki?( )
A a baba karka damu zan Iya wallahi
Karka to mata yayi Bayan yahau yace to hau muje, tana Hawa yace mu tafi gida
Shalele nah, yau Kam babu inda zakije, ke gobe ma haka, kiyi zaman ki a gida
kihuta, zanje makarantar inyi musu bayani gobe insha Allah
✍🏻
Mrs Usman ce
💕SHALELAN BABA💕
           (Romance)
Writing by Amnah El
5&6
Suna qarasawa gida ya tsaida keken, yakamata ta sakko suka shige ciki
Inna na zaune abakin wuta tana girkin dare cikin firgici tace subhanallah menake
gani haka maigida? Meyasa meta?
Yana riqe da ita yace Marka babu lokacin amsa, yanzu de muje ki bude min dakinta ta
shiga tahuta
Dasauri taje takama qyauren dakin sannan ta dage labulen tace shigo da ita Malam
Shiga sukayi dakin, abinda yabani mamaki shine duk da dakin qasa ne,Bai rasa kayan
kallo da wata dundumemiyar katifa ba, agefe Kuma ga yar tsana nan ta wasan yara
manya guda uku
Kan TV din Kuma Fina finai ne na cartoon dayawa akai
Banda wayarin din da aka ja mata a dakin Kamar wata yar kansila
Inna tace Kinga hijabin naki ma jini yataba gefensa, kawo aje awanke Miki shi
Dasauri baba yace a a, karbi de kibayar dashi, Ko maqotane karbi kibasu, ita sai
asake mata wani
Dama ai ya tsufa hijabi aka saka shi Har tsawon wata daya Kuma ai yaci duniya, sai
ayi hakuri dashi
Inna tace to maigida tana fita Daga dakin, Shima fita yayi yace mata zanje wajan
Malam yahai yarakani can cikin kasuwa, insha Allah yanzu zamu dawo
Tsaye ta miqe tana daura Dan kwalin kanta daya kunce saboda shafar Kai datayi wajan
daura alwala
A a Malam lafiya naganka da machine? Mezakayi dashi Ko acaba zaka koma ja? Yanzu
Malam saboda Allah duk Yawan gonakin da Allah yabaka basu ishekaba saika siyo
mashin kafara kabu-kabu?
Inna da mamaki yagama kashe ta atsaye tace Anya maigida? Anya maigida turbar dakake
Dora Shalele akai kuwa me dorewa ce? Yanzu Malam duk gidan nan baka saka mana kayan
kallo ba, Amma ita kasaka mata, katifar damuke kwanta haqarqarinmu akai ta tsufa,
baka sake manaba Amma ta Shalele Bata shekara, Malam itafa mace ce, duk Daren
dadewa gidan wani zata
Ajiyar zuciya yasauke yace, eh lalle Marka sai yau ta tabbatar da abinda nake
zargi, Marka zarginki nake akan kulawar danake Bawa yarki ta tsaye Miki a maqoshi
ya qarasa maganar yana Dora hannunsa awayansa
Wai shin, Shalele tarbiya ta rasa Ko nutsuwa? Addini tarasa Ko ilmi,? Tataba yi
miki rashin kunya? Marka abinda nakeso ki Gane shine, zan Iya sadaukar da komai
nawa saboda Shalele nah, ita kadai Allah yabani, Dan haka Marka, yakama kunnansa
guda daya yace Iya gani....?
Kallanta yayi yace Yauwa ashe kin fahimta, yasakai yabar gidan domin Zuwa masallaci
sallar magrib
Tana Daga cikin dakinta tana jiyo maganganun iyayen nata, inda Sabo yaci ace tasaba
da irin wanan fadan nasu, Murmushi tayi Ahankali tace baba da inna ta Kenan
Shikuwa yana idar da sallar magrib yadawo gida shida wata yarinya Amma ta girmi su
Shalele sosai, inna Tana rumfa ta idar da sallah tana lazimi tagansu sun shigo, da
mamaki tace a a Ramatu kece a gidan namu?
Tana Daria Kasa kasa tace eh Wlhy innar hanifa, nazo ganin jikin Shalele ne
Kafin inna tayi magana baba yace a a Ramatu ki fada mata gaskiya Cewa Zuwa nayi
wajan mahaifinki Malam yahai na dauko ki, ki kula da Shalele Tunda ita uwarta
tafara gajiya da ita
Murmushi inna tayi tace Malam Kenan, sannan ta dubi Ramatu tace Ramatu wuce ki koma
gida kinji, kice Ina babar Taki, Ramatu Saida ta kalli inda baba yake taga yadaga
Kai sama alamun akusa yake, sannan tace to inna natafi, Allah yaqara kiyayewa gaba
Ramatu na fita inna tace yanzu maigida saboda Allah kaje Har gida kasako yarinya
agaba saboda kawai tazo ta kula da Shalele? Koka manta zawarci take? Kabarta Taji
danata yaran mana
, inde akan Shalele ne kayi hakuri insha Allah zan kula da ita, nayima wannan
alqawarin
Sai a sannan yasakko Daga dokin naqin dayahau, suka cigaba da firar duniya
Da daddare Yan makarantarsu Shalele sukazo dubawa Ko lafiya yau basu ganta a
Islamiya ba, malamai Sai tambayar ta suke, kasancewar yarinya ce ita Mai kokari da
hazaqa, kokarin ta ne yasa dayawa Daga cikin malaman nasu take mutuqar birgesu
Bayan sunga ciwon dataji ne suka mata sannu tareda tafiya gida
*******
Shalele kafa ta warke sosai, taci gaba da Zuwa makaranta, Daga bangaren baba babu
wani Abu daya sauya wajan Yanda yake nuna mata kulawa
Yau inna ta tashi da zazzabi sosai, akwance ta wuni, Shalele duk ta damu, baba ne
yadauki machine din daya siyowa Shalele yakai inna qaramin asbitin Garin, suna Zuwa
kuwa likita ya tabbatar musu da Cewa inna nada ciki harna tsawon wata uku da Rabi,
baba Kamar yayi hauka Dan murna, itade inna Murmushi tayi, domin kuwa ta riga da
tasan dama tana dashi, haka suka dawo gida da wannan daddadan labari, Shalele naji
ta dinga ihu da tsallan murna, itama zata samu kanwa Ko Kani
Ko a Islamiya data Bawa qawayenta labari, mamaki sukai tayi, ganin yanda take
murna, Kodan Bata ganin yaran ne a gidan su oho
*******
Tilin kayan wanki ne a hannunta ta futo dashi Daga daki, Daga murya tayi ta qwalawa
Shalele kira
Shalele!
Shalele!!
Da gudu ta futo Daga daki kanta Ko Dan kwali babu tace na'am inna gani
Watso mata kayan wankin tayi tace gashi nan maza dauke kije ki wanke minsu gaba
daya, ta Cilla mata nera hamsin, taci gaba d Cewa ki dauki kudin nan kifita waje
shagon ubaliyo ki siyo kilin kiyi maza ki wanke su ki shanya
Shalele Bata kawo komai aranta ba dasauri ta dauka tace to inna, asalima ita murna
take akan wankin da aka Bata kasancewar bayi take ba, Bata wani aikin fari bare na
baki
Hijabin ta tadauka zunbulele ta fita taje ta siyo kilin din tadawo tahau kan wanki,
ta nayi Ahankali harde ta ware tafara dirzar kaya, rana tazo tatarar da ita Har
inda take sunkuye tana wankin, gumi sai zirarowa yake Daga kanta
Inna   Tana kallanta tadora kafa daya Kan daya, tana girgiza jiki, alamun ashirye
take   d kowa, kara ta riqe a hannunta tana karkadawa tana Kallan Shalele da Rana
take   gasawa
Baba   yayi sallama yashigo gidan, turus ya tsaya yana Kallan Shalele, itama dasauri
tace   baba sannu da Zuwa
Da mamaki afuskarsa yace, a a Shalele nah kece kike wanki yau Kuma?
Bata bashi amsa ba sai Daria datayi alamun Ko ajikin ta
Qarasawa yayi cikin rumfar inna take zaune tana kallansu d'ai-d'ai
Asheqale inna t kalleshi tace au Wai danna saka Shalele wanki? Masassara ce ta
kamani shiyasa Naga bazan Iyaba nabata, Ko akwai damuwa akan Hakan?
(nikwa nace tofa wata sabuwa 🙄meyake shirin faruwa a gidan baba ne?
Writing by Amnah El
7&8
Be gama mamaki ba yaji tace, idan kinyi ga tukwane can, kije kidora abincin dare
Haka nayi niyya, idan zakiyi kiyi, idan Kuma ban Isa nasaki bane saiki fadamin
Jin wannan furucin nata ne yasa jikin Shalele yayi mutuqar sanyi, dariyar yaqe tayi
tace a a Bari in Dora
Shikuwa baba yayi Shiru yanaso yaga gudun ruwan Marka, yaga yau wani take take
takeji na rashin mutunci acikin gidansa
Wanke tukwanan tayi ta Dora tuwo da miya, dayake girkin nasu bawani me yawa bane
nan da nan tagama, a lokacin baba yana Daga cikin daki yana jiyosu, tazo tace inna
angama Shima
Tana karka da kafa tace saiki share gidan ai, ba Tsayawa zakiyi akaina kina kallo
ba
Daga murya yayi daga cikin dakin yace ke Shalele, kama hanya ki shirya kitafi
islamiyya, kada wanda yake daukar ki Yazo yaga yau kinyi latti
Saida ta kalli inna, Ko zata ce wani Abu, Taji innan tayi Shiru, danhaka tashige
cikin dakinta domin shiryawa, tana shigewa ta riqe bayanta alamun wajan ya amsa,
saboda rashin Sabo da aiki, agogon dakin ta kalla da sauri ta tashi tashirya cikin
uniform dinta, tadau jakar da littattafan islamiyyar suke ciki ta futo, tace inna
natafi
, Amma Kamar da qasa take magana, haka inna ta shareta, baba yasake Daga murya yace
jeki Shalele nah, Allah yakaremin ke a duk inda kike, Allah yabada sa'ah, Saida
tasaki Murmushi saboda jin dadin adduar dayayi mata sannan tace amin baba, tafice
da sauri, Zuciyar ta cunkushe da tunanin laifin me tayiwa innarta take wannan
fishin da ita, aide aiki ne tabata Kuma tayi, Amma meyasa yau gaba daya ta sauya
mata Kamar ba innarta ba?
Acan makaranta ma, anayi musu akdari haka malamin yagama yafita Amma abinda ta
fahimta Dan qalilan ne, sabira qawar ta dake gefenta, ta fahimci ba kalau takeba,
Dan haka tace HANEEFA SURAJ ADAM, meyake damunki ne yau gaba daya Kamar kina tunani
Ajiyar zuciya tasauke tace wallahi sabira, inna ce yau take fishi Dani, Bansan me
nayi mataba
Kafadarta ta dafa tace haba de, keda innarki da ba'a jin kanku? Nafi tunanin wani
laifin kikai mata, wanda ke baki saniba
Sabira tace to idan kin koma gida kibata hakuri, insha Allah komai zai wuce, Amma
yanzu de ki nutsu akan karatun daya kawomu
Cikin gida kuwa Shalele na fita inna tahau fada, amma de Malam kasan abinda kake yi
a gidan nan baka kyauta wa Ko? Yanzu Kenan ni ban Isa da wannan yarinyar ba?
Shikkenan komai sai abinda kace zatayi? Yarinya babu wanda isa da ita, harni zansa
ta aiki Amma kasa yarinya qanqanuwa ta bijiremin
Hularsa yake kokarin sakawa da alama fita zaiyi, yace yanzu Marka mekike so ince
dake? Yarinyar Nan de kina gani lokacin tafiyar ta islamiyya ne yayi, yanzu Marka
saboda aiki can maras tushe zan daure mata gindi akan ta zauna tayi aiki kada taje
makaranta? Toni bazan dauki wannan ba, idan ma wasu ne Daga gefe suke hure Miki
kunne to kifada musu sudena, ba'a gidanaba, yana gama fadar haka yasakai yafice
yabar mata gidan
Yana fita inna tafashe da kuka, akan Shalele yake fada mata wannan maganganun?
Hakika yau tayi DANA SANIN auren surajo, ita Kuma Shalelen ai zata dawo gidan ta
sameta, da ita suke zancen
Shalele na dawowa gida gab da magrib tayi sallama tace inna nadawo
Murmushi tayi, aranta tace inna Bata huce ba Kenan, buta tadauka ta shiga bayi tayi
tsarki, sannan ta futo tayi alwala, tabarmar da inna take zaune anan taje tatada
kabbarar sallah, tana idarwa tace inna kiyi hakuri
Shalele tace Naga yau duk ranki abace yake, Bansan laifin danayi Miki ba innata
Amma kiyi hakuri
Aikin nunamin ban Isa dakeba haneefa, inda na isa dake bazan sakaki aiki kiqi yiba
Da tsananin mamaki afuskarta ta kalli innar Tata, yau inna ce Dakanta take kiranta
da Haneefa?
Meyake faruwa ne? Kota manta ne baba yace Sunan mahaifiyarsa ne? Amma Tafadi sunan
haka Kai tsaye?
Murmushin dole ta qirqiro tace to inna kiyi hakuri, Bari in tashi in share gidan,
kiyi hakuri
Yunqurawa tayi zata tashi, tana tsammanin inna zatace dare yayi tabarshi, Amma sai
Taji sabanin haka, domin kuwa inna amsa tabata da Cewa "Dade yafi Miki"
Share gidan tayi tsaf, Daga nan tashige dakinta take ta aikin kuka, Bata sababa,
batasan metayiwa inna haka me zafi ba
Koda baba yadawo ma, bece inna takawo masa abinci ba, Shalele ya qwalawa kira taje
takai masa abincin sa, haka de ta kwanta ranar jikinta duk yayi sanyi, baba kuwa
Baisan abinda yayi yaqara qona ran inna ba, haka nan takejin wata irin tsanar
Shalele aranta
*******
Washe gari dataje makarantar islamiyya, haka take fadawa sabira Cewa tabawa inna
hakuri fa Amma babu abinda yasauya, sabira tace "kedan bakya karanta littafin hausa
nefa, infada Miki akwai wani Novel Dana taba karantawa naji ance Wai masu ciki wani
lokacin cikin yana sakasu masifa"
********
Kwanci tashi babu wuya awajan Allah cikin inna ya tsufa, daqyar take zama daqyar
take tashi, halin datake nunawa Shalele kuwa babu abinda yasauya saide ma qaruwa
dayayi, baba yana lura da duk wani take takenta, jira kawai yake yaga ta haihu
lafiya, yanzun yana Daga mata kafa ne akan larurar datake jikinta,sauqin Shalele
daya, shine makaranta datake Zuwa da safe, dayake yanzun Suna ss1 ne, Amma dazaran
tadawo gida tofa babu zama, aiki ne zai biyo baya, tun maganar sabira na yaudararta
akan Cewa haka masu ciki suke Har abin yadawo Bata mamaki, domin kuwa qarara inna
take nuna tsanar datake yimata
********
Yau takama Laraba, Kuma a yaune inna ta haihu da namiji, baba yayi mutuqar farin
ciki, daya Daga cikin qannan inna ne sukazo domin temaka mata
Kayan da akayi haihuwar dashi, aka Bata da jini murja ta meqo mata shi, tana zaune
a tsakar gida, ta dungurar da bahon tace ke gashinan dauki kije ki wanke shi
Shalele Bata kawo komai aranta ba, asalima murnar tasamu qani yahana bakinta
rufuwa, daukar bahon tayi tace to anty murja, tashige bayi dashi, kwata Kwata
batada qyanqyami haka ta wanke wannan kayan jinin tas, ta shanya, ta wanke hannunta
da omo, dakin innar Tata ta shiga hankalinta yanaga Yaron tace anty nagama, tameqa
hannu zata dauki jaririn
Dasauri inna tasa hannu tace mezaki masa? Kinga barmin yaro na, bazakije ki
jagwalgwala Shiba, Har yaushe da hankalina zan Bari ki dauke shi
Idan akwai abinda yafi sanyin jiki Tona Shalele yayi, Kallan anty murja tayi Ko
zata yi magana Amma Bata sami komai Daga wajan murja bama sai amsar harara
Awannan Karon Kam Bata Iya tsaida hawayen dayake shirin zubo mataba, kuka ta zauna
ta rizga, idanunta sukayi jajir, tanajin baba yashigo yabawa murja sako yace murja
ga wannan ki dafa mata Ko zataji dadinsa, yafice
Yana fita anty murja ta qwala mata kira, dasauri ta goge hawayen idonta tace gani
anty murja, ledar da Baba yabawa murja ta wullo mata Har naman dayake ciki yafara
zubewa, tace dauki wannan wulaqantaccen naman ki wanke kidorashi awuta
Haka ta zauna Saida dafawa inna naman, sannan tazuba mata shi a flas, takai tace
inna gashi, Ko azuba Miki?
Hararar ta murja tayi tace ke awa? Eye nace ke awa? Kinga jeki ni karki cinyeni da
wannan idanun naki me kama Dana mage, gayyar na ayya
Haka yafuto Daga dakin ranta duk ajagule, inna kuwa da harara tabita, tun kafin ta
zauna, inna da kanta ta qwala mata kira tace Haneefa futo kidora muku abinci keda
ubanki
Sake futowa tayi, tadora musu abincin harta qare, zama tayi domin ta huta, ta tuna
da shara, Gara ma tayi, saboda inma batayiba zasu sake tasota
Tana gama sharar, tahada kwanukan gidan zata wanke, randar gidan ta bude taga babu
ruwa, taje gaban dakin inna, suna zaune itada murja sun bararraje sunacin farfesun
data dafa, cikin tsoron fadansu tace inna dama zanyi wanke wanke ne shine Naga babu
ruwa acikin randar
Banza sukayi da ita, babu wanda ya tanka mata acikinsu
Kallansu tayi tasake Cewa Inn... Bata qarasa fadar sunan ba, innar ta hayaiyaqo
mata, to Haneefa Bari nazo nasaka hijabi na nadebo Miki ruwan kinji, tsaya gani nan
Zuwa
Jiki ba qwari tabar kofar Dakin, dakinta taje tadau hijabi, tazari boket tafice
Daga gidan, tuqa tuqa taje tadebo ruwan tadawo, tana dawowa ta shigo zauren gidan
tahadu da Baba
Kallanta yayi yace menake gani haka Shalele nah?
Murmushi tayi tace baba babu ruwa a gidan, Kuma baka nan, naduba wajan baba Malam
Kuma baka nan shine nace kawai Bari nadebo
Bata sake magana ba ta sauke boket din, yasa hannu yadauka yace mata muje cikin
gidan
Itace tayi gaba, yabiyota Abaya, tun kafin su karasa shiga yafara qwalawa inna kira
Marka! Marka!!
Marka wanne irin rashin adalci ne wannan zaki saka Shalele diban ruwa? Har me
zakiyi da ruwan dazabaki tsaya nadawo gidan nadauko muku ba?
To yanzu Malam nikakeso nasaka hijabi naje nadebo mata ruwan? Bafa ayimin adalci
acikin gidan nan ehe
Qwafa yayi be sake cemata komai ba, yanufi randa yazuba ruwan, sannan yajuya zai
ficedaga gidan ya kalli Shalele da ke tsaye Kamar kazar da qwai yafashewa aciki,
cikin tausasa murya yace karna qara ganin kinfita waje wani diban ruwa, inde ba
makaranta zakiba, bakason naqara ganinki da makayin diban ruwa kinji Shalele nah
Yana fita inna tadaka mata wata uwar Hararar datasa Shalele sunkuyar da kanta qasa
Kamar wata munafuka
Ruwan da Baba yajuye aranda ta Diba tafara wanke kwanukan datayi amfani dasu
********
Ranar Suna yaro yaci sunan kakan Shalele na wajan uwa, mahaifin inna Kenan Abdallah
Amma inna na kiransa da aududu (🤣)
Anyi taron Suna lafiya angama kalau, taro yayi taro, inda baba yayanka wa inna
raguna Har biyu saboda hidimar Suna
Yau baba yana gida, suna zaune Dukansu arumfa anty murja Takoma gidan ta, Aududu ne
yayi fitsari inna tace Haneefa zoki sakawa Yaron nan ruwa yayi fitsari
Baba ya kalleta da tsananin mamaki, Ko kadan yanzu Bata shakkar fadar sunan
mahaifiyarsa agabansa, Ko babu komai ai sirikarta ce, duk da bata a Raye
Hannunta ta dauraye Daga wankin tsarin tuwonsu datake yi, tazo tadauki Yaron ta
wanke masa jikinsa, tasaka masa wani wandon, Bata taba daukar Aududu inde ba
wahalar sace ta tashi ba, tarasa meyasa inna Bata barinta ta dauke shi, kawo mata
shi tayi Takoma taqarasa wankin tsarin ta bazashi akan wani babban tabarman zana
Sannan ta wanke wandon da Aududu yayi fitsarin ta shanya, tun kafin ta zauna, Yaron
yayi Kashi
Baba yayi tunanin inna zata tashi Dakanta tagyara Yaron, Amma saiyaji tace Haneefa
zoki daukemin Yaron nan ki wanke masa Kashi
Hannu bibiyu baba ya zabga tagumi (🙉) Yama kasa Cewa komai
Futowa sukai Daga bayin itada Aududu tana da gashi sama ta nayi masa wasa, sai
babbaka Daria Yaron yakeyi, dasauri inna tace "Ke karki lahanta min yaro mana, ke
mahaukaciyar inace!? Eye nace ke mahaukaciyar inace zaki dinga cillamin yaro sama
kina cafewa saikace wanda kika dauki Leda
✍🏻
Mrs Usman ce
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
9&10
Itama cikin fishi tace zaka dakenine? Malam nace zaka dakenine akan nayi mata
magana saboda Dana? Idan ta kashemin shi Kaine zaka bani wani Ko ita? Da wannan din
dayaya na sameshi? To bismillah, aiga fili ga me doki, kana yin kuskuren sake
fadamin baqar magana Akan yarinyar Nan zakaga mummunan matakin dazan dauka akanta
Dukda yana cikin halin masifa, lokaci daya jikinsa yayi sanyi dajin furucin Marka,
Gabansa ya tsanananta faduwa, cikin mamaki yace subhanallah, subhanallah Marka
mekike nufi da kalamanki? Wai nikam in tambyeki, su waye suke hure Miki kunne
abayan idona?Shalele datayi tsaye tana Kallan abinda Bata taba ganiba, idanunta
babu abinda yake zuba banda hawaye, ita ya nuna da hannunsa Sannan yace Marka me
kika dauki Shalele ne? Kishiyarki ce Ko yarki?
Inna na girgiza jikinta irin tanaji da masifar nan tace masa oho shafa kaji
Gaskiya ne Marka, zan shafa, zansha fa naji yanzu kuwa, Kallan Shalele yayi
idanunta sunyi jajir sabida kuka, Bata taba ganin iyayenta Suna fadi infada da
junaba sai yau, ita kuwa wacce irin yace da zatayi silar samun sabani tsakanin
iyayenta da ba'a jin kansu Ko kadan?girgiza kansa yayi alamun ta dena kukan datake,
Saida ya sassauta muryarsa alamar rarrashi sannan yace share hawayen ki Shalele
nah, ajiye Yaron nan
Bata ajiye Shiba, ta qanqame Yaron ajikinta, ahankali baba yasake Cewa ajiye mata
shi nace, inna na kallansu tana karkada jiki tana auna musu harara
Still Bata ajiye Yaron ba, cikin tsawa, wadda tsawon rayuwar ta Bata taba ji
mahaifin ta yayi Mata ba, yace "nace Ki ajiye Yaron nan!!!"
Lokaci daya jikinta yahau kyarma ta ajiye Aududu tashige dakinta da gudu tana kuka
Baba ya kalli inna Marka yace kin kyauta, sannan yasa Kai yafice Daga gidan
Bai zarce ko'inaba sai gidan maqocinsa Malam yahai, kafin ya qarasa gidan yar
qaramar wayarsa tahau qara
Yana dagawa yace eh insha Allahu Ina nan tafe, zaku ganni Hajiya, Yauwa nagode,
sanan ya kashe wayar
Sallama ya qwala a kofar gidan, amininsa Malam yahai yanaji yasaka hularsa yafuto
kofar gidan, ayanayin da yaganshi yasan Cewa ba kalau ba, akwai damuwa, danhaka
yace a a Malam surajo, qaraso mana, mu qarasa ga dakali nan mu zauna, bece komai ba
sai zama dayayi, yakama kansa da hannunsa bibbiyu
Dafashi Malam yahai yayi yace meyake faruwa haka Malam surajo? Yanayin ka ya
nunamin ba lafiya kake ba
Marka ta sauya Malam yahai, nan take yabashi labarin duk abinda yake faruwa, Daga
qarshe yace kaji abinda yake faruwa
Baba yace yanzu Kam kaina yariga daya kulle Malam yahai, Amma dole zan dauki babban
mataki akan Hakan, ba wanan ne damuwa ta bama, Hajiya takirani Daga Abuja, tana son
ganina, Amma idan bazan samu damar zuwaba to tanaso tazo da kanta, tanason zamu yi
wata magana Mai muhinmanci dangane da Shalele nah, Amma nafada mata Cewa bama sai
tazo da kanta ba, zansa lokaci naje cikin satin nan
Malam yahai yace to ai ta kwana gidan sauqi Malam surajo, ni Ina ganin mezai Hana
kawai katafi da ita Shalelen can wajan hajiya, ai zaifi
Malam yahai tana zuwa makaranta yanzu, banaso Ko kadan na katse mata karatunta,
idan natafi da ita bazasu Bari nadawo da ita ba,, zan Bata hakuri kawai,idan Naga
gidana yagama dedeta yadawo Kamar da, sainaje, Amma yanzu bazan Iya barin Shalele
Daga ita sai Marka awannan halin ba
Malam yahai yace eto wannan dinma tunani ne Mai kyau gaskiya, babu damuwa, kada
kadamu abokina,kakira Marka ku zauna kaji menene damuwar ta, insha Allah komai zai
warware, saika kira hajiyan kabata hakuri kayi mata bayanin komai
Baba yace zan kirata insha Allah, nagode sosai da shawararka a gareni
Tashi yayi yace zanje gewaya gona, saina dawo Malam yahai
Malam yahai yace to shikkenan Nima Bari in koma gida
Daga nan baba Bai zarce ko'inaba sai gonarsa, Saida yagama dubata da kyau sannan
yadan ciccire mata ciyayin dasuka Dan futo, yahau kekensa ya wuce wata gonarsa ta
shinkafa, nanma dubawa yayi yaga ruwa ya wadace ta, sannan yazauna yana hutawa a
wata bishiya Mai sanyi, Daga nan Baisan lokacin da bacci ya daukeshi ba
Zafin dayaji aqafarsa ne yasa yafarka da Addu'ah abakin sa, hamma yayi sannan yakai
dubansa kan kafarsa, baiga komai ba, wajan dayakejin Zafin yataba da hannunsa nanma
de baiga alamun komai ba, danhaka baikawo komai aransa ba yatashi yayi miqa ya wuce
gida
Gab da magrib ya isa gida, danhaka ya wuce masallaci Saida yayi sallah sannan
yatafi gida, yana shiga ita Kuma tafito zata fita, cikin siririyar muryarta tace
sannu da Zuwa baba, yawwa Shalele nah, za'a tafi wajan tulawar ne? Eh baba zan
tafi, to shknn Allah yabada sa'ah saikin dawo
Ahankali ta amsa da ameen sannan tafice Daga gidan
Dama haka take safe tatafi makarantar boko, da yamma islamiyya, da dare muma tilawa
sai takwas da Rabi zata dawo gida
Atabarmar da inna take zaune anan yazube yana fadin wash, wallahi nagaji sosai
Kamar batason magana tace sannu da Zuwa
Yawwa Marka sannu, tashi ki   dubomin rob a daki na shafa akafata ciwo takemin
Batare datace masa komai ba   tatashi tadauko masa rob din, ya karba yashafa sannan
Yarufe idonsa, shiru sukayi   da gashi Har ita, shi yana tunanin rayuwar yarsa gudan
jininsa, ita kuwa bacin rai   ne danqare acikin ranta
Babu abinda tamin, kawai de Ina Bata tarbiya ne akan abubuwan dakake yimata, sannan
Malam zamanta a gida haka ai ya isa haka, ayi auranta mana
Murmushi yayi, aransa yace Wai tarbiya, jin dalilin nata bawani Mai tushe bane
Afali saiyace Aure fa kikace Marka, dududu nawa yarinyar take dahar za'a yi mata
zancen wani Aure! Idan kin manta lissafin ne saina tuna Miki shakerar Shalele goma
sha biyar, ni aganina tayi qanqanta da Aure yanzu, kina gani fa yaran gasunan
dayawa anayi musu auren dazaran sunzo haihuwa saisu fara yoyon fitsari, saboda
yarinya bazata Iya haihuwa da kanta ba
Yanzu de maigida Tunda ba zakayi mataba ai shikkenan saika sata agaba kana kallo
kanajin dadi
Bece mata komai ba sai Murmushi dayayi kawai, yasa hannu yadauki Aududu yafita
dashi waje, yanajinta tana sakin wani uban tsaki
**********
Washe gari kafar baba ta kumbura tayi suntum, daqyar yake Iya takawa, Shalele Bata
saniba, tun da sassafe data gama share gidan tayi wanke wanke, ta tsaya abakin
kofar Dakin ta gaida su ta wuce makaranta Bata dawoba
Shikuwa baba yana kwance a daki yahada uban gumi, Marka tana kallansa ta share shi,
ahankali yace Marka!
Tanajin sa ta qyaleshi, Saida yakirata yakai sau hudu sannan ta amsa, yace saka
mayafinki kije kikirawo min Malam yahai
Saida tagama abinda yake gabanta sannan tatashi ta leqa ta katangar su tace sabuwa,
kice wa Malam yahaya Yazo Malam yanasan ganinsa, kafin sabuwa tace to, Har Marka
tabar jikin katangar, habarta ta riqe tace tooo
Tana fadawa mijinta yafuto dasauri yashigo gidan, yace Marka Ina Malam surajon
yake? Lafiya deko?
Bata yi masa magana ba Kawai nuna masa dakin tayi da hannunta, yayi bismillah
yashiga, yana ganin baba akwance yace subhanallah Malam surajo lafiya kuwa? Yana
runtse ido yace kafata ce take ciwo tun jiya wallahi,
Yace subhanallah sannu Malam surajo, muje waje sai Naga kafar, da temakon Malam
yahai, yakama baba yafuto dashi Daga cikin dakin, acikin rumfar suka tsaya, ya
kalli Marka datake zaune agefe yace Marka temaka ki shinfida mana tabarman nan
Tabarmar ta fizgo agefe ta shinfida musu, Malam yahai yana Kallan ikon Allah, haka
ya kwantar da Baba yasaka Fillo Daga bayansa, dage kafar wandonsa yayi, ga kafar
nan ta kumbura sosai, yace Malam surajo yaushe kafara jin ciwon ne?
Tiryan tiryan baba yabashi labarin komai tun zuwansa gona Har abinda yafaru, sake
ganin kafar yayi sannan yace to gaskiya Ina tunanin miciji ne ya cijeka, kokuma
wani qwaron me mugun dafi, Bari inje gidan Dan makandi na karbo ma magani, dasauri
yafita Bai jira amsar baba ba
Maganin yakarbo Yazo yajiqa yabawa baba yasha, sannan yabashi goro yace wannan
namijin goro ne kaci, inde hasashen mu ya zama gaskiya macijin ne to insha Allah
zakaji sauqi, Allah yabaka lafiya, baba Bai Iya amsawa ba illa kansa daya Daga,
ahankali Yarufe idonsa Har bacci ya daukeshi
Sannan Malam yahai yatafi gida da nufin idan anjima kafin nan baba yatashi saiya
dawo
Har biyu saura baba Bai tashi ba, yana bacci saboda jiya baiyi baccin kirki ba
Tana shigowa gidan da sallama abakinta, dashi tafara tozali da gudu ta qarasa wajan
inna Marka tace inna lafiya baba yake kwance anan? Meyasa mi babana inna?
Inna tace kaji me uba, to sannu yar Baba, gashinan akwance ai saiki tambayeshi
Jiki asanyaye Takoma gefen sa ya tsugunna, maganin data gani ajiqe akofi duk da
batasan kona menene ba hakanne ya tabbatar mata da babanta baida lafiya, lokaci
daya hawaye yacika idonta, ganin tana kuka Amma innarta ta share ta ko rarrashi
babu yasa taqara volume din kukanta, wannan wacce irin masifa ce take cikinta? Ace
uwarka tana fishi dakai tsawon lokaci Mai tsawo haka
Shashshekar datake ne yafarkar dashi Daga baccin dayake, ahankali yace Shalele nah
kin dawo? Daga masa Kai tayi, tana share hawaye idanunta sunyi jajir, karan
hancinta yayi jajir abinka da farar Fata
Cikin kuka tace sannu baba, kanta ya dafa da hannunsa yace kiyi hakuri Shalele nah,
insha Allah zan warke kinji? Sake Daga masa Kai tayi
Yace tashi kije kici abinci kihuta, kiwuce islamiyya, cikin muryar kuka tace baba
yau Alhamis babu islamiyya, yace to tashi kije kici abinci karki zauna da yunwa
Tashi tayi takai jakar makarantar ta daki, tadauki kwano tace inna akwai abinci?
Inna tace bandafa dakuba, Iya cikina nayi, saide ki dafa muku, bazan Iya ciyar
dakuba
Cikin sanyin jiki ta ajiye kwanon tadauki tukunya tadora musu jallof din taliya yar
hausa, kasancewar batada wahalar dahuwa nan da nan tagama, tazuba akwano takaiwa
baba nasa, agefensa ta zauna ta rafka uban tagumi
Duk abinda yaje faruwa baba yanajinsu Yarufe idonsa ne kawai Amma ba bacci yakomaba
Bude idonsa yayi yace kici abincin mana Shalele nah
Baba ai kaima bakaci ba, bazan Iya ciba
Murmushi yayi yace to Bari inci, daqyar yatashi zaune, yadauki cokali yafara ci,
itama tasaka hannu anasa suke ci tare, inna tajuyo ta kallesu ta zuba tsaki
Baba kuwa Ko Kallan inda take baiyi ba, yaga alama Marka tana jiran Jan kati ne()😃
Suna gamawa tabashi buta yayi alwala, yayi sallarsa a zaune, duk yanayin hakanne
domin Shalele tasaki ranta, Amma shi kadai yasan azabar da yakeji aqafarsa
Har dare Suna nan wajan, itade inna ta dauke danta suka shige daki, baba yace
Shalele kiramin Malam yahai yakaini daki na kwanta, kema kije ki kwanta kihuta
Allah yayi Miki albarka
Girgiza Kai tayi tace baba zan kamaka, basai na kirashi ba, haka ta kamashi, ya
lanqaya hannunsa daya akafadarta takaishi daki sannan tayi masa Saida safe ta futo
Koda ta shiga dakin ta kuka taita yi, tana adduar Allah yabawa babanta lafiya, da
taga kukan bazai yimata ba tatashi ta futo ta daura alwala takai kukansu wajan
Allah, Saida dare yaraba sannan ta kwanta baccin itama anan kan abin sallar
Tana daura alwalar sallar asuba take jiyo nishin baba Daga daki, yana Kiran Marka,
batasan lokacin datayi wulli da butar datake hannunta ba tabanka kanta cikin dakin
Baba ne kwance acikin mawuyacin Hali yajiqe jarkaf da gumi yayinda ya Dora hannunsa
daya Kan kafarsa dayakejin ciwon ta
Jikinta banda karkar wa babu abinda yake yi, tace sannu baba, mekakeso nakawo ma?
Baba kafar ce take maka ciwo? Sannu
Duk tagama rikice wa, cikin karfin Hali yace mata Shalele nah inaso ne zanyi sallah
To, to baba, sannu, haka ta cacimeshi daqyar suka futo Daga dakin, yayi alwala, ta
shinfida masa tabarma da sallaya akan Tabarmar yazauna yafara sallar a zaune, Saida
taga alamun yafara ne sannan itama tayi alwalar taje tayi sallah, tana idar wa
tafito tsakar gidan nasu wajansa,, akan sallayar dayayi sallah ya kwanta yanata
uban gumi, dakin ta shiga tace inna Ina mafici zanyima baba firfita Kinga sai gumi
yakeyi
Saida taja tsaki sannan tace Dan Allah Haneefa kada kidameni, haba duk kunbi kun
cikan kunne da surutu idan maficin kike ne..... Bata gama maganar da takeba Shalele
ta juya cikin fishi tabar mata dakin
Inna tadaga murya tace iyeeee ni zakiyi wa rashin kunya? Yau kuwa zakici uban ki
surajo acikin gidan nan Dani kike zancen
Dakinta taje tadauko maficin roba, tanajin inna na zaginta batace uffan ba, babama
yanajinsu, shi kadai yasan Abinda zaiyiwa Marka, fatansa kawai yaji sauqi
Zama tayi agefensa ta nayi masa firfita, ahankali tace sannu baba,Daga mata kansa
kawai yayi alamun amsawa
sannu sannu ta nayi masa firfitar Har gumin dayake fitarwa yafara raguwa
Suna zaune acikin rumfar Har Gari yafara haske, hijabin ta dake gefe a ajiye tasura
tafice Daga gidan, Bata tsaya Ko Inaba sai gidan su sha'aban me kaita makaranta
Yayi mamakin ganinta da sassafe haka, yace Haneefa yau da wuri kikeso nakaiki
makarantar ne?
Sha'aban yau ba maganar makaranta, Dan Allah taho muje baba baida lafiya, muje
kakaimu asbiti adubashi Dan Allah sha'aban
Dasauri yace subhanallah, muje, gaba tayi, shikuma ya buga machine din yabiyota
Abaya
Tana shiga gidan tace baba tashi muje asbiti, sha'aban nan awaje zai kaimu
Daqyar yatashi zaune, tadage labulen dakin inna tace inna bamu bargo da kayan baba
Ko guda dayane zamu asbiti nasan ba lalle mu dawo yauba
Inna Marka tayi mirsisi ta qyaleta, haka Shalele tasaki labulen tazo takama baba ya
miqe suka fara takawa Zuwa kofar gida, kawai saijin saukar kaya sukayi abayansu,
atare suka juya itada baba, inna ma Bata fasa abinda takeba haka ta ci gaba da
Watso musu kayansu, jikinsu, tace gashinan kufice maza, kufi ruwa gudu, yar kare da
shegen iyayi, yar mitsitsiya dake Har kin Iya kwainane waike me uba, sauran kayan
dake gefenta na baba tadauka ta qarasa watsa musu kayan ajikinsu saikace wanda aka
basu notice a gidan haya(😢😢)
Ahankali baba yace muje Shalele, fita sukai sukabar kayan awajan ayashe aqasa, suna
fita sha'aban yatemaka wa baba yahau, itama tahau Daga baya daqyar machine din ya
ishesu su uku, basu tsaya Ko Inaba sai a Dan qaramin a sibitin Garin, sha'aban yace
Bari najiraku Haneefa, dasauri tace a a sha'aban kaje kawai, idan kaje kafadawa
baba Malam yahai abinda yake faruwa kace masa muna asbitin, yace to Haneefa Bari
naje
Yana tafiya, taje wajan baba dake zaune abenci, hannu tasa acikin aljihun Rigarsa
tadauki dubu daya, taje ta yanki kati, ganin halin dayake ciki Kuma babu mutane
sosai yasa Aka dubashi da wuri
Likitan yace yarinya meyasa baki kawo shi da wuri ba? Ai dafi ne akafar tasa,
maganar gaskiya abin yafi karfin qaramin asbiti irin wannan, zan rubuta Miki wasiqa
inturaku asbitin birni cikin Abuja, zaifi samun kulawa fiye da nan
Hawaye tafara lokaci daya, tace nashiga uku na, yanzu likita zamu Iya Zuwa gida
mudau kayanmu saimu tafi asbitin?
Yace yarinya, Ina fada Miki ciwon mahaifin ki yayi worst dayawa kina maganar gida?
Idan zai Iyu ma kawai ka wuce Daga nan, ga wannan takardar kitafi da ita, Allah
yabashi lafiya
Hawayen ta share tace to likita Mungo de, haka takamo baba suka futo Daga cikin
asbitin, a wata bishiya tace zauna baba, Bari natare mana taxi, yace to Shalele nah
Bakin titi taqarasa tafara tare taxi saide duk wadda tazo Bata tsayawa, ganin haka
yasa tafara tare duk wata mota datake wucewa
Cikin qwarewa da driving wata   mota baqa qirar   Range Rover ta kunno kanta titin
Glas din motar tinted ne baka   ganin naciki
Awannan situations din datake   ciki batada zabin daya wuce tatare motar, danhaka Kai
tsaye tashigo titin tana tare   motar, jikake qiiiiii motar tasaki qara daqyar
direban ya tsaida motar
Yana harde abayan motar, video call yakeyi da computer datake kan cinyarsa,
ahankali yadago Zara zaran gashin idonsa ya kalli direban dake jansa yace "saminu
kanka daya kuwa"?
Yallabai tuba nake wata yarinya ce takeso ayi mata lift, yasake yin kasa da kansa
yace ayi hakuri Yallabai
Computer dake cinyar sa Yarufe, ya kalli saminu da lumsassun idanunsa yace" lift"?
Acikin motata? Motata tayi kama data masu yin lift ne?
Cikin girmamawa saminu yace a a Yallabai, ayi hakuri, dama Naga tana buqatar temako
ne
Tsaki yasaki yace "no bazai wuce masu yin bara akan hanya ba, yabude brief case
dinsa dake gefe yadauko kudi dami uku Yan dubu daidai, ahankali ya zuge Glas din
motar idonsa yasauka akan baba dake zaune abishiya idonsa arufe
Tun lokacin daya sauke Glass din motar tazuba masa ido, lokaci daya Taji gabanta
yafadi
Shikuwa zafin daya bigi fuskar sa ne kasance war akwai sanyin esi acikin motar yasa
dasauri ya watsa kudin waje yazuge glass din motar Yarufe batare daya kalli
yarinyar data tare suba
Idanunsa ya lumshe Ahankali yace "saminu les go inajin gabana yana faduwa awajan
nan"
Ahankali yayi maganar inde ba zuba kunne kayi ba ba lalle kaji maganar tasaba,
Shima saminun danya saba ne yasa yaji shi
Nan da nan yacika umarnin uban gidan sa yaja motar sukabar wajan
✍🏻
Mrs Usman ce
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
11&12
Bayan motar tabi da kallo,inda idonta yakai kan number motar taga ansa SHAZALI NO.7
Saida suka bacewa ganinta
Sannan tasauke kanta qasa takalli kudin da ya wullo mata, to ai ita ba kudin tafi
buqata ba a yanzu, tafi buqatar motar akan kudin dazai Bata
Ahankali tasa hannu tadauki kudin tazuba musu ido, Tunda take Bata taba riqe kudi
masu yawa hakaba, riqe kudin tayi acikin hijabin ta, taci gaba da tare motar Har
Allah yasa wani ya tsaya, bayani tayi masa, Dan haka ya matso da motar Har bishiyar
da Baba yake zaune, idonsa arufe suke, da temakon ta da temakon Mai taxi suka saka
baba acikin motar sannan yaja suka tafi
Suna cikin tafiya, Amma gaba daya hankalinta yana kan babanta, idanunta cike suke
da qwallah tace sannu baba
Bai Iya amsa mataba kawai kansa yadaga
Sunyi tafiya ba wata Mai Nisa sosaiba suka qarasa cikin Abuja, driver yace yarinya
Ina muka nufa?
Tace Dan Allah katemaka kakaimu asbiti koma wanne ne, babana yanajin ciwo sosai,
baisake maganaba yaci gaba da driving dinsa, Saida yasake wata tafiyar sannan suka
isa wani private hospital fashmard, yana tsayawa da motar a harabar hospital din
suka bude dasauri shida Shalele, baba yafara kokarin futowa Kenan ma'aikatan
asbitin suka kawo gadon da aka tura marasa lafiya akai, nan da nan aka Dora baba
akai sukayi ciki dashi dasauri, hankalinta atashe yake tace masa nawane kudin?
Lokaci daya Yaji tausayin ta yakamashi, gata qarama, Kuma mace, Amma tana fuskantar
irin wannan rayuwar, Ko ina mahaifiyar ta? Itace ta katse masa tunanin dayake Tace
Malam nawane kudin?
Firgigit yayi yadawo Daga tunanin dayake yi, yace Kinga yarinya kibarshi kawai
Kanta ta girgiza tace a a gashi, hannu tasa cikin hijabin ta taciro kudin Daga
cikin wanda aka wullo mata tabashi, ita kanta batasan nawa taciro masaba, tana miqa
masa tashige cikin asbitin da sauri
Tana shiga wata nurse ta nuna mata dakin da aka kwantar da babanta, dakin ta shiga
afirgice taga wani likita yana daura masa ruwa, tace doctor Yaya jikin babana? Yace
Alhmdlh andaura masa ruwa yanzu, akwai allurar bacci acikin ruwan, zai yi bacci
nadan lokaci kafin babban Likitan dazai dubashi Yazo, kiyi hakuri kinji, insha
Allah babanki zai warke, yana gama magana yafice Daga dakin
Sai a lokacin ta zauna a kujerar da ke kusa da jikin gadon, a lokacin Har baba
yafara lumshe idonsa alamun allurar da suka masa tafara aiki, hannunta takai kan
nasa Ahankali ta riqeshi, cikin ranta tana Addu'ah Allah yabashi lafiya
Tana nan zaune riqe da hannunsa itama bacci yafara fizgarta tana sake bude idon duk
Wai Dan karya dauke ta, Amma Saida yayi galabar daukarta, kanta ta Dora Agefen
fuskar baba itama tafara baccin
Bata San tsawon lokacin data dauka tana baccin ba, saide tana farkawa ta kalli
agogon dakin taga lokaci yaja, dasauri ta kalli inda baba yake kwance taga idonsa
biyu yazuba mata ido yana kallanta, tace sannu baba, yajikin Naka? Murmushi yayi
yace sauqi Shalele nah, kina bacci harma likita Yazo yaciremin qarin ruwan yanzu
inajin karfi ajikina
Murmushi tayi tace Yauwa alhmdlh, Allah yabaka lafiya baba, yace amin Shalele nah,
hijabin ta tadaga ta dauko kudin da aka wullo mata tace baba gashi
Yunkurin tashi zaune yake, tace Bari in sama Fillo abayanka baba, baiyi mata musu
ba tasaka masa, tace wannan kudin baba dazu ne wani ya wullo minsu Daga cikin mota
lokacin danake kokarin tare mana abin Hawa, nikuma Baisan ma nafi buqatar motar
akan wannan kudin ba
Kudin ya kalla sannan ya kalleta yace wannan ai kudi ne masu yawa Shalele nah,
wannan kuwa waye ne? Tace wallahi bansaniba baba, Amma baba kasan me? Ina ganinsa
gabana yafadi (😃😃😃) Murmushi Baba yayi, saboda yasan Cewa yar tasa batasan
abinda Hakan yake nufi ba, ahankali yace Allah yayi masa albarka, Naso ace naganshi
nagode masa saboda ya temaki Shalele nah sau daya arayuwa, Amma duk da haka Allah
yabiya masa dukkannin buqatunsa na alkhairi
Tana Murmushi tace amin baba, gasunan, ta ajiye masa kudin agefensa sannan tace
Bari inyi sallah baba, toilet din dake cikin dakin ta shiga tayi alwala tashinfida
Dan kwalin kanta tayi sallah, sannan ta temaka masa Shima yayi, likita yashigo yace
yakamata yaci abinci Ko Yaya ne, Ana jimawa doctor zaizo, tace to
Saida yasake kallanta sannan yace ok taso kibiyoni, tashi tayi tabi bayansa suka je
Har office dinsa, yace yarinya keda waye kukazo nan asbitin? Tace nida shine kawai
Kanta ta Daga masa tace eh, baba nane, nice nakawo shi, likita Dan Allah zaiji
sauqi?
Saida maganar ta tabashi Daria, tayaya zai sani Bayan sauqi yana wajan ubangiji?
Afili sai yace mata babanki zai warke insha Allah kinji? Kiyi masa Addu'ah, za'a yi
masa operation Dan gaskiya dafi ne yayi masa mugun kamu akafarsa na maciji, nayi
mamaki ma da babanki yakawo yanzu Bai mutu ba
Tanajin zancen mutuwa tadora hannunta aka (🙆🏻🙆🏻) ta fasa masa kuka tace nashiga
uku, Dan Allah likita karka Bari babana ya mutu Dan Allah na roqeqa
Lokaci day yaji yarinyar tabashi tausayi, yace ki kwantar da hankalinki, ni bance
babanki zai mutu ba, nace ne nayi mamaki da Bai mutu ba Har Zuwa wannan lokacin
saboda dafin yariga yayi masa illah yagama lalata masa kafarsa duka yana nema
yataba masa hantar sa , to amma zamuyi masa aiki gobe insha Allah abin bazai Kai
hakaba, saide kiyi hakuri zamu yanke masa kafarsa daya, already ta lalace bazata
amfanu ba
Kanta tadora akan tebur din dake Gabansa kawai tana kuka, tarasa me zatace masa,
gaba daya Taji duniyar tana juya mata
Daga masa Kai tayi, yadauko wani file yabata yace gashi zakisa hannu anan domin
amincewarki akan yi masa aikin, but zaku je kubiya kudin aikin naku dubu dari biyu
da sittin
Dasauri ta karbi biro din dayake hannunsa tayi sign din, mamaki yagama kashe shi a
zaune, Ina wannan yarinyar zata samu wannan kudin daya ambata? Anya Taji abinda
yace kuwa?
Saida yakare mata kallo sannan yace Daga wanne gari kukazo? Cikin rawar murya tace
ku.. Kuje
Yace ok, zaki Iya tafiya, kibasu kudin, zamu shiga dashi operation gobe da safe
insha Allah, yanzu yana karkashin kulawar mu Har Zuwa goben
Dasauri tafice Daga office din ta shiga dakin da Baba yake ciki, yana kwance idonsa
biyu yanzu, batayi masa magana ba sai kudin dazu data dauka tafice da gudu, Saida
taje tabiya kudin komai sannan tadawo da chanjin dake hannunta, wanda batamasan Ko
nawane yayi saura ba
Tana dawowa takifa kanta akan gadon nasa tasaki wani irin kuka, cikin ranta kuwa
tana ambaton Innalillahi wa inna ilaihirraji'un, yanzu baban ta zata yanke wa qafa?
Hannunsa yasa yashafa kanta yace kiyi hakuri Shalele nah, kinji? Insha Allah zan
warke
Daga masa Kai tayi, idanunta sunyi jajir, haka wuni awannan halin, batama neman
abinci, to awannan halin datake ciki wanne abinci zata nema? Har dare yayi idonta
biyu babu alamar bacci, baba nede yakeyi, Amma itakam idonta biyu, takama hannunsa
ta riqe, haka ta kwana a zaune, Washe gari Suna idar da sallah nurse's sukazo suka
sauya masa kayan jikinsa Zuwa light blue, na operation Kenan, lokaci daya hawaye ya
zubo mata, ya tabbata de kafar baba za'a cire
Sun fara turashi Kenan zasu kaishi dakin tiyatar Yadubi nurses din yace Dan Allah
'ya' yana kubani minti biyu zanyi magana da yata, suka ce to babu damuwa suka fita
Daga dakin
Suna fita yakamo hannunta yariqe yace HANEEFA
Cikin kuka ta kalleshi tace baba meyasa zaka kirani da wannan sunan? Murmushin
karfin Hali yayi yace dole ce tasa, inaso ki saurareni da kyau, ki dauki magana ta
da muhinmanci, HANEEFA Marka ba mahaifiyarki bace
Lokaci daya ta zaro idonta waje 😳😳meyasa takejin labarai marasa dadi ne Daga jiya
Zuwa yau
Ya lura da yanayin data shiga, danhaka yasake Daga mata Kai yace qwarai kuwa ba
mahaifiyarki bace, mamanki tarasu tun kina koyon zama, halaiya da kama gaba daya
nata kika dauko, su biyu iyayensu suka Haifa akwai yayarta tana nan cikin Abuja
Hajiya Hafsat, nayi mata alqawarin Cewa zan riqeki amana bisa gaskiya hakanne yasa
ta yarda tabarki a wajena, Kuma Alhmdlh nasan nayi Miki riqon da Ko mahaifiyarki na
Raye abinda zata Miki Kenan, insha Allah dazaran anyimin aiki lafiya zan kaiki
wajanta kiga yayar mahaifiyarki,munyi magana da ita akan zanje wajanta muyi magana
Mai muhinmanci akan ki, nasan bazai wuce akan maganar karatunki ba, koma de menene
idan natashi qafata qafarki zankaiki wajanta
Abu nagaba koda ace Allah baiyi zan koma gidaba ki kula da Aududu, kada kiga rannan
nace ki ajiye shi, rainane yabaci, shi din dan'uwanki ne, bakida kamarsa aduniya,
duk inda zakije kije dashi kada ki yarda ki Rabu dashi, ki riqe mutuncinki na ya
mace aduk inda kike, sai Abu nagaba, Koda ace ban dawoba kifadawa Marka Cewa
nasaketa SAKI UKU
Hannu takai tarufe masa baki tana girgiza masa Kai a a baba karkayi haka baba
meyasa Hakan baba? Taqarasa maganar tana kuka, hannunta ya janye yace akan Hakan na
aureta Haneefa, munyi da ita zata kula dake bazata karya alqawari ba, munyi da ita
arubuce Malam yahai ne sheda, idan ta karya alqalamin data dauka zamu Rabu, Kuma
gashi ta karya din
Kafin tasake magana nurse suka shigo suka fara turashi zasu tafi dashi, itama Binsu
tayi hannunta yana cikin nasa, Murmushi shinfide asaman fuskarsa, Saida suka je
shiga dakin ne sannan suka dakatar da ita likitocin, tanaji tana gani tasaki hannun
babanta yana mata Murmushi ta nayi masa kuka, suna shiga suka rufo kofar, haka ta
zauna jagwab agaban dakin kan wata kujera da aka tanada domin zama, takifa kanta
acinyarta tana kuka
To masu kallanmu Ayau ne zamu tattauna da wannan de fitacce Kuma mashahurin Dan
kasuwar da ake ji Dashi awannan qasa Tamu dama wasu sauran qasashen qetaren
Dakatawa tayi da kukan datakeyi takai dubanta kan TV din dake manne ajikin bango
kasance war asbitoci dayawa Suna saka kayan kallo aciki domin debewa marasa lafiya
kewa
Lokaci daya gabanta yafadi, Ahankali ta bude pink lips dinta tace Shine.... Tabbas
shine wanda ya cillo min kudi jiya, inda Bai bamu wannan kudin ba Ina zamu samu
kudin da za'a yiwa babana aiki?
Plasma TV din tazubawa ido tana kallo
Mutane dayawa sunajin sunan SHAZALI Amma dayawa Daga cikin su basu San menene
sunanka na gaskiya ba, menene ainashin sunanka?
Sosai aka nuno shi yayi mutuqar kyau cikin suit baqa, Saida yayi Murmushi Har
dimple dinsa suka motsa, sannan yace Sunana HANEEF BUKAR SHAZALI, shazali sunan
kaka nane abokai da yan'uwa suke kirana dashi Har sunan yabini
Kanada kamfnin shinkafa Shazali's Rice Mill, wanda babu wani kamfani daya kaishi
girma bangaren aikin shinkafa a nahiyar Africa gaba daya, dakuma kamfaninka na
takalma wanda muka tsinci labari a jarida Cewa kakashe maqudan kudade Har nera
billion 10 wajan kirkirar wannan kamfani, katsam Kuma sai muka samu labari kana
sake kafa wanin na sugar a gwagwalada Shazali's sugar processing company, Malam
Haneef Yaya abin yake ne, kasance war ka matashi Amma ka mallaki wadannan
masana'antu menene sirrin?
Ahankali Kamar me rada yace sirrin shine adduar iyaye kawai, sannan ba komai yasa
nayi sha'awar bude kamfanin sugar ba nayi hakane saboda asamu a dauki matasa
awannan kamfanin marasa aikin yi
Sannan su kansu masu sana'ar Saida rake Hakan zai musu dadi
Banda Aure
To Haneef shazali Mungo de da wannan lokaci daka bamu wajan tattauna wa dakai
To masu kallanmu anan muka kawo karshen wannan tattauna wa Tamu da shahararran Dan
kasuwa Kuma young billonia Haneef bukar shazali, mutara a wani satin domin jin.....
Bata gama jin maganar ba saboda muryar baba Malam dataji abayanta yana Cewa Haneefa
Ina baban naki?
Ajiyar zuciya tasauke tasanar dashi komai,ciki kuwa harda sakin da Baba yayiwa
inna, yazauna Agefen ta ya rafka tagumi yace Innalillahi..., kiyi hakuri yata insha
Allah za'a dace, fatanmu Allah ma yabashi lafiya, naje asbitin mu nacan gida jiya
Likitan daya turoku nan yatafi gida sai yau nakoma da safe shine yamin bayanin Kuna
nan asbitin
******
Cikin dakin operation kuwa kalau suka gama aikin lafiya, likitocin sai gaisawa suke
da junan su sunama juna murna, baba ya kalli babban Likitan yace yaro Yaya sunanka?
Cikin Murmushinsa Mai tsada yace baba Sunana doctor Bilal
Murmushi Baba yayi yace Bilal banaji zan qara minti goma aduniya, Tunda naganka
naji ka kwanta min araina zaka Iya Bawa yata duk wata kulawar data dace, Dan Allah
ka riqe min yata amana Kamar Yanda zaka riqe yayanka na cikin ka, ka dauka Cewa Kai
muharraminta ne, kadauki Haneefa katafi da ita gidan ka, nabaka ita duniya da
lahira, sunan mahaifiyar ta khadija, akwai yayar amahaifiyarta anan Abuja, zaka
samun duk wani bayani dazai taimaka maka wajan sanin Hajiya Hafsat yayar mamanta ta
hanyar wayata,ka riqe min ita amana, yatace idan tayi kuka nine nayi, idan ranta
yabaci Kamar nawane yabaci, banida tamkarta aduniya, Bilal kada kabar Haneefa
awajan Marka, kada kabar Haneefa awajan Marka... Kada... Bai qarasaba yayi salati
tare da kalmar shahada yace gagarinku nan.... 😭😭
Doctor Bilal Baisan lokacin daya zube qasa yazauna ba, wannan bawan Allah hakika ya
Dora masa babban nauyi akansa, wacece Marka? Meta yi ake Cewa kada abar Haneefa
awajan ta? To waima wacece ita Haneefan da akeso yazame mata uba?
Jiri yaji yana dibarshi, sauran likitocin kansu abin yabasu mamaki, haka sukaja
farin mayafi suka rufe wa baba fuskarsa
Doctor Bilal dake qasa a zaune suka kama suka miqar dashi, kafadarsa suka Bubbuga
suka ce kayi hakuri doctor
Haka yakamo hanya yafuto Daga dakin tiyatar cikin sanyin jiki
Yana futowa Shalele da Malam yahai sukai wajansa, atare suka ce likita ya aikin?
Shalele tace doctor angama lafiya Ko?
Shima Malam yahai dafatan anyi wa abokina aikin lafiya Dana
Cikin qwallah yace saide kiyi hakuri Allah yayiwa mahaifin ki rasuwa, kiyi hakuri
yabani umarnin Cewa intafi dake
Lokaci daya ta Dora hannunta akanta dayake barazanar rabewa biyu, tace doctor
mekace? Numfashin tane yake sama sama sai riyammm Tafadi qasa sumammiya
(haka rayuwar take, zaka tashi cikin tsananin gata da kulawa, Amma bakasan Yaya
karshan ka zai kasance ba, zamu tashi da iyayenmu Suna sanmu muna sonsu Amma
ubangiji daya fimu sansu ya dauke manasu 😭😭😭😭bawai Dan munfishi sansu ba
✍🏻
Amnanku ce
💕SHALELAN BABA💕
         (Romance)
Writing by Amnah El
13&14
Bata tashi farkawa Daga Suman datayiba sai akan gado, baba Malam yana zaune a
kujerar gefen gadon, yayin da doctor Bilal yake zaune akan gadon saitin kafafunta
Dishi Dishi tafara gani, ahankali harta bude idonta, baba Malam ta kalla tace baba
Malam da gaske ne baba na ya mutu? Baice mata komai ba sai hakuri daya Bata
Tashi tayi zaune tamaida kanta kan cinyarta tafashe da kuka Mai ciwo, sunkuyawar
datayi ne yasa Dan kwalin kanta yafadi, Bata damu dashi ba taci gaba da kukanta
Bilal yana Kallan kanta Gabansa yafadi, wanne irin gashi gareta saikace aljana?
Anya yarinyar Nan kuwa bahaushiya ce? To Amma ai gashi tana hausa
Cikin nutsuwa da manyan ce yace mata, kiyi hakuri, mutuwa tazama dole, muma dukanmu
ita muke jira, nayi Miki alqawarin zan riqeki amana, babanki yabani umarnin intafi
dake gidan mu, kada nabarki da Marka
Dago kai tayi ta kalleshi,   baba Malam yace hakane Shalele, yayimin bayanin komai,
Kuma awajan nasa Ina ganin   zakifi samun kulawa fiye da wajan Marka, Bayan hakama
yanzu bakida wata alaqa da   Marka
Kiyi hakuri ki bishi, idan   yayi bincike yagano inda yayar maman ki take shikkenan
saiya maidake can
Babanki ba kuka yake buqata ba a yanzu, Addu'ah yake so, nizan wuce gida dashi akai
shi makwancinsa kema ki bishi kutafi
Idonta ta share tace baba Malam Yaya sunan mamata?
Sunan ta khadija, Kuma kamarta kikai babu abinda yarabaku da ita, mahaifin ki kuwa
kin riga da kinsan baida kowa, iyayensa sun Dade da rasuwa, inda yanada dangi dazai
sanar dake, nine danginsa Nima shine dangina
Bilal yace Nima babanta yayimin bayanin komai, Dan Allah idan kunje gidan kayi
kokari kadauko min wayarsa, zanzo nakarba dole saita nan ne zamu gane komai
Sannan Dan Allah baba kayi hakuri ayi masa komai anan, muma na nan Ko zamu samu
Ladan jana'iza, inyaso idan kaje gida saika sanar dasu komai, Nima din zanzo
Baba Malam yace to shikkenan babu damuwa dana
********
Acikin asbitin akayi wa baba wanka, Bilal yasanar da mutane nan da nan kuwa suka
taru Kamar ansan shi, jama'ah sukai ta tsayawa aka hadu aka sallaceshi Aka kaishi
gidan sa na gaskiya
Wajanta yakoma ya sameta a zaune ta rafka uban tagumi, domin ya kawar mata da
tunani yace my daughter kidena tunani haka kinji?
(tofa😃😱 kaji su Dr Bilal manyan iyaye)
Kiyi Addu'ah Ina ganin Hakan shine yafi , maza tashi mutafi gida
Batace dashi komai ba ta tashi tabi bayansa suka futo harabar asbitin, bude mata
gaban motarsa yayi ta shiga, sannan Shima yashiga yajasu, babu wanda yake magana
acikinsu , sai karatun qur'ani dayake tashi acikin motar, tayi lamo tana saurara,
rayuwa Kenan tazo da babanta yanzu Kuma zata koma ita kadai
Tana duniyar tunani batasan adadin tafiyar da sukai ba sai gani tayi sun shigo
gidan, megadi yabude masa gate yashiga
Yana tsayawa yafuto dasauri zai bude mata, saita bude da kantama ta futo, yace mata
taho mushiga ciki
Abaya take binsa Har suka shiga falon gidan, wata babbar mata zaune akan kujera sai
wata yarinya bazata wuce 20 ba, tana kwance akan kujera Agefen ta
Duk ido suka zuba masa ganin yashigo gidan tare da baquwar fuska
********
Babban office ne qayatacce, wanda aka Qawata shi da kujeru lafiyaiyu, biro ne
ahannunsa yana zagaye cikin office din yayi masifar kyau cikin suit ruwan toka
Meyasa tun jiya Hankalinsa yakasa kwanciya da ganin wannan bawan Allah? Ko kalau
yake yazauna abishiya yana bacci?
Yasan Cewa bashida alaqa da yarinyar da saminu yace tatare su, yasan Cewa wannan
kudi kawai take nema, Amma Har yanzu Zuciyar sa takasa nutsuwa da rashin tsayawa
awajan, gashi lokaci daya yaji Gabansa yana faduwa, menene dalilin Hakan? Oh ya
Allah shazali wannan ba halinka bane meyasa ka aikata Hakan? Sumar kansa ya
hargitsa afili yace Allah yasa ba abinda nake tunani bane, Allah yasa batare suke
da yarinyar data tare muba
Yana tsaye wata ma'aikaciya ta shigo office din nasa, takardu tabashi tace yallabai
ga takardun dakace ayi kokari ahada makasu
*******
Kuka take yi haiqan tana ihu, kan gari take danna ihu tana jama'ah kukawo min
dauki, nan da nan aka cika gidan nasu
Kowa tambayar ta yake lafiya kuwa? Nuna musu shi tayi da hannu, gashinan Malam
yahai ne Yazo yacemin Wai mijina yamutu, wallahi bazan yarda ba nasan hada baki
sukai shida Haneefa suka je suka ba dashi awajan masu shan jini wallahi bazan yarda
ba kotu ce zata rabani dakai yahai, idan mutuwa yayi Ina gawarsa take? Wayyo Allah
jama'ah kukawomin taimako yahai yagama cutata yasiyar min da mijina
Malam yahai yace Marka kiyi hakuri, wannan iface ifacen naki babu inda zai kaiki,
nide gaskiya nafada Miki Allah yayiwa Malam surajo rasuwa, yana gama fadar Hakan
yakada babbar Rigarsa yabar mata gidan, domin kuwa Har yanzu radadin rabuwa da
amininsa Bai barshi ba
Shin tana wannan haukan tayaya zai sanar da ita Cewa Malam surajo yasake ta? Idan
ta gama saiya dawo suyi maganar anutse
********
To hajiya kinji abinda yafaru, Ina fatan zaki so yarinyar Nan Kamar Yanda zaki Soni
Babu damuwa Lal, Allah yabamu ikon riqeta, dubansa yakai kan qanwar sa sadiya yace
Sady, ga qawa nan nakawo Miki
Kikaita daki tahuta Ko?
Tana Daga kwancen tace Yaya ga dakin can taqarasa ta zauna, Bansan tashi ni wallahi
nagaji (😔😔)
Bilal Yadubi Hajiya,, tagane nufinsa Dan haka tace zaki tashi ki rakata dakin Ko
saina saba Miki, nonsense
Tashi Sady tayi tana zumbura baki tayi gaba, Bilal Yadubi Shalele yace tashi kibita
Haneefa
Bayanta tabi tana Kallan ikon Allah, itama Sady cikin qunquni take Cewa mutum sai
shegen San girma Kamar gyanbo, shi meyasa bazai kaita dakin ba, suna Zuwa dakin ta
dubi Shalele tace ga dakin nan, gakuma toilet nan idan zaki shiga
Ahankali tace mata to, ta zauna Agefen gadon tafara tunanin sauyin rayuwar data
samu lokaci daya
Acan falo kuwa, Hajiya ta kalli dannata tace Lal Yaya sunan yarinyar ne? Yana
Murmushi yace Haneefa sunanta Hajiya, tace to Allah yajikan mahaifin nata, yace
amin
Tashi yayi yabi Bayan Shalele, yana Zuwa yaganta a zaune tayi Shiru, yace nace
kidena tunani fa haka, kada wani ciwon yakama ki, cire tagumin tayi tace to,
Kitashi kiyi wanka, ga wardrobe nan kisake kaya, kafin muje asiyo Miki wasu, Nima
zanje na watsa ruwa
Daga masa Kai tayi, sannan ta tashi tashige cikin toilet din
Shima cikin kwanciyar hankali yayi dakinsa ganin yarinyar tasamu karbuwa awajan
hajiyar sa
Bilal mukhtar Kenan Dana farko awajan Hajiya Halima, suna kiranta da Hajiya,
mahaifin sa yadade da rasuwa shine yake kula da mahaifiyar sa dakuma qanwarsa
sadiya datake University yanzu, Hajiya babu ruwanta tanada abin Daria, batada
matsala kokadan, Bata cika boye abuba, Kai tsaye zata futo fili tafada babu ruwanta
da boye boye, idan tanaji da gayu Bata Cewa Bilal saide ace masa lal🤣tofa Shima
idan yaji Hakan yasan Yan gayun nata Suna kusa, Shima de babu ruwansa, matsalar sa
daya San girma, yanada masifar son yaga Ana bashi girma
Wannan Kenan
********
Yana zaune akan lafiyaiyun kujerun falon, yadora kafarsa daya Kan daya akan dining
table din dake Gabansa Dan qarami, gorar ruwa ne akan table din da Glas cup, yariqe
jarida yana karanta wa
Qannansa dasun doso falon Suna ganinsa zasuyi birki su koma daki, momy ta futo
falon ta zauna tazuba masa ido tana kallansa, leshin jikinta kadai zaka kalla kasan
Cewa anzubar da dukiya awajan
Sake kallansa tayi yayi Shiru yana karatun jarida hankalin sa kwance, wannan wacce
irin rayuwa ce ace mutum idan yana gida qannanka bazasu sake ba, saikace wani dodo
yara su dinga gudun masifar ka
Ajiyar zuciya tasauke tace wato Kai Haneef anyi fira dakai Ana tambayar ka Ko
kanada Aure shine isa isa kace bakada shi, a a abin Bai tsaya haka bama Saida
kaqara da Cewa babu wadda tayima
Saboda kana ganin mun zubama ido muna kallanka, ai Kai da kunya ma kace bakada
Aure, dasai kadan sakaye kace inada Aure, rabuwa mukayi 😃kokuma kace inada Aure
mutuwa tayi matar tawa🤣
Amma inaaa, awajan Yan jaridar ma saika nuna halin ka, to nikam nagaji, nagaji da
wannan zaman Naka haka
Kallanta yayi da lumsassun idonsa, yace yanzu momy so kike nayi karya? Momy kowafa
yana Kallan wannan tattaunawar, tayaya qanne na zasu ganni babba Dani Ina qarya
Au ashe kana kunyar qannan Naka, ai nayi zatan baka kunyar su shiyasa kayi mirsisi
da maganar Aure
Kafin yabata amsa wayarsa tayi qara, ahankali Kamar mace cikin muryar sa me kama da
rada yace momy zan amsa waya Ina zuwa, yatashi yafice Daga falon
Ajiyar zuciya tasauke tadauki remote din gabanta, tasan Cewa ba dawowa zaiyiba, ya
silale kenan😃
********
Tunda baba ya mutu tasauya, tadawo Shiru Shiru babu magana, zaka sata komai tayi
but walwala Kam babu ita, idan tayi Shiru kawai tunanin rayuwar da sukayi da Baba
take, Allah Kenan baya barin wani dan wani yaji dadi, shikkenan inna saiki zuba
ruwa aqasa Kisha baba yatafi yabarmu dagani Har ke
Tana zaune acikin daki da daya Daga cikin kayan da Dr Bilal yasiyo mata na kanti
masu kyau da tsada, yau ake ukun mahaifin ta Shima yatafi Bai dawo ba Har yanzu,
tasan Cewa Tunda yamma tayi yakusa dawowa
Wani magazine ne Agefen ta tasa hannu tadauka ta bude tana karanta wa shafin farko
photon sane ya baiyyana aciki yana tare da wasu mutane Kamar ma turawa
Zara zaran yatsun hannunta tasa shafa fuskar sa, wannan mutumin yanada kyau, ita
kanta tasan Cewa yafita kyau nesa ba kusaba, Abu daya zata fada masa shine hasken
Fata
Hannunta yana kan face dinsa tatafi tunanin lokacin data fara ganinsa, sajen dayake
fuskarsa tatuna, Har gobe bazata taba mantawa dashi ba, mutumin daya temaketa da
kudi Har akayi wa babanta aiki, badan yabata wannan kudin ba tasan Cewa da kafin
ayiwa babanta aiki ma zai rasu, Tunda dole saita koma gida an hada kudin, koma ace
sai anzo Ana sayar da wata kadarar
Qasan photon ta Kallah inda aka saka sunansa, HANEEF BUKAR SHAZALI, Murmushi tayi
afili tace takwarana
Batayi aune ba Taji an fizge magazine din hannun nata, tana dago kai taga Sady ce
sai huci take
Ke wacce irin shashasha ce zaki daukamin Abu na kina kalla? Kinsan waye wannan din?
To shine rayuwa ta😳😳, Har gobe neman inda zan ganshi nake bansamu ba, saide na
ganshi a photo Ko video shine saboda wulaqanci photon Dana samu Ina ganinsa zaki
dauka Shima ki lalata min?
Kanta tadafe da hannunta Otace yar qauye Wai sadiya, Sady ake Cewa kingane? Fuuuuu
tashige toilet tare da banko kofar toilet din
Shalele cikin ranta tace ikon Allah, wato shi wannan din Har San ganinsa ake anrasa
Yaya za'a yi, shine ni na ganshi a araha a titi 😃
Tashi tayi tafice falo wajan Hajiya, tana zaune tana kallo, tace Hajiya akwai aikin
da za'a yi? Hajiya ta kalleta da sauri ta kawar da kanta gefe tace a a Haneefa jeki
daki kihuta babu komai
Tace to shknn, tareda Juyawa tana mamakin Hajiya meyasa yau Kuma batasan kallanta?
Koma menene Allah masani
Da daddare ta idar da sallah tana azkar Dr Bilal yashigo dakin yaganta, gefen gadon
yasamu yazauna, zuba mata ido yayi, yana yaba tsantsar kyau irin nata, dazai Iya
ajiye San girman sa agefe daya Aure ta, but bazai Iyaba, shifa Tunda akace anbashi
ita jiyake tamkar shine babanta, kyautar mutum sukutum batare dakasha wahala ba?
Aishi yanzu babu yashi yazama babba🤣🤣
Saida tashafa yace mata nadawo Daga kuje yanzu, munfara magana da Malam Yahya akan
issue naki but bamu gamaba nataho saboda ciko war mutane Amma nace masa zan koma,
inaso ayiwa Marka bayanin komai tare Dani
Dasauri yace what? Dr kikace kome? Kada kisake fada banasan jin wannan sunan Daga
bakin ki, Ko kice daddy kokuma uncle, kin fahimta?
Tunda baba yarasu yaune tayi daria, Kai wannan mutum wallahi dason girma yake, 😃
😃😃Ko Aure baida shi yana saurayi Amma Wai ince masa daddy
********
Zaune suke a dining su uku Suna break, Dr Bilal ya kalli Sady yace ke tashi kije
kikiramin yarinyar can adaki
Kallansa tayi tace yanzu Yaya yarinya da girman ta ita ba qarama ba Amma kana
cemata yarinya?
Ina ruwanki? Yarki Ko yata?
Tace yarka ce Yaya, aranta tana Cewa Wai shi Ala dole yasamu "ya
Bata tashiba sai kira data qwala mata da karfi
Futowa tayi daga daki da gudu kanta Ko Dan kwali babu, dama gashin nata babu kitso,
tana zuwa wajan Hajiya ta kalli gashin kanta taga Abu dogo Kamar aljana, ta kalli
idonta taganshi wani Kala daban qwayar idon ba baqa bace Kamar ta mage
Dasauri tayi qasa d kanta, Haneefa data lura da yanayin ta tace Hajiya Ina kwana?
Kan Hajiya aqasa tace lafiya Haneefa, Dr Bilal yace me kikeyi ne a daki bazaki futo
muyi break ba? Ahankali tace to uncle Ina zuwa, ta juya tayi cikin daki domin dauko
dankwalinta
Washe gari Alhamis kwanan baba shida da rasuwa, Dr Bilal na dawowa Daga aiki Hajiya
tace Bilal yace na'am Hajiya
Bilal, na'am Hajiya
Bilal na'am Hajiya
Saunawa nakiraki?
To Bilal ba shawartarka nakeba umarni nake baka kadauki yarinyar Nan kamaidata
garinsu, banasan ganin qwayar idonta, tsorata nake 😃😃Bilal ka tattara ta kutafi
Dan Allah, ni wallahi tsoron ta nake
Toshi yanzu ya zaiyi? hanyar dakin Sady yayi, yana shiga yaga tana Daria, tace
uncle kada kadamu, naji komai, nasan Hajiya nasona, bada niyya tayi hakanba, dama
Kuma zamana anan nasan bawani dadewa zanyiba, Tunda dazaran kagano inda dangin
mamata suke zaka maidani can, kada kadamu, zan zauna a gidan baba Malam harka Gano
inda yayar mamata take nakoma can, kaga sainaci gaba dazuwa makaranta ta Nima, aiba
wani dadewa zanyi ba aqauyen ma idan nakoma
Ajiyar zuciya yasauke yace kin amince da Hakan? Hakan yayi Miki?
Tace eh yayi uncle, ita kuwa tayi hakanne kawai domin tasan Yanda zatai tacika
burin baba na karbe Aududu Daga hannun inna marka
********
Washe gari sukayi sallama da Hajiya zasu tafi, sadiya ma da batasan baqi saitaji
babu dadi, Shalele harda tsokanar Hajiya tace to hajiya saina sake dawowa zan zauna
kiyimin kitso da kwalliya 😃😃Hajiya de ba um bare um um
Basu tsaya ako'inaba sai Garin kuje, suna Zuwa kuwa kofar gidan danqam da mutane
Ana sadakar bakwai, lokaci daya mutuwar baba tadawo mata sabuwa, yana yin parking
din motarsa suka futo, yagaggaisa dasu Malam yahai, sannan Malam yahai yayi masa
jagora Zuwa cikin gidan, Adede soron gidan Dr Bilal yace Malam inaga yau yakamata a
fadawa Marka komai, sannan inasan zan karbi wayar baba intafi da ita can Abuja,
baba Malam yace to likita babu damuwa, mu qarasa cikin gidan
Suna shiga cikin inna taga Shalele, nunata tafarayi   da hannunta tace gatanan
tadawo, Gara da Allah yakawo ki Haneefa, yau saikin   fadamin gidan uban wa kika
kaimin mijina? Kinje kinbawa masu shan jini shi Ko,   nan da nan kunsan mata da
tsegumi aka fara magana qasa qasa wasu Suna salati,   inna tataso tacakwami wuyan
Shalele ta shaqeta, lokaci daya tafara Tari
Dr Bilal da ransa yayi mutuqar baci yace kisaketa mana kada kiyi mata illa, inna ta
kalleshi da jajayen idonta tace bazan sake taba tsohon magulmaci ai dakai aka hada
baki aka salwantar min da mijina
Kasa controlling kansa yayi yadaga hannu ya wanke Marka da kyakkyawan mari
(💕Dan Allah karka karanta bakace komai ba, inasan Sharhi da comments,pls🙏🏻🙏🏻
 Ina whatspp readers masu tambaya yaushe Shalele zata hadu da shazali Dan Allah
kudena tambyata, mekukeci nabaka na zuba? Lokacin haduwar ne Baizoba idan Yazo dole
zasu hadu, babu wata wadda zata rubuta labari batasan qarshan saba, labarin yanada
tsayi , shiyasa nake kokarin yi muku meyawa, nide fatana ku kasance tare Dani
idan mutum yasamu dama zai iya tura shi Zuwa Ko ina😊 🙏🏻
                                                     😊 🙏🏻
                                                       😊 🙏🏻
                                                         💕
✍🏻
Mrs Usman
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
15&16
Zafin Marin dataji ne yasa tasaki wuyan Shalele   dasauri, gida ya kaure da hayaniya
Ana ayi hakuri mana, wasu suka fara tafiya Suna   Allah wadai da Hali irinna Marka,
banda shirme yaushe yarinya da ubanta zataje ta   siyar dashi
Dr Bilal banda huci babu abinda yake
Baba Malam yace meyasa kayi haka Dana? Bai Bawa   baba Malam amsa ba ya kalli inna
Marka data riqe kumatun ta inda aka mareta,
 Nunata yayi da hannu yace idan kinyi wa babanta ya qyaleki, ni bazan dauki wannan
ba
Baqin ciki Kamar ya kashe Marka, ita kuwa me zatayiwa wannan yaro da Shalele ta
huce? Anty murja ce tazo taja hannun inna Marka suka shige daki, haka ta dinga
tausarta harta Dan sakko, tace kiyi hakuri Yaya, nasan abinda zamuyi
Atsakar gida kuwa sabuwa matar baba Malam ce tazo takama Shalele suka zauna agefe,
dayake duk Suna gidan
Tace kiyi hakuri Shalele, me hakuri yana tare da Allah
Baba Malam yaja hannun Bilal sukabi Bayan Marka daki, suna shiga baba Malam yace
Marka akwai maganar data kawomu wajan ki me muhinmanci, Amma yanzu kafin nan munaso
kibamu wayar Malam surajo akwai abinda zamu duba aciki
Saida ta watsa musu Kallan harara sannan tace za'a duba, Shima Dan tana tsoron shan
wani Marin ne
Baba Malam yace to shikkenan muje Daga waje Bilal, suna fita murja tace me zasuyi
da wayarsa?
To wacce irin magana zakuyi Kuma? To Allah yasa de ta rabon gadonsa ne abaki
kasonki Dana danki, kekam ai kece da dukiya keme da namiji
Marka aka turo dankwali gaban goshi tace wallahi kuwa (nikwa nace zakiga gado😃
Shima baban ai yasan meyake)
Awaje su Dr Bilal suka zauna Har aka gama sadakar bakwai, Har kusan magrib Saida
mutane suka watse sannan, su baba Malam suka shiga gidan, baba Malam yace sabuwa
kuje gida keda Shalele tahuta, sabuwa tace to Malam, takama hannun Shalele suka
tafi, sukuma suka tsaya a yar rumfar, murja ta futo tsakar gidan ta shinfida musu
tabarma, gidan ba kowa duk an tafi, tace musu ga wajan zama, suna zama Marka ta
dauko musu wayar baba me coculan,Saida ta tsaya tacire Sim card din ciki tun a daki
sanan takawo musu tace ga wayar, wacce magana ce Kuma kuka zomin da ita?
Yace Ina nufin Malam surajo yayanke igiyar Aure tsakanin ki dashi, yace asanar dake
saboda cutarwa dakuma azabar dakika Bawa yarsa yace yasakeki saki uku
Marka tadauki hannu ta Dora aka, tace nashiga uku ni Marka, Innalillahi wa inna
ilaihirraji'un, nacuci kaina Marka, Malam yahai wannan maganar taka da gaske ne?
Baba Malam yace hakane Marka saide kiyi hakuri, kuka taci gaba dayi haiqan
Kiran sallar magrib da akayi ne yasa, baba Malam yace likita muje muyi sallah mu
dawo muji Yaya za'a yi
Suna fita, murja tace Kai amma surajo Bai kyautaba, yanzu duk irin riqon dakikayi
wa yarinyar Nan ashe baya gani? Dan gadon damuke jira shine yayi mana buqulunsa?
Yanzu duk uban gonaki irin nasa shikkenan kefa kin tashi atutar babu
Marka ta goge hawayen idonta tace Niba wannan nema ya dameniba, Tunda akwai kason
Aududu aciki ai shikkenan, abinda yafi damuna ya qonamin rai shine saqon sakin daya
Bawa Shalele ta fadamin, yarasa wazai aika sa saqon Cewa yasakeni sai ita? Yanzu
murja Malam idan be Iya rubutu ba, aiya Iya ajami
, gashi shi wannan Yaron danme tsaurin ido Yazo yatsaya harda mari nah, waini Marka
uwar Aududu ni zai mara? Bazai Iyuba saina dau fansa akansa murja, itama Shalele
bawai taci banza bane, saita gane Shayi ruwa ne akan abinda zanyi mata
Murja tayi Ajiyar zuciya tace Gaskiya de abin babu kyautata wa aciki, kome zasuyi
da wayarsa Kuma?
Marka tace sai yanzu nagane abinda zasuyi da wayar Malam, murja tace me zasuyi da
ita Yaya?
Murmushi tayi tace bazaki ganeba murja, Amma idan suka dawo zaki gane komai, tashi
muyi sallah, suna yin sallah basu idar bama su Dr Bilal suka dawo, suka zauna akan
tabarman Daga gefe
Suna idar wa Marka ta sunkuyar da kanta qasa Kamar ta Allah, baba Malam yace yanzu
Marka Yaya za'ai? Kina ganin za'a raba gadon Malam surajo ne abawa danki ka sonsa
ku kama hanya kutafi gida kokuma Yaya?
Hawayen baqin ciki yazubo mata, tace yanzu Malam yahai ba wannan ne agabana ba, Dan
Allah kakiramin Shalele na roqi yafiyarta, wacce irin mace ce ni ace mijina ya mutu
da baqin ciki na? Dan Allah ka temaka kakiramin ita
Malam yahai yatashi yaleqa ta katanga yakira Shalele, Aikuwa tasaka hijabi ta futo,
tana zuwa inna tafashe da kuka tace kiyafemin Shalele, wallahi ni kaina nasan
nacutar dake, kiyi hakuri ki yafemin yata
Ahankali yace to inna nayafe Miki, Allah yayafe mana baki daya
Dasauri Shalele ta dago kanta ta kalleshi cikin faduwar gaba, yanzu Yaya zatayi
Kenan?
Marka tayi Murmushi tace, wayar Malam a kashe take yaro, banma taba kunna taba bare
nasan akwai layi aciki Ko babu, ni kuwa dagani Har Shalele Bai siya mana wayaba
Marka tayi hamdala acikin ranta ganin tarkon yafara aiki, dasauri tace kanaso
kakira Hajiya Hafsat ne?
Gaba dayansu suka bita da kallo, Shalele mamaki yakamata, dama inna ma tasan yayar
mamanta? Amma shine Bata taba nunawa ba?
Dr Bilal yace eh inasan ganinta dasauri
Marka tace kada kadamu, Aina fadama Nima Kamar uwa nake wajan Shalele, nayi nadamar
abinda nayi mata Abaya, Kuma inde wannan ne karka damu, nasan Hajiya Hafsat, Kuma
nayima alqawarin gobe Ko jibi zata gana da Shalele, zansa akai Shalele Har wajanta
Bilal yace Kinga malama ki tsaida mana rana daya, in gobe gobe, in jibi jibi inzo
indaukeku amotata muje Dani da Malam yahai muganewa idonmu gidan
Marka to shknn nayima alqawarin kadawo jibi, saimuje gaba dayanmu, sauran magana ta
gado Kuma akwai Malam yahai akusa
Dahaka tattaunawar tasu taqare, Baba Malam yace to Shalele tashi mu tafi wajan
sabuwa saiki kwana acan, dasauri Marka tace a a ba za'a yi hakaba, Malam yahai nifa
Naga Kamar baka yarda daniba, Dan Allah kabarta ta kwana awajena, muyi firar yaushe
Gamo, kaga tasamu damar dazata hada Yan kaiyaiyakinta ma
Dr Bilal yace zata kwana, Amma karki yarda kiyi mata wani Abu, idan kika cutar da
yarinyar Nan nadawo jibi tasanar Dani ranki zaiyi mummunan baci, inna tace na
yarda, wallahi na yarda Dana
Dahaka suka futo Daga gidan shida baba Malam, Shalele Saida tarakoshi Har kofar
gida, tace uncle ka gaida su Hajiya, zuba mata ido yayi baice komai ba, baba Malam
yana ganin haka yayi Murmushi yashige gidan sa, cikin ransa yana Fatan ace soyaiya
ce a tsakaninsu
Hankali nane Bai kwanta da matar nan ba, kina ganin zaki Iya kwana kuwa?
Zan Iya uncle, Koda zataci gaba da ganamin azaba zan jure, Tunda kwana dayane
kawai, inma naji bazan jure ba, aiko ta katanga zan dira gidan baba Malam
Daria sukayi gaba dayansu, jin wannan maganar Tata, yace to shknn saina dawo jibin,
Ko akwai abinda kike buqata?
Tace a a uncle babu komai, yace to Saida safe yashiga mota yatafi, Saida ta jima
Awaje tana Kallan motarsa harta qule sannan ta juya ta shiga gidan
Inna Tana ganin ta tace zo Shalele, adarare ta qarasa tabarmar ta zauna, inna akace
kiyi hakuri kinji? Munyi rashin Malam dagani harke saide mu bishi da Addu'ah,
ahankali tace hakane inna
Anty murja tace Haneefa kiyi hakuri Dan Allah akan abinda yafaru Abaya, tace babu
komai anty
Inna tace to Bari muyi sallar ishsha'i, kema kije dakinki kihuta, ta tashi tashige
dakinta, suna idar wa ta kunce gefen zaninta ta dauko Sim card din baba tasaka
abakinta ta tauneshi, murja tana kallanta tasaki Murmushi
Tace murja tashi kirakani wani waje, Tunda Allah yayi banida rabon takaba, Daga
murya tayi tace Shalele zanje nan maqota nadawo kinji yata
Dasauri ta futo tace to inna saikun dawo, suna fita ta zauna atabarmar tsakar
gidan, tatafi duniyar tunani, Allah Allah take jibi tayi taganta awajan dangin
mamanta, haka kawai duk da yarinya ce Taji wannan tuban na inna Bai shigetaba,
yanzu menene mafita Yaya zatai ta dauke Aududu? Ta wacce hanya?
Su inna Suna fita, ta Cewa murja, ai tarkona yagama ci murja, Allah yakaimu gobe
kiga aiki da cika wa, yanzu de rakani gidan ladidi tijara yar Abuja jiya tazomin
gaisuwa nasan tana gari,
Sun dauki hanyar gidan ladidi suka hadu da yawale qaninsu wani tantirin mashayi,
yawale yace nida nake shirin Zuwa wajan ki kiban na sigari, Marka tace to kaje ka
jirani ganinan Zuwa
Yana tafiya murja tace Anya Yaya kina ganin kuwa bazai yiwa yarinyar Nan wani Abu
ba? Marka tace kyaleshi yaje, Shima yasamu rabon sa, Aikuwa suka sheqe da Daria
suka tafa, suka shiga gidan ladidi, Marka tafara Koro mata kwanan zance dakuma
abinda yakawo su wajanta, babu wata wata ladidi tace ta amince, tadauki kudi dubu
hamsin tabawa Marka, suka juyo gida
********
Acan gida kuwa yawale yana Zuwa ya kwala sallama Daga soron gidan, Shalele ta leqa
tace a a kawu yawale (dayake haka take fada masa)
Yana ganinta haka babu hijabi yaji ya kwadaitu da ita, yajuya bayansa yaga babu
kowa, ya lashe baki saikace baqin maye, yace a a Shalele, ashe kin dawo
Ya matso kusa da ita yace Shalele Shalele, wato dama akwai wata magana data Dade
tanacin dunduniyar zuciyata🤣inaso nafada Miki Amma nakasa
Matsota yasakeyi Har yana gogar jikinta, dasauri ta matsa baya, yayi sauri yamata
kyakkyawan riqo yace wallahi Ina sonki Shalele, zaro ido tayi ta rufe bakinta da
hannunta 😳tace mekace kawu?
Shikuwa yana ganin ta Dage hannunta yayi zuruf yasaka hannunsa Akan kirjinta, Yan
madaidaitan na shanunta yakama yafara matsewa
Ai Shalele najin haka tadaga hannu Iya karfinta ta maka masa bugu akansa, tsinanne
kasakeni nace, azzalumi, Allah ya isa na, wuta balbal Dan iska
Ta kwasa da gudu tashige dakinta, tasaka sakata, sai huci take, jikinta ko'ina yana
rawa
Tana jinsa Yazo gaban dakin nata yadaga murya Yanda zata jishi yace yarinya dakin
tsaya kema aida kinji dadi, abin nakima babu laushin kirki da alama nine nafara
tabawa, saide Kuma da alama zasuyi girma sosai, kinyiwa kanki, yajuya yafice Daga
gidan
Tanajin fitar sa tasaki Ajiyar zuciya, Bai Dade da fita ba su inna suka dawo,
tanajin ta tana kwala mata kira, tadaga murya tace inna zazzabi nakeji na kwanta
Saida safe
********
Washe gari da safe ta shiga gidan baba Malam suka gaisa, sannan tadawo gida, babu
wani Abu da inna ta nuna mata, suna zaune lafiya, Har la'asar, ta shiga daki tana
sallar la'asar inna tace Shalele!!!! Dasauri tashafa Addu'ah ta futo, tana futowa
taga inna dawata mata gabjejiya, taci kwalliya taci uban mayafi, ta Cewa matar Ina
wuni
Ladidi tace lafiya, sannan ta kalli Marka tace to ni zan wuce Marka, inna Marka
tace Shalele baki gane wannan bako? Daga Abuja take, maqociyar Hajiya Hafsat ce
yayar mamanki, jiya muka hadu nake cemata muma ai Gobe zamuzo
Cikin tsananin murna tace laaaaa Dan Allah kinsan yayar mamata? Ladidi tace yanzu
hakama dazaki bini Har wajanta zan kaiki
Inna tace ah meze Hana, Shalele kawai kibita, Tunda muma gobe zamu biyo bayanku
dasu Malam yahai, saiki dauki wasu kayan ma kiyi gaba dasu, sauran nakawo Miki
goben
Dasauri tace to, tashige dakinta Bata dauki komai ba sai kayanta Kala biyu da
photon baba, ta futo suka tafi, inna tace insha Allah muma da safe zaki ganmu
kinji? Shalele cikin murna tace to inna saikun zo
Sun futo Daga gidan ta dubi ladidi tace Dan Allah zanyi sallama dasu baba Malam,
ladidi tace to shiga amma kiyi sauri
Shalele tashige gidan baba Malam ta inna sabuwa Ina baba Malam, sabuwa tace Malam
yafita Shalele, Ina zaki da kaya ahannu?
Inna sabuwa Malam yahai baiyi mata bayanin komai ba jiya, tayi tunanin da wannan
baqon likita zasu tafi, danhaka tace to Allah yakiyaye Shalele, tace amin tafice da
gudu
Suna fita suka yi bakin titi, suka tare mota suka shiga sai cikin Abuja, tafiya
anayi da dadi ba dadi Har dare, mota duk aragargaje, tun tana Kallan hanya harta
dawo ta daina ta kwantar da kanta acinyar ta
Sai dare suka isa gidan ladidi, gidane Dan qarami Mai kyau madedeci, daki biyu da
falo da tsakar gida,ladidi tafada cikin kujerun falon nata tace wash Allah nagaji
wallahi
Shalele kuwa ta zauna akan hannun kujera tace Toni intafi idan kin huta kyazo?
Inane gidan Daga ciki? Nagaba ne kokuma wannan na Bayan damuka Bari?
Ladidi ta kalleta tace kije Ina? To Marka aikatau tace nadauko ki nakawo ki Abuja
(tab gaskiya gobe akwai kafce, 💪🏻, menene zai faru idan Bilal Yazo ya iske wannan
labari? Anshaqe mata wuya ma yayi mari to inaga ya nemi yarsa 😃 😃 😃 😃 yarasa??
Yaya makomar inna Marka gobe?
✍🏻
Amnanku ce
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
17&18
Tsananin mamaki ne yahanata magana, aikatau? Batasan lokacin data zame dagakan
hannun kujerar datake zaune ba, sai jinta tayi jagwab aqasa
Ladidi tijara tace menene abin faduwa, nabata dubu hamsin kudin aikinki Kenan na
wata daya, saboda akan haka nake bada farashin yaran danake bayarwa aiki
Zuwa yanzu Kam Zuciyar ta ta tsike, idanunta qamas   babu alamar kuka, meta yiwa inna
Marka ne haka datakesan ganin bayanta?tukunnama su   waye dangin mamanta? Su waye?
Huci tafara Kamar zakanya, idan tayi karatu tazama   lauya! Idan tayi karatu tazama
lauya saita kashe inna Marka (😠😣😠gaskiya Shalele     yau rai yakai mutuqar baci)
Ladidi tijara ganin yarinya ita kadai tana huci Kamar kububuwa tace, zaki dakenine
saboda nafada Miki gaskiya? Kinga yarinya ni babu abinda yadameni dake, bazaki rasa
ci da shaba agidana, Abu daya nasani bazan barki kije ko'ina ba, batare dakin
biyani kudi naba, ki danqamin dubu hamsin indanqa Miki kudin Mota kikoma gidan ku,
inba haka ba kuwa Sunana ladidi tijara wallahi tijara zan nuna Miki
Hawaye ne yazubo mata, Bana komai bane saina haushin kanta dataji saboda rashin
karbar number uncle Bilal jiya, Allah sarki, yanzu haka yaji ajikinsa ne bazai sake
ganinaba shiyasa jiya yacemin shi tuban inna Bai kwanta masa Arai ba
Hannu tasa ta goge hawayen idonta, yanzu Kam Ko ance mata ga hanya Takoma Garin
kuje babu inda zata, da masifar yawale zataji Daga karshe ma ya lalata mata rayuwa
kokuma da rashin dangin uwa da uba? Yanzu dama inna batasan inda dangin mamanta
suke ba shine jiya tayi tuban muzuru ta nuna musu zata kaisu gidan?
Bazata taba komawa kujeba sai tayi aikin da inna ta Dora ta akai, tasamu kudi
tazama lauya, Daga karshe taje takashe ta
Allah yakareka Aududu, Allah yakareka a duk inda kake
Kayan hannunta ta zubar aqasan ledar falon ta futo tsakar gida, ladidi na kallanta
batace komai ba, aranta tace yarinya bani kudi na, nabaki hanya
Ita kuwa Shalele alwala tadauro tadawo falon ta kunce Dan kwalin kanta ta shinfida
tafara rama sallolin dake kanta na magrib da ishsha'i
Ta Dade tana ma kanta Addu'ah itada Aududu, sannan tashafa, ladidi ta tashi takawo
mata abinci jallop din shinkafa tace ga abinci kici, girgiza kanta tayi batare da
tace mata komai ba, tabe baki tayi ta dauke abincin ta
Awannan wajan datayi sallah anan ta kwana, ladidi tabata wajan kwanciya tayi banza
ta qyale ta, itama kuwa ta shareta tashige daki ta dauko katifa babba tashinfida a
falon tayi kwanciyar ta, Shalele na zaune akan Dan kwalin ta, anan wajan tazame ta
kwanta itama
********
Washe gari da safe wajan karfe goma, wani Alhaji yayi sallama yashigo sai kada key
din motar dake hannunsa yake, Bayan sun gaisa da ladidi yace ladidi akwai yarinya
kuwa wadda zata dinga yiwa iyalaina wanki da guga ? Shalele tana jinsa tana zaune
agefe Ko ina kwana batayi masaba (lalle Shalele ankaita karshe😅😂)
Dasauri ladidi tayi zuruf tace ah haba Alhaji Yusuf ai ba'a rasasu a gidan nan,
Bana rabo dasu ai, yanzu ma ga wata nan a zaune idan tayima, ta nuna masa
Shalele 😃😃kallanta yayi, yaga yarinya Kamar dutse Ko motsi batayi, yace no ladidi
wannan tayi qarama dayawa, bazata Iya daukar nauyin aikin gidanaba, zan dawo wani
lokacin Ko za'a samu wata, haka yafice,Shalele tabi bayansa da harara, Dan renin
hankali, in banda ma rayuwa harya isa ya kalleta yace tayi masa wanki? Tona ubanta
ma batayiba bare nawasu iyalansa😀😃😀
********
Sabuwa yi kokari ki daukomin asuwaki na a daki in samu in fita kofar gida injira
Yaron nan likita, nasan yanzu duk inda yake yakusa Zuwa mutafi
Sabuwa tace a a Malam Ina zakuje? Yace Abuja zamu shiga, zamu Kai Shalele wajan
yayar mahaifiyar ta
A a Malam ba jiya jiya shi Likitan Yazo yadauki shalelan ba da yamma? Jiya tazo
tamin sallama zata tafi,harma ta tambayeka nace kafita, Dama batare take dashi ba?
Gaban Malam yahai yafadi yace Wai wacce shalelan kike nufi ne sabuwa? 😳
Wajan zama yanema yazauna jagwab aqasa yadafe kansa dake masa ciwon nan take yace
sabuwa kin kasheniPP
*******
Nnamdi Azikiwe   international   Airport
Cikin takunsa na qaqqarfan namiji yafuto Daga cikin Airport din, yana dauke da
brief case dinsa ahannu
Matum biyu ne majiya karfi suka qaraso gareshi da sauri, daya Daga ciki yayi sauri
yakarbi jakar hannunsa, dayan kuwa sai muzurai yake yana Kalle Kalle awajan
Kamar kullum yauma wankan Suit yayi, Amma fara, sosai yayi masifar kyau, Kamar ka
saceshi, suna futowa waje yanufi wajan da motocin sa suke jere guda uku, daya Daga
cikin guard din ne yayi saurin bude masa motar tsakiyar Prado launin ash
color,number motar ansa SHAZALI NO.4 yana shiga suka rufe sukajashi Zuwa gida
Megadi najin dirin motocin yatashi yabude da sauri, suka shigo, bude masa motar
sukai yafuto, aka biyo bayansa da brief case dinsa
Saida suka kawo shi Har bakin kofar falon sannan yakarbi jakar sa, yace zaku iya
tafiya, yajuya yayi cikin falon
Momy na zaune dawasu yara yanmata guda biyu, daya na danne danne awaya, daya nayiwa
wani yaro karami home work
Salamu alaikum
Gaba dayansu suka dubi maiyin sallamar, dasauri yaran suka fara Cewa Yaya sannu d
Zuwa, daya tashige daki, itama dayar takama hannun Yaron zasu tafi daki, momy tace
ke samah, barmin yarona anan, kude kuje
Murmushi Haneef yayi yace to Yanzu momy ni Daga dawowata kinji nayi musu magana ne?
A a ai Kai dinne halin ka nasani Haneef, yanzu zaka fara masifa babu gaira babu
dalili
Murmushi yayi baice mata komai ba dama itama batasa ran zaiyi maganar ba
Lallausar sumar kansa yashafa yace momy kwana biyun? Ko kinyi missing Dina ne?
A a wanne missing? Inrasa wazan yi missing sai tsohon tuzuru?
Momy I'm tired, zanje part Dina, dasauri yafice yabar falon yayi part dinsa
Yana shiga tun daga falo ransa yafara baci, hannunsa yasa akujerun falon farare,
sannan yaduba hannun yaga qura ajiki
Dakin yashiga, ya cire takalmin kafarsa, Taku daya biyu yayi, sannan yakai dubansa
ga safar kafarsa, ya cire safar yayi jifa da ita, yafuto yanufi part din momy rai
abace, meyasa yaran nan suka renashi ne? Koda yaushe sude kawai burinsu subar masa
dakinsa da datti, daki duk ya lalace ko'ina qura
********
Yana parking motarsa yaga Malam yahai zaune a kofar gida yayi tagumi, futowa yayi
daga motar yabashi hannu suka gaisa, yace a a yanaganka a zaune anan, tashi mu
qarasa mana, yakamata ai su futo mutafi da wuri
Baba Malam yace likita akwai matsala
Wacce irin matsala Kuma? Meyake faruwa ne? Baba Malam yakwashe komai yafada masa
Kamar Yanda sabuwa tabashi labari
Becewa baba Malam komai ba yanufi gidan Marka, baba Malam yayi sauri yariqoshi yace
tsaya likita mekake shirin yi?
Baba Zuwa zanyi intisa qeyar Marka takaini gidan da takaimin yarinya, domin na
tabbata dole akwai saka hannunta aciki, nide banzo na dauke taba, Toda wanne shege
zatayi tafiya? (tofa kaji masu yarinya😃😀)
Baba Malam   ya lura idan yabar Yaron nan yashiga to za'ai batacciya Dan haka yace
muje, muje   wajanta tare
Suna shiga   gidan kuwa inna na zaune Atsakar gida, ta Dora kafa daya Kan daya, tana
ganinsu ta   turo Dan kwalin ta Gaba, dama tasan wannan lokacin yana nan Zuwa
Ihunta sabuwa Taji, itama tayafa mayafi tabiyo bayansu, Malam yahai tatarar yana
riqe Bilal wanda yake dukan Marka haiqam Kamar Allah ya aikoshi, dasauri ta cire
mayafinta taci damara dashi, tafara kokarin cetar inna Marka, daqyar Malam yahai ya
tsaida Bilal Daga dukan Marka, ransa abace yana huci yafice yabar gidan jikin
motarsa ya tsaya, wannan matar meyasa batada Imani ne?
Dasauri yadauko wayarsa yakira police, sannan ne yaji ransa yadan fara yin sanyi,
yana tsaye a kofar gidan Har Saida motar police din tazo sannan ya nuna musu gidan,
Aikuwa suka shiga aka tisa qeyar inna Marka, Shima yabisu Abaya tareda sabuwa da
Malam yahai duk suka rankaya Zuwa police station din
********
Yana komawa part din momy yagansu sundawo falon gaba dayansu, nunasu yayi da hannu
yace ku!!! Dukansu suka kalleshi lokaci daya cike da tsoron masifar sa
Ni zaku yiwa rashin kunya Ko? Yaushe nafara wasa daku? Eye yaushe nafara wasa daku?
Momy dake zaune tana ganin ikon Allah tace haba Alhaji shazali 😃me yayi zafi ne
haka ido zaici wuta? Me sukayi ma Daga dawowar ka kahau minsu da fada?
Yanda kasan yayi kuka, cikin takaici da shagwabar dashi kansa Baisan ma yayi ba
yace shekaran jiya da zanyi tafiya nacewa Samah su tabbatar sun gyaramin part Dina
Amma yanzu Ina shiga ko'ina qura, ni Dan qazamin inane dazan kwanta ahaka?
Nunasu yafara yi da hannu yace kingani Ko? Kinga irin renin hankalin nasu Ko momy?
Kasa yarinya aiki saboda tagama renama hankali tace ba ita kasaba
Momy tayi Murmushi ganin yanda yadage yana shagwaba agaban qannansa kokuma Baisan
yanayi bane?
Tace to Kai Haneef mashirmacin inane da za'a Haifi Yaran agabanka Amma ace Har
yanzu kakasa banbance su?
Yaga alama momy Bata dauki maganarsa serious ba, danhaka ya kallesu yace Dan Allah
ku Bari natashi Daga bacci nakoma part din na ganshi da datti, yasa kafa yayi ball
da wayar wata acikinsu dake qasan kafet, itama Baisan ta wace ba acikinsu , saboda
wayar ma iri daya suke riqewa,🤣 yayi dakin momy yana masifa cikin ransa, da wannan
masifar harkokin nasa zaiji kokuma da tsayawa yana banbance wasu yara
********
Acan police station kuwa, d.p.o ya kalli Dr Bilal yace meke tafe daku ranka yadade?
Dr Bilal yadauko ID card dinsa ya nuna musu sannan yabasu labarin duk irin azabar
da inna tabawa Shalele, ya Dora da Cewa, yallabai Hakan datayi be ishe taba, Saida
ta yaudaremu tace yau muzo zata kaimu wajan yayar mahaifiyar yarinyar Nan, ashe
batasan inda takeba, Sim card din babanta dazamu samu kowanne information aciki ta
cire ta taune, Kai Daga qarshe ma ta tura yarinyar Abuja Wai aiki
Dpo ya kalli Marka yace hakane baiwar Allah?
Tace eh hakane
Saboda mijina yana fifitata akaina, ba yayimin komai sai abinda yarinyar takeso,
Daga karshe ma yabata saqon saki tafadamin, ta nuna Bilal da hannu tace Sannan shi
wannan Dan tsaurin idon harda marina, shiyasa nadauki mataki dakaina
Nakaita wajan ladidi tijara, nace takai ta koma inane tayi aiki, nide fatana kada
Taji dadin rayuwa
Dasauri Bilal yace Aikuwa Nima yau zan nuna Miki Sunana Bilal Dan tijara 😂
Dpo yace kayi hakuri ranka yadade
Sannan ya kalli Marka yace yanzu Ina zamu samu ladidi a karbo yarinyar awajan ta?
Tace sun tafi Abuja jiya, Bansan gidan datake ba, Bansan unguwar datake ba
Shi kansa Dpo din mamakin karfin halin ta yake, yace Amma Yaya akai kika Santa Har
kika dauki yarinya kika Bata?
Anan Garin take, Amma Bata zama tana zuwa ne lokaci Zuwa lokaci Takoma Abuja
Dr Bilal yace dakata yallabai, yasa hannu ya fizge Aududu Daga hannun Marka yace
Yanda kika dauki 'yata kika turata duniya, to Nima zan dauki danki yanzu, mushiga
duniya dashi tare, bazaki sake ganin saba Har sai lokacin danaga 'yata, yakalli Dpo
yace yallabai bakuda matsala Dani wajan kudi, Ko nawa kuke buqata zan aiko muku,
Abu daya nakeso awajan ku shine, kuci gaba da riqe wannan maha'inciyar ahannunku
kuci gaba da gana mata azaba, kada kusaketa har sai nabaku umarni
Aikuwa nan take aka tisa qeyar Marka aka kulle, sai ihu take tana Kiran sunan
Aududu
Dr Bilal da Malam yahai da sabuwa suka kamo hanya sukayo gida, Malam yace yanzu
likita Yaya zakai da wannan Yaron? Murmushi yayi yace ai baba babu abinda zaka yiwa
uwa Taji ciwo irin karabata da danta, tarabani da 'yata Nima narabata da danta🤣🤣
Sabuwa tasa hannu ta karbeshi suka shiga mota, da tambaya suka isa gidan ladidi
tijara, gidan a kulle yake, Saida suka tambayi duka maqotanta Ko sun San gidan
datake a Abuja kokuma unguwar datake, Amma kowa yace baisani ba, asalima Ko number
ta basu dashi, saboda batada mutunci yanzu zata nunama tijara
Haka suka dinga yawo Ana tambayar ladidi, kokuma wanda yasan wani nata, Amma babu
wani bayani, Har yamma lis sannan Dr Bilal yace yabawa Malam yahai katinsa yace duk
lokacin dayaji wani bayani, Toya kirashi yasanar dashi
Yasa hannu yakarbi Aududu ahannun sabuwa, sabuwa tace yanzu yazakai da yaro likita?
Ka barshi zan riqeshi ahannu nah
Yace karki damu inna, insha Allah zai samu kulawa sosai, Kamar Yanda zan Bawa
yar'uwar sa
Haka sukai sallama dashi rai duk babu dadi, shi kansa yana driving wani qullutun
baqin ciki yakeji aransa, yana ganin Kamar yakasa cika burin Malam surajo ne akan
Shalele, Aududu kuwa yana zaune akujera sai wasansa yake
Kai tsaye gida yaje yabawa Mai aikinsu Yaron yace ta kula masa dashi idan Baya nan,
idan yadawo Daga aiki Kuma zaici gaba da kula dashi, Hajiya ma ta amince da Hakan,
yayin da Sady ma tayi murna da Yaron kasancewar basuda qaramin yaro a gidan
Tabbas Addu'ar wanda aka zalunta batada hijabi tsakanin ta da Allah, Allah ya amsa
adduar ki Shalele, haqiqa Aududu yafada hannun wanda bazai taba Yada Shiba
********
Washe gari da safe Suna yin break fast da momy da daddy, Haneef Safah Samah,
huzaifa
Safah tanaci tana chtting, yayin da Samah take leqawa tana ganin abinda yar'uwar ta
take
Saida yadau minti biyu sannan yayi magana, (nikwa nace aaaa to inaga Dan awajan
uban ya koyi rashin magana😃😂)
Hajiya wannan shine Karo na biyar da ake kawo wa Yaron nan Mai gyara masa part
dinsa yana korarsu
A a Alhaji ba za'a yi hakaba, kayi hakuri kasa akawo masa, insha Allah wannan Karon
ba za'a samu matsala ba
Baice mata komai ba, yadauki waya yakira abokinsa, hello Alhaji Ghali, idan babu
abinda kake Dan Allah Mai dakina tanaso kasa a turo mata me Aiki guda daya
Shiru yayi daga yana sauraron abinda ake fada, yace a a idan ansamu din koma yaushe
ne, kawai a turo ta, ok, ok to ngd
Yakashe wayar yaci gaba dacin abincinsa, Hajiya tayi Murmushi tace godia Muke
Alhaji, Shikuwa baice mata uffan ba
********
Suna zaune Atsakar gida, ladidi ta kalleta tace ow nikuwa zan Dade banga mutum Mai
baqin jini irin naki ba😃😒ace kowa Yazo neman Mai aiki basa daukar ki? Koda yake
ai na lura da niyya kike musu rashin mutunci, Kuma wallahi dakinqi dakinso sai
kinyi aikin nan, yarinya idan bakyason aiki danqamin hamsin Dina na danqa Miki
hanya
Shalele najinta tayi banza ta kyaleta, suna wannan zaman doya da manjan wayar
ladidi tayi qara, kawai Cewa tayi ah akwai, yanzu ma akwai wata yar ahannu, Dan
Allah wannan familyn ne suke buqata? 😳a a yanzu zanje nakaita, ngd Hajiya sai
anjima, takashe wayar ta dubi Shalele tace saiki tashi mutafi
Ansamu wani gidan dazan kaiki, Nima cikin satin nan zanbar gari, dama ke kika
tsayar Dani, saboda baqin jini
Shalele batace mata komai ba ta tashi tashirya, tadauki kayanta da photon baba,
suka fita Daga gidan, taxi suka tare suka shiga, tanaji ladidi nayi musu kwatance
Har sukazo kofar wani gida da wani mekeken gate
Suna shiga harabar gidan Shalele tazama yar qauye tuburan domin kuwa Kai bazakace a
Nigeria kake ba, shukokin fulawoyi Tako Ina
Har suka je falon, gaskiya falon yahadu, ita da za'a Barta a Iya falon ma kadai ya
isheta rayuwa Allah sarki Shalele 🤣🤣
Wasu yara tagani guda biyu, bazasu girme taba, tsananin Kamar dasuke ne yasa takasa
banbancesu , Hakan ne ya tabbatar mata da Cewa Yan biyu ne
Ladidi ce cikin fara'ah tace yanmata sannunku, Safah tace yawwa, Amma Samah Ko
Kallan inda suke batayi ba
Ladidi tace Hajiya Ina kwana? Dama anyimin waya ne akan nakawo Miki me aiki, shine
nasakota agaba nakawo ta
Momy ta kalli Shalele taganta yarinya, tabe baki tayi tace ok, eh gaskiya muna
neman me aiki,akwai aikin da za'a Bata, Amma yanzu de nawa za'a dinga baki kudin
aikinta duk wata?
Ladidi tace Hajiya ai mukam bamuda zabi, Ko nawa kika yanke yayi
Tace ok, Jakarta dake kan kujera ta dauka tace to za'a dinga Bata dubu tamanin duk
wata
Ladidi ta Washe baki cikin farin ciki
Ta kalli momy tace Hajiya yayi, momy ta zaro kudi tabawa ladidi tace to ga kudin ta
na wannan Watan, inyaso duk wata saiki dinga Zuwa kina karba mata
Ladidi tace a a Hajiya, adinga Bata abinta, wannan ma abinda yasa na karba nayiwa
mamanta alwaqari ne zan Kai mata kudin aikin yarta na farko
(Shalele ta kalleta, jin wannan qarya, aranta tace a a zaki riqe kudin ki de)
Momy tace to shknn za'a dinga Bata insha Allah, Ladidi tayi sallama tatafi
Momy ta kwalawa baba Hanne kira, dasauri tazo, tace Hajiya gani
Momy tace ga yarinya nan aje atufatar da ita, itace sabuwar me aikin dazata dinga
gyarawa Haneef part dinsa
Adaure ayi Sharhi Dan Allah 🙏🏻 dafatan wannan shafi ya muku dadi
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
19&20
Haka kawai Taji matar ta kwanta mata Arai, Daga gani   batada matsala, Murmushi tayi
mata tace Sunana SHALELAN BABA
Shiru tayi, lokaci daya jikinta yayi sanyi, baba Hanne tace menene sunanki na
gaskiya?
Zamanta tagyara tace yawwa kawai zaki share masa ko'ina ne, saiki goge, aikin Iya
mopping Ko?
Yawwa toshi dakike ganinsa bayasan qazanta, yanaso kullum yaga waje tsaf, zaki
share ko'ina ki goge, ki wanke masa toilet, ki gyara duk wasu abubuwa da kikaga
basu yiba, kiyi Ahankali dashi, Bai cika magana ba, Amma masifaffe ne, qannansa ma
Bai barsuba, ni kadai yake ragawa a gidan nan Bayan iyayen sa, Shima Dan yaga na
manyanta ne, Haneef bayason qazanta, karkiyi mamaki idan nace Miki sau biyar Ana
kawo masa masu aiki yana korarsu
Baba Hanne takama hannun Shalele tace ta farko saboda tayi shara batayi mopping ba,
tayi tunanin bazai ganeba, shikuma yagane, hakanne yasa yace tanada ha'inci
yakoreta
Na uku sai aka kawo namiji, shikuma satinsa daya yace bazai Iyaba, yagaji da wannan
aikin inde baso ake ya mutu ba🤣🤣
Ta hudu Kuma shishshige masa take, yana shareta, Koda yaushe yana nuna mata Baisan
ta nayi ba, ita Kuma taqara shige masa, Daga qarshe sai tsintar kayanta tayi abakin
gate
Ta biyar Kuma, sata take masa, idan yayi ajiya sai yaga babu, Daga karshe yakama
ta, Saida ya nada mata shegen duka sannan ya koreta
Tun daga lokacin yace qannansa su dinga yimasa aikin, sukuma karatu yasa sun
sangarce basu Iya komai ba
To yanzu de kece ta shida, shiyasa nace Miki kiyi Ahankali, Amma ni ganin farko
Dana Miki naji kin kwanta min, nayaba da hankalinki
Ina Miki fatan alkhairi
Ajiyar zuciya Shalele tayi tace, to amma baba da wannan canje canjen meyasa ba
zaiyi Aure ba yahuta?
Yace babu wadda yake so, Amma duk wannan halin nasa na masifa da miskilanci yanada
temako, zaiyi wahala yaga kana cikin halin buqata yarabu dakai
To Allah yasawaqe
Baba Hanne tace amin, Bari nakawo Miki abinci kici kihuta Zuwa goben
********
Gidan Alhaji bukar shazali Kenan, babban gidane Mai dauke da part biyu dakuma Dan
qarami guda daya, babban shine na Alhaji da yaransa, madedecin shine na Haneef, sai
Kuma Dan qaramin na ma'aikata maza
Daga can Baya wajan part din Haneef akwai Swimming pool me shegen kyau, Saikuma
gidan gaba daya dayasha adon fulawa ja da green
Bangaren Alhaji da Hajiya, anan yaransu mata suke, sai dakin baba Hanne inda akace
ta dauki Shalele su tafi tare
Alhaji bukar yanada yara bakwai, babbar yarsa itace anty jiddah, sai Haneef, sai
Fadila, sai iklas, sannan twins mata, Safah da Samah, sai Dan qaramin su huzaifa
Anty jiddah tana zaune a Abuja, da yaranta biyu mace da namiji, duk sunkai sa'annin
Shalele, sai anty Fadila danta daya namiji, sai iklas tana goyan yarta mace,
Dukansu Suna nan Abuja a zaune da mazajen su, yanzu gidan yarage Daga Haneef sai
Yan biyu da huzaifa
Rayuwar su Suna gudanar da ita cikin jin dadi, matsalar su daya masifar Haneef,
yacika fada dayawa
Shekarunsa 33 miskili ne na gaske, idan ya harde awaje yana bada order kaika rantse
Dan wani Sarkin ne, bayasan raini kokadan, dogo ne ba gajere ba, idanunsa a lumshe
suke always, saikayi tunanin bacci yake idan yana zaune Yarufe idon, nan kuwa Sarai
yana Kallan ka, ahankali yake magana, yamafi wata macen magana cikin sanyi, idan ku
biyu ne awajan saika nutsu sannan zakaji maganar sa, idan kanaso kaji yana magana
sosai da Daria , to da momy ne sai daddy, Saikuma abokinsa Ajmal,anan Kam zakaga
Daria harda dimple sai sun futo, rashin son raini yasa bayama kula qannan nasa
Wannan Kenan
*******
Washe gari da asuba Suna idar da sallah Shalele tafara karatun alqur'ani dawani
data gani a dakin
Baba Hanne tanajin ta, Saida gari yayi haske suka gaisa, baba Hanne tace ashe kema
kin Iya karatun yarinya
A a kede Tunda kin Iya zaki dinga Ko yamin, da jikata ce take koyamin Kuma tayi
Aure, Amma yanzu Tunda gaki Kinga aina huta
To baba, yanzu yaushe zaki rakani wajan aikin nawa? Ba yanzu zamu jeba?
Ke kuwa inake Ina tafiya part din Haneef yanzu? Ai Yanzu be tashi ba yana kwance,
aike yata aikin ki me lasisi ne, Kisha baccinki da safe, saiya shirya yatafi office
zakije kiyi masa gyaran, Kinga baya nan kema zakifi jin dadin aikinki, ga kayan
sakawa nan, su zaki dinga amfani dasu, wannan na jikin naki sun tsufa
Kiyi zamanki yata, aikin gidannan yawa gareshi, kada na gajiyar dake
Shalele tayi Murmushi, kada kidamu baba, muje wallahi Nima nadinga koya
********
Daddy ne yadawo Daga masallacin gidan, da carbi ahannunsa, dama haka yake qa'ida
idan yatafi sallar asuba sai gari yayi haske yake dawowa gida, direct part din
Haneef yanufa
Yatura kofar falon yashiga,
Falon nasa yanada girma sosai, Daga gefe daya kayan motsa jiki ne masu yawa, wajan
ya nufa Aikuwa yaganshi akwance da gashi sai wando three quarter, da baqar singlet,
yana 'Daga wani uban qarfe muscle 💪🏻 dinsa sai motsawa suke, gaba daya jiki a murde
qirar kakkarfan namiji, sai gumi yake hadawa
Daddy yace wato Kai bakada aiki sai Daga qarfe, da yamma gudu da safe Daga karfe
Ajiye karfen yayi agefe, yadauki handkerchief ya goge face nashi, yace morning
daddy
Yadauki goran ruwa faro me sanyi agefensa yakafa Kai Saida ya shanye sannan ya
wullar ta awajan yayi cikin dakinsa
Acan part din su Hajiya kuwa, su baba Hanne Suna kitchen Saida suka hada komai
itada Shalele, duk abinda Bata ganeba tambayar baba Hanne take, tana Bata amsa
Baba Hanne tazuba musu nasu tabawa Shalele tace gashi yata, kikai mana daki kizauna
kici, Nima zan Kai musu nasu dining
********
Dukansu Suna zaune Suna break babu me magana acikinsu, yau Kam qananun kaya   yasaka,
wandon jeans da riga dark green saiya Dora wata rigar fara asama me hade da   hula,
kayansa Kenan dama, Daga suit sai kananun kaya, sai yar saman dayake dorawa   me hade
da hula, Kala Kala, duk kayan daya saka to yar saman dazai Dora itama kalar   ta
daban
Da wahala ka ganshi da manyan kaya
Daddy ne yamiqe yayi daki ya kalleshi yace kai inka gama Ina jiranku a daki   kaida
Hajiya, yayi dakinsa
Shima Haneef Bai zauna ba yatashi yabishi, momy ma haka, aka bar yaran awajan su
kadai, adan qaramin falon daddy suka zauna Haneef yazauna aqasa, kansa aqasa yanaso
yaji dalilin Kiran
Bai dago kansaba yace am.. Daddy ni Har yanzu... Dama.. Ban sa..
Dakata Haneef   what's wrong with you? Haneef kanada lafiya kuwa? Kokuma insa doctor
ya dubaka?
Afili saiya girgiza kansa yace daddy I am a good health, babu wadda nakeso ne
To Tunda hakane kaje gidan abokina Alhaji Sadiq akwai babbar yarsa tana nan, kaje
ka ganta Hairat nasan insha Allah zatama
Haba Alhaji, wacce irin magana ce wannan? Kasan fa Qawata Hajiya Amina ta Dade tana
qulafucin muhada zuria da ita, kawai de Dan yasamu mun Daga masa kafa ne, Amma idan
akai haka ai Inaga Kamar ba'a yi adalci ba
Cikin rashin damuwa daddy yace to shknn, kawai ya Aure su su biyun, ya kalli Haneef
tokai idan kasamu lokaci saikaje ka gansu
Kallansu yasakeyi da mutuqar mamaki yace momy daddy Ina zan Kai mata biyu? Daddy
kubar dayar de, Amma Yaya zanyi da mata Har biyu? Gaskiya daddy akwai damuwa zasu
kasheni wallahi, idan ma basu kasheni ba zan mutu, wallahi momy mutuwa zanyi
Momy ta kalleshi, bazaka mutu ba Haneef, zaku zauna lafiya tashi kaje
Tashi yayi yafuto ransa abace su Samah Suna dining sai ganinsa sukai yafuto ransa
abace, duk suka bishi da kallo
Shikuwa yana fita saminu ya bude masa mota dasauri yashiga suka wuce office
Murmushi daddy yayi ya kalli momy, tace Alhaji yanaga kana Daria?
To ai al'amarin Haneef ne abin nasa akwai abin dariyar, Wai zai mutu, ni nasan
yarona jarumi ne, Ko mata hudu na aura masa zai iya dasu
*******
Suna tafiya ma sai tsaki yakeyi shi kadai, saminu de yayi Shiru babu damar tambaya,
Dan yau uban gidan nasa akusa yake, suna Qarasawa company ma bejira yabude masa
mota ba, dakansa yabude yafice dasauri cikin bacin rai saminu yadauko jakarsa
yabishi da ita
Bedade da zama ba saminu yashigo masa da jakarsa, yace yallabai gashi, kayi
hakuri... Daga masa hannu yayi alamar Baisan jin komai Daga gareshi, cikin sauri
saminu yafice Daga office din
Wayarsa yadauko yakira Ajmal yace oga, yaufa akwai matsala, Dan nakawo yallabai
office yanzu Amma da alama akwai abinda yake damunsa, dasauri Ajmal yace ok gani
nan Zuwa saminu, godia nake
Ko 30 minutes ba'a yiba Ajmal Yazo office din nasa, ganinsa yayi ya Dora kansa akan
tebur din Gabansa, ahankali yatako Yazo kansa yatsaya, abokina meyake damunka?
Tagumi yayi 😱😱idan mutum daya cema aida sauqi, Har mutum biyu, Ajmal Ina nake da
time din dazan Bawa mata biyu? Yau Ina can gobe Ina can, dayar ma dayaya, dole sai
tayi hakurin zama Dani kokuma tabini mutafi tare
To su waye?
Yar abokin daddy, da yar qawar momy, sunce in samu lokaci inje nagansu, Ajmal
banasan auren nan wallahi, nafison na auri mace Babba, wadda tahada komai danakeso
ajikin mace...
Ajmal ya karbe zancen da fadin, yar boko, wadda zaka zaga, da ita ko'ina aduniya
bakaji kunya ba, wadda ta goge da ilmi, idan aiki yayima yawa ta karba tayi ma, me
manyan Boobs.... Haneef Bafa ma'aikaciya zaka dauka ba, mata zaka aura wadda zata
haihu dakai ta kulama da yaranka, aganina kawai ka amince yafi ace koda yaushe kana
dirkawa kanka tablet, Koda yaushe kana jin feeling yakama ta ace kayi auren
Shawarata biyuce Haneef, idan mukaje ka gansu ka zabi daya kawai, kabawa su momy
hakuri kace musu zaka auri daya,fatanmu ta kasance yar boko ce Kamar Yanda kake
buqata, shawara ta biyu kama cire maganar Cewa sai manyan mata ne suke da manyan
Boobs, Haneef acikin yara ma akwai masu manya, kawai kayi fatan Allah yabaka me shi
Tunda kanaso
Dan Allah Ajmal kadena min wannan maganar, tayaya qananan yara zasu samu wannan
abun?
Kaga ni yanzu ba wannan ba, damuwa ta daya yanzu shine duk su biyun narabu dasu,
bazan Iya ma auren suba
Ajmal yadanne dariyar sa, yaga alama shi Haneef mata biyun ne suka tsaye masa Arai
Dan haka yaqara tunzurashi yace may be su momy sunga alama kaidin jarumi ne shiyasa
Becewa Ajmal komai ba yadauki wayoyinsa da brief case dinsa yace nabarka lafiya
Yanda yakejin bacin rai acikin Zuciyar sa, bayajin zai iyayin wani aiki yanzu, Gara
yaje gida yahuta
*********
Yauwa yata, Dan Allah kingane komai?
Murmushi tayi tace eh nagane baba, insha Allah zan yi duk Yanda kika gwada min
Baba Hanne tace yawwa to zanje nadan huta, saikin zo
Baba Hanne nafita, takalli falon, taganshi tangameme, wajan dayake Jim ta kalla,
ahankali tataka taje wajan, tasa hannu zata Daga karfen dayake dagawa Taji nauyi,
tace Wai, wannan Ina zan Iya, barin wajan tayi, ta dauki tsintsiya tafara share
falon, babu wani dattin kirki, sai tarkacen kwalayen lemuka, da goran dayasha ruwa
dazu da safe, duk ta tattara tazubar
Takalli kujerun falon afili tace wannan tsarin su beyiba, hijabin jikinta ta cire
taci damara dashi, duk ta juya kujerun falon, tasake musu wani design din
Sannan tayi mopping, tashige qaramin kitchen dinsa, tagyara shi tsaf, ta goge
ko'ina Har jikin lokokin Bata barsu ba, fridge din dayake ciki ta bude, babu lemuka
aciki sai ruwa, cikin frizar din ta bude taga lemo na kwali qwaya daya
Dube dube tafara a kitchen din harta ga lemuka da ruwa agefe katan katan, Aikuwa ta
fasa takwasa tazuba wasu acikin fridge din sannan tarufe ta nufi dakinsa
Kitchen din ta kalla da falon, tayi Ajiyar zuciya afili tace Karo na farko, nagode
inna Marka, domin kuwa da baki horar Dani akan aiki ba, inajin Dana kafa tarihi a
gidan nan, nazo ata shida, to kuwa zan bar tarihin Cewa ma'aikaciya ta shida
ankoreta Washe gari😃😂
Dakin tashige duk furnitures din dakin nasa farare ne, gadon dakin ta kallah
taganshi wani Kala me round ga radio a manne Agefen gadon kusa da bedside drawer,
agaban gadon an shinfida wani kafet me mutuqar kyau
Da table irin jikin gadon Dan qarami akan kafet din shikuma andora masa computer
akai qirar apple
Saida tagama Kalle kallenta tace tab, wannan ai dole kace ayima gyara, kaya duk
farare ba baqi😃
Dressing mirror ta kallah, taduba taga turaruka birjik babu wanda tasani , tace um,
wannan Ko waye duk Yanda akai Dan qarya ne 🤣🤣 inba hakaba wannan uban turare
saikace wani maceToilet din tashige, taganshi kalau, Amma haka tazage tasake wanke
shi tas, mirror din dake jikin bangon toilet din ta kalla, taga nanma turaruka ne,
karanta wa tayi taga na wanka ne sai Kuma Air freshener, cikin murna tace yawwa, ta
dauko guda daya Mai Qamshi, tadawo falon tayi ta fesawa saida Taji Qamshi yabaza
ko'ina sannan Takoma toilet din, ta goge jikin mirror din, nanma tasaka wani
turaren Mai wani qamshin daban, dakin tadawo ta share, duk kayansa aqasa riga a
gado wando aqasa, haka ta dauke su, tayi mopping ta kalli gadon, taga Bedsheet din
ansaka ja, girgiza kanta tayi afili tace inaaa wannan Beyi ba
Labulen dakin ta kalla taganshi light green, Aikuwa Kamar Yanda baba Hanne ta nuna
mata komai, haka ta bude wardrobe din tadauki wani bedsheet din green and white,
tasaka a gadon, ta cire dayan
Ita kanta gadon Saida ya birgeta, Murmushi tayi tare Ajiyar zuciya tace yawwa
nagama aikina nayau alhamdulillah, saura turare, tasake shigewa toilet domin dauko
wani kalar Air freshener din, ta dauko ta fesa, Shima dakin yabada nasa kalar
qamshin daban
Tunda yashigo gidan Ko part dinsu momy Bai kallah ba ya wuce part dinsa, Dan yau
Kam fishi yake da kowa a gidan, Tunda akace za'a masa auren da bayaso
Direct part dinsa yanufa
Tun Afalo wani irin Qamshi ya ziyarceshi, cikin ransa yace masha Allah Yan biyu sun
fara hankali 😌
Dama ai yasan yaran zasu Iya aiki, kawai de Dan momy Bata sakasu ne, kujerun falon
ya kallah, duk da yana cikin bacin rai Saida yayi mamaki, yaga an sake musu tsari,
yace toooo 🤗
Kace yau aikin nayi ne, dasauri yashige dakinsa, Adede lokacin ita Kuma ta futo
Daga toilet din, Dama ta shiga ne ta maida Turaren datayi amfani dashi
Karaf akai sa'ah idanunsu yahadu, lokaci daya faduwar gaba ta ziyarcesu
Amnah El
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
Lokaci daya wani irin farin ciki da batasan dalilin sa ba ya ziyarceta, yau gata ga
mutumin daya temaketa ita da babanta a lokacin da suke buqatar temako
Inama ace tanada number uncle Bilal, data fadawa anty Sady ga rayuwar ta taganshi a
araha yauma😂
Saitin inda Zuciyar shi take bugawa da karfi yasaka hannu, why yakejin faduwar gaba
me tsanani haka?
Ya kalli yarinyar datake Gabansa ta tsaya masa qiqam tanata fara'ah
Cikin bacin rai da tsawa yazaro mata ido yace ke😳, mekike yi adakina!!!?
Runtse idonta tayi cike da tsoro, ita Kam Kuma shikkenan ta shiga ukunta yau dama
ance mata masifaffe ne
Zuba mata ido yayi, ganin yanda ta runtse ido cikin tsananin tsoro
Wata tsawar yasake daka mata yace get out of my room, da sauri taraba ta gefensa ta
fice Garin gudu ta yarda hijab dinta aqasan dakin, batabi ta kansa ba tafice Daga
falon ma da gudu baki daya
Shi kadai yake huci cikin bacin rai, meyasa ake barin Ko wanne yara Suna shigo masa
part ne? Shikkenan yanzu haka taga wandon sa aqasan dakin 😳
Wajan daya yar wandon ya kallah, yaga wayam babu shi
Saiga Haneef jagwab yazauna asaman gado, shikkenan Kuma yarinyar Nan tagama ganin
komaiPP
Innalillah...
Idonsa ne yafada kan gadon, anan yaga gadon ma ansake masa sabon bedsheet, Saikuma
yafara Kalle Kalle a dakin yana ganin yanda kamarsa ta canja
Kwantawa yayi a gadon yanaji Zuciyar sa na bugawa da sauri da sauri, what is wrong
with me ne? Na Dade rabon danaji wannan abin, Kuma sai yau zai dawo? Bayasan
faduwar gaban nan wallahi😔 🤣🤣
********
Duk da atsorace ta futo Daga part din nasa, haka kawai ta tsinci kanta cikin farin
ciki, still gaban ta Bai bar faduwa ba
Turus tayi ganin momy dasu Samah a zaune a falon, lokaci daya ta nutsu, ta tsugunna
Har qasa tace Hajiya Ina kwana? Kallanta sosai momy tayi, ita sai yau ma ta qarewa
yarinyar kallo, lokaci daya tagano tsananin Kamar datake da Hajiya Hafsat
To ai Kuma wannan ba haneefan baba bace, babu ma abinda zai kawo Haneefa gidan
aiki, Ko gidan sarki ne tasan baba bazai Barta ba (tofa wata sabuwa 😃
                                                                    , ashe de
baba kowa yasan hali)
Itama Shalele cikin jin Haushin dariyar da wadannan yaran suka mata tace eh haka
Sunana
Ahankali ta tashi tayi cikin dakinsu tarufe kofar, baba Hanne tana kwance tana
bacci, saita zauna Agefen gadon tafada duniyar tunani
Menene yasa ne take wannan farin cikin? Ita kanta takasa Bawa kanta amsa, ashe dama
shine wanda zata yiwa aikin? Aikuwa inde aikin wannan kyakkyawan ne kullum saitaje
tayi Kodan ta ganshi, shida anty Sady tace ba'a ganinsa saide a video Ko jarida?
Wallahi saide Nima ya koreni Dan kullum sainaje na ganshi (nikwa nace ai kuwa
                               😃
wataran zaki ci duka awajanx sa)
********
Futowa yayi daga dakin zai dauko ruwa Mai sanyi yasha, yayi hanyar kitchen nanma
yaga irin gyaran dayasha, yabude fridge din yaganshi ansaka komai da komai, haka
yazuba wa lemuka da ruwan daya gani aciki ido Kamar yana tsoron dauka, Daga qarshe
yadauki ruwa yayi dakinsa
Saida yasha ruwan yadanji ransa yayi masa sanyi, abinda be sababa yau yafara wato
chtting, duk Dan yadena tunani, Amma tsabar massage din dasuke shigo masa lokaci
daya saboda an ganshi online ne yasa dasauri nanma yasauka, ya runtse ido duk
bayajin dadin Garin
Baba Hanne ta tashi Daga bacci taga Shalele na zaune agefe, hamma tayi tace yar nan
bakya tashina in Dora abincin rana?
Murmushi tayi, to ai Naga bakiyi bacci ba da safe shiyasa
Yar nan inani Ina bacci, Bari inje kitchen yanzu, itama dasauri ta tashi tabi
bayanta suka shiga kitchen din, suna tsaka da aiki Samah tashigo kitchen din tana
waya, Saida tagama sannan ta kalli baba Hanne tace am baba Hanne yau inason
farfesu, adafamin shi da wuri please
Baba Hanne tace Samah, insha Allah za'a Miki, Shalele ta kalleta, itama ta kalli
Shalelen ta sakar mata harara hade da tsaki tafice Daga kitchen din
Tana fita Shalele tace Amma baba Yaya ake kike Iya gane wadannan? Ba Yan biyu bane?
Murmushi tayi, abinda yasa nake ganesu dayane yata, Kuma sudin yanbiyu ne Kamar
Yanda kika fada, Samah itace babba, Amma batada kirki, tacika masifa dayawa Kamar
yayansu, itace Hassana, Ko ina ansan Hassana nada hakuri Hussaina Kuma fada, to
banda nan gidan, ita babbar itace me fada, ita Kuma qaramar Safah Kenan tacika
tsokana, haka zatayi ta tsokanarta sunayi,duk Ina gidannan aka haifesu, ita Samah
tana cemin baba Hanne, ita Kuma Safah kawai baba take Cewa
Tota hakanne nake ganesu, inde kinji ance baba kawai, to qaramar ce itace Bata
fadin Sunana , idan Kuma baba Hanne akace to babbar ce
Ajiyar zuciya tayi, ai baba tun dazu da safe Naga daya acikinsu tanamin wani irin
kallo, dazu ma hajiya tana tambaya ta Sunana Wai saboda nace Shalelen baba shine
sukamin Daria
Zasuyi, wallahi yata inde wadannan yaran ne zasuyi yafi hakama, musanman ma Samah
Shiyasa dan'uwan nasu baya raga musu, Shima kansa baya banbance su, saboda Shiba
shiga sabgarsu yake ba
********
Da yamma yasaka gajeren wando fari qal dashi, da singlet fara, yafara motsa jikinsa
Amma na gudu, yana kan injinsa na motsa jiki kawai yana gudu
Da sallama yashigo part din nasa, yayi wankan manyan kaya, kallo daya yayi masa
yadauke Kai yaci gaba da abinda yake
To inka gama nikam Ina Daga ciki, yayi hanyar dakinsa, Yazo wajan da kujerun sa
suke, yatsaya yayi turus, yadaga murya yace yau Kuma sakewa falon Naka tsari kayi?
Haneef Bece masa komai ba, ya share shi
Ajmal dinma yasan Tunda yaji Shiru to bazai samu amsa ba, Dan haka yayi hanyar
dakinsa, yaci Karo da hijabi a yashe aqasa, dauka yayi yadaga harda warashi da kyau
danya gani sosai, ahankali yace wallahi hijabi ne 🤣
Da hijabin ahannunsa yanufo wajan Haneef yace abokina Ina kasamu hijabi Kuma? Kona
yanbiyu ne suka manta shi?
Who?
Dena motsa jikin yayi yataho yanufi kujerun falon yazauna yana maida numfashi yace,
sabuwar me aiki
Daria Ajmal yayi, yanaso yaji Yaya akai me aiki tabar hijabi a dakinsa Dan haka
yace ikon Allah ita Kuma da cutar mantuwa tazo Kenan
Yasake Cewa Allah sarki inajin mantawa tayi, ta barshi (Dan jaraba 🤣🤣)
Shi Haneef duk be gane abokin nasa zurashi yake ba, Zuciyar sa daya yace "ta
tsoratane kawai"
Ido Ajmal ya zaro 😳yace tsoro? Tome tagani Taji tsoro, Kai masu aiki ma wani
lokacin da shirme suke 🤣🤣
Wallahi kuwa, in banda shirme meyasa zata dauki wando na a daki Har tasa hannunta
tadauka, shiyasa nayi mata tsawa nace tafice, shine ta yarda hijabin Garin gudu
Wannan Karon Kam Daria sosai Ajmal yayi, Haneef ya kalleshi, why kake Daria? Wannan
ba abin Daria bane
A a ni bance Ina nufin komai ba, gani nayi Dan kawai yarinya tadauki wando ta sauya
masa wajan Ajiya duk kabi kadamu kanka
Nadamu kaina fa kace Ajmal, yarinya tasa hannu tadauki wando na, wandon namiji,
baligi
To Menene aciki danta dauke? Kaide kafadamin gaskiya Ko akwai abinda tagani Bayan
wandon, kawai katsaya Kanata wani kwane kwane
Wannan Karon shida kansa Saida ya ware idonsa😳, Ajmal mekake nufi? Ai babu macen
da za'a yi taga komai, ba'a haifeta ba
Ni wannan cika bakin Naka batamin rai yake Haneef, lokacin dazaka nuna mata ma waya
sani, lokacin kashiga Daga ciki, Amma yanzu a tuzurinka kake, ni kaga ba wannan ba,
tashi karakani,zanje zance wajan Sajida, my Sajeey
Mutsws yasaki tsaki, dawa zakaje wajan Zancen? Dani? Inrasa inda zan rakaka zance
sai wajan wannan tatsitsiyar yarinyar, Kuma saita ganni gidaiyya Dani na rako
abokina zance wajanta, Daga nan tasamu kofar rainani
A a Ajmal, Dade wajan wata ne zani, Amma banda 'yata, yarinyar yayata, anty jiddah
Zaman hularsa ya gyara yace Toni kaga tafiya ta, zanje wajan tatsitsiya ta 😃, Kai
saika zauna anan kana neman masu bigi
********
Washe gari ma da safe, tare suka shiga kitchen itada baba Hanne
Saida suka gama suka shiga dakinsu, wanka tayi tashirya ta zauna Allah Allah take
taje part dinsa kawai danta ganshi, Amma Kuma baba Hanne tace saiya fita ake
gyarawa, Kamar Yanda tayi jiya,baba Hanne ta kalleta tace Kekam yar nan bakya
kwalliya ne? Tunda kikazo banga kinsa Ko kwalli a idon ki ba, babu ruwanki da irin
kwalliyar dasu Samah sukeyi
Murmushi tayi baba yanzu ni danazo aiki wacce irin kwalliya zanyi? Ai Gara nayi
abinda yakawo ni
Toke yanzu Yarinya aigara kiyi kwalliya, kokya samu miji, kiyi auren ki, Kinga
kinhuta da wannan aikin, Amma yanzu hankalin iyayenki ma bazai kwanta ba, tun kina
qaramar ki Gara kisamu Miji kiyi auren ki
Baba Kenan, ai banda iyaye, ni marainiya ce, mamata tarasu tun Ina qarama, babana
yarasu baima Dade da rasuwa ba, yanzu kishiyar mamata ce takawo ni aiki, abinda
yasa nasaka araina Cewa zanyi aiki tsakani da Allah, saboda in samu kudi ne inyi
karatu in zama lauya inje inkamata
Baba tayi daria, yarinya duk Bawa mumini da yafiya aka sanshi, gaskiya na tausaya
Miki, tun kina qaramar ki kina fuskantar matsalar rayuwa, Amma komai me wucewa ne,
kiyi hakuri
Tagaji dajin wannan hakuri hakurin inde Marka ce babu maganar hakuri atsakaninsu,
Dan bataji abinda ta mata bane, danhaka takatse maganar da Cewa baba yaushe ne yake
fita aiki ne? Karfe nawa?
Haka ta zauna tana jiran lokaci, ajima ta kalli agogo, asake jimawa ta kalli agogo
Har karfe goma tayi, ta miqe tace baba natafi, to saikin dawo yata
Samah tace wannan yarinyar kanta yana rawa, Kuma zan sauke mata shine
Safah tace Kekuwa Samah me yayi Miki zafi da ita? In fact ma ba matsayin ku dayaba,
nikuma wallahi Kinga Tunda naganta naji tana birgeni, babu ruwanta, komai cikin
nutsuwa
Ke ai kowama birgeki yake, ai saikije kiyi tayi, ta tashi tayi dakinsu, Safah
tabita da kallo
********
Yauma Ahankali ta shiga falon, tataka tayi hanyar kitchen, Saida ta qare masa kallo
taga babu abinda akai aciki, dozbin din kitchen din ta kalla, taga sai goran ruwa
dayawa aciki, sama sama ta Kade kitchen din ta goge shi, tafitar da sharar waje
Sannan tasake gyara falon, hijabin ta na jiya tagani akan kujera, tace oww ashe ya
dauke min, awajan ta barshi tashige dakin, gadon tafara lelayewa, sannan ta share
tayi mopping, a tsakiyar dakin ta tsaya tana dube dube
Daga wajan labulen dakin taga wani Abu Kamar photo, tana dubawa kuwa taga
photunansa ne, Ko meyasa ya juya su? Aikuwa saide yayi hakuri saina futo dasu, guda
uku ne, manya manya, daya yasa manyan kaya, daya da suit daya da qananun kaya
Duka photon tasa agaba tana kallo tana zuba Murmushi, tarasa meyasa idan taganshi
take tsintar kanta cikin farin ciki
Daya Bayan daya ta ajiye photunan a inda yadace, Aikuwa Hakan datayi saiya qarawa
dakin kyau
Toilet ta shiga domin wankewa, saitaga kayansa aciki, dasauri taduba taga singlet
ce guda biyu da gajerun wanduna guda biyu, zama tayi tasaka su cikin ruwa ta wanke
su tass😃
Sannan tafara neman inda zata shanya tarasa, to su ba wanki sukeba bare kasamu
igiya a gidan, saide akai wajan wanki kokuma abawa ma'aikata su wanke shi da
machine
Aikuwa ta futo ta shanya su akan fulawoyi, sannan Takoma ta wanke toilet din, yauma
Saida ta fesa turare a ko'ina
Sannan tafice taje inda ta shanya kayan ta zauna, Saida suka bushe sannan ta dauke
tadawo dasu dakin tasaka masa cikin wardrobe
Sai yamma lis yadawo gidan, direct part dinsa yanufa, yanaso ya watsa ruwa yaje
wajan momy
Yana shiga falon ya lumshe idonsa, dama Abu a lumshe 🤣
Kallan falon yayi yaganshi very neat, aranshi yace "yauma tazo Kenan"
Dakin nasa yaqarasa, still wani Qamshin yaji, ya kalli pictures dinsa data ajiye
waje daban daban, dasauri yaqarasa wajan yasa hannu zai dauke Saikuma ya fasa, ya
cire kayansa, yashiga toilet yayi wanka, Saida yagama wankan tsaf yatuna dazufa da
safe yabar qananun kayansa a toilet dinnan, dubawa yayi Bai gansu ba, Allah yasa de
                                          😂
ba yarinyar Nan ce ta sake dauke masa ba ()
Innalillah... 😳wannan yarinyar ita Kuma da salon datazo dashi Kenan?Ina korar
wadda ta nuna tana sona ashe ita wannan me kankat ce?
Jiya Ina fada ta dauke dogon wando, ashe yau Har gajeren wando na zata dauka ta
wanke?
Afili yace Gara nayi maganin yarinyar Nan tun kafin abin nata Kuma yadawo kaina,
tana dauke dogon wando tadawo wanke gajeren wando, to tun kafin tsaurin idon nata
yadawo kan me kayan, Gara nayi maganin abin
Cikin sauri yasaka qananun kaya yafuto Daga part din yayi nasu momy
********
Yakusa Zuwa part din yahangota a zaune awaje, Kamar ance ta waigo sai ganinsa tayi
yana nufo inda take
Lokaci daya tafarajin faduwar gaba
Shima anasa bangaren haka yake, afili yace ai zuciya ki dena bugawa nakusa yin
maganin komai 🤣🤣🤣
Shalele kuwa ganin da gaske ita yake nufowa yasa tayi sauri tashige ciki, momy na
zaune Afalo ita kadai, ta russuna tace Hajiya sannu da hutawa
Dakinsu tashige itada baba Hanne, baba na ganinta tace yawwa yata, gobe zaki fara
biyamin karatun kinji? Nabawa megadi saqo dazu yasiyomin littafin
Inajin ki 'yata
Murmushi Baba tayi, ba'a dauke wa yata, Ko an dauke wuta agari Sunada solar, ai
kinsan solar Ko,?
Agogon dakin ta kallah taga biyar da Rabi na yamma, Tome zaizo yi nan part din
yanzu? Ko abinci zaici? Meyasa nake murna ne danna ganshi?
Ajiyar zuciya tasauke ta dubi baba Hanne tace baba dama akwai tambayar danake so
namiki
Baba tasake Murmushi, gaskiya tanajin dadin Yanda yarinyar Nan take kiranta baba,
tace Inajin ki yata, fadamin tambayar Taki nabaki amsa
Wai baba yanzu misali idan kaji gabanka yana faduwa idan kaga wani mutum menene
Hakan yake nufi?
Kuma idan ka ganshi saikaji Kanata murna Kai kadai, menene Hakan baba?
Gabanta yabata Dam lokaci daya, zaro ido tayi tace baba so Kuma? 😳😳
Qwarai kuwa yata so de dakika sani, me girma ma kuwa, Tunda kince idan kika ganshi
kinajin farin ciki, to wannan so ne
Dade ace Iya faduwar gaba kikeji kawai Toda sainace Miki kina da wata alaqa ne me
girma tare da wannan mutumin
Yata Bari inje kitchen ingano girkin dare, Ina zuwa, baba ta tashi tafice
Shalele na ganin fitar baba tafashe da kuka, ta shiga uku, 🙆🏻 Ina ita Ina son
mutumin dayafi karfin ta? Yau inda ace wata alaqar ce tsakanin su ma Toda sauqi
akan ace sone
Zuciya ta meyasa zaki kamu dason wanda Bai sanki ba? Yafi ki komai da komai? Kudi,
kyau, aji, ilmi,? Innalillahi... Taqara rushewa da kuka, tasan Ko giyar wake Tasha
wannan mutumin bazai taba sonta ba
********
Yana shigowa falon yaga momy a zaune, kusa da ita ya zauna, yace momy gaskiya akwai
damuwa
Akan wannan yarinyar me yin aikin nan da kuka tura part Dina
Shiru yayi shi kadai, yanzu me zaice mata? Gajerun Wandunan sa take dauka ta
wanke?🤣🤣🤣 Kokuma cemata zaiyi Gabansa ne yake faduwa idan yaganta?
Shin idan aka sallameta hankalinsa zai kwanta ne Ko Kuma akasin haka?
✍🏻
Amnah El
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
23&24
Salamu Alaikum
Hararar sa tayi, sannan tace babu ruwana da Yaron nan momy, bayasan Zuwa gidana
Wai meyi masa gyaran bangaren sa ne bayaso, shine Yazo yake fadamin
Yanzu momy shikkenan shi baida aiki sai korar yara masu aiki? A Iya sanina ankawo
wa Yaron nan masu aiki sunkai hudu
Momy ma'aikata Har shida, Kuma kuka zuba masa ido yana abinda yaga dama, gaba daya
kun gama shagwaba shi
Tashi yayi yace Bari inje masallaci momy, anty saina dawo
yaga alama anty jiddah bazata dena cemasa yaro ba idan ba fita yayi ba, yanzu shi
Har yanzu awajan ta a yaro yake? Shi yana can yana Cewa yazama babba baligi Amma
ita tana qara maidashi baya 🤣
Anty jiddah Tace toka dawo da wuri Nima Ina idar da sallah zan tafi
Yana fita, ta kalli momy tace yanzu momy Ina yarinyar zata idan tabar nan?
Momy tace
Toki dauke ta a sauka lafiya
Wallahi Alhaji yace yaje yaga yar abokinsa, Nima Kuma nace yaje yaga yar Qawata
Momy mata Har biyu? 😳Yaya zaiyi dasu? Momy ai saisu kashe shi
Waike jiddah bakida aiki da anyi wa Haneef magana saikice zai mutu zai mutu, to
zabin nawa zai Bari kona ubanku?
Mayafinta tacire ta miqe tsaye tana cire agogon hannunta, momy, yanzu nawa   yake da
zaku Dora masa nauyi tun yanzu? Yaro tun Bai tafasa ba zai qone
Toke jiddah dakike wannan haqilon ke Hakan ba shagwaba shi kike ba?
Saida tayi sallah, sannan taje gaban mirror din momy tasake gyara fuskar ta, sai
tayi Das da ita Kamar ba itace yayar wannan qaton ba
Falon tadawo tadauki handbag dinta tace to momy zan tafi, Ina yarinyar take?
Su Samah ne suka futo Daga daki da sauri suka rungume ta, tace Yan biyu ai saiku
kadani
Ina kukaje kuka bar min momy nah Afalo ita kadai?
Anty muna assignment nefa
Toku je kukiramin me aikin Haneef zamu tafi, kasancewar sun sanshi da sauye sauyen
me aikin, shiyasa basu damu ba, Safah ce ta tafi taje dakin baba Hanne, a lokacin
Shalele na zaune asallaya, baba Hanne tana gefe akwance
Tayi sallama ta dubi Shalele, Wai kizo inji momy zakibi anty jiddah gidan ta
Gabanta ne yafadi, Ina za'a kaita Kuma? Shikkenan yanzu tadena ganinsa?
Momy tace zata koma canne, tana fadar haka ta juya tafice
Baba Hanne tace Kash Amma gaskiya banji dadi ba, yanzu yata Yaya maganar karatun
mu?
Baba kiyi hakuri, wataran inda rabo zanyi Miki, ni kadaina nagaji da wannan yawace
yawacen
Ledar da kayanta suke ciki tadauka ta futo da hijabin datayi sallah ajikin ta,
kyakykyawar fuskar ta tayi kyau acikin hijabin nata me hula, tayi fayau babu wani
tarkace a fuskarta Baba Hanne tarakota Har falo, suka gaisa da anty jiddah Tace
baba zan dauke Miki me tayaki aiki Ko,kiyi hakuri insha Allah zata dinga Zuwa Miki
lokaci Zuwa lokaci
Ta kalli Shalele taga yarinya batayi kama da masu aiki ba, tace zomuje
Sallama Shalele tayi musu sannan suka fice Zuwa harabar gidan
Inda anty jiddah tayi parking suka je, anty jiddah ta bude mata kofar ahankali ta
shiga, sannan itama ta shiga, tadauki wayarta ta kirashi
Tace to Kai ango zamu wuce
Gabanta yafadi, waye ango? Kafin tagama tunanin nata ta hangoshi, dasauri   kawar da
idonta tana Kallan wani wajan daban
Anty jiddah ta kalleshi, cikin tausayawa tace ashe su daddy sunyi maka mata
Duk maganar dasuke tana jinsu wannan Karon Kam Bata Iya tsaida hawayen idon taba,
lokaci daya suka zubomata masu dumi, tasa hannu ta share, anty jiddah Bata gantaba,
duk abinda tayi akan idonsa
Anty jiddah Tace to yanzu yaushe suka tsara yin bikin? Kai wanne lokaci kakega yayi
ma?
Any time anty, zanje shan ice cream yanzu, I will call you back ok?
Yafadi hakanne saboda yanaso yabar wajan, Baisan kukan mace Ko kadan
Tace To shikkenan qanina sai munyi waya, taja motar sukabar gidan, dazasu fita Daga
get din gidan Shalele ta rushe da kuka, yanzu shikkenan Hakan fa yana nufin ta
rasashi Kenan? Ya Allah gani gareka, dole ta cire shi Daga ranta, Allah ka Temakeni
nadena tunanin wannan mutumin, insha Allah Daga yau zansa araina Cewa banma sanshi
ba, dole zan cire shi Daga Raina
Anty da batasan kukan da biyu ba, tayi Murmushi tace kiyi hakuri, insha Allah zan
dawo dake wataran inde bakyajin dadin zaman gidana kinji? Zan dawo dake wajan baba
Daga Kai tayi, ta share hawayen ta, haka anty jiddah taci gaba da driving cikin
qwarewa, Har sukazo gidan, tanayin parking suka futo, anty jiddah takama hannun ta
suka shiga ciki
Mutum biyu ne a zaune a falon mace da namiji Suna kallo,namijin zaikai 25, sai
Sajida me 16 years, sa'ar Shalele
Anty jiddah Tace Sajida sannunku da gida, me kika dafa mana ne, wallahi yunwa
nakeji
Batace komai ba tace mama baquwa mukai ne? Anty jiddah Tace eh a gidan momy nadauko
ta, kinsamu qawa, ta kalli Shalele tace wannan shine babban Dana ayaz, sai Sajida,
da na dauko ki ne kidinga temaka mata da aiki, Amma Tunda naganki naji Ina sonki,
naji Kamar yar'uwa ta ce ke, ki daukeni amatsayin uwa Kamar Yanda Sajida zatayi,
kiyi duk abinda kikeso, nan Kamar gidan ku ne, sannan ta kalli yaran nata tace, ga
yar'uwa nakawo muku, shikkenan Sajida kin huta da fada keda ayaz, kinsamu qawa
kema,
Ayaz yace mama Yaya sunan ta? Anty jiddah ta kalli Shalele tace, kifada musu
sunanki
Kallansu Sajida tayi tace Sunana Haneefa, Amma Shalelen baba ake cemin
Dasauri anty jiddah Tace Aikuwa akwai wata yar'uwar su momy akuje, namanta sunanta,
Amma zan tambayi momy
Anty jiddah tayi Murmushi jin dadin sunan da Shalele ta kirata dashi
Ayaz yace to mama sannun ta da Zuwa, Amma kifada musu banasan raini, Sajida tace
jishi Ko mama saikace me shekara talatin
Nikam kun isheni, Daga dawowata, banasan hayaniya Dan Allah, kuje ciki Sajida, kuyi
sauri kufito muci abinci
Jan Shalele tayi suka shige daki, haka ta dinga janta da fira, tun tana noqewa
harta ware, sai gashi sune harda yin game awayar sajidan
Saida ayaz Yazo yakirasu sannan suka futo falo Dukansu suka fara cin abinci, suna
cin abinci tanata nuna mata Abu awaya, abbansu yashigo, sukayi masa sannu da Zuwa,
yace baquwa mukai ne? Anty jiddah Tace eh doctor, yace to sannu da Zuwa, yashige
dakinsa, ahankali Shalele ta amsa, anty jiddah ta tashi tabi bayansa, Sajida tace
wannan shine abbanmu babban doctor ne
Ayaz yace oh uwar gulma harta fesa, tace eh nafesa din, Murmushi kawai Shalele
tayi, wannan drama tasu saisu
Acan daki anty jiddah Tace doctor nayima laifi nadauko yarinya a gidan momy banyima
bayani ba, Amma kayi hakuri, yace haba jiddah Ko mutum dari kika kawo ai bazance
Miki komai ba
Yace yanzu de matso kiji wata magana, Hararar wasa tayi masa, ta tashi Ahankali
taje ta rungume shi
Washe gari weekend Suna zaune Afalo Suna kallo, Sajida tace mama anjima zamuje da
Haneefa wajan qawayena su ganta
Babu inda zaku, Nima Ina gama Kallan wanna episode din zaku tashi mufita shopping
abbanku yabada kudi ayiwa Haneefa shopping, ta kalli Shalele tace ke Kuma kicire
wannan hijabin, haba tun jiya kina Fama da Abu, dasauri tacire hijabin tun kafin
itama ayi mata fadan 🤣🤣
********
Kai tsaye wajan shopping suka je, Shalele sai Kalle Kalle take, ayaz da Sajida sai
janta suke Ana selfie
Saida anty jiddah tasiya mata, atamfofi masu kyau, materials, takalmi, jaka, kayan
kwalliya, kayan bacci, sannan suka wuce wajan me dinki, aka Bawa ayaz tip din ya
gwada ta, sannan tazubewa me dinkin kudi tace express takeso, basu koma gida ba
suka wuce wajan saloon
Manyan kalbar datake kanta aka tsefe, aka wanke mata kanta, nan da nan gashi yaji
gyara yaqara tsawo, dama dayaya bare Kuma aka gyara shi, ita kanta sai takejin wata
irin iska na shigarta, da akayi mata parking saita dawo Kamar yar turawa, to gashi
ne da uban tsawo, gata da fari, nan da nan tafara sauyawa
********
Yadawo Daga office ya kalli dakin nasa duk yahada datti, rabon da ayi masa gyaran
daki Mai kyau harya fara mantawa
Tun yarinyar Nan tana nan, tsaki yasaki, yanufi wajan momy
Tana dakinta zaune yace momy, yau kwana biyu Kenan yaran nan basa Zuwa Suna share
min da kina
A a, dazufa suka dawo suka cemin Daga part din Naka suke,sun gyarama shi
Zama yayi Agefen ta yadafe kansa Pcikin ransa yace gaskiya akwai damuwa
(tukunnama yaro 🤗)
********
Bayin Allah yanzu ashe bakuda Imani? Kukama ku tsareni awaje daya? Nabaku hakuri
Nabaku kunqi ku Rabu Dani? Tafashe da kuka tace Dan girman Allah ku qyaleni,
wallahi Daga yau babu ni babu Shalele
Hanyar datake Bima bazan sake biba, wallahi idan naqara kwanaki awannan dakin me
duhu mutuwa zanyi
Ke Dalla malama kiyi mana Shiru, babu me sakin ki, sai oga Bilal yabamu dama, inna
Marka tafashe da kuka
********
Yau Tunda lesson teacher dinsu yatafi ta lura sister ta tana cikin damuwa, Bari
tayi Saida suka shiga dakinsu sannan tace sister meyake damunki?
A a Haneefa, kada ki boyemin Dan Allah, idan damuwar ki karatu ne ai mama tace kiyi
hakuri mu gama wannan term din idan zamu koma first term tare za'a maidamu, muyi
zamanmu ajinmu daya, mu dawo gida ga mama, to Menene Kuma abin damuwa? Yau Watan ki
daya a gidan nan, Ina lura dake kina Yawan tunani Haneefa, meyake damunki?
Kafin Shalele tace wani Abu wayarta tayi qara, tana dubawa tayi Murmushi, ta Daga
tace Yaya Ajmal, zan kiraka, I am busy now
OK Yaya bye
Kashe wayar tayi tace, inajin ki sister, cikin damuwa tace sister nakasa cire shi
araina, tana fadar haka tafada jikin Sajida tasaki wani irin kuka
Jikin Sajida yayi sanyi, tafara Bubbuga bayanta Ahankali, tace kiyi hakuri sis,
waye shi din? Fadamin waye?
Batace uffan ba ta dauki wayar sajidan ta shiga gallery takamo photon sa ta nuna
mata
Anty jiddah dataji su Shiru, ta biyo su dakinsu domin ganin ko kalau suke?
Takama handle din dakin zata shiga saita fasa, ta tsaya Taji me Haneef yayi? Me
qaninta abin sonta yayi?
Cikin daki kuwa Shalele tana hawaye tace eh shi Sajida, Ina sonsa wallahi, nayi
nayi nacireshi Daga Raina nakasa
Amma sis Haneefa Yaya akai kika sanshi hakika fara sanshi? Kokuma awannan Dan zaman
dakikai ne a gidan momy?
Ba anan bane Sajida, tun aqauyanmu nafara ganinsa, tiryan tiryan tabata labarin
komai
Ajiyar zuciya Sajida ta sauke, gaskiya sis kinyi kokari, na tausaya Miki, Nima fa
haka infada Miki lokacin Ina zuwa gidan momy nake ganin Yaya Ajmal shida uncle
Haneef din, wallahi sis tun daga lokacin naji inata tunaninsa, Amma ni da Allah ya
rufamin asiri sai akai dace Shima yace yana sona, to kinji inda nadanji sauqi
To Amma matsalar uncle Haneef dinne baya Zuwa gidan nan bare muyi masa Yan dabaru
Ko zamuja hankalinsa, Amma kiyi hakuri wannan girman kan nasa da miskilancin dayake
                                😃 Yanda nakeso Yaya Ajmal ya Aure ni, kema sai
ji dashi zamu sauke masa shi tas,
uncle Haneef ya aureki, Kinga shikkenan mun auri abokai Ko?
Shalele tayi Murmushi suka rungume juna
Anty jiddah datake tsaye abakin kofa Daria ta Kamata, lalle yaran nan wato dan'uwan
nata ake hadawa tarko tana zaune bonono
Barin kofar Dakin tayi, ta shiga duniyar tunani, yanzu Haneefa Nason Haneef, ga
Haneef Kuma a gida anhadashi da manyan mata, Yaya zatayi ta temaki yarinyar Nan,
tanajin Haneefa aranta Kamar itace ta haifeta, dole zata temaka wa yarinyar tasamu
abinda takeso (to gafa second Bilal 😃😃)
Zama tayi akan kujera ta dauki wayarta takira Haneef yana dagawa babu alamar wasa
atare da ita tace sai yaushe zaka zo gidan? Kokuma Sai nan da wasu watanni? Haneef
nakusa Yin wata biyu rabon Dana ganka fa, aiki hauka ne? 🤣
Oh anty jiddah Kin cika damuwa wallahi P, yanzu natashi Daga wajan aiki, zan shigo
kafin natafi gida
Qwala musu kira tayi, dasauri suka futo falon, ta zuba musu ido tana qare musu
kallo, babu abinda yaranta suka rasa, musanman ma Haneefa, zaman datayi a gidan
tana hutawa, tana abinda takeso, hankalinta kwance, yasa komai nata yasake futowa
musanman hips dinta, yaqara bajewa, sai shining yarinyar take, insha Allah zatayi
duk Yanda zatayi taga Haneef ya Aure ta, wannan ai bazai Iyu ace Haneef yayi rashin
taba
Qawancen su ya birgeta, basa boyewa juna komai, gashi yau dalilin Haneefa itama
tasan damuwar Tata yar
Anty ta jiddah ta kalleta, riga da sket ne ajikinta, dinkin yayi bala'in karbar ta,
rigar me breas cup ce sai tayi Kamar tasaka brezia, nan kuwa Bata sakaba
Tace dama zan fada muku ne abbanku yace gobe yanada baqo da safe, kunga yanzu yamma
tayi, inaso ku shiga kitchen kufara Har hada abubuwan dazamu girka masa, abinda
babu sai nayi masa waya yataho dashi kafin yashigo da daddare
Atare suka ce to, sukayi kitchen din, anty jiddah tabisu da kallo, tayi Murmushi,
su Sajida masu tarko😃Wai Har sunyi girman dazasu San wani Jan hankalin samari, oh
zamani
Suna aiki a kitchen, saminu yayi parking motarsu, dasauri yafuto yace saminu minti
biyar, zanga anty jiddah na futo mu wuce gida
Kai tsaye falon nata yashiga, Kamar kullum yana cikin suit, light blue, yayi
bala'in yin kyau
Anty jiddah na ganinsa tace hmm ai wallahi nakusa fishi
Murmushi yayi, banda rikicin anty ya za'ai naqi Zuwa, ai dole ne inzo de in ganki,
yanzu ba shikkenan ba?
Ina yaran suke ne?
Ayaz yatafi ball tun dazu Bai dawo ba, sai su Sajida Suna kitchen, ta Daga murya
tace Sajida, ga uncle dinku Yazo kuzo ku gaisa
Sajida najin ance uncle taja hannun Haneefa tace laaa kinji uncle dinma Yazo, zo
muje
Au bazaki ba? Aikwa saina fadawa mama, ta juya ta fita, tana zuwa falon tafada
jikin Haneef tace uncle sannu da zuwa
Uncle bakasan Zuwa why?
cikin ransa yace HANEEFA, suna me dadi, wacece wannan me irin sunansa?
Yanda anty jiddah take Qwala mata kira yasa ta futo dasauri, gabanta yana faduwa,
Har falon taje, Amma takasa kallansa, saita kalli anty jiddah Tace mama gani
Sai a lokacin ta Kalle shi, idonsu yahadu, dasauri ya janye idonsa jin Gabansa yana
faduwa, ahankali tace masa "Ina yini?"
Yasake kallanta yace "lafiya"
Juyawa tayi zata koma kitchen Sajida ma tabi bayanta tace uncle bye bye, yace ok my
daughter
Yabi bayansu da kallo, Amma azahiri hips din Shalele yakafe da kallo, yana ganin
yanda suke Juyawa
Au Wai baka gane taba? Haneefa cefa yarinyar datake gyarama daki, harna taho da ita
Oh Allah anty nace Miki babu komai, kawai de Naga tanada komai ne, like yar tsana
haka, shiyasa nake kallanta
Murmushi yayi dimple dinsa yafuto yace Kinga anty ni sai wani lokacin ki gaida
doctor idan Yazo, Daria tayi tace to zaiji, Shima dasauri yafice Daga gidan, anty
jiddah Tace mataki na farko Kenan, zakaga yar tsana😃
********
Washe gari gida ya kaure da Qamshin girki, kowa yaci kwalliya Ana jiran Zuwan baqon
Abba, sun jera komai a dining, sun dawo falo Suna zaune Dukansu
Tsayawar motar Abba sukaji, hakanne ya tabbatar musu da Cewa Abba Yazo shida abokin
nasa
Da sallama suka shigo cikin falon, Dukansu suka maida hankalinsu wajan kofar falon
Lokaci daya Anty jiddah Taji kishi, yauga yarinyar datake so qaninta ya Aure ta
tana qirjin wani daban ba Haneef ba
Dasauri yafara janyeta Daga jikinsa gudun kada tasashi a wani Hali uba yayi abin
kunya😃
Wayarsa yadauko Daga Aljihun wandon jeans dinsa, yayi kira yace hello inspector
zaku iya sakin matar nan yanzu
Daga hannunsa yayi sama, yace alhamdulillah, Allah nagode maka, Haneefa jeki dauko
jakar ki, yau qafarki qafata
Anya kuwa anty jiddah zata yarda tabar Shalele?
Toshi kima Bilal me yarinya Anya yau kuwa zai iya barin Shalele tasake subuce masa?
Masu Cewa nayi 2pages kuyi hakuri, babu lokaci, kowacce mace Bata rasa ayukan gida,
shiyasa yau nayi dayawa saboda ku😃😃😃Amma da tun lokacin da anty jiddah tajisu
Suna sirri zan tsaya, saboda ku naqara masoyana, ku kasance tare Dani, Nima Ina
sonku sosai
✍🏻
Amnah El
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
25&26
Doctor Sulaiman yace a a doctor Bilal me kake nufi ne? Wai shin dama kunsan junane?
Anty jiddah tayi Ajiyar zuciya tace haba doctor, me kake nufi da qafarka qafarta?
Ina ne zaka tafi da yata?
Doctor Bilal yayi Murmushi yakamo hannun Shalele suka zauna akujera, Suma su anty
jiddah duk suka nemi waje Suka zauna
Ya kallesu da kyau yace Haneefa yata ce, dama nemanta nake ido rufe, bansameta ba,
mahaifin ta tun kafin yarasu yace nadauketa yabani ita halak Malak, nazama uba
agareta, sharrin matar ubane yasa Har tazo gidannan domin yi muku aiki, Amma
                                      😃 daddy manya, Kai Bilal ka shige su da
wallahi da gatanta, daddynta yana raye(su
son girma)
Ahankali anty jiddah tasaki boyaiyar Ajiyar zuciya, sai yanzu hankalinta ya kwanta
da Bilal, Amma da Kam gaskiya qaninta take tayawa kishi
Tace doctor Haneefa ba aiki tazo yi gidan nanba, a gidan mu take aikin, nikuma na
dauko ta na riqeta tamkar yata, yanzu doctor idan karabata da yaran nan Suma kansu
ba zasuji dadi ba, sun riga da sun saba, doctor ayi hakuri abar mana ita mana
Babu damuwa uncle, mama tana sona sosai, Abba ma haka, sun riqeni amana Kamar Yanda
kayi
Ya kalli su anty jiddah, yanzu de matar aboki kin qwace wa uba yarsa karfi da yaji
Gaba dayansu suka rankaya Zuwa dinning, anacin abinci kowa nata fara'ah, wannan ya
tsokani wannan, wannan ma haka, Har suka kammala
Suka dawo falon suka zauna anata kallo, Amma Shalele tana gefen Bilal Suna fira
qasa qasa, cikin nutsuwa
Ya kalleta yace yarinyar uncle duk kin canja kin girma, ai Gara Dana ganki Dan inje
gida infara Tara kudin da zanyi bikin yata
Cikin kunya ta rufe ido, Kai uncle Dan Allah ni bawani Aure da za'a min yanzu
Cikeda murna tace laaaaa uncle Dan Allah? Yaya akai inna tabaka shi?
Nan take Bilal yabata labarin komai, Aikuwa ta dinga Daria, itama tabashi labarin
Yanda sukai da ladidi tijara Bayan sun taho
Yace ai Ko yaushe Naga wannan matar, saina nuna Nima Dan tijara ne, ba'a taba yata
a zauna lafiya
Qasa qasa yayi da murya sosai cikin rada yace mata aide da gaske nan din babu wata
matsala Ko? (tab wallahi Bilal idan anty jiddah tajika nide ba ruwana🤭🤣)
Shalele tayi Murmushi tace eh uncle babu komai fa wallahi, Ina anty Sady da Hajiya?
Duk Suna nan kalau, zance kina gaishe su, idan nasamu lokaci ma ai zanzo na daukeki
muje
Doctor Sulaiman yace wato de yanzu baqon namu ya zama Iya baqon Haneefa ita kadai
Daria Bilal yayi yace to abokina tuba nake, sannan yajuyo sukaci gaba da firar
Dukansu
Dazai tafi gida, Har wajan mota suka rakashi, yashiga motarsa yadauko ATM dinsa
guda daya, yace wa Shalele ki riqe wannan ATM din, Ko zaki buqaci kudi aciki, ni
inada wani, sannan ga kati na nan, duk numbers Dina Suna jiki, idan wata matsalar
ta tashi, zaki Iya nemana, pin din ATM din qarshan number tane, kingane?
Eh uncle nagane, nagode sosai, Dan Allah ka gaisheda hajiya sosai, da Aududu, da
anty Sady
Karki damu my daughter zasuji, Saida taga fitar sa, sannan ta juya cikin gidan
itama, ayaz ne kawai Afalo, anty jiddah tana daki wajan Abba, sai kawai itama
tatafi dakinsu ta adana katin da ATM din cikin jakar kayanta, a gado ta zabe kusa
da Sajida Suka fara maida baccin gajiya, kasancewar sunsha aikin tarbar baqon
abbansu
********
Juyi yayi akan gadon nasa, yasake Jan blanket dinsa fari qal qal dashi, akaci gaba
da bacci
Azahiri ma maganar sa Ahankali yakeyi Kamar mace, yanzun ma hakance ta kasance
dashi cikin baccin, ahankali yabude bakinsa yace "karki tafi"
Yaci gaba da baccin kadan, alamar mafarki yakeyi, da aka jima ma cikin sigar
shagwaba yasake Cewa "nace karki tafi fa"
Ahankali yasaka hannu yaja Fillo din dake gefensa ya rungume shi aqirjinsa sosai
yace "Stay with me please"
Yaci gaba da baccin sa cikin kwanciyar hankali, wayoyinsa guda uku dake ajiye akan
bedside drawer ne daya Daga ciki ta dauki qara
Runtse idanunsa yayi, ahankali yabude idon nasa, lokaci daya yaji wani irin bacin
rai, meyasa za'a kirashi akatse masa mafarkin sa? Waima da meyasa ya manta ne Bai
kashe suba?
Yanajin wayar na ringing harta katse be Iya dauka ba, Saida aka sake kira akaro na
biyu ne sannan ya meqa hannu yadaga, Ajmal ya akayi?
Kai Sarkin nawa, kazauna Kanata kwalliya kaiba budurwa ba, already anyi sadaka
dakai, kaqi futowa office da wuri, mutane Suna nemanka wayoyinka duka a kashe,
shine wani daga ciki yakirani yace idan inada wani layin Naka infadama Suna can
Suna jiranka akan meeting din dazakuyi
Ajmal, kafada musu su dage meeting dinnan, banida lafiya bazan Iya fita ko'inaba
Shima Haneef anasa bangaren ajiye wayar yayi yazuba wa saman dakin nasa ido,
bagarama rashin lafiya ba akan wannan tsinannan tunanin dayakeP
Tun shekaran jiya yake Fama da tunanin yarinyar Nan, shi Kam wannan yarinyar inaga
masifa take neman zame masa
Tashi yayi yafuto falo da kayan motsa jiki ajikinsa, Kamar kullum yauma Saida ya
ajiye robar ruwa agefensa me sanyi, sannan yafara motsa jikin
Yayi Nisa da motsa jikin kawai ya tuno idanun nan nata, zazzaqar muryarta "Ina
yini"?
Ya tuna gaisuwar datayi masa, lokaci daya jikinsa yasaki, gudun dayake yi yadena,
ya sunkuya yakama gwiwoyinsa da hannayen sa, Kamar me ruku'u yana maida numfashi
Awannan halin Yazo ya riskeshi, dasauri Yazo yadago shi, subhanallah abokina Ko
ciwon cikinka ne yatashi? Shazali shiyasa nace kadena durawa kanka wannan maganin,
shikkenan Kai dakaji yar sha'awa saikaje kakama magani kasha, sannu...
Yaga alama idan Bai dakatar da wannan gayen ba, bazai daina zubaba, shi Ko gajiya
bayayi da magana, qwace jikinsa yayi yace Dan Allah Malam cikani,yamiqe yadauki
ruwansa ya kwankwada
Cikin mamaki Ajmal ya kalleshi, kaiiii, au Wai dama kalau kake shine kasa nabaro
aiki na nataho wajan ka?
Bece dashi komai ba, yayi wajan kujerun sa yazauna, ya Dora kansa akan kujerar
Bude ido yayi ya kalleshi, Ajmal meyasa me idan kaga wasu mutanan sai kaji gabanka
yana faduwa haka?
Ahankali yace" yes "ba sau dayaba, duk ganin Dana mata
What? So? sofa kace Ajmal, ni inso wannan yarinyar? Yarinyar Dana haife.... Saikuma
yayi Shiru yazari wayar Ajmal dake gefe yashiga danne danne
Tsayawa yayi ya karanta abinda yaduba, yayi cilli da wayar kan kujerar dasuke, yace
"shirman banza"
Ajmal yadauki wayarsa yaga abinda shazali yaduba, ya kwashe da Daria, au baka yarda
da maganar Dana fadama ba Saida ka duba a Google?
Yasake kwashe wa da Daria yace Allah sarki, ashe wannan ne rashin lafiyar dakake,
shiyasa yau kaki Zuwa office, abokina wacece wannan yarinyar? Wacce me sa'ar ce?
Daga fara kamuwa da sonta anqi Zuwa office Tokuma idan aka aureta Yaya za'ai Kenan?
😂😃aikin za'a ajiye duka?
Ajmal kadena Daria mana, wannan abin fa ba abin Daria bane, da gaske banida lafiya,
kullum naganta sai gabana ya fadi, kaga wannan ma ai babbar jinya ce, ni babu wani
so danake wa kowa, Daga Kai Har Yan Google din duk qaryar banza ce, aikin banza
aikin wofi 🤣
Me Ajmal zaiyi inba Daria ba, yace gaskiya ne abokina, wanan Kam babbar jinya ce
Tsaki Haneef yasaki yatashi yashige dakinsa, Daga nan yayi toilet domin watsa ruwa
********
Suna zaune akan gadon su, da daddare Suna fira, Sajida ta dubeta tace Wai kuwa
sister Dan Allah jiya da uncle Yazo Yaya kikaji?
Ajiyar zuciya ta sauke tadauki Fillo ta Dora a cinyarta, ai wallahi bakiji Yanda
naji dadi ba, Kamar karna bar falon, saide Kuma ba dama
Um ai sister Haneefa shiyasa danaji ance Yazo nace kizo muje kikaqi Zuwa
Ke gabana nefa yaje faduwa, Kuma ni idan Ina ganinsa sai Inga yamin kwarjini nakasa
komai, Ko kallansa kasawa nake wallahi, ninarasa wannan wanne irin so ne
Lalle sis, wanne irin kwarjini? To tsaya anan yana Miki kwarjini wadancen yanmatan
su kwace Miki shi(karfin Hali irin ya zama natan nan🤣🤣)
Toya zanyi sis Sajida, shi din wani irin mutum ne na daban, ga aji, jiya fa Wai
nace Ina yini, akace min "lafiya" shikkenan fa bass
Bakiji Yanda yasake birgeni ba, Allah Kasa idan akwai Aure atsakanina dashi Toya
tabbatar mana da alkhairi, idan Kuma babu Allah kaciremin Sansa araina
Dasauri Sajida tace akwai ma insha Allah sis, babu wani family dazaki tafi, kina
nan a shazali's family insha Allah
sukasa Daria gaba dayansu
********
Yashirya kansa cikin qananun kaya, sai zuba Qamshi yake
Momy da daddy Suna zaune, ya tsugunna Har qasa ya gaishe su, ya kalli daddy yace
daddy dama.. I want talk with you
Inajin ka Haneefa
Am daddy gyaran dakin da yaran nan sukemin bayamin, kwata Kwata Kamar ma basa taba
wajan wallahi, shine nakeso asamomin wasu masu aikin please daddy
Shima daddy yace yes, Alhaji shazali, bahaka suke fadama ba? Wato Kai bakada aiki
sai akawo ma yarinya me aiki, Washe gari ka Koreta, shazali Anya kuwa? Anya zaka
Iya riqon Aure kuwa?
Daddy yaci gaba, toka bace kabani waje, babu wata yarinya da za'a sake kawoma, aiba
Haifa ta kayi ba, sannan munyi waya da Alhaji Sadiq yace bakaje kaga yar tasaba
tsawon wannan lokacin, ba shawara nake bakaba, umarni nake baka, yanzu basai anjima
ba kanemi Ajmal kuje ku ganta, zanyiwa babanta waya nasanar dashi
Ajiyar zuciya yasauke, baicewa iyayen masa uffan ba, yatashi yafice Daga falon
idanunsa jajir, shifa Yama manta da batun wadannan yaran, ashe su daddy Har yanzu
abin yana ransu
Tsaki yasaki Bayan yagama karanta wa, Daga gefensa yaji ance Yaya gashi Wai inji
momy, kakai mata
Kallanta yayi, yaga wata Leda ahannunta , baisaniba Samah dince Ko Safah, Harara
yabi yarinyar dashi, yace ajiye anan
Ajmal nazuwa ya miqa masa wayarsa, yace kakaimu wannan address Ajmal, bazan Iya
driving ba, daddy ya matsa akan naje Naga yaran nan, wallahi banasan maganar auren
nan
Kafadarsa ya Bubbuga kayi hakuri abokina, insha Allah Allah zai kawo mafita
Daukar ledar dake qasa Ajmal yayi, suka shiga motar sukabar gidan
Aharabar gidan suka tsaya, babban gidane na gaske, da alama itama mahaifinta yana
dashi sosai
Wani ne Yazo yayi musu iso, Zuwa dakin baqi
Dakin yayi kyau, ga sanyin esi dayake tashi
Ma'aikata ne suka fara shigowa da girke girke, Kala Kala, Saida suka ajiye girki
yakai kusan Kala takwas
Sannan aka ajiye musu lemuka
Suka Daga Kai Suna kallanta, baqa ce ba fara ba, saide mayukan datake shafawa yasa
tadan Washe, babbar mace ce sosai, shi kansa da kadan zai girme ta
Mayafin jikinta Dan qarami ne, saita yafashi Iya kafadarta daya
Zama tayi a kujerar datake fuskantar su tace Sannunku fa
Munyi magana da dad Dina, yacemin za'a turo min Kai in ganka kokamin, well nide
awajena banda matsala, Tunda naganka yanzu naji kayimin, zaka Iya Zuwa kasanar a
gida, mun dede ta kanmu, kawai ayi maganar Aure
Lumshe idanunsa yayi, shi aka turo mata tagani Ko yamata? Hmm
Ajmal daya Dade da mamakiin wannan uban girki yace, to ranki yadade wannan abubuwan
ai sunyi yawa, ruwa ma kawai ya wadatar, saide fa kiyi hakuri kinsan manyan mutane
basu cika cin abinci ba awajajan da aka gayyacesu, musanman ma shi angon naki
Murmushi tayi, to aini aganina wannan ma yayi kadan, a kullum Ana girka min abinci
fiye da ashirin arana
Ajmal ya miqa mata ledar dasuka zo da ita, yace to ga wannan amarya, kyauta ce Daga
ango
Ledar ta karba, ta bude ta, turare ne aciki, guda uku, masu tsada, aqalla Ko wanne
daya acikinsu zaikai dubu hamsin
Yatsina fuska tayi, tace Haneef wannan wanne irin turare ne? Ai sunyi araha dayawa
Kamar fiyawota😃
Masu tsada nake shafawa, na dubu Dari biyu, Suma duk wata saina sake wasu koda kuwa
basu qare ba
Amma babu damuwa, ngd, kuyi hakuri ban fada muku Sunana ba, ni Sunana Hairat Alhaji
Sadiq dala, Haneef abinda nakesan fadama shine, arana Ana girkamin abinci kusan
ashirin
Ina zuwa gyaran gashi duk Bayan kwana biyu, Amma Tunda zan auri Haneef Shazali zaka
dinga kaini wajan gyaran gashi kullum 😳
Duk wata babana yana kaini yawon bude ido qasashen qetare, Bana girki, zaka samomin
ma'aikata Kamar Yanda kagani a gidan mu
Bafa anan abin yatsaya ba duk wata dubu dari tana shiga account Dina Daga bankin
babana wannan ta Zuwa shan ice cream ce
Kai meyasa ma zan Bata lokaci na wajan yima bayani, nasan banda matsala dakai inde
wajan kudi ne, duk da mom Dina tana Cewa Yan kasuwa su a kullum burinsu shine Yanda
zasu samu riba, basu yarda da rashin riba akan kasuwanci ba
Ajmal yana Kallan yanayin sa aransa yace wannan tun kafin ya wankawa yar mutane
mari, babanta yadauki mataki akanmu Gara najashi mutafi
Cikin sauri yace to hajiya Hairat, ga kati nan me dauke da numbers din angon naki,
zaki Iya kiransa idan kinsamu time, mu zamu wuce, sai Kuma next time idan mundawo
Suna shiga mota, Yadubi Ajmal, meyasa kace zamu tafi baka Bari nayi mata shegen
duka ba 😃
Meyasa zaka hanani?
A a Haneef nifa dama Tunda Naga yanayin ka nasan idan na qyale ka, to bazamu Rabu
da yarinyar Nan lafiya ba, shiyasa nace mutafi
Huci yaci gaba da yi, matsiyaciya harni zata kalla tace Wai anturo mata ni taga Ko
nayi mata? Talla nake dakaina?
Ajmal yayi Daria, au Kai wannan ne damuwar ka? To maganar data fadawa Yan kasuwa
fa? Bata duba dukanmu Yan kasuwar neba, yaci gaba da Daria
Haneef yayi tsaki, Wai gyaran gashi duk Bayan kwana daya Kai kaji wani bala'i
Tsaki kawai Haneef yake ja, turaren jikinta Ko nawa baikai tsadaba, shine zatace
wanda aka kawo mata yayi araha dayawa, ni batasan ma bada kudi na nasiya mataba
Haneef de Haushi ya cika shi, yace no bakwa gobe ba, saide jibi Ko gata, ai babu
wajan wadda zan sake Zuwa gobe, saina huce da wannan baqin cikin
********
Washe gari yana zaune a qayataccen office dinsa, takardun dasukai meeting akansu
yake dubawa, yaduba yaduba yakasa fahimtar komai
Ya tattara su ya ajiye agefe, yazuba tagumi
Meyasa ne Tunda yaga yarinyar Nan tunanin ta yahanashi sakat?
Shide yasan baya sonta, to meyasa zaiyi tunanin ta?
Yasan Ajmal kawai fada yayi, Amma shi yasan babu wata yarinya dayake so
Kawai de yanaji aransa yanaso yasata agaba yanata kallanta, kawai tana birge shi ne
yarinyar gata yar qarama Amma tanada abubuwan hutawa masha Allah, shiyasa yake
ganinta Kamar yar tsana
Toshi de yanzu idan yakoma gidan anty jiddah yau, dole zata masa wata fassara, dama
rannan Daga Dan Kallan yarinyar tafara Watso masa questions
Murmushi yayi lokaci daya yace yessss, wayarsa yadauka yakira Ajmal
Hello abokina yaushe zakaje wajan Zance ne?
Ajmal yace, Haneef Anya kuwa ba wani Abu kake qullamin ba? 😃kaine yau zaka ce zaka
rakani wajan yarka zance?
No serious fa abokina da gaske nake, Naga Nima jiya kana yin aiyukan ka na katse ma
nace kazo ka rakani, shiyasa Nima yau zan rakaka, idan zakaje Nina gama aikin
danake, kawai ka futo mutafi
Ajmal Bai kawo komai aransa ba yace to shikkenan, ganinan Zuwa, zanje Naga my
sajeey
Saida Yazo kamfnin su Haneef sannan sukabar motar Haneef awajan saminu, yace saminu
zaka Iya wucewa gida, akwai inda zamu
Saminu yace to yallabai asauka lafiya
Suka shiga motar Ajmal suka tafi
Saminu yabi Bayan motar su da kallo
Yarasa Ina su yallabai suke Zuwa su kadai kwana biyu, kokuma yakusa samo musu
uwargida ne? 😃
Ajmal na driving Amma Haneef gani yake Kamar bayasan tuqa motar, haka de yadan ne
komai aransa Har suka je gidan anty jiddah
Anty jiddah yau tana kitchen da kanta, sukuma su Shalele Suna daki, Sajida tace
Kamar fa Nocking nakeji
Riga da sket ne ajikinta English wears, takama gashin kanta tayi parking, jelar
gashin nata tanata bin bayanta
Tatashi ta nufi kofar falon, Zuciyar ta daya ta bude
Sai ganin sa tayi agabanta, Zuciyar ta ta tsinke, Shima anasa bangaren ido yazuba
mata yakasa dauke wa
Cikin in.. Ina tace sannunku da Zuwa, tajuyo cikin falon da sauri
Idanunsa Bai tsaya ko'inaba sai akan dogon gashinta
"masha Allah, me irin wannan gashin itace zata ce akaita wajan gyaran gashi kullum
aciki umarni akaita "
Cikin daki tashige da sauri, ta Cewa Sajida ke wallahi su uncle Haneef ne, shida
wani
Sajida tace haba? Kode Yaya Ajmal ne? Bari naje nagani
Falon ta futo, tana ganinsu tatafi da gudu tafada jikin Haneef, uncle sannunku da
Zuwa
Yace yawwa my daughter, Ina anty takene? Kiramana ita mana, tace to, sannan ta
kalli Ajmal tace Yaya sannu da Zuwa
Yawwa my sajeey
Yana ganin tafiyar ta, yace gaskiya Haneef bakamin kara wallahi
Agabana yarinyar Nan sai rungumarka take😃
Haneef yace shikkenan Ajmal kaima rungume ta, rungume ta inka isa, wallahi Daga
ranar bakai ba ita
Kawar dakai kawai Ajmal yayi, sai can Kuma yace kai abokina wacece wannan yarinyar
data bude mana kofa?
Tsaki Haneef yaja, yanzu Kai harka zuba mata ido kagane wanne irin ido ne da ita?
To yarinyar datake min aiki ce kwanaki
OK Wai me hijabi?
Ajmal yasake Kallan abokin nasa, qarara yaga kishi a idonsa, toko itace wadda yace
masa yanajin faduwar gaban? Wato kawai Daga yabon yarinya Har kishi yakamashi,
shikuma Kenan yamutu shida ya rungume masa budurwa? 🤣kenan da shine hauka zaiyi
Shiru sukai ganin anty jiddah tazo, aranta tace dama nasan zaka dawo yaro 🤣
Gaisawa sukai Ajmal sai sunkuyar dakai yake, waishi me suruka
Su Shalele suka futo itada Sajida suka ajiye musu ruwa da lemo, Har qasa ta
tsugunna ta gaida su
Anty jiddah Tace Ina zaki Kuma? Waike bakya gajiya da zaman daki ne?
Baisan dalili ba cikin ransa yace Alhmdlh, jin furucin anty jiddah
Garin satar kallanta anty jiddah ta kamashi, dasauri yace am anty dama na rako
Ajmal ne, shine nace Bari Nima nazo naganki
Gudun kada tace masa meyake kallo irin rannan, tasa yaji kunya saiyayi fuska yace
anty zamu wuce, sai wani lokacin
Sajida de Saida tabi bayansu suka Dan zanta da Ajmal sannan tadawo gida
Suna tafiya amota Ajmal na kallansa sai fara'ah yake shi kadai, lalle akwai ayar
tambaya akan abokinsa
Shikuwa Haneef tunani yake Yaya za'ai yadinga zarya a gidan anty jiddah? Wannan ai
saita dauka ma son yarinyar yake, Bayan Kuma shi yasan ba haka bane 🤣
Kawai de yanaso yana ganin yarinyar ne, sha'awa take bashi wallahi Kamar yar baby 🤣
Gaskiya dole ya nemi mafita
Ajmal na sauke shi a gida, Bai wuce part dinsa ba, part din momy yaje, yanaso yayi
Mata maganar Amma saiya kasa
Zama yayi suka gaisa sannan tace yaushe zakaje wajan yar qawar tawa ne? Yace gobe
zamuje insha Allah
Momy Tunda daddy yace bazai sake samomin me aiki ba, kifadawa anty jiddah tadawomin
Dame aiki na🤣
Yanzu Kai Alhaji shazali Ina kataba ganin anyi haka? Itama fa Acan din aiki
yarinyar take mata
Bugu daya ta Daga, Bayan sun gaisa momy tace jiddah babu me gyarawa Haneef dakinsa
fa yanzu, yakamata ki dawo da yarinyar Nan haka, taci gaba da gyara masa, yaro duk
yanata mita anbar masa dakinsa da datti
Anty jiddah najin haka cikin ranta tace wannan ba aikin kowa bane saina Haneef
Shegen yaro ni zaiyi wa wayo? Tanan ya bullomin kenan🤣
✍🏻
Amnah El Yaqoub
💕SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
27&28
To yanzu jiddah Tunda shi wanda yayi silar zuwanta yace a dawo masa da ita basai
abar magana ta wuce ba ita Kuma yarinya tadawo bakin aikinta
Quruciya de momy, yanzu Haneef dinne me quruciya? Yaron da kuke shirin liqa masa
mata biyu
 Yanzu de jiddah Kinga babu wani tone tone Dan Allah kihado mata kayanta tadawo
gida, sai anjima, qit takashe wayar saboda kada ma anty jiddah tasake Cewa komai
Yanajin Yanda wayar ta qare wani farin ciki ya mamaye Zuciyar sa, yace yawwa momy
to yanzu ba shikkenan ba, kema Yan biyunki sun huta
Kallansa tayi, to kaima Kuma Haneef saika kiyaye gaba, banasan wannan kore koren
dakake wa masu aiki
A a momy babu komai, Bari inje daki na huta, sum sum yatashi yayi part dinsa yana
gudun karyaci gaba da zama Kuma momy ta harbo jirginsa
Yana Zuwa part dinsa yafada kan gado, ya janyo computer sa yafara aiki cikin
kwanciyar hankali, haba ai Gara haka, Gara tadawo insata agaba ina kallanta San
Raina, yafi ace kullum Ina zarya a gidan anty, Tunda inada ikon dawo da Mai aikina,
(tofa kaga masu yar aiki😃)
********
Sister Kinga wannan brezia din na siyo mana su a school dazu da safe, Kinga wannan
babbar zata Miki
To brezia sai anyi candy ake sakawa? Nikam saka abata zanyi wallahi
Shalele tace a a nikam babu ruwana, bazan sakaba, aisai inji kunya ma, kowa Yana
ganinka yasan me kasaka
Au kunya Ko? To shikkenan ai sai ki zauna da Abu turu turu babu Rigarsa
Anty jiddah ta turo kofar Dakin nasu ta shigo, gefen gadon ta nema ta zauna, tace
Haneefa kinason Zuwa gidan su momy?
Ba aikenku zanyiba Haneefa, inaso ne kikoma can gaba daya, dazu munyi waya da momy
tace Haneef dakinsa yana zama da datti, shikuma Kinga Baisan qazanta, shiyasa tace
kikoma
Wannan babu damuwa akan haka, zanyi magana da Haneef yasama mata lesson teacher din
dazai dinga yimata karatun, kokuma shi yazauna yayi Mata, Bayan wata daya sainayi
masa maganar karatun inji Yanda zamuyi dashi
Kiyi hakuri Haneefa Nima akwai dalilin dayasa zan barki kikoma can din, insha Allah
zakiga ribar Hakan agaba, yakamata ku kwanta yanzu dare yafara yi
Taja musu kofar tayi dakinta, dalilin dayasa zatabar Shalele tatafi guda daya ne,
tanaso yarinyar ta kusanta da Haneef, yakasance a kullum tana kusa dashi, ta
hakanne zaisa ta cimma burin ta akansu
Doctor Sulaiman ma dayaji dalilin nata sosai ya gamsu
Wajan sha biyu saura Sajida ta dubi Shalele data fara bacci tafara tashin ta
Cikin magagin bacci tace Sajida lafiya?
Haneefa ta tashi zaune, tace meyake faruwa ke baki fara bacci ba?
Sister shawara zan baki, duk lokacin dakika koma gidan momy, kada ki yarda ki
nunawa uncle kina sonsa
Kinsan halin maza, idan sukaga mace tana sansu tofa babu zaman lafiya Daga ranar
zasu dinga tashin Kai (🤭 nikam ba ruwana Sajida ce tafada)
Sannan koda wasa kada kisa aranki Cewa Wai bazai Iya sanki ba, a kullum anaso Bawa
yasa aransa Addu'ar dayake yi ta riga da ta karbu
Kawai kisa aranki uncle nakine ke kadai
Maganar kina sonsa kuwa kiyi biris ki share shi, kiyi Kamar bakisan komai ba
Ajiyar zuciya ta sauke, gaskiya Sajida maganr ki Hakan take, Kuma naji dadin
shawarar dakika bani insha Allah zanyi amfani da ita, Amma yanzu please ki kwanta,
dare yafara
Sajida tace to shknn gud 9yt, Daga nan sukaja bargonsu suka kwanta
********
Washe gari da safe anty jiddah da Sajida suka tayata tahada kayanta, momy tace ta
turo iliya direban yara zaizo ya dauke ta
 idanunta suka cika da qwallah, ni mama banasan rabuwa dake, Dan Allah kice musu
nide su barni awajan ki
Haneefa nafada Miki inada dalilin dayasa banyi musu ba akan komawarki gidan, nan
gaba kadan zaki gane dalili na, tashi muje iliya tun dazu yana jiranki
Haka suka futo Har wajan motor sa, Suka sake sallama, sannan ta shiga suka tafi,
Sajida ta zauna tayi Shiru Kamar marainiya, dama haka ne sabo yanada dadi rabuwa
babu dadi
Suna shiga gidan ta harari part din Haneef, aranta tace a kanka gashinan ansa
narabu da Sajida ta
Momy da yara Suna falo, huzaifa yana cinyar Samah yanayin game awaya, tayi sallama
tashigo gidan
Momy tace sannunki da Zuwa
Ahankali tace Yauwa momy nagode
A a babu komai, kije kihuta kici abinci, da yamma kyaje kiyi masa gyaran, yanzu Kam
jeki huta
Cikin girmamawa tace godia nake momy, tayi cikin dakinsu itada baba Hanne 🤣
Samah tace oh momy kuwa radau abakinta, Kamar ita tasaka Miki
Safah tace to laifi ne danta fadi Hakan? Kede da neman magana kawai
Baba tace Kai amma naji dadi alhmdlh, sannu yata, sannu da Zuwa
Tace amin baba, tana ajiye truly dinta yar qarama Daga gefe
Baba wallahi nagaji, Kuma wai momy Ina shigo wa Wai inzo in huta anjima naje nayi
masa aiki
Ni wallahi aikin nan ya isheni, gidan mama jiddah yafi nan dadi wallahi
Baba tayi Murmushi to kiyi hakuri mana yata, nan dinma abinda yasa bakya jin
dadinsa saboda Yan biyu basa janki ajiki ne, can Kuma akwai Sajida, Sajida Kuma
sauqin Kai Gare ta
Kiyi hakuri zakiji dadin nan dinma wata Rana, harma ki zauna din din din
Yata nifa Tunda naganki Naga kinfi dacewa da Haneef, Amma iyaye duk sunje sun
hadashi da wasu yanmata masu budadden ido, to baka Isa kayi magana ba, kinsan Yan
boko
Momy dake falo wayarta tayi qara, tana dauka tace Haneef Ina jinka
Wacce yarinya?
Afili tace tazo Haneef, tana dakinsu tana hutawa, nace taje tahuta, anjima saitaje
tagyara ma dakin, kokuma abarta sai gobe?
Dasauri yace a a a a momy, tana hutawa taje tayi aikinta, yawwa Takoma bakin
aikinta 🤣
Momy tace yaushe zakaje wajan yarinyar? Lokaci daya annurin fuskarsa ya gushe, yace
yanzu ma Ajmal nake jira Yazo Daga office dinsu saimuje
********
Suna hanyar Zuwa gidan su qawar momy wayarsa tayi ringing
Anty jiddah yafuto baro baro ajikin screen din
Dasauri yadaga yace anty nah ya gida yayarana
OK da sauqi Ko, to shikkenan dama nakira ne infadama inada niyyar saka yarinya a
school momy tace a dawo ma da ita, Dan haka alhakin karatun yarinyar Nan yana
kanka, idan anshiga sabon term ka tabbatar ka maidata makaranta
Sannan akwai lesson teacher dayake Zuwa gida yayi musu karatu
Kamarya menake nufi Haneef? Tanaso taqara tabbatar da abinda take zargi Dan haka
dasauri tasake Cewa
Nifa Haneef aikin nan ba dole, yanzu saina sa hijabi na inzo in dauke yarinyar Nan,
babu zafi
Dasauri yace a a anty, basai kinzo ba, za'a nema mata (🤣)
Kince asamo mata lesson teacher, shine nace za'a samo mata
Babu wanda zaka samo mata Haneef, Kai zata yiwa aiki, danhaka Kaine zaka koya mata
karatu Har Zuwa lokacin dazaka sakata a school
Amma anty....
"zanyi "
Tace ok sai anjima takashe wayar, Murmushi tayi Wai zanyi, bazai cede zanyi mata
ba, saide zanyi, wannan miskilanci na Haneef yana Bata mamaki
Yanzu ne tasake tabbatar wa Haneef ne yasa momy ta kirata akan Haneefa, afili tace
Haneef kakira wa kanka, Kuma Nima ka ragemin aiki, domin kuwa zamanku waje daya,
zaisa yarinyar taqara shiga ranka fiye da yanzu
Kafara son yarinya baka saniba, sannan ka gagara baiyyana kowa, ba irin wannan
soyaiyar nakeso ba Haneef, nafison kaso Haneefa ta Yanda zakaji aranka Cewa zaka
Iya baiyyana wa kowa, ciki harda iyayenmu, rashin budurwa ne yasa suka hadaka da
wannan yaran, aganina kawo musu Haneefa zaisa su janye wannan maganar yanmatan
Ajmal yana ganinsa Kuma yaji duk wayar da sukai, Amma be tambayeshi akan menene ba,
yanaso dakansa yayi masa maganar, idan abinda yake damunsa yakai intaha dakansa
zaizo yayi masa magana
Har suka je gidan qawar momy, Shima gida ne Dan madaidaici haka, Amma bazaka
kirashi da gidan talaka ba, Afalo akayi musu iso suka zauna
Gyaran murya yayi yace, Hajiya barka da futowa, ni Sunana Ajmal, abokin Haneef
Shazali, tun muna yara
Wannan shine angon naki, munzo mu ganki ki ganmu, Ko za'a samu fahintar juna
Shide Haneef babu um bare um um, kallansa tayi tace Kai baka magana ne?
Inayi mana, kawai de dake dinne banasan... Ajmal ne ya zungureshi Daga gefe jin
baran baramar dazai musu
Ya Kalle ta yace to Mungo de mu zamu tafi, ga katin sa na waya, Ko zaki Iya nemansa
Suna fita harabar gidan Ajmal yace Allah sarki, wannan saliha ce wallahi 🤣 babu
ruwanta, hajara duniya ba zafi
Haneef yace nikaina nayi mamaki wallahi, qila itama bataso Kamar ni, shiyasa Ko
katin ma Bata karba ba
Yanda kasan an doka masa guduma haka yaji, ashe ita Naga abin na gaske ne, ita
harma tafi waccen
Ganin sunyi Shiru yasa ta bude Bayan motar ta shiga tasaka Jakarta ma, tace ku
shigo mutafi mana 🤣
Haka suka taho, ahanya babu me magana acikinsu saide ahada ido ayi shiru😃
(maganinku Kenan, yau kun hadu da wadda tafi ku tsiya)
Suna Zuwa gida cikin bacin rai yayi part dinsa, Ko kallanta Bai sake yiba itama
kuwa taja Jakarta tayi part dinsu momy
********
Saida tagama hutawa sannan ta tashi tafara gyara falon, riga da sket ne ajikin ta
Yan kanti
Yana shigo wa falon yaganta tana mopping Ahankali yasauke Ajiyar zuciya duk da yana
cikin bacin ran wancen jarababbiyar Saida yaji sanyi aransa
Zuba mata ido yayi yana Kallanta, Yanda take mopping din yake kalla saide ko'ina
ajikin ta rawa yake, musanman qirjinta
Dasauri yadauke idonsa akansu
Masha Allah manya dasu, Zuciyar sace tasake bashi shawara, babu wata wata kuwa yabi
shawarar Zuciyar sa yasake maida idonsa kansu
Dama haka nakowa yake atsaye?
Alamu Taji Kamar Ana kallanta, ahankali ta dago kanta ta kalleshi, suna hada ido
duk da duburbuce Amma tana tuno shawarar Sajida saita saki jikinta
Tace uncle sannu da Zuwa, Ina yini?
Fuskar nan atamke yace lafiya, Daga nan yashige dakinsa yafada kan gado, niktile
dinsa yacire yayi wulli dashi qasa, Allah yasa de yarinyar Nan bataga abinda yake
Kallan mata ba ta Raina shi
Itama kafada ta dage tace kome aka masa oho, taci gaba da aikinta
Hanyar dakin ta nufa, kafin ta shiga Saida tace nutsu Shalele, karki ji tsoro ki
nutsu kishiga ciki kawai
Ahankali ta tura kofar Dakin ta shiga, yana kwance akan gadonsa Amma kafafunsa Suna
qasa, idanunsa a lumshe, Amma Sarai yana ganin duk abinda take, ita kuwa tayi zatan
bacci yake, ta wuce toilet ta wanke shi, tasaka abin Qamshi
Sannan tadawo cikin dakin, kallansa ta tsaya yi, taga bacci yake sai kawai tafara
aikinta
Harta gama shara, taje wajan data ajiye masa photunansa tadauka ta goge su sannan
tasake gyara musu zama
Shide yana kallanta, yana ganin irin wannan baiwa Tata, gata qarama Amma tana
wannan uban aiki saikace inji🤣
Wani iri takeji hau gata gashi a daki daya, duk Bata cikin hayyacinta dande ta dake
ne kawai🤣
Mopar ta ta dauko tafara mopping dakin, cikin sauri, tanaso tagama tafice tabar
cikin dakin nan
Duk yana kallanta, cikin ransa yace to ai Gara haka, Gara tadawo nan din Yanda zai
sata agaba yayi ta kallo
Garin saurin datake wajan mopping santsin tiles yajata zata fadi qasa, da karfi
tace Auch!!! Asukwane yatashi zaune yace lafiy... Kafin Yarufe baki tasowar dayayi
zaune ita Kuma zata fadi qasa yasa jikinsu ya hadu
Aikuwa lokaci daya tafada kansa
Wadannan abubuwan guda biyu dasuka sauka akirjinsa yasa jikinsa yasaki yaji baida
kuzarin dazai tareta haka yanaji yana gani suka fada kan gadon
Atake ya lumshe idonsa, wannan karan Kam bawai yana ganin nata bane, da gaske
lumshe idon yayi
Ita kuwa tsoro yasaka runtse idonta,tana tunanin faduwa aqasa, jin ajikinsa tafada
yasa tafara bude idonta Ahankali, harta bude shi fes akansa, taga ya lumshe ido, ta
sauri ta janye jikinta Daga nashi
Daga masa Kai tayi, tazari Mopar dazata fice Daga dakin
Qasa tayi da idonta tace to, sannan taja masa dakin tafice dasauri gabanta na
faduwa, yau itace ajikin Haneef? Oh ya Allah
Tana fice wa cikin ransa yace meyasa Bata saka wannan abin ne? Yanzu Kuma inda
wanine tafada kansa haka Shima fa zaiji irin abinda yaji yanzu Ko?
Nan da nan kishin Yan maza yatashi 🤣🤣
Key din motarsa ya Zara yafuto waje, a lokacin Ana Kiran sallar magrib, Saida ya
tsaya akai sallah sannan yashiga mota da kansa yafice da gudu
********
Tana shiga dakinsu tafada duniyar tunani, meyasa bataji Haushin abinda yafaru
tsakaninsu ba yanzu? Kodan San datake masa ne? Haka taita murmushi Baba Hanne tana
kallanta, tasan Kuma Sarai Daga part din Haneef yarinyar take, Ko menene ya wakana
take wannan farin cikin oho musu, yaran zamani de ba'a iya musu 🤣🤭
********
Wani babban boutique yaje, yayi parking yadauki ATM dinsa yashiga ciki
Wadanda suka sanshi sai kallansa suke Ana nuna shi, haka yafara zagaye wajan yana
dube dube, to abinka da mutumin dabai sababa, saide yayi waya yabada umarni ayi
Daqyar yagano wajanda kayan mata suke, wata budurwa yagani awajan yaqaraso wajanta
"sannu fa"
Tana Juyowa taga Haneef Shazali, ai tuni tafara fara'ah, tayi tunanin ko zaice yana
sonta ne, tace yawwa, yace am Dan Allah inane ake Saida vest na mata, tace laa kaga
wajan can, gashi can
Yace ok, yayi gaba, ganin yatafi baice mata komai ba Kuma tasan basake ganinsa
zatayi ba saitasha Gabansa tace Dan Allah Ko zan Iya yin selfie dakai?
Yatsaya sukai, baisake kallanta ba yayi gaba, ita kuwa tace jeka de, inma bakace
kana sona ba ai de munyi photo 🤣🤣
Yana Zuwa wajan yadebi panties da brezia dozin biyu, yatafi yaje yabada ATM Dinsa
suka ja kudin su, Daga nan yayi gida
Yana Zuwa gida yayi parking motarsa yafuto da kafarsa daya yazuba wa ledar hannunsa
ido, brezia din dake ciki ya kallah latest ne shegen masu kyau, aransa yace Ko zasu
yi mata? To Wai ma tayaya zai iya Bata? Yace mata me? Karfa tayi masa wata
fassarar, Kuma shi gaskiya idan yana ganin wadannan abubuwan ahaka gaskiya akwai
babbar matsala 🤣
Haka de yafuto Daga motar, yayi part din momy, inyaso kawai ya ajiye mata ledar
agaban ta yajuya, yana ganin kawai Hakan shine mafita 🤣🤭
*********
Hajara na zaune Afalo ta Dora qafa daya Kan daya tana kallo, a lokacin Shalele na
daki tacewa baba Hanne baba Bari inje kitchen in dauko ruwa, qishi nakeji
Tafito Daga dakin taga baquwar fuska a falon, wannan Kuma wacece yaushe tazo gidan?
Kosu momy baquwa sukai? Dazu Bata ganta ba
Hajara na Juyowa taga Shalele atsaye, ta miqe dasauri tace iyeee kece Anan gidan?
Tafidda hannu ta wanka mata mari, tace dama nafada Miki inde nasake ganinki,
wallahi sai jikinki yagaya Miki
Rannan ma dakika ga na qyale ki, ba tsoron ki nake jiba 🤣🤣
Shalele Taji zafin mari tuni tafara hawaye tace Mena Miki zaki mareni?
Au ni kike tambaya me kika min? Tasake Daga hannu zata sake mata wani Marin
Cikin tsawa Hajara!!!
Juyawa sukai Dukansu, Haneef ne atsaye abakin kofar falo, duk abinda yake faruwa
akan idonsa
Shalele ta juya tayi daki da gudu (nace jeki dama rabon shan mari ne yafuto dake🤣🤣
🤣)
Haneef yana Zuwa wajan Hajara babu tambaya babu komai, Kuma dama ga Haushin ta da
yakeji tunna dazu Shima yadaga hannu ya watsa mata mari
Meyasa bazaka tambayeni abinda tamin ba? Yarinyar Nan awajan shopping naganta
tayimin rashin kunya, na qyale tane kawai saboda tana tare da bodyguard Yan Sanda
Kansa yadafe da hannunsa Pyayi gaba yabarta anan, Hajara tanason saka masa ciwon
Kai (um ahakan zakayi mata biyune?)
(wata sabuwa, mude asaninmu Shalele Bata taba Zuwa shopping da Yan Sanda ba Ko
fans🤔
Zaku samu amsoshin ku Zuwa jibi insha Allah, gobe babu posting 🤗 ranar hutu ce, Nima
hutawa zanyi inyi karatun novel Kamar kowa ehe😃😃😃
Zan huta na kwana daya, muhadu jibin kawai my fan's 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 ngd sosai
✍🏻
Amnah El
💕SHALELAN BABA💕
        (Romance)
29&30
Tana shiga dakin dakuka baba tace subhanallah yata keda wa daga fitarki yanzu?
Jikinta tafada cikin kuka tace baba watace afalo ina fita ta mareni wai tataba
ganina nayi mata wulaqanci
Baba tasa hannu tafara bubbuga bayanta kamar qaramar yarinya kiyi hakuri budurwar
haneef ce ,kina can part dinsa tazo dazu
Baqin ciki goma da ashirin ya kamata ,lokaci daya taji batasan ta,daga kukan mari
sai aka wuce Dana kishi(😂)
********
Zama yayi aqasan kafet din dake malale afalonsa yadafe kansaP,su mata akoda yaushe
inde suka hadu su biyu tofa ransu bayayin fari harsai sun saka mutum cikin
damuwa ,yanzu ita wannan banda Neman fitina me wannan qanqanuwar yarinyar zatayi
mata hartayi mata irin wannan hukuncin ?ai marin yayi mata yawa irin haka ai sai
yataba lafiyarta(😃)
Kuma koba wannan bama ai shi duka kangarar da yara yake,bawai ya shiryasu ba
Ledar hannunsa ya kallah ,yanzu damuwarsa daya tayaya ma zai fuskanceta yabata
wannan abin nasu🤣?
Shiya koreta saboda ta wanke masa gajeren wando ,yanzu yaje yasiyo mata
brezia ,shikuma ayaya yake kenan ?
Allah yasoshi bai futo fili yabaiyana dalilin dayasa yace tatafi ba
Dakinsa yashiga da ledar yaboyeta,daga nan yashige toilet domin watsa ruwa
******
Washe gari yana fita aiki shalele taje tagyara masa part dinsa sosai sai qamshi
yake da daukar ido,tadawo daki tayi zamanta tana jiran yadawo taje ta tambayeshi
maganar karatu
********
Yana tsaka da aiki wayarsa tayi ringing, new number yagani ,baiyi picking ba ya
ajiyeta yaci gaba da abinda yake
Aka sake kira ,yayi rejecting ,bai amsa kiran number dabai saniba ,akaro na uku da
aka sake kira cikin masifa yace wai waye?
Hairat is my name
Haneef nakiraka kana cemin ya akai ?sai wani abu yafaru ne sannan zan kiraka ?
Am dan Allah kinga hairat yanzu I'm very busy ,kit yakashe wayarsa
Gaskiyane ,idan yasan bayasan kiran meyasa zasu bata Katin? Cikin bacin rai take
jijjiga kai tana cewa gaskiya ne,gaskiya ne
Safah ce takawo masa abinci,, ko kallan hajara batayiba tayi cikin dakinsu, ita
Dama ta tsani wannan matar wallahi tafison anty hairat , ita Kuma Samah San hajara
take 🤣
Ahankali yasa hannu zai dauki spoon yafara cin abincin, hajara tayi sauri ta riqe
haannunsa
Haba my Haneef Ina zaune? Kawo nayi saving dinka mana
Kallanta yayi, yasake kallan hannunsa data riqe Ahankali yace waike wacce irin
mashirmaciya ne ce?
Sakemin hannu
To laifi ne danna riqe hannunka?
Jikinka na riqe?
Tsaki yayi yagirgirza kansa sannan yazare hannunsa daga nata yace mummunan tunani
daga mummunar Mata
Bata sake cewa komai ba tayi cikin data sauka, Shima cikin nutsuwa yafara cin
abincin sa
Shalele da baba Hanne suka futo zasu Dora abincin dare, suna Bude kofar sukaga
hajara ta futo da qatuwar truly dinta
Sai suka dakata daga Nan bakin kofa
Haneef na ganin hajara da wannan uwar jaka yatashi ya nufeta, bece Mata komai ba
yakama jakar ya riqe
Cikin tsananin masifa tace kaga Haneef kasakar min jakata, wallahi yau yau dinnan
gidanmu zan kwana
Afili yace hajara me kike nufi ne? Damafa Naga jakar tayi Miki nauyi ne shine zan
Kai Miki ita bakin gate 🤭🤭🤣
Shima murmushi yayi yazauna Yana shan lemo, abincin dabai qarasa ciba Kenan yatashi
yayi part dinsa, hajara ta cika damuwa da yawa wallahi 🤣
********
Saida suka gama shan dariyarsu sannan shalele tace baba dama haka yake?
Ai inde haneef ne zaiyi yafi haka ,itama narasa dalilin bin saurayi gidansu,hakan
ba mutuncin mace bane ga me hankali
Tashi sukai suka shiga kitchen, cikin ranta tana tunani yaushe ne lesson teacher
din zaizo ?tayaya zataje ta tambayeshi ?
Tana wannan tunanin baba tace kinga wannan kunun gyadar karbi kiyi da kanki yau
nagani
Yauwa baba kullum saikin dama kunun gyada wai waye yakesha ?Alhaji ne?
Shiru tayi tana tunani ,kota karba ne ?wannan ce kawai hanya mafi sauqi dazata
kaita gareshi
Cikin kunya tace to baba ki aikeni mana
Zubawa tayi ajug tasaka mata akan try da qananun kofuna ,tace to dauki kije yata
********
Kadan kadan gabanta yake faduwa harta tura kofar falon nasa ahankali tashiga
Adede lokacin yayi shirin motsa jiki ,dagashi sai farar singlet da gajeren wando 🤭🤣
Sau daya ta kalleshi tayi sauri tasauke idonta Qasa
Bata taba ganin namiji azahiri ba ahaka saide ko yan ball kokuma a TV
Wannan wanne irin jiki gareshi duk a mummurde ?kalli qirjinsa duk gashi
Lokaci daya taji tsoro duk ta diririce ,ita kuwa meyakaita San wannan qaton ?Ina
zata kaishi?
Bece mata komai ba yazauna a kujerar ,itama ahankali ta tsugunna agabansa tafara
zuba masa kunun acikin cup (🤭to ita kuma wannan me za'ace mata kenan ?)
Yana kallanta yasaka hannu ya karbi kunun ,ahankali yafurta "thank you so much"
(Tab gaskiya shalele kinyi sa'ah yau Haneef shazali ne dakansa yake gode miki😃)
Zama tayi aqasan kujerar shikuma yana kai azaune,yana satar kallanta Qasa Qasa
Wasa take da yatsun hannunta ,cikin ransa yace masha Allah dogaye dasu
Yar yarinya da ita me hankali hartasan takawowa babba abu tazuba masa da kanta
🤣🤣
Yaga tazauna bata tafiba ,shikuma dai bazai koretaba ,inda zataci gaba da zamama
anan beqi su tabbata ahakanba🙈
Ganin baida niyyar yimata magana cikin ranta tace maganina kenan ai da shegen cusa
kai 🤣🤣qilama ya gane sansa nake shiyasa yake manna min🤣
Batace masa komaiba tatashi tafice,kenan shine zaiyi mata karatun ?to Allah yasa de
yasaka kayansa kafin tadawo🤣🤣
Tana zuwa part din Momy ko kallan kitchen batayiba tashige dakinsu ta dauko
littafin nata tatafi,baba hanne kawai sai gilmawarta tagani da littafi ahannu tayi
murmushi tadaga hannunta sama Allah kasa abinda nake tunani yazama gaskiya,tacigaba
da aikinta
Tana komawa falon nasa, taganshi da baqar jallabiya ,ahankali tasaki ajiyar
zuciya ,taje gabansa tamiqa masa littafin tace gashi
Karba yayi yabude ya dudduba sannan shima yadawo kasa yazauna yana fuskantarta
Cikin qwarewa yakeyi mata explain din komai ,yanayi yana Watso mata tambayoyi Tana
bashi amsa ,suna karatu yana nazarin yarinyar
Har suka gama karatun bata kalleshi ba ,tatashi zata tafi yace "kinga"
Tsayawa tayi shikuma yashige dakinsa,yanzu ne yakamata yabata wannan abun nasu🤣🤣
Yes ita
Tasaki murmushi tasa hannu zata bude yayi sauri yace no kibarshi idan kinje ciki
kya duba
Yana dagawa yace shazali Allah yasa de baka manta da maganar taron nanba gobe
Taron da za'ayi a Russia mana na qarawa juna sani dakuma habbaka harkar
kasuwanci,kada kacemin ka manta
Kansa yashafa yace Abbas wallahi na manta
,kawai nahakura bazan samu zuwaba
Abbas banyi visa ba,yaushe zan samu viza ayau zuwa gobe?
Haba shazali meyasa kacika damuwa ne ?waya daya zakai kayi magana zance
yawuce,nidama zan fadama ne nariga Dana tura musu sunayen mu ,sun tanaji hotels da
abubuwan daya dace,kuma kada ka manta kowa da matarsa zaije idan bakada ita saikaje
da budurwarka
Budurwa Abbas😳
Yes haka qa'idar take ,menene abin damuwa shazali dama kowa ya matsu yaga yarinyar
dazaka Aura, kaga shikkenan saiku tafi tare ,nima daga nan zan dauki matata
Dan Allah karkace komai shazali saimun hadu ,qit yakashe wayarsa
********
Tana zuwa dakinsutafara duba ledar hannunta ,brezia ce aciki masu kyau,kai sajida
da jaraba take saida ta biyota dashi kenan🤣🤣amma ina tasamu kudin dazata siyo
wannan ?dan daga gani kasan zasuyi tsada
Baba tace kai amma sunyi kyau sosai yata,yauwa baba bani aron wayarki nakirata nayi
mata godia🙆🏻🤭
Sajida na dagawa tace mata sis naga saqo nagode,gaskiya sunyi kyau kuma kamar kin
gwadani wallahi zasumin Dede
Menake nufi koke me kike nufi ?ai dama nafada miki abunnan gasu nasiyo mana daga
mkrnta kikaqi karba kisa
Cikin daria sajida tace oho muku wayasani ko shima gani yayi suna tsone masa ido ?🤣
😃
Wayyo Allah itakam yau tashiga uku,🙆🏻da wanne ido zata kalleshi?
Baba hanne tayi murmushi dan tagama jin komai,dama tasan yaran nan kamarfa sunfada
son junansu,inba hakaba shi meyasa zai siyo mata idan ba sonta yakeba?
Baba tayi daria tace to ayi hakuri mana tunda anriga ansiyo ai sai kisa 😂
aranar haka tawuni adaki ,taqi yarda tafuto danma kada taganshi
********
Washe gari tunda safe yayi report a office cewa zaitafi Russia wajan taro na tsawon
kwana uku
Ajmal yayiwa waya yasanar dashi komai, ajmal yace to ai bawani abin damuwa bane,ni
ina ganin kawai kaje kadauki Hairat kutafi,dan tadanfi hajara wayewa
Sannan ita tanaji da tashen boko, nakega bazaka samu matsala da itaba
Eh nima abinda nake tunani kenan, shikkenan duk yanda ake ciki zakaji
Daga haka sukai Sallama yawuce gidansu hairat ,yau saboda yana sauri dakansa yake
driving dinsa🤣🤣🤣
Yana zuwa gidansu hairat yatura maigadi yayi masa magana da ita
Aikuwa tanaji ance haneef ne tafuto,dama datasu yakashe mata waya rannan😂
Daqyar Kamar anmasa dole yace am dama zaki rakani wajan wani taro ne
Wato duk da baka nemeniba ,sai yanzu da buqatarka tatashi zaka nemeni,?wato zakaje
dani taro danna rufama asiri😂
Katseshi tayi,Malam kajuya katafi babu inda zani ,kaje wulaqancinka ya nema ma wata
Haushi yaji dabai karbi number hajara ba ,yanzu dolensa yaje gidan baida wani zabi
Yana zuwa gidansu kuwa aka kaishi falo ,hajara tafuto, ta tsaya akansa takama qugu
tariqe
Shima tsaye yatashi yace hajara akwai inda nakesan ki rakanine
Nice zanma rakiya haneef? Ina zakaje da mummunar mata?Aida kunya ,kaje de ka nemi
sarauniyar kyau ta duniya😃
Da bacin rai yataho gida ,ko Neman ajmal baiyiba bare yasanar dashi abinda yake
faruwa 🤣🤣
Part dinsa yaje yadauki kayansa ,yawuce part dinsu Momy yayi mata Sallama itada
daddy
Haba shazali ,dan Allah karkace komai,danni harna Riga nasanar da friend's dinmu
cewa zakazo mana da matar dazaka aura😳
Acikin gida kuwa shalele suna kitchen itada baba ,tace baba nagaji zanje daki
nahuta,baba tace to yata Dan Allah dauki wannan towel din kidan shanya min shi akan
fulawa,saikije ki kwanta
Tana futowa adede kofar lokakcin Kuma Samah takawo kai itama
Cikin masifa samah ta fardo rigar jikinta tace nikike fadawa magana ?wacece ke ?Yar
wacece ke dazakimin rashin kunya ?
Cikin fishi shalele ta fizge jikinta tace bansaniba kiyi abinda zakiyi ,tafuto
harabar gidan cikin bacin rai
Ahankali yatako yazo gabanta ,yasaka hannu yabude mata mota dakansa (tab matsayi🤣)
Shima yagane hakan,lokaci daya yasha kunu ya tamke fuska cikin Qasa Qasa da murya
yace "shiga mota mutafi"
Yafada mata hakanne saboda yana tsoron itama kada yace tarakashi tace bazata
ba ,dan haka yasha kunu yace tashiga sutafi
Ganin babu alamar wasa a fuskarsa yasa babu musu tashiga ,yarufe ,sannan ya zagaya
yaja motar sukabar gidan
To masu korafi banyi typing ba jiya shikkenan de magana ta qare gashi har yau din
tazo 😃
Tunda nafara rubuta littafin nan bantaba   fashin turo mukuba,ai yakamata nima amin
azuri,na kwana daya de
Nidama namuku uzuri tunda nasan soyaiyarku ga SHALELAN BABA ne yasa kukai hakan
Sharhi ,comment,share ,dan Allah karku manta🙏🏻
Writing by Amnah El
31&32
Juyo da kansa yayi ya kalleta yaga sai cika take tana batsewa ,toya zai mata ?yasan
bacin ran baiwuce tace yadaukota daga gida batasan inda zasuba ,idan kuwa ya
kuskura yayi mata magana tace yamaidata gida tofa shi shikkenan tasa taqare dan
baisan kuma wazai kamaba🤣
Kai tsaye wajan passport sukaje ,yanayin parking ya kalleta yace "muje"
Shima bece mata komai ba sai zagayowa dayayi side din datake yabude mata kofar
motar,ganin da gaske yake yasa ta warware dankwalin kaanta tayafashi ,dukda beje
mata ko'inaba
Tun kafin sushiga cikin wajan taga mutane sai gaidasu suke
Suna shiga cikin office dinkuwa dasauri ma'aikatan dakansu suka tashi suka basu
abin zama
Abinka da manyan mutaje,nan take yadauki kafa daya yadora akan daya ,sabanin ita
datai zamanta normal
Ahankali suka bashi hannu suka gaisa,sannan yace akwai tafiyar da zamuyi ne very
important, but batada passport
Tafiya zasuyi ?ina zai kaita ?aikuwa bari su fice daga nan ta tambayeshi
Haba yallabai haneef,ai yanzu za'ayi mata, photon ta suka dauka,nan take suka fara
yimata
Shekaru fa
Tafada masa komai ,yabata wani Biro dayake daure da wata na'ura yace tazo tayi sign
Sannan yadauko ATM card dinsa yabasu,suka saka cikin p.o.s dinsu ,dakansa ya karba
yacike musu komai har adadin kudin sannan yazare abinsa
Fara'ar dataga sunayi kadai ya tabbatar mata da cewa kudin daya basu ya wuce Qa'ida
"Unguwa"
Shiru tayi ta rabu dashi ,basu tsaya ko inaba sai wajan saloon, yana tsayawa ya
kalleta yace "futo"
Tana ganinsa tafara fara'ah ,itade shalele aranta tace ikon Allah shi ansanshi
ako'ina kenan
Gefe daya suka koma yayi mata bayanin komai ,sannan ya dubeni yace kije,shikuma
yafice
Zaije yakai passport's dinsu wajan visa dakuma nema musu ticket din jirgin dazai
tashi anjima
Gyaran gashi tafarayi sannan ,sosai aka gyara matashi sai qyalli yake,ta nade
matashi abaya yayi donut
Sannan sukaje wajan kwalliya ,ta tsantsara mata kwalliya ,lokaci daya tasauya kai
bazakace shalelan baba ta qauyen kuje kaganiba🤣dan qaramin lips dinta bata cika
mata janbaki ba ,kawai pink din jambaki tasaka mata shima kadan
Alokacin yadawo ,ma'aikatan suka sanar dashi cewa suna ciki basu gamaba
Aciki kuwa wajan kaya suka shiga ,matar tayi shiru tana tunanin wanne kaya oga
yasaka
Jijjiga kai tayi bayan tagama tuno kalar suit din datake jikinsa ,milk colour
Tadauki doguwar Riga fitet gwon me kyau ,rigar batada ado sosai sai dutsina dake
jikinta farare masu qyalli,kafadar rigar ayanke take ,irin me bulalliyar kafadar
nan ,tabata tasaka ,aikuwa Riga tazauna mata sosai ,musanman hips dinta yabada
tashi gudunmawar ,dan kwalin rigar babba ne danhaka tayi mata rolling dashi
Wow gaskiya wannan wanka koni nayaba ,takalmi tabata me tudu tasaka ,da Yar qaramar
jaka ,suka futo
Yana aikin zagaye falon sukazo suka sameshi,matar tace yallabai shazali we are
finish
Yana juyowa yaganta lokaci daya gabansa yafadi ,kasa dauke ido yayi akanta ,matar
ta kalleshi ,ta kalli shalele ,gaskiya ya'iya zabe,sunyi mutuqar dacewa da juna
Gyaran murya tayi ,dasauri ya kalleta ,yace sorry fa ,yabats ATM dinsa suka
saka,dakansa yatura musu kudin
Sannan yajuyo ya fuskanci shalele datake tsaye tana kallan ikon Allah, su Kansu
maaikatan wajan sunyi bala'in birgesu
Sake kallansa tayi ,taga yakafe mata idonsa,ahankali ta Dora hannunta akan
nasa,lokaci daya suka karbi wani saqo daya ziyarci cikin jikinsu
Hannta Yakama suka fita ,yabude mata motar dakansa tashige sannan yaja suka
tafi ,suna tafiya yadauko wayarsa yayi dialling number Anty Jidda, tana picking
yace Anty zamu danyi tafiya ne
Sarai tagane inda zancensa ya dosa ,yafuto fili yace da haneefa muka tafi,shine
bazai iyaba,gaskiya haneefa saitayi da gaske inma auren wannan yaron tayi kafin ta
saitashi
Anty zamuje Russia ,wajan wani taro ,kwana uku kacal Anty nah
Innalillah...haneef zaka dauki yata kutafi wata uwa duniya har tsawon kwana uku
amma kanacemin kacal
Wanne irin kacal
To Anty yaza'ayi
Yanda za'ai kawai kadawomin da yata
Nikake cewa amisali?babu wani misali ,agaske,inna yankatanka ,meyasa bazaka tafi
dasuba
Kuma shi abinda yatashi zuwa sai yazo yasauka akan yata
Wayyo Allah Anty ,zaki sani ciwon kai ,yanzu ina driving zamu qarasa Airport
bye ,yakashe wayarsa
Tana wannan tunanin taji yaana magana da saminu akan yazo yatafi da wannan motar
Suna qarasawa cikin Airport din suka fita ,jakarsa kadai yadauka ahannu sai
passport's dinsu
Suka tsaya saminu yazo wajan, shide sai kallanta yake,wannan ba me aikin yallaabai
bace?
Haka de yakarbi key din motar ,sukuma sukai ciki
Basu Dade da zamaba jirginsu yatashi,itace agefen window, shikuma yana gefe yadauki
jarida yana kallo kamar ba acikin jirgi yakeba
Ta leqa ta kalli window, taga gajimaren nan sun keta taciki sunyi samansa ,tadawo
da kanta gefe cikin tsoro
Yana kallanta ta gefen idonsa ,yayi dan qaramin murmushi, yasaka hannu yadanna wani
abu aqasan window din nan da nan jikin window din yayi duhu
TV din dake jikin kujerar gaabansu ya kunna mata ,sannan yamaida hankalinsa kan
jarida kamar ba shiba
Kallansa tayi ,takawar dakai,ina ita ina wani kallo ana wannan halin,kafarka daya
aduniya daya alahira 😃
                     ai saide adduah
********
Wannan karon da Yar qaramar jaka tazo ,tayi nocking falon nasu
Samah da Safah ne azaune afalon ,samah sai kumburi take akan abinda yafaru
tsakaninta da shalele
Hakan yasa Safah tabude kofar,da hajara tayi tozali ,to kunsan dama tsakanin nasu
       😃 tsaneta
ba dadita
Samah ce ko Safah?
Safah tace Samah ce ,tasan idan tace safah ce zata raina mata hankali ,amma samah
datake da masifa ,yanzu za'a zauna lafiya
Tace OK ,ina yayanku ?
Murmushi tayi,wallahi kuwa ,Yaya anacan sararin samaniya yanzu ,🤣,saide kiyi hakuri
dabai sanar dake qasar dazai tafi ba ,may be yana fadawa mutane masu muhinmanci ne
awajansa
Tana gama fadar haka ta rufe kofar ,hajara tace wannan yarinyar karya takemin ,ba
samah bace ,safah ce,dukda samah tanada masifa ai tana sona
Ko sake nocking batayiba taja Jakarta takoma gida ,dama dan mamanta ta matsa matane
akan tazo tabishi ko hakan zaisa su qara son juna 😃
********
Malam yahai katemaka ka kiramin wannan yaron dayasa aka rufeni,na nemi yafiyar
shalele awaajansa
Sannan inji Yaya Dana yake?
                                                                      😱
Ina aududu na,tunda suka sakani adakin duhun nan har yanzu idanun babubana
gani,bana ganin komai
Malaam yahai yace marka kiyi hakuri,amma wannan yaron likita dakike gani dan boko
ne ,bazaima kula kiba ,yafi karfinki marka
Fashewa tayi da kuka ,innalillahi...wai yanzu ni marka nice bana gani nice awannan
hali
Yanzu Malam yahai dan Allah kakaini gidanmu wajan murja ,ko zata dinga temaka
min,zamana anan gidan nikadai bazai iyuba,babu Malam surajo,babu shalele,babu
Aududu
Rayuwar kenan😢
********
Jirginsu na sauka ,suka futo a gajiye ,tafishi galabaita saboda akwai nisa,Abbas
yana ganinsu yaqaraso suka gaisa ,haneef ya harareshi
Murmushi tayi,ta sunkuyar dakanta Qasa ,uncle dayake babba ina zaiyi wata shagwaba
Motar suka shiga ,suka wuce hotel din da ake saukar baqi
Motarsu na tsayawa matar Abbas ta qaraso dasauri cikin fara'ah ta rungume shalele
Sannuku da zuwa ,sannunku,sai da suka gaisa da shazali sannan Abbas yace kuje ciki
sweety tahuta gamunan zuwa muma
Ciki suka shiga itada shalele, zama sukai agefen gadon,dakin yayi kyau sosai babu
tarkace dayawa kamar de yanda hotel suke
Tace sannunku
Dadi taji,lokaci daya taji son yarinyar, daga gani badata raini,tace sunana
zainab,mijina kuma Abbas
Abokin haneef dinki ne ,suna kasuwanci tare🤣🤣
Sunana haneefa
Wow nice ,wato shazali saida yajemo kyakykyawa kuma me irin sunansa sannan yafara
soyaiya,shiyasa yadade bai samu budurwa ba
Kamar shazali ,na tabbata kallan dayake binki dashi naso ne,tunda kikaga ya zabeki
yadaukoki yataho nan dake to yana sanki ne,bazai iyu ya nunawa abokan kasuwancinsa
wata wadda ba ita zai Aura ba
Kiyi kokari kiga kin mallake zuciyarsa,tahakanne zaki tabbatar da abin danake fada
miki
Inaji awajan mijina yanmata dayawa suna sonsa ,suna kai masa hari ,harkokinsa ne
kawai dasuke dayawa yasa baya samun lokacin saurarensu
Bude kofar akayi ,Abbas ne da shazali ,Abbas yace mata kenan ,memakon kikaita
dakinsu tayi wanka tahuta a a ,sai kuka baje kolin fira
Anty Zeey tace a a to itama ai gara tayi wankan kawai dakunci abinci saita kwanta
tahuta
Abbas yatashi yabishi wajan kofar ,kallansa yayi yace abbs yaza'ayi ne
Kamarya ?
Ina nufin tazauna su kwana da zainab, saimu tafi dakai dayan dakin
Haba Abbas...
Yadubi zainab yace ke zainab rakata dakin su, Anty Zeey tayi murmushi takama hannun
shalele da takeaway dinsu na abinci suka tafi dakin da aka tanada domin su
********
Momy tace a a to ina yarinyar nan zata shiga ?Tun safe ana nemanta
Safah tace Momy samah tacemin sunyi fada dasafe,saide in zuciya tayi tatafi garinsu
Ta kalli baba hanne tace baba bari nakira Jidda naji ko can tatafi
Ana kiran Anty Jidda Momy tace Jidda yarinyar nan kuwa tana gidanki?tun safe muke
nemanta bamu gantaba
Tuni Anty Jidda tadau haske😃hakan yana nufin babu sanin yan gidan ya dauketa kenan
To alhamdlh tunda tana wajan naki,wai fada sukai itada samah shine tayi fishi
tataho nan wajan naki
Kuma yanzu Jidda komai na duniya ba dan hakuri bane ?🤣
Idan taqi dawowa shi kuma yana dawowa daga tafiyar nan zai sani agaba ince kidawo
da ita
A a Jidda yanzun ki barta,idan haneef din yadawo itama saida dawo,tunda shima
yanzun baya nan
Wayar takalla tasake daria kai,Momy kenan,wani bikin sai agidan momu kina zaune
agida ana wani budirin baki saaniba😃
Momy ta kalli baba hanne tace to baba kinji tana gidan Jidda
********
Suna shiga dakin Zeey tabata abincin nasu ,tamatso kusa da ita tayi mata rada
akunne
Ki kwantar da hankalinki qanwata ,nasan halinsa babu abinda zai miki,tana fada mata
hakan tace musu saida safe tafice
Yana ganin fitar Zeey ya kalleta ,duk tatakure kanta ,girgiza kansa kawai yayi
cikin ransa yace yarinta kenan🤣
Bece mata komai ba yafara cire suit dinsa ,yajefata kan gadon ,niktile dinma ya
cireshi ,agogon hannunsa ya kunce ya ajiyeshi daga gefe yakalleta atsaye ita bata
zaunaba ita bata fitaba
"Idan kingama tsewar zaki Iya zama,nizanyi alwala nayi sallah"
Yana fada mata haka yashige toilet, tabi bayansa da kallo tasaki murmushi wannan
mutumin yana birgeta ,zama tayi agefen gadon tana jira yafuto itama tashiga tayo
alwala,tagumi tayi hannu bibbiyu😱 tana tunanin yanda zata kwana dashi daki daya
Sanarwa
(Wannan sanarwar ta fan's dinane na Facebook kadai,har yanzu ban bude group nawa
nakaina a facebook ba
Ku fahimta niba admin bace akowanne group na Facebook, nima member ce kamar yanda
kuke members aciki
Idan naturo muku littafi bazai iyu Ku ganshi alokacin Dana turoba,dole sai admin
sungani saannan sukuma su sakeshi,kowa yagani ,dafatan kun fahimceni ,ina jin dadin
comment dinku sosai wallahi hakan yana qaramin qwarin gwiwa akan yin typing kullum
nagode🙏🏻🙏🏻
Writing by Amnah El
33&34
Tana nan zaune harya futo daga toilet din, sannan tasaki ajiyar zuciya
Kallanta yayi, "kitashi kiyi alwaya ayi sallah ko"
Ga mamakinsa saiya tsinci kansa da jiranta, haka yatsaya Saida tafuto sannan yajasu
sallar
Saida suka Rama duk sallolin dake kansu sannan yaita karanta musu addu'oi suka
shafa saika rantse wasu sabin amare ne🤣
Dubanta yayi yasaki Dan qaramin murmushi,haka kawai yakejin wani irin nishadi na
shigarsa, Anya kuwa Ajmal ba gaskiya yafada masa ba?gaba daya ko tunanin gida ma
bayayi tunda yaganshi tareda ita
Ajiyar zuciya yasauke
kinajin yunwa ko?
Wani yarrr yaji ajikinsa, Allah yaso sallah suka idar, Toda ansamu matsala gaskiya🤣
Abincin yadauko musu yasaka musu agaba, shinkafa ce wadda taji kori, da gasashiyar
kaza aciki
Yakalleta cikin maganarsa ta sigar rada yace Mata taso kici Abincin
Aikuwa hajiya shalele babu musu ta matso tasaka hannu tafara cin abincinta
(hoo yunwa ba dadi 🤣🤣
)
Tagumi yayi Yana Kallanta, shi baifara ciba, ta kalleshi uncle Kai bakajin yunwa
ne?
Emana sosaima
Ta kalleshi meyasa?
Matsowa yayi dab da ita, Har gabanta yadan fadi, jikinsa Yana gugar nata, atsorace
ta kalleshi
Shima yaga Hakan kawai saiya share, yasaka hannunsa acikin Abincin ya karyo kazar
babba yakai Mata bakinta
Yanda ya matso tan Kamar zaiyi Mata kiss, ahankali yace "eat"
Jikinta yayi sanyi, kasala ta Kamata, ta kalleshi, Shima ya Kalle ta yace ci mana
Yanda takecin abincinma kadai abin kallo ne, yazubawa pink lips dinta ido, komai
nata me kyaune
Tace to
Saida yaga shigarta toilet din sannan yasaki ajiyar zuciya, meyake damunkane
shazali? Wadannan abubuwan dayakeji na menene?
Karfa maganar Ajmal ta tabbata, Innalillah... How? Wannan qaramar yarinyar? Sannan
ma yar aiki, yar aikinsa
                                                                  😃
Idan yagama tabbatar wa kansa gaskiya, tofa da an dafka abin kunyaAida kunya ma
yatunkari Ajmal da wannan maganar bare Kuma su momy, Kai Allah yasa Bahaka bane
Bama
(to zamu gani de🤣)
Kadan yaci Abincin, yasake tafiya duniyar tunani, daga karshe ma saiya fice daga
Dakin domin yabarta tashirya
Ita kuwa Tana Gama wanka taga babu towel, dube dube tafara sai can taga wata rigar
fara, Jikinta Mai laushi, tadauka tasaka, rigar dukanta iyakarta gwiwarta, hakade
ta Kalli kanta, tasake kallan kanta, Anya kuwa zata Iya fita ahaka?
Saida yadau lokaci sannan yadawo Dakin, Yana shigowa yaga duhu, kunna wutar yayi
yahangota ta makure akarshan gadon,Koda wanne kayan ta kwanta? Basu taho da
kayantaba ko daya
murmushi yayi yasake kashe Mata wutar sannan Shima yashiga toilet yayi wankansa
cikin nutsuwa, jallabiya yasaka yafuto, yadauki fillon dake gefensu yasaka shi
atsakaninsu 🤣sannan ya kwanta batare daya rufaba
Cikin dare yaji sanyi, yaja bargon yaci gaba da baccinsa, itama tana bacci taji
anjanye bargon, dasauri ta matso tasake shigewa ciki
Da asuba, shine yafara farkawa, ahankali ya Bude idonsa yaganta, sai yanzuma yatuna
tare suke, fillon dayasa atsakaninsu Yana nan, tana kwance tana baccinta, gashin
kanta duk ya barbaje
Sunkuyawa yayi zaiyi kissing dinta🙆🏻🙈saiya fasa, yasaka hannu yashafa gashin nata
ahankali sannan yashige toilet yadauro alwala
Kawai saiya share ta yatada sallah, yasan baccin gajiya take saboda Bata sababa
(zakayi bayanine🤣)
Juyi tayi hadeda hamma tabude idonta, sannan ta karanta adduah tatashi daga bacci
Jikinta ta kallah, tashafa Jikinta, aranta yace um uncle baimin komaiba 😃Dama anty
zeey tace bazaimin komaiba
Tatashi tayi alwala tayi sallah sannan tayi wanka tasaka kayan ta na jiya
Saida Gari yayi haske sannan yadawo Dakin da Kaya ahannunsa, yace gashi, kije da
wannan wajan zainab tana jiranki
Saida ta gaisheshi sannan takarbi kayan tafita, tana zuwa daki wajan anty zeey suka
gaaisa, ta kalleta tace dafatan lafiya ko?
Murmushi tayi tace babu komai anty, wallahi baimin komaiba
Tabawa anty zeeey Daria yanda tayi maganr 😁, Sosai zaka Fahimci da gaske take
Shiryawa sukai anan, anty zeey akwai gayu lokaci daya ta sauyawa shalele kamanni
Tayi kyau Sosai acikin doguwar Riga, light blue, harda jakarsu da takalminsu,
takalmin yayi tsini dayawa, tana sakawa tace gaskiya bazan Iya tafiya da wannan
takalmin ba
Kiyi hakuri haneefa haka Zaki zaka, shine yasiyo Miki su, yazakiyi
Haka tasa takalmin tana turo baki gaba, suka zauna suna fira kadan kadan
Sai wajan karfe Tara sannan Abbas yashigo Dakin Shima yasaka suit baqa yayi kyau,
yace ku tashi mutafi
Shalele ta gaidashi ya amsa Mata cikeda fara'ah, ahankali shalele take tafiya anty
zeey ta kamata, Yana harabar hotel din yajuya baya Yana waya sai Daria yake, tana
hangoshi tace kodawa yake waya?
Juyowa yayi yaga sun futo, cak ya tsaida idanunsa akanta, tayi masa kyau Sosai,
tafiyarta ya kallah yasan Dama daqyar zata Iya tafiya dashi
Ahankali Shima yataho Yana fuskantarsu, Saida sukazo dab dashi sannan yayi sallama
awayar yace to anty sai anjima
Babu kunya yasa hannu yakamo hannunta, Abbas ya kalleshi yayi murmushi Kai shazali
Dan duniyane wallahi
Yakalleshi, shazali ni baka fadamin sunan babyn takaba, yasan da biyu yayi masa
wannan maganar saboda kowa yasan cewa shazali bayasan qaramar yarinya
Kafahimta?
Hannunta Yana cikin nasa suka qarasa cikin Mota, zeey na gaba abbas na driving
Itadashi Kuma Abaya, yaqi sakin hannun nata, ahankali yake murzawa, laushi hannun
nata kamar Bata aikin komai shiyasa yaqi saki
Ita kuwa duk wani iri takeji, idan Yana murzawa saitaji wani iri haka ajikinta,
ahankali tafara zare hannunta, Amma saiya sake riqewa
Yajuyo ya kalleta cikin rada yace Mata why?
Kasa tayi da idonta,batace masa komaiba, Shima saiya kawar da kansa zuwa kallan
titi Amma Bai saki hannun nataba, Har motarsu ta tsaya
Su zeey suka fita, mutane damqam a wajan, Yan Nigeria dakuma sauran qasashe turawa,
Kallanta yayi yace Mata "wait"
Dakatawar tayi kuwa yayi sauri yafita ya zagaya yabude Mata motar dakansa, abinda
yayi ba qaramin birge mutanan wajan yayi ba, ita kanta zeey Saida tace gaskiya
yarinyar nan tayi Dace da samun shazali
Kafarta daya tasakko sannan tafuto gaba daya, masu camera kuwa me zasuyi dauka, Yan
jarida da sauran gidan TV kasancewar ansanshi bane mu'amala baane da Mata, duk
taron dazaai shi kadai yake zuwa, Amma abin mamaki yau gashi ga budurwa mace sai
Hakan ya birgesu
Hannunsa ya miqa Mata, Saida ta kalleshi sannan tadora nata Akan nasa, yariqeta
suna tafiya ahankali
Sun kusa shiga wajan takalmin Kafarta yagurde kadan, 🤣🤣Allah yasosu hankalin mutane
ba Akan takalminta yake ba😅, a kansu yake
Cikin sauri ya saketa ya tsugunna a gabanta, yakama Kafarta ta Yana dubawa kamar me
neman wani Abu, yadago kansa yace Mata sorry, sannan yakai kafar bakinsa yasakar
Mata wani zazzafan kiss
Zeey de yau tana ganin ikon Allah, takalli shalele ta kalli shazali, gaba daya sun
birgeta🤣
Yan jaridafa ansamu abinda akeso, tun lokacin daya tsugunna suka fara daukarsu
photo
Kamata yayi suka shiga wajan, wajan yatsaru matuka, abinci nan agaban kowa da ruwa
da lemuka
Kamar yanda suka fada haka aka tsara kowanne mutum bibiyu
Cikin kwanciyar hankali aka fara Kiran sunayen mutane suna gabatar da kansu, Har
akazo kansu suma suka fadi nasu😍
Sannan aka fara taron, Wanda suka dauki tsawon awa uku Ana wayarwa damutane Kai
wajan habbaka harkar kasuwancinsu
Kallanta yayi, baya ganin fukarta Sosai, saboda gashin ta daya Dan saqqo yarufe
Mata fuska
Pls kidan janye gashin nan ki, Yana bani tsoro, ya qarasa maganar cikin sigar wasa
Daria yabata, Saida tayi Daria Sosai sannan tasaka hannunta ta janye gashin ta
Text ne yashigo cikin wayarsa yabude "" Shege abokina wato kana zaune Ana gyarama
gashi, gaba daya ka rikicewa yarinya qanqanuwa""
Murmushi yayi, Kai Abbas, abbas bashida damuwa wallahi, kana wajan zamanka Amma
hankalinka Yana Kan wasu🤣
Suna zaune Har aka Gama taron, inda suka yiyyi photuna, kowa sai tayashi murna yake
Akan samun shalele, harda masu cewa sai sunzo biki
Shikuwa Yana amsawa kamar ya manta da maganar iyayensa
Hotel suka koma, tabi zeey dakinsu taqi komawa nasu dakin🤣
Sai can yamma Sosai abbas yashigo sannan tatafi, tabasu waje
Tana shiga Dakin taganshi zaune Yana amsa waya dawata Leda akusa dashi, da Alama
daga office dinsune
Ina zamuje?
Tace eh inaso
Dasauri tatashi, ta cire mayafin kanta, gashin ta ya kallah tayi fakin sai qyalli
yake, tasaka rigar agabansa, sannan tadora mayafin Iya kanta, Shima yasaka tasa
suka fice daga hotel din, Hannunsa Yana cikin nata
Tafiya sukai Sosai akafa Yana nuna Mata wajaje daban daban, wani waje ma daya nuna
nata ruwa Yana futowa ga fulawa masu kyau a wajan, ta kalleshi tace uncle kaimin
photo anan idan munkoma na nunawa sajida da mama
Wace mama?
Tace mama de
Tace nasani
Yace ki tambayeta kiji, zata fada Miki ko ita ko qawarki,🤣🤣 tace masa to
Photon yayi Mata, wani mutum daga gefe Yazo yakarbi wayar yayi musu su biyu, yanda
ya rungumeta ajikinsa akayi musu photon Kai saika rantse Samah da Safah ne🤣🤣
Har dare Suna yawo, daga qarshe sukaje waani shago yasai Mata waya qirar sumsung
Sannan suka dawo, dakansa yasaka Mata wayar acharge sannan sukai sallah sukaci
abinci
Zama tayi shiiru agefen gadon, yaje yadauko wayar dakansa yazauna dab da ita
Yace ga wayarki
Nine yakamata nayi Miki godia, dakika boyoni batare danayi Miki bayaniba
Kallansa tayi, babu komai uncle, yanzu zan Iya Kiran waya?
Wazaaki Kira?
Uncle Bilal
Lokaci daya ransa yabaci, yanzu yanzu yasiya Mata wayar Amma tana cewa zata Kira
wani?
Waye Bilal? (um kaji manya wato Waye Bilal Bama Waye uncle Bilal ba 🤣🤣)
Babanki?
Tace eh, shine babana, banda kowa saishi, mamata tarasu babana yarasu, shine gatana
banida wani uba saishi saikuma anty jidda
Sunana haneefa suraj daga kuje,..... Tsaf tabashi labarinta kaf Bata boye masa
komai ba
Sosai ya tausaya Mata no wonder take aiki, yasan cewa ayanda tabashi labarin
babanta babu yanda za'ayi yabarta tatafi aikatau wani gida
Ajiyar zuciya yasauke, kiyi hakuri, insha Allah komai zai wuce
Nasan kuje, akwai wata yar'uwarmu acan, Amma tarasu da dadewa
Kwanaki ma nawuce ta Garin, munje gwagwalada Akan aikin company na da akeyi acan
Tace acikin Mota zankai babana asbiti na tsaida motarku ku rage mana hanya kuka
tsaya Amma Baka futo ba ka Watso min kudi kuka tafi, da wannan kudin nayi amfaani
wajan biyan kudin aikin da aka yiwa babana
Murmushi tayi tace wallahi uncle babu komai, ni gode makama nayi, da Baka bani
kudinba Aida bansan Yaya zanyi ba
Kidena maganar kudin nan, nawa yake ma? Pls kin hakura?
Uncle nahakura fa
Yace toshikkenan
Bari nakoya Miki yanda zakiyi amfaani da ita, matsowa yayi kusa da ita, Har jikinsu
yahadu sannan yafara koya Mata wayar, tun suna zaune Har suka dawo tsakiyar gadon
Eh nagane, nan danan tafara yi masa bayanin abinda yakoya Mata, yazubawa Dan
qaramin bakinta ido
Tana bayanin Yana kusantota, shiru tayi tazuba masa ido
Ahankali yasaka hannu ya janye Mata gashinta, ya Matso da fuskarsa dab da Tata,
burinsa kawai ya sumbaci wannan bakin nata
(Haji shazalinmu🤣🤣🤣)
Baidawo dakinba Saida tayi bacci, sannan yasaka musu fillo yauma, ya kwanta Shima,
tunani yafaara Akan yarinyar nan, yanzu Kam zuwa wannan lokaci haqiqa ya tabbatarwa
da kansu son yarinyar ya Kamashi
Yanzu Yaya zaiyi dasu momy? Tayaya zai fuskancesu da wannan maganar?
Cikin dare fillo yayi gefe, babu Wanda yasani atsakaninsu, ga sanyin Gari Gana esi,
kowa najin sanyi, hakanne yasa suka Matso jikin juna
Dumin dayaji ajikinta ne yasa yasake janyota jikinsa ya rungume ta Sosai, itama
batasan lokacin data sake rungume Shiba, sukaci gaba da baccinsu cikin Jin dadi 🤣
********
Washe Gari suna farkawa da asuba sukagansu manne da juna, Dasauri suka rabu, kunya
yakamata, shikuwa Yama kasa kallan ta, haka yashige toilet, baiyi alwalaba Saida
yayi wanka🤣
********
Mami yakamata kidena wannan tunanin haaka, idan kina tunani Ina kikeso Musa kanmu
ne?
Afrah kalli wannan yarinyar da aka nuna atv yanzu daga gidan talavijin na Russia
TV din ta kallah, taga sunyi kama da yarinyar Sosai, haka babu abinda zasu fadawa
juna, wanima idan yaganta yaga haneefan zaiyi zatan yanbiyu ne
Ajiyar zuciya tayi, Mami kidena wannan tunanin, haneefa datake kuje mezai kaita
wata qasa?
Afrah bakisan wannan Wanda yariqe Mata hannun ba?
To haneef ne Yaron wajan momy, cousin sister dinmu nida zainab mahaifiyar haneefa
Oh ashe shine Mami, ai bansanshiba kinsan kwanaki danaje Nigeria 🇳🇬, dahar zanje
gidan, tokuma naje shopping super Market, wata yar'iska tabatamin rai, da niyyata
insa yansandan daddy suyi Mata duka kuma Dai saina shareta
 (mekaratu dafatan kungane labarin hajara 🤣🤣, aikuwa wallahi afrah kindauki alhakin
              😃
Marin shalele )
Afrah tun lokacin Dana Kira Malam surajo yacemin zai kawota Har yanzu idan
naakirashi wayar Bata shiga, Amma dazaran kungama bikin candy naku, dole zanje
Garin kuje dakaina indauko haneefa
Idan kuwa bansameta ba, to tabbas wannan yarinyar Dana gani tareda haneef din momy
to haneefanmu ce, dole inje gidan momy nasamu haneef yanemomin haneefa (tab shazali
kaga ta kanka🤭🙆🏻🤣)
Afrah tace to Mami Allah yakaimu, tashi muje daki ki kwanta kihuta
********
Tana zaune a dakinta tana kallo, kamar yanda tasaba bibiyar al'amuransa yauma haka,
tazauna tasaka TV agaba tana kallo, tunda taji ance yatafi Russian 🇷🇺, tadinga dube
duben tashoshin dazataga an Nuna shi, kamar wasa kuwa tana cikin duben taga wata
Tasha tana haska haneef shazali da wata yarinya
Tuni tatashi zaune, dede lokacin daya kama kafar yarinyar Yana kissing
Ana hasko idon yarinyar tace kaiiiii wannan ai haneefa ce, Waye yahadata da haneef
shazali? A'ina ta sanshi?
Cikin sauri tadau wayarta tafara neman number Bilal domin ta fada masa cewa toga
yarsa can awata qasa da wani 🙆🏻🤭
(sorry sady😢)
********
Yau Kam a hotel suka wuni, kamar wasu surukai haka suka zauna a Dakin, ita takasa
sakewa dashi, tana tuno yanayin jiya daya Matso zaiyi kissing dinta
Shikuma Yana tunanin dumin jikinta nayau dayaji
Gaskiya dole ma duk Wanda ya auri yarinyar nan yahuta, dan haka yazama dole shiya
aureta, yarinyar tanada kayan more rayuwa
Haka suka yi shiru shi sai amsa waya yake, ita Kuma tana game da wayarta, Amma kuma
sun kasa kallan juna 🤣
Yauda dare yayi kuwa fita yayi daga Dakin sai can daya dedeci tayi bacci sannan
yadawo
Shima ya kwanta
Washe Gari dasafe sukai shirin tafiya, yauma anty zeey ce tazo Har dakinsu ta
shiryata, doguwar Riga tasaka yar Dubai
Rigar nada fadi, sai mayafi qarami kalar adon dutsinan dake jikin Rigar
Kwalliyar da zeey tayi Mata ta karbeta Sosai, girar nan Tasha gyara
Zaunawa tayi abakin gado, tana daddanna wayarta, ai suna komawa Nigeria 🇳🇬 zata je
Har gidan anty jidda tanunawa sajida
Saide Tarasa dalilin wannan kyauta ta uncle haneef
Shigowa yayi Dakin Shima cikin qananun Kaya, ta daga Kai ta Kalle shi
Sai qamshi yake, yace tashi mutafi, yaje yadauko jakar kayansu, da wadda yasiya
Mata dakuma tasa dayazo da ita
Tashi tayi tsaye, tasake Kallansa Dan gaskiya yayi Mata kyau sosai
Shima tana tashi yazuba Mata ido Yana kallan ta, zuciyarsa na tunzurashi Akan
yasanar da ita abinda yakeji game da ita
Takowa yakeyi ahankali Yana tunkarota, itade tana binsa da kallan mamaki
Yana binta tana yin baya ahaka Har sukaje jikin bangon Dakin
Bece Mata komaiba yasaka hannunsa yakama kyakykyawar fuskarta da duka hannayensa
biyu, yamatso da fuskarta dab da tashi
Ahankali yadora bakinsa Akan nata, yanayi Mata wani irin kiss me zafi, dan qarami
lips dinta yakama yanasha,
Sun dauki tsawon minti biyar ahaka sannan yazare bakinsa daga cikin nata
Tana Bude ido taga idonsa akanta dasauri tayi qasa da kanta
Baisaki fuskarta da hannun nasaba, cikin rada yace "Haneefahhhh... Yaja sunan nata
Yasake Kallanta, cikin rada yace Mata" I really luv you so much, Zaki Iya aure nah
"???
(yau kaam kasa nakasa magana shazali, wallahi ku soye harku qone, Nigeria tana nan
tana jiranku☺)
To dafatan de yanzu kowa yasan matsayin momy da hajiya hafsat dakuma maman shalele
Duk kubiyoni zuwa gobe domin Jin Yaya zata Kaya, Ina yinku Sosai fans
Writing by Amnah El
35&36
Fuskarta ta qwace daga cikin hannunsa tafice daga cikin Dakin dasauri
Shima yabita da kallo, murmushin daya gani a Fuskarta kadai ya gamsar dashi wajan
samun amsarta
Murmushi yayi Shima yabiyo bayanta da jakar kayansu, haka suka futo harabar hotel
din, tana gaba Yana binta Abaya, zeey da abbas suna tsaye awaje suna jiransu, zeey
tace Kai Ina jambakin Dana shafawa yarinyar nan?
Adede lokacin suka qaraso wajan, babu Bata lokaci suka tafi, suna zuwa Airport
jirginsu yatashi zuwa Nigeria
********
Tana samunsa awaya tace Yaya yanzu Naga haneefanka a TV wallahi
Yaya wallahi yanzu naganta da haneef shazali, suna Russia shida ita
To ita mezai hadata da shazali? Tayaya ma ta sanshi? Kinga sady idan nagama aiki
zanje gidan datake ingani
Toshikkenan Yaya sai ka dawo, Ga Abdallah Yana gaisheka, OK tokishafamin kansa, bye
********
Jirginsu na sauka sukayi sallama dasu zeey, baima yi waya azo daukarsu ba, kawai
taxi yatare musu suka wuce gidan jidda Kai tsaye, alokacin uku saura
Suna zuwa gidan sajida ta rungume ta, sukayi ciki, Shima afalo ya zauna shida anty
jidda, tace mutanan Russia, Yaya taro? Alhmdlh anty, mundawo lafiya, kuma nagode
Sosai
Ba godia zakamin ba haneef, fadamin zakai dalilin dayasa ka dauki yarinyar nan,
haneef meyasa zakai haka? Idan wani ne yadauki yanbiyu zakaji dadi qanina?
Ajiyar zuciya yasauke ya kalleta cikin serious voice yace anty kiyi hakuri nasan
nayi laifi, Amma naje wajan hajara da hairat sunqi yarda mutafi, anty alokacin
Banda zabin daya wuce hakanne, shiyasa nace tashiga Mota mutafi, Amma itama ba'ason
ranta ba, saboda Dana dauketa ma da bacin rai muka tafi,Amma kiyi hakuri, insha
Hakan bazai sake faruwa ba, ki yarda da qaninki anty, bazai yi abinda zai cutar da
'yar kowaba
Anty jidda tace Toshikkenan, Allah yashige mana gaba, Allah kuma yasa kada wannan
labarin ya Isa kunnan Wanda zaice Yana sonta zuwa gaba, domin kuwa bazaiji dadi
macen dayakeso tafita da wani namiji daban qasar wajeba
Anty wacce irin magana kike haka? Dama haneefa akwai Wanda zata aura ne daya wuce
ni? Haba anty, duk da babu abinda yashiga tsakaninmu ai bazan yarda ta auri waniba,
Bayan na dauketa na nunawa Dunia cewa itace wadda zan aura, idan naki aurenta ma ai
sai Allah ya kamani
Dadi yakama anty jidda, tace haneef kana nufin zaka auri haneefa ta?
Zan aureta anty, wannan dalilin nema yasa nabiyo ta wajanki ban wuce gidaba, anty
nasanar dake inason haneefa, itama nafada Mata Ina sonta
Toshikkenan anty, nizan wuce, duk yanda mukai dasu zakiji, to qanina sai anjima
Yana tafiya takira haneefa tazo tazauna agabanta, tabita da kallo
Ahankali tace mama Dan Allah kiyi hakuri, wallahi shine yace nashiga mutafi
Tokuma haneefa danyace Kishiga saiki shiga? Idan yace Kishiga wuta ma Kenan saiki
fada?
Hawaye ne suka zubo Mata zirrr, tace mama kiyi hakuri Dan Allah
Haneefa duk da haneef qanina ne, bazanso ya cutar dakeba, dole zanyi kokari Naga na
qwato Miki yancinki awajansa, yasanar Dani cewa Yana sonki, sannan zaije yafadawa
su momy komai
Dasauri ta kalli anty jidda
Anty jidda tace eh haka yafadamin, kada kidamu kiyi muku adduah insha Allah babu
komai kinji?
Daga Mata Kai tayi, anty jidda tace tashi kitafi, da yamma sai nasa driver ya
maidake
Tana tafiya, anty jidda tadaga hannu ta godewa Allah, wani farin ciki Yana qara
ratsata ratsata, alhmdlh addu'arta ta karbu
Godia tayiwa Allah, yanzu dabasu dawoba me zata fada masa? Tasan da daga yau Zaman
yarinyar yaqare agiidan su, shikuwa Bilal da biyu yayi Mata wannan tambayar domin
ya tabbatar da mgnr sadiya, shin tana wata qasar dinne kokuma tana gida
Anty jidda ta kwala Mata Kira sannan tabata wayar tayi cikin dakinsu tana magana
dashi
Da yamma kuwa anty jidda tasa driver da sajida suka rakata gidan momy
*******
Tunda suka dawo daga Russia yau tsawon kwana biyu Kenan, tadena zuwa gyara masa
daki saide intaga bays gidan zatayi sauri tagyara masa tadawo, Shima anasa bangaren
Bai nemetaba, yasanar da Ajmal komai Shima kuma yadada karfafa masa gwiwa Akan
Hakan, saide Har yanzu tunanin yanda zai fuskanci iyayensa yake da maganar
Kwanansu uku da dawowa tana falo tana goge goge tana Taya baba Hanne, dan gyaran
part din momy Dama baya daga cikin aikinta, kawai yau din ne take Taya baba Hanne
Shigowa yayi cikin Shiri zaiyi tafiya shine zai sanar da momy
Kawai ya ganta tana goge goge, Dasauri ya qaraso wajanta yariqe towel din, meyasa
kike aiki?
Daga masa Kai tayi, ya Matso da bakinsa saitin kunnan ta yace zamu tafi England
yanzu nida Ajmal zamuje kallan gasar premier
Insha Allah idan muka dawo zan sanar dasu momy komai, kinji?
Qaran kofin dasukaji abayansu ne yasa suka kalli wajan dasauri, daya daga cikin
yanbiyu ne, basu gane ko wacece ba acikinsu
Kallan haneefa yayi yace saina dawo OK?
********
Tun lokacin daya tafi, tafara yiwa baba Hanne karatu Sosai, Amma idan tatuna
maganar da uncle yafada Mata sai jikinta yayi sanyi, Tasan cewa rabuwarsu tazo,
yanbiyu kuwa idan sun ganta harara ce take rabasu, Tasan kuma Hakan baya rasa
nasaba da ganinta dasukai afalo itada haneef duk da batasan wacece tagansu ba
acikinsu
Haka take kokarin sharesu
Har suka dawo daga England shida Ajmal, da yamma suka dawo, Bata Samu ganin saba,
sai washe Gari dasafe da akai baqi agidan
Anty fadila da anty iklas ne qannansa dasuke binsa sukazo, sai hidima ake dasu
agida
Yaron anty fadila namiji kyakykyawa dashi taji tana son Yaron, afalo tazuba musu
ido tana kallan su Yaron Yana sakawa haneef ice-cream abaki, sai nishadi suke
Har yamma suka Kai sannan suka tafi, da daddare tana falo tana kallo duk da ba
dabi'arta bane, Shima yashigo falon yazauna
Ruwa tatashi takawo masa, Takoma qasan kafet tazauna Shikuma yanakan kujera,
Kallanta yayi
Daria sukasa gaba dayansu, Safah tafuto falon alokacin zatai kallo
Kallan tuhuma tahau yi musu, yaushe Yaya yafara sakewa masu aiki haka?
Saida ta kalli shalele sannan tace kayi hakuri Yaya Tajuya ciki
Yau Kam ta yarda da maganar Samah, gaskiya Yaya yafara son wannan yarinyar me zubin
fulani
********
Washe Gari yashirya tsaf cikin shirinsa na fita office
Qananun Kaya yasaka dasukai mutuqar karbar jikinsa
Gabansa ne yake faduwa idan yatuna yau yakeson fadawa su momy maganar haneefa
Kai tsaye yatafi part din nasu Yana adduah cikin ransa
Saida yabari suka Gama yin break sannan yakalli momy da daddy yace daddy Dama inaso
zanyi magana daku kafin nawuce office
Dama zan sanar daku ne, nasamu wadda nake so, nida ita muna kaunar junanmu, kuma
nayi Mata alqawarin aure
Mekake fada haka haneef? Tokuma maganar yar abokinafa? Da yar qawar momynku?
Daddy Danaga Dama rashin wadda zan aura ne yasa zaku hadani dasu kuma yanzu nasamu
Lokaci daya idanunsa yacika da qwallah, abinda basu taba ganiba a wajan haneef
Ya kallesu, yace momy daddy, yarinyar nan itace bugun zuciya ta, wallahi idan ban
auretaba mutuwa zanyi
Cikin masifa momy tace Wai Kai haneef ba kada Aiki da anyima Abu saikace zaka mutu
zaka mutu to wallahi wannan Karon saide Allah yaji qanka🤣🤣
Wacece haneefa?
Daddy yace Dan Allah hajiya kiyi shiru yasake kallan shazali yace jeka turomin
yarinyar inyi Mata tambayoyi
Ahankali yatashi yafuta daga falon, kansa namasa mugun ciwo, dan kada tagane
yanayin dayake ciki saiya Dan nutsu
Ya tura dakinsu, tana zaune itada baba Hanne suna karatu, yace Mata haneefa zo
mana, Gabanta ne yafadi, tasan kuma shikkenan magana ta qare
Saida suka futo yaqara kwantar Mata da hankali sannan suka shiga Dakin
Gabanta Banda faduwa babu abinda yake, kallan da momy take binta dashi kadai ya Isa
ya tabbatar Mata da cewa babu hairu alamarin🤣
Daddy ya Kalle shi yace haneef jeka Dakin momynka kabaamu waje
Saida yajuyo ya kalli haneefa sannan yatafi, suna ganin fitarsa daddy yace yarinya
meyasa kikeson haneef? Dan kudinsa ko? Kokuma wani ne yaturoki aboye Bamu saniba?
Momy tace toki tattara yanaki yanaki kibar gidan nan yanzu basai anjimaba, kinji
nafada Miki, akwai yaran damukeso danmu ya aura
Cikin kuka tace eh, kuyi hakuri, tatashi tafuto tana share Hawaye, Dama tasan haka
zata faru, tasan cewa haneef yafi karfin tunanin ta, kawai tana yaudaran kanta ne
Truly dinta taja, tacewa baba kiyi hakuri baba zamana a gidan nan yaqare, sai wata
Rana, tafuto falo tanajan jaka tana ruskar kuka
Samah na ganinta tace sai aqara gaba kuma, Safah kuwa batace da ita komaiba
Itama Bata Kalle suba, tawuce tafuto harabar gidan, tana tafe tana share hawaye
Dakanta tabude gate din gidan tafuto, kanta yasara Mata, afili tace tabbas kowa
yabar gida... Allah yaji qanka baba, na tabbatar babu Wanda zai Soni aduniyar nan
Sama dakai, zan koma kuje Koda kuwa Hakan Yana nufin Inna zata kasheni Dan azaba,
zan zauna a gidan ubana, inda babu me korata bare ayimin gori
Jakarta tabude tasaka number Bilal takirashi, bugu daya yadauka, tace uncle Dan
Allah kazo ka daukeni
Haneefa lafiya?
Lafiya uncle nide Dan Allah kazo, tafashe da kuka, yace subhanallah gani nan, kina
Ina yanzun?
Ta kwanta ta masa wajan sannan takashe wayarta baki daya ta jefata acikin jaka,
kallan gidan tayi, Bata marmarin qara shigowa gidan nan, su riqe dansu Itama ta
riqe mutuncin ta
Tafiya tafarayi akafa, harta hango motar Bilal, Yana zuwa kuwa tashige suka tafi
Meyake faruwa haneefa? Kisanar Dani mana
Tayi shiru, Kenan tana sonsa 🤣yasake cewa shi haneef din Yana sonki?
Yace to kunyi sa'ah kunason juna, wallahi dayau saiya gayamin shegen dayasa ya
daukeki yafita dake wata qasa, ni tun farko ma Dakin sanar Dani halin dakike ciki a
wannan gidan wallahi dabazakiyi kwana daya acikiba, Amma sai kika nunamin a gidan
jidda Zaki zauna
Rufemin baki ni, mezaki fadamin (tofa ran uba yabaci 🤣🤣🤣)
Motar yaja suka fara tafiya, tace uncle kuje zaka kaini
Mezaki yi a kuje?
Dan Allah uncle kada ka tambayeni dalili, natuna baba ne pls kakaini can
Tausayi tabashi Dan haka bece komai ba suka tafi kuje, suna zuwa kofar gidan kuwa
sukaga wata danqareriyar Mota,dawata motar Abaya, da kuma yansanda kusan biyar suna
tsaye
Bilal na tsayawa shalele ta futo, mekuma inna marka tayiwa Yan Sanda?
Dasauri ta kalli matar taga suna mutuqar kama Sosai, afrah tatafi da gudu ta
rungume shalele
Hajiya hafsat ma haka, gaba daya sukasa kuka, Bilal kansa Saida yayi qwallah,
Hajiya hafsat tace nice mamanki haneefa
Yace dogon labari ne, zanzo gidan kibani address dinki, aikuwa Mami agun tabashi,
taja hannun shalele suka shige cikin Mota, ko gida Bata Bari tashigaba
Saida Bilal yaga tashin mortarsu yasaki ajiyar zuciya alhmdlh Allah nagode ma,
haqiqa yau nacika alqawarin Malam surajo
********
Yaga zama zama su momy basu kirashi ba, dan haka Yakoma Dakin daddy yaana zuwa yaga
Bata nan
Iyayen nasa ya kallah yace momy daddy Ina haneefa take?
Kai tsaye momy tace mun koreta, Gabansa yafadi yasaka hannu ya dafe qirjinsa yace
momy Saida nace muku yarinyar nan I tace bugun zuciyata Ina sonta momy Ina son...
Bai qarasaba yafadi a wajan sumamme
Lokaci daya Iyayen sukai kansa, momy ta Dora hannu aka tafasa ihun kuka tace
munshiga uku alhaji🙆🏻
(congratulations shalelan baba, shalelan haneef shalelan Bilal, yanzu kuma shalelan
mami💃🏻💃🏻💃🏻)
Shin momy zata yarda da aurensa da 'yar qawarta kokuma zatayi amfani da Karin
maganar nan na wata kusan....?
Sanarwa
Nafarko Dama nafada cewa labarin shalelen baba yanada yawa, shiyasa nake kokari
nake yin page me tsayi Dan muyi muyi mugama, Amma mutane suna fadamin cewa typing
din danake yayi yawa, har wasu suna cewa wallahi sungaji da karantawa, imagine nida
nake zama naabata lokaci nayi typing bance nagaji ba saiku da kawai riqe waya
zakuyi a hannu Kuna karatu, 😣😣😣dan haka daga yau zan rage yawan page insha
Allah, zanyi komai ataqaice kamar yanda nayi wannan, kamar kuma yanda kukeso,
nimafa macece kamar kowa, inada ayyukan gida, Amma nake tsayawa Ina wannan
rubuttun)
Saina biyu, wasu suna cemin Wai bekamata shazali yafita da shalele qasar waje ba,
wannan ba al'adar bahaushe bace, jama'ah me kuka dauki novel ne?
Kudinga banbancewa tsakanin true life story dakuma qageggen labari, labarin
shalelan baba qageggen labari ne Dana zauna nikadai nahada abina kuma na fidda
mafita, Abu biyu kowannne novel yake daauka a Dunia, Abu Mai kyau da marar kyau,
saika dauki Mai kyau ka watsar da marar kyau, bance Wai dole sai an dauki abinda
narubuta acikin wannan labarin ba,
Sannan kuma shi shazali daya dauketa suka fita kun tsaya kunga sakamakon sa ne? Kun
tsaya kunga naqare littafi na batare Dana nunawa shi shazali illar hakanba?
Idan kukaga nagama rubutu na batare Dana nuna rashin dacewar hakaba saiku yimin
magana, Amma bawai ku katseni yanzu ba
DAN ALLAH naroqeku da babbar murya, kudenamin katsalandan acikin labari nah🙏🏻
Kamar yanda na roqeku tun farko kuci gaba da bibiyata Dan Allah kubini, kudena
yanke hukunci sai kunga qarshan labari ngd 🙏🏻
Writing by Amnah El
37&38
Ihun da momy tasa tana Kuka ne yaja hankalin su Samah dasuke falo
Aguje suka shigo falon na daddy, suna ganin yayansu akwance kamar Matacce suka fara
Kuka sukai kansa
Yaya katashi! Momy munshiga uku ko Yaya yamutu ne?
Daddy ne yayi karfin Hali yace kurufa mana baki, wacce irin mutuwa kuma? Kutashi
kubani ruwa
Fridge din falon sukaje suka daukowa daddy ruwa, nan aka yaiyafa masa, Amma shiru
kakeji babu wani bayani
Tofa al'amarin yafi karfin tunanin sa, fita yayi waje yakira ma'aikata, babu Bata
lokaci akayi asbiti dashi
********
Cikin Kuka Sosai take magana, idanunta sunyi jajir da Fuskarta, abinka da farar
mace
Haneefa ki yafemin, ban riqewa zainab alqawari ba, nayi watsi dake, kuma Hakan
yafaru ne sanadin babanki suraj, yahana kowa daukarki, yace Yana so yarsa ta shaqu
dashi fiye da kowa
Munyi waya dashi kwanaki yace zai kawoki, nace masa ni yabarni zanzo Amma yace
nabari zai kawoki dakansa
Daga lokacin bansake jinsa awayaba, kuma Ina tsoron inzo yahanani tafiya dake,
saboda bansan dalilinsa nacewa kada nazo ba
Mezata cewa Allah? Ai sai godia atsakaninsu, yau da ace Bata Samu yayar mamanta ba,
ta tabbatar dazata Iya kamuwa da yawan jini, saboda baqin cikin abinda momy tayi
Mata
Dan Adam ako'ina daraja ce dashi, idan sunyi Mata magana cikin fahimta ma dole zata
rabu da dansu, bawai sai anhada da tozarci ba, na farko qannansa sunyi Mata ta
shanye, shi yayi Mata da farko duk da ance halinsa ne fadan baya San raini
tashanye,yadauketa cike da iko yatafi wata qasa da ita, ita ba'a Mata ba, ita ba'a
budurwarsa ba, kuma ita ba'a karuwa ba
Duk ta shanye
Dama hakane, duk Dan da beji maganar iyayensa ba to tabbas zaiga ba daidai ba, baba
yayi Mata nasiha kafin yarasu Akan ta riqe mutuncin ta na ya mace, Amma tayi watsi
da Hakan, yanzu ga sakamakon data Samu nan
sannan mahaifiyar sa tayi Mata, ta koreta daga gida mama jiddah ta rufa Mata asiri
ta dauketa, daga qarshe akaro na biyu tasake korarta, to ita kuwa kosan hauka take
masa ai yaci ace tahakura dashi
Waya sanima koba San gaskiya yake Mata ba, kawai yanason wani Abu Natane, inba
hakaba meyasa tunda farko baisanar da ita ba sai Bayan yagama kissing dinta ya
shanye Mata baki🤣
Kai wallahi ma bazata yardaba saiya biya Mata bakinta, aiba Nasa bane natane🤣
Hajiya hafsat tace nasan namiki laifi, kiyi hakuri haneefa, ke kadai zan gani yanzu
naji kamar zainab nagani
Cikin sauri ta juyo ta kalli hajiya hafsat🙆🏻tab ashe Afili tayi maganar, 🤣
Afrah ta Kalle ta tace Mami, nikuma afran Mami, kekuma haneefan Mami, Shikuma Yaya
ameer Banda shi
Daria tabasu gaba dayansu, hajiya hafsat taja haneefa da afrah jikinta ta
rungumesu, tace Allah yajiqan Malam suraj, sukace amin gaba dayansu
********
Tunda sukazo asbitin suka kasa zaune suka kasa tsaye, momy Kuka yanbiyu Kuka, daddy
ne yake kokarin kwantar musu da hankali, sunyi kusan 30minutes a wajan sannan
doctor yafuto, cikin sauri sukai wajansa
Cikin Kuka momy tace doctor wanne irin Mu kwantar da hankalinmu kace Dana Yana
cikin matsanancin Hali 😭
Eh zaku Iya shiga, Amma Dan Allah Banda surutu, anyi masa allurar bacci, idan
yatashi zamu saake dubashi, yawuce office dinsa
Dukansu zama sukai a Dakin sukai jugum jugum dasu, abin tausayi 😢😱
********
Suna zuwa gida, aka wangale musu gate, still harabar gidan ma Yan Sanda ne,itade
shalele cikin ranta tana cewa ko meyasa suke yawo da yansanda?
Momy ta riqeta afrah ta riqeta haka suka qarasa cikin falon, gaskiya gidan yahadu
ba qarya
Ameer na zaune afalo ya tusa computer agaba Yana typing yadago kansa ya kallesu, da
tsananin murna ace a a Mami sannunku da zuwa, ya kalli shalele yace inye Mami kinga
yanda haneefan baba ta girma, Yara duk sun girma sai aure 🤣
Daquwa Mami tamasa, ungo nan Ameer, Kai basu ce kayi aure ba sai Kaine zaka fada
musu haka? Sosa kansa yayi yamaida hankalin sa Kan computar, yace sannu da zuwa
haneefan baba, murmushi tayi tace yawwa sannu
Afrah ta kalleta tayi Mata rada, haka yakefa, kullum cikin aiki kamar computar, ba
shida magana yanda kikasan damo🤣
Cikin nutsuwa tace a a Yaya, taja hannun shalele sukai daki, Mami ma tabi Bayan
yaranta, Saida sukai wanka taci abinci sannan suka baje kolin fira, lokaci daya
tasake dasu, Mami babu ruwanta hada Kan yaranta take ta rungume 🤣
Shalele tabasu labarin komai Nata, Amma Bata basu labarin aikin datayi agidansu
shazali ba, fatanta daya ta manta da ahalin gidan ayanzu
Mami azuciyarta tace toba haneefa bace suka gani atv ba rannan
To Amma meyasa Bata basu labarin abinda yarabota da gidan jiddan datace ta zauna
ba? Haka kawai zata dawo gida ne? Kai dole akwai abinda yake faruwa Amma ta Barta
tasake sakewa dasu kadan kafin ita da kanta tasanar dasu komai
********
Haka suka zauna shiru a Dakin, Har dare bai farkaba, yanbiyu sun fara gyangyadi
daddy yace sutafi gida, badan sunso ba driver yazo yatafi dasu
Momy da daddy suna zaune agefensa babu abinda yake tadasu sai sallah
********
Shalele kuwa afrah Nata Bata labari da daddare, sun ware sai zancensu sukeyi, afrah
tace Wai haneey bakida boyfriend ne?
Banda shi afrah, mutum daaya de yataba cewa Yana sona kuma mun rabu🤣
Ayya sorry sister haneey insha Allah, ubangiji zai kawo wasu
Wallahi yatafi arewa, Amma may be yadawo jibi, dagani sai Mami sai Yaya Ameer ne a
gidan dakuma security
Afrah Tai Daria, aiya Dade da Gama mknrta, yanzu yana aiki ne dawani company na
qera computar, shiyasa zakiga kullum Yana cikin sarrafata, bashida magana, haka
yake shiru, babu ruwansa yanada hakuri Sosai
Haka sukaci gaba da firansu Har afrah tayi bacci, ita Kuma tafada tunanin haneef
To meyasa ma zatai tunanin sa? Mutumin daya cuceta yagama tsotse Mata lips, ai
wallahi tana sane Kuma saiya biya Mata abinta tunda iyayensa basuda mutunci 😱
********
Washe Gari Dr Bilal yaje gidan, ta hanyar adress din da Mami tabashi, ankarbeshi
Sosai, Shima kuma ya ware kamar Dan gida, Yana basu labarin irin gwagwar mayar
dayasha da Marka Akan neman hajiya hafsat 😄
Sai Daria suke yi abin gwanin birgewa
Daria yayi ai Tasha kukanta, kawai Marka takawo wata Mata Wai maqociyar kice zata
kawota wajanki, shine yarinyar nan saboda tsabar shirme tabita
Sukayi murmushi Dukansu, Saida yadade agidan sannan yayi musu sallama zai tafi
Mami ta dubeta ki tashi ki rakashi mana
Tace to, tatashi tabishi cikin kunya, Mami fa kada tayi tunanin wani Abu ne
atsakaninta da uncle, 🤣wannan me shegen son girman a'uba yadauki kansa
Suna zuwa wajan motarsa ya dubeta, idan nasamu lokaci zan kawo Miki Abdallah ya
wuni, but dashi zan koma, bazan barmiki shi ba
Sosai ma
Saida tayi qasa da kanta cikin kunya tace to uncle kayi aure mana, tana Gama fada
Takoma gidan da gudu🤣
Bayanta yabi da kallo, tab to tunda yarinyar nan tafara maganar aure Gara yasamu
wata ya aura, yarinya me kunya tana ganin girman sa to me akayi kuma idan tafara
futowa qarara tana cewa uba yayi Aure 😱
Murmushi yayi yashige motarsa ya koma wajan aiki, Dama daga asbitin yake yafatse
ayyukansa yataho
********
Doctor yazo ya dubashi, aka cire masa oxygen din da aka aka Saka masa, sai ruwa
daya daura masa yayi masa Yan gwaje gwaje , ya kalli su momy yace hajiya, Alhaji
maganar gaskiya danku Yana cikin matsananciyar damuwa,Har Hakan yaso taba zuciyar
sa
Hawaye momy ta share, Dama yace yarinyar nan itace bugun zuciyar sa
Cikin mamaki ya kalleta, yanzu hajiya Dama kunsan damuwar Dan naku?
Daddy yace wata yarinya yakeso, mukuma munriga munyi masa Matan dazai aura, dalilin
hakane yafadi yasuma
To gaskiya Alhaji shawarata agareku itace kode kubashi wadanda Kuka zaba masa ya
auresu Shikuma ku rasashi, kokuma kubashi wadda yakeso ku zauna da danku
Momy kuwa kallan haneef take cike da tausayi, gashi takori wannan yarinyar, Ina
zasuje su nemeta ta Ina zasu fara?
Jidda ce tafado Mata, batazo da wayarta ba, ta kalli daddy tace Alhaji ko zaka Kira
mana Jidda muji ko yarinyar nan can tatafi
Tace eh daddy haka ne sunanta, Amma shalelan baba ake fada Mata
Daddy yace um aijinake karyar haneef ce Bahaka sunantaba, sunan ma Ara Mata yayi
shiyasa yace mana haneefa🤣🤣
Daddy meyake faruwa? Ni batazo nan ba, wani abun haneef din yace akanta?
A a jidda qaninki de gashinan akwance rai a hannun Allah, tun jiya muna asbiti Har
yanzu Bai farfado ba, Amma likita yace zai Iya tashi kowanne lokaci, yace yanason
yarinyar ne, mukace bamu amince ba
Shine yafadi yasuma, Wai itace bugun zuciyar sa🤣🤣🤣ke kinji fa wani shirme jidda,
yaushe zaka tsananta son mace Har haka?
Innalillah... Yanzu daddy haneef din Yana kwance a asbiti Amma Baku fadaamin ba?
To jidda muna cikin wannan tashin hankalin wama muka fadawa? Babu Wanda muka fadawa
wallahi
********
Futowa tayi falon dawata doguwar Riga ajikinta ta bacci, Me kauri, da kadan rigar
tawuce Mata gwiwa
Zama tayi akusa da Mami ta Dora kanta akafadarta, afrah kuwa tana kwance,tace gashi
Mami
Daga daya bangaren momy tace hajiya hafsat lafiya wallahi, yaushe kika dawo qasar?
Shekaran jiya nadawo hajiya, Dama zan fada Miki ne jiya naje kuje fa nadauko
haneefan baba
A a hajiya hafsat kuma kikama hanya kitafi wajan baba Amma kikasa sanar Dani, haba
hajiya gaskiya banji dadi ba
Ina haneefan take yanzu?
Mami ta kalli haneefa tace gatanan hajiya, yau zamuje nayi Mata shopping ne, gobe
zata koma makaranta , Amma insha Allah gobe zamuzo nan dinma gaba dayanmu Har su
ameer yarama suga junansu
Toshikenan hajiya, Allah yakaimu goben Amma inaga mukam saide ku samemu a asbiti,
haneef ne a kwance bashida lafiya
Shalele naji ance haneef gabanta yafadi, meyake shirin faruwa ne?
Mami   tace yar aiki kuma? Me wannan Yaron yakeso ya nuna mana ne? Yarasa wazai kwaso
mana   viking family sai yar aiki duk ajin haneef shazali da kudinsa?hajiya Meyakeso
muce   ranar auren?
Toma   wacece wannan yarinyar?🙆🏻
(gatanan agabanki 🤣)
Momy tace bar matsiyaciya hajiya, nakoreta ai jiya, yanzu de Allah yakaimu goben
sai kunzo
Mami tace to hajiya, insha Allah gobe zamu zo idan ameer yataso daga wajan aiki
Idanunta ta rufe, kamar me bacci, yanzu Kam tagama fahimtar komai, ko tantama
batayi wannan momy ce akai waya da ita
Cikin ranta tace Tab Kan bala'i🤣🙆🏻Kenan cousin din namanta ce ta koreta?
Aikuwa babu inda zataje, tariga datayi fishi dasu, suje su riqe dansu
Itama ta riqe mutuncinta,wallahi gobe batada lafiya, kawai gobe ba lafiya Dan haka
tun safe ma zatayi kwanciyarta adaki cikin bargo 🤣ba ita ba gidansu momy
********
Momy tayi shiru tayi tagumi adaki ita kadai, tana kallan haneef dake kwance Yana
bacci, yau da ace haneefan baba yace Yana so ma Aida yafi, shikkenan sai ayi tuwona
maina, 🤣
(ai momy ko shinkafata miyata za'ayi mun fasa muma bamayi😏😏ki riqe danki mu riqe
mutuncinmu 🤣🤣)
Anty jidda na zuwa tafara tattaba jikinsa, jikinta sai rawa yake, momy yanzu yaza'a
masa?
Haba jidda kuma de haneef yarasa wa zaiso sai yar aiki? Haba jiddah
To momy tunda shi yagani Yana sonta Kuma shi zai zauna da ita ba shikkenan ba?
Ajiyar zuciya tasaki tace hakane, yanzu a"ina zamu ganta jiddah?
Ke yar dakinki ce Bata fada Miki inda taakeba? 🤣🤣
Cikin tsananin mamaki tace kuje!!!? Sannan kuma haneef yacemin sunanta haneefa,
lokaci daya gaban momy yafadi
Momy sai cewa kike kinshiga uku, Wai meke faruwa ne?
Kanta da Dora daga gefen gadon da haneef yake zaune, tace Barni jiddah, jiri nakeji
wallahi 🤣🤣
Saida tayi kusan minti uku a kwance, tadena Jin jirin tace jidda Ina tunanin
yarinyar nan yar wajan baba ce
Cikin fada momy tace baba de, mijin zainab qanwata me rasuwa ta kuje ha'a, Ana Miki
magana kina ta dawo min da Abu baya🤣
Anty jidda tayi murmushi tace momy kefa kika kori yarinyar Naan kuma ni yanzu momy
saiki huce akaina?
Hannu ta daga Mata ✋🏻dakata Dan Allah jidda, kibarni da abinda nakeji 🤣
Wai jidda tayaya Zaki fadi haka, ke bakiga yarinyar tana kama da hajiya hafsat ba?
Anty jidda tayi jimm sannan tace gaskiya ne momy, suna kama gaskiya Amma ita wannan
tacemin babanta yarasu, namanta ma haka, Amma akwai uncle dinta wadda take gidansa,
nikuma abokin babansu sajida ne, inama da number sa, zan Kira shi yanzu, sai kuje
ku sameshi yakaiku inda za'a Samu haneefa, idan kuma Bata wajansa to sai kuje can
Garin nasu, kuduba nasan bazata wuce waje biyun nanba
Nikuma zan zauna da haneef nakula dashi, insha Allah, Allah zai tashi kafadunsa,
Allah kuma ya baiyana ta
Haneefa!
Haneefa!!
Haneefa!!!
Daga momy Har jidda suka juya wajan haneef suka bishi da kallo, lokaci daya qwalla
tacika idon momy, Kinga ni ko jiddah, farkawa ma da ita yake farkawa abakinsa
Anty jidda ta matsa jikin gadon ahankali tace haneef, Bude idonka nice jiddah
Cikin muryar rashin lafiya yace anty su momy sun koreta, sun koreta anty, wallahi
Nima binta zanyi, Allah bazan zaunaba🤣
Anty jidda ta dafe Kanta, Ohaneef, kayi hakuri mana, tashi nahadama tea kasha
Anty ni bazan Bude idonaba, banasan ganin kowa, tunda suma basason ganinta
Saikuma yaga momy, lokaci daya ya kawar da kansa gefe yayi shiru
Momy takama hannunsa tace haneef tunda kanason haneefa yaya zamuyi, zanje nakawo ma
ita da kaina kaji? Kadena damuwa Dana
Momy ta kalli anty jidda, cikin fada akace tun dazu kince Zaki kirashi, nazuba Miki
ido, Naga alama bakida niyyar Kiran kema de jidda
Yace a a ai yanzu kece da aiki, kidauki yar tawa qwaya daya jal, kikaita gidan
                                 😳
aiki, Kinga kuwa ai ke kikai aikiaini bakimin adalci ba jiddah, 😳
                         😳
(kaikai jiddah Kai tsaye )
Doctor bazaka gaaneba, dogon labari ne, idan muka hadu zanyima bayanin komai
Wallahi doctor akwai matsala, qanina Yana kwance a asbiti saboda yarka, but doctor
yace dole sai an Nemo masa abinda yakeso ko hankalin sa zai kwanta, dan Allah
doctor na roqeka, kayi hakuri, nayima alqawarin zanyima bayanin komai idan muka
hadu
Saida yagama shan qamshi sannan yace gaskiya yanzu na tashi daga aiki ne, saide ku
Bari zuwa gobe, kusameni a office saimuje
Saida yayi hamdala a ransa Jin iyayen Yaron ne zasuzo, dadin yanda zai nuna musu
yarinyar tanada daraja tana amfani
Yace babu damuwa, zan turo Miki adrees din asbitin sai suzo gobe dasafe su sameni
Dahaka sukai sallama, aikuwa a lokacin yaturo musu adrees din komai
Ita Kuma tabawa momy
********
Momy tace hajiya hafsat babu lokacin bayani, Ina haneefa?
Afrah na zuwa suka futo tare, ganin su momy yasa gabanta yafadi, lokaci daya tahade
girar Sama data qasa
Har qasa ta tsugunna tace daddy ina kwana, momy Ina kwananku
Atare suka amsa Mata, momy tace haneefa kiyi hakuri kinji? Dan Allah ki yafe mana
abinda muka Miki, dan Allah naroqeki kiyi hakuri kizo muje kiga haneef, kina sonsa
Yana sonki, mukam indan Tamu ne mun amince wallahi🤣🤣
Duk falon ita aka zubawa ido, Kanta aqasa tace momy kiyi hakuri, ni yanzu Bana
Sansa
Kowa yayi mamakin furucinta, daddy yace yata kiyi hakuri, yanzu de kizo muje
kiganshi Asamu lafiyarsa daga baya ayi maganar komai
Yadubi hajiya hafsat yace kiyi hakuri hajiya mun barki aduhu, kutashi muje asbitin
nan gaba dayanmu tunda kuma nan Kuka nufa
Qwace jikinta tayi, tadauki wayarta, Shima cikin sanyin jiki yace Mata sorry, yayi
gaba.
Shalele sai kumburi take, wallahi badan Mami tace dole saitazo ba, wallahi da
bazata zoba
Anty jidda da Ajmal ne a Dakin nasa, sai gani sukai baqi suna shigowa
Haneef Yana dago kansa yayi ido hudu da shalele, yakafeta da kallo, Ajmal na
zungurinsa Amma inaaa🤣🤣hankalin yatafi
Hajiya hafsat na ganin kallan da haneef yake Mata ta fahimci komai, Kenan
haneefanta ce take Aiki a gidan su? Kenan haneefa haneef yadauka suka fita qasar
waje? Ita din tagani a TV Kenan? Itace momy suka Kora agidansu?
Lalle akwai matsala, dole sai haneef yagane kuransa, aiko ameer dinta ne yadauki
haneefa suka tafi wani waje batare da sanin taba dole zata masa hukunci
Dan haka bataga laifin shalele ba, datace Bata sonsa yanzu
Anty jidda tana kallan Samah da Bilal suna hararan juna, tace to yau kuma masifa ce
tahadu daa San girma kenan🤣🤣
Tana juyawa taga Ameer Yana satar kallan Safah, itama tana Kallansa qasa qasa 🤣🤣
Tayi murmushi wannan tun kafin ayi abin kunya agaban surukai Gara su fice, Allah
yaso babu sajidanta 🤣🤣🤣da abin yayi yawa, Dan haka tace daddy, momy, Mami muje waje
mudan basu waje
Cikin gunguni tace kawai nace bazan zoba bazan zoba sai anmin dole
Yajita Sarai, murmushi yayi yace congrats Ina tayaki murnar samun mamanki, but
banji abinda kike fadaba
Cikin fishi tace cewa nayi ni Bana sonka, kuma abiyani bakina, bazan yardaba
(naji korafinku, kuma ngd Sosai, insha Allah zamuci gaba kamar yanda muka saba,
nagode Sosai da kaunarku agareni 🙏🏻)
Wanda sukaga banyi musu refly Akan comment dinsu ba suyi hakuri,massages ne sukamin
yawa wallahi
Menene zai faru tsakanin Dr Bilal da Samah? Me damo sarkin hakuri Ameer yake nufi
da daya sarkin hakurin Safah?
Anya kuwa Haneef zai Samu haneefa cikin sauqi dangane da furucin hajiya Hafsat?
Writing by Amnah El
(🙏🏻kuyi hakuri Dan Allah bisa mistek din Dana Samu jiya wajan rubutu, akwai inda ya
goge atsakiya, inda su daddy sukaje suka nemi Bilal, da irin Jan ajin daya musu
kafin yakaisu gidan hajiya hafsat, dakuma sabanin da suka Samu shida Samah Har suke
hararar juna a asbiti, da irin yanayin da momy tashiga itada daddy lokacin dasuka
tabbatar shalele yar'uwarsu ce, sannan ne akayi inda daddy yace a Kirata kuma aka
Kirata tace bataso, kungane yanzu? To wajan me ya goge wallahi, babu yanda zan
gyara saboda nariga nayi posting dinsa, Amma wasu sunce sun gane ahakan, ngd,
dafatan za'a Fahim ceni 🙏🏻)
39&40
Yunqurawa yayi yatashi Yana yamutsa fuska, alamar baijin dadi Sosai
Yataso yazo gaban kujerar da take Kai, ya tsugunna, yakafeta da lumsassun idanunsa,
sannan yasaka hannunsa yakama face nata, yamatso da bakinsa dab da nata, Cikin
sauri ta qwace Fuskarta, takawar da Kanta gefe, murmushi yayi, kikace nabiyaki
bakinki, to tayaya zan biyaki idan banyi Miki irin nada ba?
Kallansa tayi tafashe da Kuka, ta Dora Kanta Akan jinyarta tana Kuka Sosai harda
shashsheka, Shikuma gashi a tsugunne a gabanta, Hakan da tayi saiya qara musu
kusanci Sosai
Meyasa take Kuka? Anya kuwa su momy basu zagi yarinyar nanba? Jin kukannan nata
yake Har cikin ransa, jiyake kamar yajata ya rungume ta a jikinsa ko zaiji dadin
lallashinta
Sumar kansa yashafa, yayi ajiyar zuciya, kansa yamatso dab da nata datake sunkuye
tana Kuka, saitin kunna ta yasaka bakinsa, "kiyi hakuri, nasan iyayena sun Bata
Miki rai, kuma nasan cewa abinda suka Miki ne Nima yashafeni Har kika fadaamin
wannan maganar,
(aikwa de hakane shazali tunda a lokacin Ina ganinta ta lumshe ido 🤣🤣🤣)
Yaci gaba da cewa amma kiyi hakuri, nizaki duba basuba, Dani Zaki zauna ki rayu
kiyi Zaman aure Dani basu ba, Koda ace kowa baya sonki aduniyar nan ni Ina sonki
haneefa, kiduba kiga halin danake ciki, soyaiyarki ce tasa na kwanta a gadon
asbiti, kiyi shiru, insha Allah komai zai wuce, watarana su momy zasu soki, kiyi
hakuri, kada kisake cewa bakya sona, inba hakaba wallahi zan tabbata a gadon
asbitin nan
Adede lokacin iyayen nasu suka dawo Dakin, anty jidda na ganin qaninta a tsugunne
agaban shalele mamaki yakamata, lalle soyaiya Mai gyara mutane, yau haneef dinta ne
agaban qaramar yarinyar nan, kome yake rokonta? Oho musu
Jin sun shigo dakinne yasa yatashi yakoma gefen gadon sa ya kwanta
Mami tace a a Dana wanne kwanciya kuma Bayan ka ware Sarai, Saida ka ganmu zaka
koma Kan gado ka nade 🤣🤣
Duk Dakin sukai Daria
Daddy yayi gyaran murya yace to alhmdlh, godia ta tabbata ga Allah daya bamu ikon
haduwa a wannan wajan, yadubi shalele da idanunta sukai jajir saboda Kuka yace
Haneefa takanki zan fara, kiyi hakuri dangane da sabanin fahimta da aka saamu,
munsan cewa mu masu laifi ne agareki, Amma kiyi hakuri komai ya wuce, kada kisake
cewa bakya son haneef, Koda bakya yimasa so na aure aayanzu Kam haneef dan'uwanki
ne, dole Zaki soshi kuyi zumunci
Kiyi hakuri kinji yata? Ahankali ta share qwallar idonta, tadaga masa Kai, haneef
Yana Kallanta, bayasan kukannan datake, jiyake kamar Shima yayi, Amma tayaya ta
zama yar'uwarsa?
Daddy yakatse masa tunani da fadin, haneef, Samah, Safah, dakuma ke jidda, Haneefa
yar'uwarku ce, itace yar gidan qanwar mahaifiyar ku, ke jidda da haneef zaku Iya
saninta, nasan iklas da fadilama zasu Santa, yanayin rayuwa ne yasa tazo Aiki
gidanmu, kuma alhmdlh mungodewa Allah dayasa zuwan nata yazama me mana alkhairi
gaba dayanmu,
Sannan ya nuna musu Mami yace nasan kun Santa, duk da ba ziyartar juna akeba,
wannan itace wadda suke ciki daya da zainab mahaifiyar haneefa, ga babban danta
Ameer, dakuma qaramar Afrah
Hajiya hafsat kiyi hakuri, munsan cewa abin babu dadi, Amma idan Zaki duba zakiga
komai yafaru ne bisa rashin Sani, kuma munyi DANA SANI Akan Hakan
Mami tace babu komai Alhaji, Allah yakiyaye gaba, Dukansu sukace amin, doctor yazo
zai duba jikin haneef sai gani yayi daki yacika dam da mutane, yace a a, yau ko Dan
qaramin biki ake a Dakin ne?
Yace to masha Allah, Bari na dubashi, Yana juyawa sai yaga Dr Bilal, yace a a kamar
babban doctor nake gani
Bilal yayi murmushi yace wallahi nine, nazo ganin marar lafiya ne tare da yata
Wacece yar taka? Yanuna haneefa yace gatanan a zaune, ai itace yarinyar da marar
lafiyar taka yake nema
Cikin Daria doctor yace alhmdlh, gaskiya naji dadi, to ai kawai Bari nabaku waaje
saika dubashi
Dr Bilal yace a a haba doctor qarasa aikinka wlhy, Nima daganan wucewa zanyi nakoma
wajan aiki
Likitan ya dubi daddy yace Alhaji wannan abokin aikinmu ne, Amma sune manyanmu,
Aida nasan kun sanshi da tun farko ma can wajansa zan turaku
Tajuya ta kalli Dr Bilal tasaakar masa harara, Shima anasa bangaren hararar yasakar
Mata
Doctor na dubashi yace zasu Iya tafiya, idan wani Abu yataso zasu Iya zuwa wajan Dr
Bilal
Tashi sukai suka tafi, haneef farin ciki yacikashi, ashe ma yar'uwarsa ce, aikuma
yanzu maganar momy taqare, saura ta daddy, Shima insha Allah komai zai wuce
Suna zuwa harabar hospital din, momy tace ai hajiya hafsat saimu wuce gida gaba
daya ko, Kinga yau sai mu wuni tare
Shalele ko kallan haneef batayi, Ana cewa a shiga Mota ma cikin sauri tashige,
haneef na ganinta, yasan saboda shi take komai
Mazan ne suka dakata, sukuma Matan suka tafi,shima Bilal yayi musu sallama yatafi,
Saida su momy sukaje gida sannan saminu yazo yadaukesu
Suka tafi gidan suma, direct part din haneef sukayi, Ajmal yace lover boy, yanzu
shikkenan ka ware ko? Wai Dan Allah abokina me kake rada Matane muka shigo Dakin
Hararar sa yayi yace to bazadai kajiba, wannan sirrin Wanda suka kusan shiga daga
ciki ne 🤣
Ai bazatayi Bama
Ameer yayi Daria yace wa Ajmal tokai kaji sai kayi hakuri sirrinsu ne
********
Yanmatan Dukansu suna dakinsu Samah, afra ta miqe agado tana daddanna waya, Samah
takamo hannun shalele tace kiyi hakuri yar'uwata, nasan nayi Miki laifi Mai yawa,
Amma kiyi hakuri ki yafemin, Kodan yayana da yar'uwata
Nima wannan masifar tawa tana damuna wani lokacin 🤣🤣wallahi, kuma duk saurayinki ne
yagogamin wallahi, dan Bahaka yanbiyu na takeba Safah
Afrah Tai Daria takalli shalele tace toke saiki zauna tana fadawa saurayinki magana
Safah tace kiyi hakuri antynmu, komai yawuce, adena tuna baya
Murmushi tayi tace babu komai Safah, Allah yakiyaye gaba kuma
Bari inje wajan baba Hanne, ta yunkura tatashi, Samah tariqeta tace a a wallahi,
babu inda zakai zama zakiyi muyi fira
Safah tace ni wallahi harna matsu ma Inga aurenku keda Yaya, saboda Inga yanda zai
nuna Miki soyaiya, idan kaganshi haka kamar bazai yiba
Amma nasan mutane masu shiru shirun nan, sun Iya soyaiya Sosai, akwai lokacin Dana
ganku afalo kuna Daria, sainaga kamar ba yayan Dana saniba
Samah tace Nima sun birgeni lokacin Dana gansu afalo tana mopping Shikuma Yana
gefenta yawani Matso Yana Mata rada, baki gansu ba wallahi
Samah tace a a barmu mugani, taa kalli shalele tace wannan baban naki yacika son
girma dayawa wallahi, kamar shi yafi kowa, jiyafa da zamuje gidan Mami nazauna
akusa dashi amota wallahi haka yasa kafa ya danne min kafata, bakiji zafi ba, gashi
fari tass Amma zuciyar sa baqa😏
Shalele tace kede Samah kifadamin gaskiya idan kina ciki, Kinga Dan fari zubin
larabawa
Haba de sister haneefa, harfa cewa yayi zai zaneni, idan na aureshi kuma ai dukana
zaiyi
Afrah tace Nima ina ganin ku a asbiti kuna hararan juna, wasu kuwa kallan kallo
suke qasa qasa waisu ustazai 🤣🤣
Safah tayi murmushi laaa Wai Yaya ameer ke babu komai wallahi, kawai Kallansa nayi
sai aka Dace Shima ya kalleni
Saida tayi fari da idonta 🙄wallahi wani Dan abokin daddy ne, Yana Lagos, a India
nahadu dashi
********
Dukansu sun hadu a dining suna cin abinci, haneef Kam babu kunya yaje ya zauna
akusa da kujerar da shalele take
Wai kawai dagowar dazaiyi saiyaga kafar haneef Akan ta haneefa 🤣🤣tab gaskiya
shazali Dan duniya ne
Shine asama ya nunawa mutane babu ruwansa da ita, Amma daga qasa Yana abinda yaso,
ashe shiyasa ya maqa daga gefen ta
Dagowa yayi yace yawwa qanwata, ya kalli haneef, kallan nasan komai 🤣
Yaci gaba da shafa kafarta da tashi kafar, Sarai tana jinsa, Amma ta shareshi, duk
wani iri takeji, tajanye kafarta yasake Dora Mata, kowa ya kalleshi bazaice wani
Abu yana faru ba, Amma itakam ta naji ajikinta, sai kuma Ajmal daya gansu🤣🤣
Al'amarinsa Yafara fin karfinta, Bata isa tace yabiyata ba🤣, tunda dazu ma data
fadi haka taga abinda ya biyo baya
Dan haka ta share shi, Har suka Gama, da zasu tafi ameer yakoma wajan Mami ya yi
Mata rada
Ameer naji momy tayi magana yayi wuf yafice daga falon
Mami tace tun dazu Yaron nan yadameni Wai a fadawa daddy shi Yana son yanbiyu,
shine yanzu yake sake cemin Wai kada namanta de🤣
Safah kuwa kamar tashige cikin qasa Dan kunya, cikin gudu Takoma dakinsu 🤣
Momy tace to ai shikkenan, kuma menene abin boye boye baanda abin ameer, ai Dani
yasamu Kai tsaye ya fadawa
Mami tace ai ameer dakike ganinsa Har yafi wata macen kunya
Momy tace ita ma Safah haka take, Allah yasa ayi Damu
Momy tace Amma de hajiya ai zakibar shalele anan gidan kukutafi ko, tunda Dama anan
take
Mami tayi murmushi ai hajiya an maidata makaranta, gobe zata fara zuwa, yauma
abinda yasa batajeba saboda zuwanmu nan ne
Lokaci daya kunya takama momy, meyasa ma tayi wannan tambayar, duk Zaman yarinyar
agidansu Basu taba tunanin Sakata a school ba, Allah de yakiyaye gaba
Haka suka tashi suka fara haramar tafiya, haneef ya matsa kusa da Afrah yace
qanwata idan kunje gida Dan Allah kice tabude wayarta
Shalele taje kusa da anty jidda tace mama zamu tafi, kicewa sajida da ayaz zan
kirasu
Kiyi hakuri mama, naso nazo gidanki Bayan nabar nan, Amma kiyi hakuri,
Duk sukai rakosu wajan Mota, suka shiga suka tafi, Ajmal da haneef sukayi hanyar
part din haneef din
Ajmal yace Wai Naga mutuniyar taka sai fishi take dakai
Ajmal ansamu abinda akeso, shide arayuwarsa Yana so yadinga Jin dramarsu 🤣🤣🤣
Yace fishin me?
Kiss haneef😳😳
Innalillahi....
To sarkin kwakwazo, menene aciki danna fadama gaskiya, kissing dinta nayi, shiyasa
take fishi kuma nabata hakuri, itama abin dayasata fishin nasan abinda su momy suka
Mata ne, Amma a lokacin ai batama nunamin komai ba,
Ajmal yace lalle haneef Kai Dan duniya, inbanda iskanci kayi abun kazo kana
fadaamin haka
Babu wani dauri Ajmal, kawai ni abinda nasani shine da inje inyi Abu aboye, Gara
inyishi afili, Wanda suka nuna basayi din ai ba'asan me sukeyi aboye ba, itama kuma
nasan fishi ne yasata fadar haka, insha Allah zata yi hakuri
To shine take fishi, Wai dazu ma ita Bata sona, nabiyata bakinta
Haneef yace to yarintarfa, Aida ta tsaya Dana biyata, kaga daga nan ma nasake
tsotsa
A a shazali kafi karfina, wannan Gara ayi muku auren nan muhuta
********
Bayan kwana biyu su daddy sukaje gidan hajiya hafsat, nemawa haneef auren haneefa
shida makusantan abokansa
Alhaji Tahir yace to ai Alhaji bukar, wannan ba abin damuwa bane,saide wannan
yarinyar akwai babanta Bayan ni, mahaifinta tun kafin yarasu yace yabashi ita halak
Malak yariqe ta amatsayin Uba, dan haka Bari nakirashi nasanar dashi halin da ake
ciki, nan kuwa aka Kira Bilal yace zaizo daga baya, yabashi Dama yayi komai, ai
Shima mahaifinta ne,
Nan daddyn Afrah yayi masa godia yaakashe wayar, sannan yadubi su Alhaji bukar
yace, Dama Nima inaso inzo da tawagata nemawa Dana ameer auren yar wajan ka
Babu Bata lokaci anan wajan aka tsaida ranar aure nanda wata daya
Alhaji Tahir yace saide kuma wani hanzari ba gudu ba kasan yarinyar tana ma karanta
a yanzu
Daddy yace a a wannan ai ba abin damuwa bane, Nima yaran wajena University suke
shirin tafiya, kaga kowa sai tayi karatunta a Dakin mijinta
Nan da nan kuwa kowa yayarda da wannan hukunci na daddy, aka sake gaisawa sannan
suka tafiya gida domin yasanar wa dasu momy hukuncin dasuka yanke
Shima Alhaji Tahir yashiga gida domin sanarwa da hajiya hafsat abinda yake faruwa,
yashiga gidan da goron sa da alawa nasaka Rana
41&42
Yau gidan anty jiddah anyi baqi, yanbiyu sunzo sai fira suke da sajida, kasancewar
ba zuwa suke Sosai ba, sai zuwan nasu yayi Mata dadi
Anty jidda na waya da mijinta adaki, Bayan sun Gama takira Bilal
Tace doctor Har yanzu Baka zoba Akan maganar danace zamuyi shekaran jiya
Jiya kuma bakabimu gidan momy ba daga asbiti saika wuce wajan aiki
Yace eh wallahi, bansamu lokaci nazo ba, Amma yanzu Dama zanje gidan hajiya hafsat,
kawai zan shigo tanan, daganan Saina wuce
Tace to saika zo
********
Yana shiga cikin falon yaganta a harde akujera, cikin fara'ah ya Bata goro da
alawar hannunsa yace hafsat riqe wannan
Nasaka ranar yayanki ne, ameer da haneefa, nanda wata daya insha Allah za'a daura
musu aure, saiki fara shirye shirye
Ita hajiya Amina Aina fada Mata namaida yata makaranta abinda suka kasa yimata
Kwana da kwanaki tana zaune agidansu, amatsayin me aiki, sun zaunar da ita tana
musu bauta, sannan ni da take musu aikinma bantaji haneefa tacemin tana karbar
kudinsu ba, saide faman wahala datasha
Tsakani da Allah abban Afrah, gida de kamar gidan Alhaji bukar tayaya zasubar
ma'aikatansu batare dasun sakasu a makaranta ba, aiko yar islamiya ce sa sakasu
aciki
Kuma haka kawai saboda rashin adalci dason Kai irinnasu suzo dawata magana ta aure?
OK sai yanzu ma nagane, saboda dansu Yana kwanciya jinya saboda ita, shine za'a
katsewa yarinya karatunta ace za'a Mata aure, bazai iyuba
Kaje kafada musu cewa ni nan, nace bazan Bawa dansu auren yata ba, ai itama tanada
gata ba marar galihu bace, shide ameer din tunda namiji ne kuje kuyi masa, Amma
Banda haneefa
Yanzu ni din kike so naje nasamu shi Alhaji bukar da wannan maganar?
Cikin fishi taace toshi kuwa yazo yasameka da ita? Qarewa mafa Yaron nan zuwa yayi
yadauki haneefa yafita qasar waje da ita, yarinyar Bata nuna masa korafin komaiba,
sannan Bata samu iyayensa tafada musu maganar ba
Saikace wata marar gata, wallahi baban Afrah ko ameer dinane yadauki haneefa suka
fita wani waje batare da sanina ba dole zan hukuntashi Akan haka
Idan yarinya bame kamun Kai bace wayasan mezai faru?saboda kawai suna taqamar cewa
ita yar aikin su ce? Shin masu aiki basuda iyaye ne? Kokuma idan andaukesu aiki
Hakan Yana nufin za'a iyayin komai dasu?
Kuma still yanzu azo ace Wai anbada ita, saboda me? Bazai iyu Bama Alhaji, kamaida
musu kayansu, ta watsar da goron aqasa 😭
Hannayenta yakama yace hafsat, kiyi hakuri, nasan Yaron nan da iyayensa sunyi Mata
laifi, kuma sunzo Har gida sun Bata hakuri kema kuma sunbaki, sannan sun sake neman
yafiyarku
Kisani Allah mafa muna masa laifi kuma yayafe mana
Bare mu Yan Adam, yanzu hafsat idan kikace nakoma namaida musu kayan Saka ranarsu,
mekike tunanin zai faru? Kina nufin suma zasu Bawa danmu ameer yarsu ne?
Hafsat bazasu bashi ba, saboda muma mun hanasu tamu yar
Alhaji Dan Allah kadenamin maganar wannan marar mutuncin Yaron 🤣🤣tatashi fuuuu tayi
dakinta, Alhaji Tahir ya girgiza kansa sannan ya tsugunna yasaka hannu ya tsince
goron da alawar
Cikin ransa Yana cewa nide bazance komaiba kiji babu dadi kice nayiwa Dan
yar'uwarki maganar daba daidai ba🤣🤣🤣
********
Yana zuwa yadanna door bell,   Sajida tatashi tabude, tana ganinsa tasaki murmushi
laaa uncle ashe Kaine, sannu   da zuwa
Ashe yau da babban baqo kazo   mana, kawoshi, ta meqa hannu takarbi Aududu dake
hannunsa
Tajuya tana cewa Bari nakira   mama
Akujera ya zauna, Safah takalleshi tace uncle sannu da zuwa Ina yini?
Shima Yace lafiya ataqaice,🤣 wato wannan yarinyar shi zata gaisar asheqale
ko,yagama lura bataso ma ta kalleshi, to menene da jikin nasa daza'a qi Kallansa?
Itama anata bangaren takaici ne yakamata, ita bazai tambayata ko Yaya gida ba?
Batakai ba Kenan
Tasake dubansa tace uncle ashe kaima kana zuwa gidan anty jiddah
Daria tayi tasake cewa to ai yanzu Bata nan uncle, ko wajan wata kazo🤣🤣
Dasauri yace no, no, nazo wajan antynku ne, daganan kuma zan wuce wajan haneefa
Aikuwa uncle muma saimu bika muje muganta, rabonmu da ita tun shekaran jiya
Cikin fishi Shima ya kalli Samah din yace ke wato bakida kunya ko? Ba'a Isa dake
ba, ba'a Isa asaki bako?
Dede lokacin anty jidda tazo tatarar da wannan rikicin nasu, Safah kuwa Daria kamar
me, in Banda Abu irinna uncle Bilal meya Saka Samah din taqi yi? 🤣🤣
Yawwa anty
(mamaki yakamata, yau Bilal dinne yace Mata anty🤭to inajin de da biyu🤣)
Safah tace anty, sannan ta kalli Bilal tace uncle inkun Gama ka tabomu saimu wuce
Suna tafiya anty jidda tace Dr Dama zan Baka hakuri ne Akan komawar haneefa
gidanmu, banyi Hakan dawata manufa ba, saide Inada babban dalili na nayin Hakan
Dr haneefa itace tafara son haneef, naji hakaanne lokacin dasuke fira itada
sajidata
Nan ta bashi labarin komai
Sannan taci gaba da fadin nabarta Takoma can dinne saboda shaquwa tashiga
tsakaninta da haneef Har Shima yasota, saboda a lokacin anriga da anyi masa Matan
dazai aura
Kuma sai gashi alhmdlh yafara yimata sonda ita Kanta tasan Bata sonsa Har haka,
likita cewa yayi zuciyar sa zata Iya samun matsala idan ba'a bashi abinda yake soba
Anty jidda tace to wannan ne dalili na, Amma ban karya alqawarin Dana dauka maba
kayi hakuri
Yace a a Wai baki saniba? Dazu fa su Alhaji Tahir suka kirani Wai naje manema
auren haneefa sunzo
Ai anma Saka Rana nanda wata daya biki, itada ameer da Safah
Yanzu hakama zuwa zanyi gidan inji menene za'a fara shiryawa
Cikin mamaki tace to aikuwa su momy basu fada ba, kuma da alama ma yanbiyu basu
saniba
Tana zuwa Dakin tace yanbiyu tahowarku kuwa daddy Yana gida?
Suna zuwa wajan motarsa sukaga Yana waya, aikuwa suka Bude suka shiga baya Dukansu,
Aududu Yana hannun Samah
Yana Gama waya, yashiga yatada motar, yajuya ya kallesu, waiku driver Kuka samu
kome? Duk kun shige baya 🤣🤣
Yakalli Samah data riqe Aududu, yayi tunanin Safah ce, saboda yasan cewa Samah
bazata karbi dansaba, dan haka tunanin sa yabashi Safah ce yace, Shiyasa nace Miki
banason damuwa😣
Cikin fishi ta kalli sajida da Safah tace Aidama Saida nace muku karmu shiga karmu
shiga Kuka nace, aiga irinta nan
Tabude murfin motar tafice ko rufewa batayi ba
Ita kuwa tana tsaye, yaleqo ta window yace idan bazaki shigo ba kifadama na muwuce
Tace wallahi bazan bayarba, kuje kawai, driver anty jidda yakawoni
Nifa bance kishigo ba, cewa nayi Bani Dana,sai driver yakawo ki, Nima ai banqi Taki
ba🤣🤣
Kut lalle yarinyar nan, nizata maida mahaukaci Ina Mata magana ta kyaleni tatafi
Burum yabude motar yafuto, yanufeta gadan gadan, yasha gabanta yatsareta da ido,
lokaci daya yayi Mata kwarjini taga yacika Mata ido
Lokaci daya qwalla tacika idonta cikin muryar Kuka tace Allah bazan Baka Shiba
Suna tafiya ahanya ta kawar da Kanta can gefen window, Bama ta kallan inda yake
Samah tafara kici kicin budewa taji Mota arufe,tasan Sarai shine yarufe, Tajuya ta
kaalleshi cikin mamaki
(da alama de hajiya hafsat tadauki fishi dayawa, abin yamata rauni🤣Dan yafi karfin
ciwo)
Wannan page din nakune masoyan wannan littafi, nabaku shi kyauta🤗
Masu sharhi wallahi kunfi kowa birgeni, dan Allah adinga sharhi tahanake zanji dadi
Har insamu qwarin gwiwar yin wani typing din 😊, sharhi Yana temaka wa Sosai, Amma
wasu basayi saide acema tnx, wasu kuma suce godia, Wanda sukafi Bani Daria ma sune
masu cewa t, Wai t , nide dakacemin t Har gara kacemin sannu wance😃😃, nasan ka
kulani
Posting din yau zakuga baida yawa wallahi zazzabi nake, tun Daren jiya, dan yau
banmayi tunanin zanyi posting ba, to Amma nasan za'a jirani, ajini shiru, Shiyasa
nace bari naayi ko yayane yafi ace anji shiru din, babu sanarwa
Koda ace kunjini shiru to wallahi zazzabi ne yahanani typing, idan kuma kunjini
shikkenan Dama haka akeso, gani nande under probability
Ngd Sosai 🙏🏻
Amnah Muhammad El yaqoub ✍🏻SHALELAN BABA💕
          (Romance)
Writing by Amnah El
Jinjina gareku
D prince Abba
Princessiko
Maman maama
Samira Aliyu
Nawara Ahmad
Maman Ja'afar
Maman mee'ad
Fatima salihu
Maman Yasmeen
Samira Yahya(gaisuwarki tana samuna)
Ummu farouq
Kai bazaku lissafu ba, Amma Sarai nasan kowa😃Har masu cewa T, nagode Sosai da
yanda kuke bibiyata, dakuma Jin lafiya ta, Alhmdlh nagode da addu'arku agareni
dukanku masoyana baki daya, zamu Dora daga inda muka tsaya🤗🤗
43&44
Abazata maganar tasa tazo Mata, aure Kuma? Ta kalleshi, menene hadinka da aure na?
Dan Allah kabudemin kofa na fita, wannan wacce irin tambaya ce ta qwa qwa? Tambayar
yaushe zaka mutu na auri maatar ka? Dan kaga budemin infice, inba hakaba...
Katseta yayi inba hakaba me?
Kallansa tayi ido cikin ido tace Aure de? Ni in aureka? Allah yasawaqe ko maza
sunkare 🤣budemin kofa nafita Malam
Aikuwa aure dole, da kinqi da kinso saikin aureni, a Hakan kuma mazan basu qare
dinba kinaji kina gani dolen dolenki ki zama tawa
Batace masa komai ba tafara kici kicin Bude kofar saide abin takaicin yaqara Bude
Mata
Kanta tadafe Osai hawaye, lokaci daya jikinsa yayi sanyi, yace sorry, yamiqa Mata
hannu yace Bani Abdallah na saina Bude Miki kifice
Yace, kibanishi mana, tasake shareshi, yasaka hannu zai daukeshi da kansa, Tariqe
Yaron gam 🤣
Cikin fada yasake cewa nace kibani shi nabude Miki kifice kinqi Bani, kinzo kin
tisani agaba kinamin ihu, mekikeso namiki? Yamaida hannu Kan Aududu Yana kokarin
daukeshi
Itama tafara kici kicin rikeshi 🤣, Garin kokarin qwatar yaro hannunsu ya sarke da
juna, lokaci daya wani irin shock ya kamasu, cikin sauri kowa ya janye hannunsa
********
Suna shiga falon sai Mami suka gani ita kadai, cikin fara'ah ta kallesu tace a a
yau yanbiyu ne a gidan Namu? To wacece ne acikin ku Samah ce ko Safah? 🤣
sajida tace Mami wannan Safah ce, nikuma sajidan anty jiddah
A a, sajida sannunku da zuwa, ta kalli Safah, kuma ke Banda abinki sai kiyi shiru🤣,
aini ba sirikarki bace maminki ce, taso kidawo nan ki zauna, ta nuna Mata waje kusa
da ita
Cikin kunya ta girgiza Kanta, murmushi Mami tayi tace tokushiga Dakin nasu, suma su
Haneefan suna ciki
Sajida tace to Mami, suka miqe sukayi ciki
Mami tabi Safah da kallo, ita kunya ameer kunya, ko Yaya za'ai wannan Zaman aure 🤣🤣
Samah ce tashigo da yaro ahannu, mami ta kalleta taga alamun kamar tayi Kuka, ga
kuma yaro a hannun ta, Amma Sai tayi shiru, Har qasa itama ta gaisheta cikin
fara'ah Mami tace Samah sannunku da zuwa, wannan din Yaron Waye ahannunki?
Bilal ne yayi sallama yashigo, ta kalleshi, anan Mami tagane Kenan Dan nasane,
Samah tatashi tayi hanyar Dakin da batasan ma ko shine nasu haneefa ba, sai tayi
dace shine 🤣
Mami tace a a likita bokan turai, Saida yashafa sumar kansa yagaishe ta cikin
murmushi
Tace lafiya kalau muke baban haneefa, Ina kasamo mana yaro ne?
Ina Tambayar Samah Naga tana kallonka, ga idonta kamar tayi Kuka
Mami Abdallah nefa, qanin haneefa, nakawo Mata shine, rannan munyi magana da ita
tace tana so naganshi, nakawo Mata shi, shine Samah ta karbeshi
Kuka kuma saboda nace ta aure nine, shine take Kuka, waai ko maza sun kare🤣
Murmushi Mami tayi, Kai Bilal wannan fadan naku babu ruwana aciki, yafi karfina😃
Tatashi tsaye Bari naturo Maka abban afran Yana ciki
********
Tana shiga Dakin duk suka bita da kallo, sajida tace kaga masoya
Ku futowarku daban ce
Qyaleta tayi tanemi waje a gefen gadon ta zauna, ta ajiye Abdallah, shalele tasa
hannu ta daukeshi cikin murna, ya kalleta yaga baisan taba aikuwa yafara Kuka
Takalli Afrah tace Kai kiga Yaron nan Afrah nizaiwa qiwa, Afrah tace ato Ina
yasanki
Sajida tace wallah muma bai sanmu ba, Amma damuka daukeshi baiyi Kuka ba
Ta Kalle shi tace Kai Aududu, tsabar rashin m karasa wa zakayiwa qiwa saini?🤣
Afraah tace Dan Allah ki ajiye Yaro yaje gun Wanda yakeso anan,kawai kin matsa masa
Sajida tace kawoshi, takarbeshi, aikuwa yayi shiru, suna zaune Yana hannun sajida
saiya koma wajan Samah, Kodan yaga ita tashigo dashi ne oho
Ita Kuma tana cike cike da haushin Bilal, kuma tashigo ma ba Wanda ya kulata🤣,
saita shareshi, kawai tasaka Kanta acinya tasa musu kuka
Kunsan Yaro, idan yaga babba Yana Kuka Shima kukan yake, dan haka Shima Aududu
yasaka Kuka
Duk suka juya suna kallan su, Safah tace a a me aka musu ne, dagake Har Yaro kuna
Kuka
Safah na ganin haka tafara hawaye, tace Samah Wai miye na kukan,? Wallahi idan baki
daina kukan nanba Nima bazan Dena ba, ai kinsan de abinda Hakan yake jawo mana
Sajida tayi murmushi tace um yau munga Yan biyu🤣🤣, wato muda ba Yan biyu ba, mune
kukan baya jamana komai 🤣
Haka suke wallahi, daya na Kuka yanzu dayar ma zata fara koba dalili, aide yanzu
kingani, tunda bataji komai ba tahau kukan itama🤣, idan jinya daya takeyi to itama
dayar yanzu zakiga ta kwanta, Dama can haka suke, karku damu
Cikin Kuka tadago Kanta tace Wai cewa yayi wallahi saiya aureni, nace masa banaso
banaso Amma yace shi wallahi saiya aureni, nikuma wallahi bazan yardaba yaje ya
aureni yakaini gidansa yaita jibga🤣🤣
Safah ta share hawayenta ta harari Samah, tashige toilet domin wanke idonta 🤣
Afrah tace kuma yanzu menene abin Kuka Samah?gayen baida matsala, kawai de kunsamu
sabanin fahimta ne, ni banga aibunsa ba
Shalele tace nikam nayi murna, zanyi farin ciki idan kika aure shi, sannan ta kalli
Afrah kekuma Afrah karki sake cewa babana Gaye, saikace wani Yaro?
Afrah tace to sister haneey tsoho🤣Kema Naga alama zamanki dashi yafara shafa Miki
son girman
Tace eh naji
Sajida tace yanzu de Samah kiyi hakuri, Kinga dukanmu muna San abin nan, idan kika
amince shikkenan zance ya qare
Safah data futo daga toilet itama tace ku kurabu da ita, tana Sansa gulma ce, gashi
nan ta riqe masa da, idan Bata Bata Sansa ai bazata so Yaron saba
Afrah tace laaa waiji kuke dansa ne?qanin haneefa nefa, Yana son Yara ne kawai
shiyasa ya riqeshi
Samah da sai yanzu tayi magana tace au dama ba dansa bane shine yaketa nuna min
wani iko? Harda cemin nabashi dansa ni driver yakawo ni?
Wallahi DANA SANI tun a lokacin zan ce masa yabari saiya Haifa tukunna
Yayi shiru a office dinsa shi kadai, ga ayyuka agabansa nan yakasa qarasawa,
yarinyar nan tana so ta kashe shi,Ptun ranar dasukazo gidansu Har yau taqi Bude
wayarta, Yaya takeso yayi? Hauka takeso tasashi kuma Bayan jinyar daya kwanta
adalilinta?
Wayarsa tayi qara, yadauka yakara akunne, yallabai anturo design din takalman
dakayi magana a kansu tun jiya Amma bakayi maganar meeting din da za'a yiba
"Zan nemeka Bayan naduba" abinda yace Kenan, daga daya bangaren akace Okey sir
Turo kofar office din nasa akayi, wani ma'aikaci ne, yace yallabai ga wadannan
takardun Wanda zaka duba ne kafin a shiga meeting, anriga da angama aikin komai,
saide dubawarka dasaka hannun ka da ake jira
Sannan akwai turawa dasuka turo mana appointment latter daga Singapore 🇸🇬
Karbar takardun yayi yace OK munir zan duba, sannan meeting asanar za'a zauna gobe
insha Allah
Saida yaga yaci karfin aiyuka dayawa sannan yatafi gida yamma lis
********
Mami tace Alhaji bazaka fahinceni bane, bakasan inda magana ta ta dosa bane
Cikin zafi yace aikuwa inde ban Fahimci inda maganar ki ta dosa ba, to bazan
fahimta ba kuwa hafsat, nide nafada Miki babu inda zan maida Kaya, saboda me? A
wanne dalili? Sunyi laifi anbaku hakuri, yaran nan daga haneef Har haneefa yaranki
ne
Bilal yayi murmushi yace Mami kiyi hakuri, tsakanin da kunya ace Ana maida abun
Saka Rana, sannan sunasan junansu, kawai ayi musu adduah abarwa Allah komai
Kallansa tayi, Bilal haneefa batasan haneef, jinake a gabanka tace ita batasan shi,
to saboda me za'a takurawa yarinya, a Barta tayi karatunta
Alhaji Tahir yace, hafsat anriga angama magana Akan karatun yaran nan, zasuci gaba
da zuwa school dinsu, sannan Alhaji bukar yace zai hadata da yaransa su shiga
University tare, hafsat me kuma kike buqata Bayan haka?
Tace Shikkenan Alhaji, Amma Bari na Kirata naji ta bakin ta, hankalina zaifi
kwanciya
Hajiya hafsat da Bilal dabasusan da wannan magar ba sukace kudi kuma? Yaushe ?
Tace akuje
Nan tabasu labarin komai, sannan tace shiyasa nake Sansa amma saisu momy suka
Koreni, shine nace nafasa
Saida Bilal yasake Bata hakuri, tanuna masa komai yawuce, sannan su Afrah suka futo
suka rakosu wajan Mota zasu tafi
Da Aududu yakoma, Saida yakai su Samah haar gida sannan ya karbi number ta a wajan
Safah, data Daddynsu, yaja motarsa yayi gida baiko kalli Samah ba🤣🤣
********
To Alhaji kunje gidan Alhaji Tahir Amma kazo kayi shiru bakace mana komai ba
Momy tace alhmdlh, Allah nagode maka, yanzu kuma saide in Kira hajiya laraba nabata
hakuri Akan hajara
Suna zuwa suka dawo dashi, daddy yace to Dama magana ce Akan aurenka, dazu munje
mun nemama auren haneefa a wajan Alhaji Tahir, kuma anbamu harma ansa Rana nan da
wata daya biki, dakuma na Safah da Ameer
Haneef yayi murmushi yace to daddy godia nake, Amma daddy ya maganar hairat?
Hairat tunda kace bakaso ai shikkenan, Alhaji shazali ai munfi San lafiyarka Akan
jinya, yaqarasa maganar cikin barkwanci 🤣🤣
Ai farin cikima daaya Kenan Ajmal, daga yau kawai ka kirani da angon next month
Yace wallahi, Nima yanzu daddy yake fadaamin, Amma fa yarinyar nan sainayi da
gaske, wallahi taqi Bude wayarta, gaba daya ta toshe kafar da zan sameta
Sai Bayan sallar magrib sannan Ajmal yazo suka wuce gidan Mami
Suna zuwa, suka zauna afalo, Mami tana ganinsu tace a a su haneef ne a gidan Namu,
sannu ku da zuwa, Alhaji Tahir yadawo daga masallaci Shima suka gaisa sannan yayi
ciki yanayiwa hafsat kallan maganin ki kenan🤣🤣tunda gashi anfara Mata sintiri
agida, baga Mata ba, baga maza ba🤣🤣
Mami ta kallesu tayi hamdala da yaran Nata basa falo, tace haneef saide fa kuyi
hakuri, mutuniyar Taku yanzun nan suka fita, sunje zasusha ice cream sudawo,
yanzunnan suka fita, da kunzo kafin minti biyar ma Dakun samesu 😲
Kansa yadafeP, to Mami idan nakirata wayarta a kashe, kuma taqi nemana, Mami metake
so namata ne?
Dasauri tace a a haneef, kada kuzauna Kuma su Bata muku lokaci, zansata takiraka
idan sun dawo, yace toshikknn Mami, mu zamu wuce
********
Washe Gari momy takira Mami Akan kayan lefen Yara, tace hajiya hafsat Yaya kike
ganin za'a tsara kayan nasu?
Mami tace hajiya ai kece babba, duk yanda kikace, Yara ai duk na kine
Momy Taji dadin furucin hajiya hafsat tace to nida cewa nayi haneefa sutafi da
jidda da haneef saisu siyo abinda takeso da Kanta
Mami tace eh hakanma yayi, babu damuwa, abinda basu siyoba sai ayi ordering nasa,
momy tace to shikkenan wannan de duk maganar mu ce, bamusan Yaya su alhajin
zasuceba, duk de yanda Kuka yanke keda Alhaji Tahir din naji, Nima nan idan Alhaji
yadawo saina fada masa naji yanda zaice
********
Da yamma Yana dawowa daga wajan aiki yayi wanka, yashirya cikin Qananun Kaya,
meeting suka Gama Yagaji Sosai, key din motarsa yadauka ko abinci baici ba yayiwa
momy sallama yatafi gidan hajiya hafsat🤣
Yaarasa gane maganar wa zai yarda da ita acikinsu? Ita Afrah ranar dasuka zo, tace
zata yi Mata magana ta Bude wayar, ita Mami jiya tace dasun dawo zata sata ta
kirashi, Yana tunanin akwai abinda Mami take boye masa, to Gara yaje wajanta Kai
tsaye yaji dalilin wannan shariyar, yafi sauqi, yau Kam inta kama ko kwanane
saiyayi a gidan Mami, Amma bazai taho ba saiya ganta, 🤣🤣
Yana zuwa kuwa yayi parking yashiga falon, Mami na zaune cikin ranta tace yau Naga
idi🤣🤣
Tace sannu da zuwa haneef, Bari nakawoma ruwa, tashige kitchen tana tunanin irin
dabarar dazata masa yau 🤣
Yana ganin shigarta kitchen yatashi yayi wuf yashige dakinsu Afrah
Suna zaune suna karatu itada Afrah sai ganinsa sukai yashigo Dakin da sallama
Afrah tace Yaya Ina yini
Mami na futowa daga kitchen hannun ta daukeda ruwa da just taga falon Wayam babu
kowa🤣
Adede lokacin Afrah tafuto daga Dakin nasu danta basu waje
Dakin ku?
Sharhi
Comment
Share
Dan Allah🙏🏻
45&46
Bazade ki sakeniba ko Afrah
To yanzu Mami in kinshiga me zakiyi? Haba Mami Yaya haneef nefa? Dan Allah ki zauna
Zama tayi Akan kujera tace to Afrah bari nazauna Naga da idon dazai futo ya kalleni
Uwa tana zaune kashiga Dakin yarta
********
Saida ya qare Mata kallo, Yana tsaye, uniform ne ajikinta da alama daga school
tadawo
Kanta babu dankwali Amma akwai kitso manya, sai littattafai dasuke gabanta
Ita Kanta taji kunyar ganinsa, saboda tasan tayi masa laifi, but mazan ne Sai ka
Dan gwarasu wani lokacin za'a daidai ta duk da kana sonsu, Hakan bazaisa ka zaqe ba
Ajiyar zuciya yasauke, yatako yazo gar gaban gadon ya zauna daga gefe
Yazuba Mata ido
Uncle kisa.. 🤭
Yes, gashi kin hanani ganinki, kin kashe waya, bakya nemana, ke ko ajikinki, jiya
munzo kunfita kuma dakuka dawo baki nemeniba, kuma Saida nace zan jiraki Mami tace
Baku Dade da fitaba
Shiru tayi tana tunani, unguwa kuma? Itade tasan suna gida, to may be Mami ce
tafada masa haka🤣
Baice Mata komai ba yatashi daga inda yake yadawo gabanta ya tsugunna daga kasan
gadon, hannayensa duka biyu suna zube Akan gadon
Yayi qasa da murya yace ba hakuri Zaki banida, ni bakimin laifi ba, kuma nasan
bazakimin insha Allah, kawai nide ki Bude wayarki, rashin Jin muryar ki zai haddasa
min damuwa fa, yanzu ma kinsa duk na kasa aiki a office, duk kinbi kin susutani
Kinshiga cikin zuciya ta kin zauna haneefa, bazan Iya rayuwa batare dake ba
Wata irin kunya ce ta kamata, Wai yau haneef ne a tsugunne a gabanta Yana fada Mata
wannan kalaman, tasa hannun ta tarufe idonta 🙈sannan tace Kai uncle please nide
katashi
Dogayen yatsun hannunta ya kalla, a hankali yasaka hannu yajanyesu daga Fuskarta
Yariqe hannun cikin nasa, sannan yatashi ya zauna dab da ita, ya kalli takardun
gabanta yace meyasa kikamin wannan abubuwan?
Wani iri takeji ajikinta, dazai gane daya sakar Mata hannu,ahankali tace eh
Kinyi alqawari?
Nayi uncle
Ta gyada masa Kai, Ina ganewa abinda ban ganeba Afrah tanamin bayani
Yanzu ma itace take sakemin
Yanajin abinda take yasake riqe hannun, hannun Nata very soft, Shiyasa yakejin
dadin riqewa
Karatun yafara yimata, yanayi Yana murza hannunta, hannunsa na yawo acikin tafin
hannunta
Kanta a sunkuye takasa Kallansa, shikuwa duk bayanin da zai Mata idonsa akanta
yake, basuyi da yawa ba ta dauke littafin tace uncle ya Isa, tayi hakane hakane
danta qwace hannun ta, taga alama bazai gane irin yanayin datakeji ba, wani iri
haka duk ba dadi
Kallanta yayi yasaki murmushi, yace Toni bai isheniba, yakai hannunta bakinsa ya
lumshe idonsa, sannan yasakarwa hannun Nata wani irin zazzafan kiss
Sannan yasaki hannun, ya gyara zama Sosai, Yana fuskantarta, yasaka littafin
atsakaninsu, sannan yayi gyaran murya yabude muryar sa Sosai yafara yimata karatun
dalla dalla 🤣
Mami afalo taji shiru, tace um Afrah bakida hankali ke yarinya ce, Bari kiga na
dubo yaran nan🤣
Mami na zuwa tagansu a zaune a gadon, ga littafi atsakaninsu Yana yi Mata karatu 🤣
Saida yadan Sosa kansa sannan yace wallahi Mami Ina tayata ne
Har cikin ranta taji dadi, haka kuma lokaci daya tasaki sisiyar ajiyar zuciya 🤣tace
to idan kungama haneefa kizo ki hada masa abinci
Tace to Mami
Sai wajan biyar da wani Abu suka Gama karatun, tagane Sosai yanda batayi zato ba,
tashi tayi ta ajiye book din yabi bayanta da kallo, wannan yarinyar ai dole ma tayi
nauyi irin wannan uban hips din Nata 🤣
Ita kuwa Batasanma yanayiba, ajiyewa tayi tace muje uncle, nazubama abinci
Da lumsassan idonsa ya kalleta, saide kiyimin kunun gyada idan kin Iya
Murmushi tayi masa tace Bari inje inyi maka, tayi gaba, Dasauri yasa hannu yariqo
Nata, sannan yace muje
Falo suka futo, shiya zauna Yana canja Channel din kallo zuwa labarai
Ita Kuma taja Afrah suka shiga kitchen
Suna aikinsu suna fira, Afrah tace nikam Yaya haneef soyaiyarsa taana birgeni, babu
ruwansa dawani boye boye, kinsan Mami fa Nina hanata shiga dazu🤣wallahi cewa tayi
saita shiga
Shalele tace Mami na Kenan, aigara tazo tasani ko yankewa yarta Kai zaiyi?
Dukansu sukayi daria, Har suka kammala sannan suka kawo masa, Har qasa ta tsugunna
tazuba masa, ta kalleshi to uncle gashi
Murmushi tayi tatashi tabar wajan, Afrah na kallan su daga gefe, kome yace Mata?
Shide komai nasa a hankali cikin sigar rada, inba kana kusa dashiba, ba lalle bane
kaji meyace
Shi Yana gefe Yana shan kununsa Yana kallo itada Afrah suna gefe a zaune, Har aka
Kira sallar magrib, yaje yayi sallah yadawo, ya kalli Afrah qanwata ku shirya mana
muje ku rakani unguwa
Afrah Dama Zaman ya isheta, kullum mutum Yana gida ba yawo tace to Yaya, sukayi
daki suka shirya cikin sauri, Dakin Mami sukaje sukayi Mata sallama sukai fice,
afraah na baya, su kuma suna gaba
Har yakaisu wajan shan ice-cream, su kasha, ya lodo musu wani, Yana ganinsu sau
murna suke, Shide kawai kallan su yake, yarintama da dadi take 🤣🤣daga zuwa wannan
wajan shine abin murna, sude Yara kullum basa gajiya da Abu, inba hakaba jiya jiyan
nanfa sukazo🤣🤭
Daga nan sukaje yasiya musu shawarma dasu boga sannan suka tafi gida, a harabar
gidan ya ya tsaya, Afrah ta kwashe musu kayan tayi cikin gida, Shikuma ya dubeta
yace kada ki manta fa, kibude wayarki
Wani irin yanayi yashiga sakamakon wannan shagwabar data masa, Har baisan lokacin
daya kwanta da kansa a jikin seat dinba
Shiru tayi, can de tace masa I luv you uncle, thnks you for everything Tabude motar
tafice da gudu, murmushi yayi, sannan yaja yarufe yayi gida, Yana hanya saiyaaji
kamar ansauke masa wani nauyi a kansa
********
Washe Gari takama weekend, Mami takira Dr Bilal yazo Har gida, suka dunguma gaba
dayansu suka tafi kuje, suna tafiya ahanya sunata fira abin gwanin birgewa Mami da
shalele da Afrah Abaya sai Aududu dake cinyar Mami, Shikuma Dr Bilal suna gaba
shida ameer
Ta kalli gidan, aduk lokacin data zo kuje babu mutumin dayake fado Mata irin baba
Rayuwarfa Kenan, Har anzo anyi antafi
Da gudu taje ta rarumi shalele tace, shalelan baba? Wai kuwa kenake gani?
Inna sabuwa tabisu Mami da kallo tace wannan ai hajiya ce dasukazo kwanaki,
sannunku da zuwa
Tashinfida musu tabarma, suka zazzauna, aka sake gaisawa, sannan tace gashi kunzo
malam baya nan yatafi kewaya, Amma bar atura yaro yakirashi
Nan da nan tatura danta yatafi Kiran baba malam, shalele tace Inna sabuwa baki gane
wannan bane? Tanuna Mata Aududu
Inna sabuwa ta kalleshi tayi shiru, shalele tayi daria Inna Aududu nefa
Laaa Wai Aududu ne ya girma haka? Kekiga yaro yayi bulbul jajir dashi Dan Allah 🤣🤣
Tace hajiya ai ba abin daria bane, yaro duk ya sauya kamanni, tatashi tafice
saigata yadawo da ruwa pure water 💦me sanyi
Dukansu kuwa suka Sha, akaci gaba da fira, malam yahai na zuwa yace a a a a kice
yau shalelan baba ce dakanta, Dukansu Saida yabasu daria
Baba malam yace ai hajiya Kowama anan Garin shalelan baba yake cemata, saide Yan
makarantar su ne suke kiranta da haneefa
Amma kinga malam surajo, tunda nake dashi zaiyi wahala kiji yace haneefa, saide
yace Shalele nah, komai de Shalele nah
Lokaci daya qwalla tacika idonta, tace hakane kam baba malam, ni tunda nake da baba
ma bantaba ji yakira sunana ba, saina ranar dazai rasu
Tana fadar haka tafashe da Kuka
Gaba dayansu jikinsu yayi sanyi, barinma Bilal da agabansa akai komai, shi kansa
yaji mutuwar mutumin, suna wannan halin shiyasa a lokacin yayi mamakin Ina shalele
tasamu wannan kudin aikin da akayiwa babanta, yaga alokcin Yana fada babu ko dar
tace zataje tabiya, ashe Shikuma wannan ta dalilin haneef tasamu, Dama can Allah
yariga daya tsara komai, Shiyasa ya aiko Mata shi a lokacin daya dace kuma akayi
sa'ah ya temakesu Akan kudin
Baba malam yashare qwallarsa yace naje wajan liman nayi masa magana Akan gidanku da
kuma gonakin malam surajo, akwai gonakinsa na shinkafa guda biyu saiwata gonar
dayake shuka ayaba, dakuma wasu guda biyu dayake shuka kayan gwari aciki saikuma
fili guda daya, sai kuma Yan kudadensa dasuke wajena gaba dayansu, ansanar aagari
idan akwai Wanda yake binsa bashi to yazo yasameni yayimin bayanin komai, to
Alhmdlh babu kowa, ko mutum daya babu
Saikuma amfanin gonarsa yafuto ancire, nakaishi kasuwa ansiyar, Shima duka kudin
Yana nan a ajiye
Liman yace nabar takardun a hannu na idan kika zo sai ahada da kudin Araba muku
keda dan'uwanki Aududu
Jin wannan bayanin na baba malam saiya Sakata Kuka riris, shi kansa baba malam din
hawaye yake, sai sharewa yake da babbar rigar jikinsa
Afrah Kam tuni takasa tsaida hawayen ta, Kai Allah yaqarawa iyayenmu lafiya da
nisan kwana, ta tausayawa shalele, haqiqa taga rayuwa, itadin abar atausayawa ce
Mami ce tayi karfin hali tace malam yahai ai baza'ai hakaba, Har gobe Kai ubane a
wajan haneefa, kunyi zama na Amana atsakaninku, babu maganar Rabe Rabe anan,
haneefa de macece, kuma duk Daren dadewa gidan wani zata, kuma abune dayake a
baiyane duka dukiyar za'a Raba gida uku, shi Abdallah yadauki kaso biyu ita Kuma
tadauki daya, kamar yanda ubangiji yafada acikin aqur'ani, cikin suratul nisa'i
ayata goma, saboda haka Kaci gaba da amfani da gonakin nasu, Har Allah yaraya
Abdallah saiya riqe musu gaba daya shida yar'uwarsa, duk da tafishi shekaru shi
namiji ne, zuwa gaba shine zai jagoranci rayuwarta, batada kamarsa, Shima haka
Maganar kudi kuma kasa ayi bohol dashi a makaranta, kokuma acikin masallaci al'umar
annabi sudinga diban ruwa, Duk Wanda yayi amfani da ruwan Allah yakai ladan kabarin
malam surajo
Gaba dayansu suka amsa da ameen, baba malam yace hajiya ai duk da haka kudin sunada
yawa
Tace karka damu malam yahai, kasa ayi bohol din kawai
Yace to toshknn hajiya, daga gobe zan Nemo ma'aikata ayi famfouna da bohol
amakarantu Dama masallatai gaba daya insha Allah, abinda yayi Saura kuma za'a yi
masa sadaka dashi
A a shalelan baba, ayiwa malam surajo, Shima yayi mana lokacin dayake Raye
Shakeran jiya sha'aban me kaiii makaranta kuwa yazo yakawomin machine dinki, nace
masa a a yaje saikin zo saiya dawo
Daria tayi tace kawai kace nabar masa baba malam, yace to za'a fada masa
Mami tace malam yahai yarkafa zuwa mukai musanar dakai ansaka Rana
Tace a a bashi bane, wani dan'uwanmu ne Shima, nanda kwana 38 za'ayi insha Allah
Alhmdlh, to hajiya ai wannan babban albishir ne, Allah yakaimu lokacin, ya kalli Dr
Bilal yace to likita ya zatayi aure, Shikuma baban sai yaushe? 🤣🤣
Mami tace to idan Allah yakaimu angama biki lafiya, sai kayi shirin tafiya umara
kaida hajiya sabuwa
Ai Inna sabuwa najin haka tasaki Buda, Dukansu Saida sukai daria Sosai
Haka sukaita zubawa Mami godia, daga nan tace suje wajan Marka, akai Mata danta
taganshi
Baba malam ne yayi musu jagora, sukaje Har gidan, ahalin dasuka ganta, sun tausaya
Mata, tana Kuka tanemi yafiyar shalele, tace babu komai Inna nayafe miki, aka Bata
Aududu saide kuma babu idon gani
Dakanta tasake roqarsu alfarma su riqe Mata shi, kada su duba abinda tamusu, suduba
halin ubansa malam surajo kawai
Haka suka bar gidan cikin sanyin jiki, gaskiya dan'adam ba'a bakin komai yake ba,
anan Garin kuje suka wuni, sannan suka tafi gida yamma liss
********
Washe Gari Dr Bilal yashirya cikin manyan Kaya, yayi mugun kyau, yadauki hajiya da
sady da Abdallah sukayi gidan mami
Mami tace a a kace neman auren yayi Nisa, Gara de anema Kam, kowa sai yayi masa
yace zaiyi auren ya, shi baiyi ba
Hajiya tace ato ai Gara kidinga fada masa, qanwarsa ma sadiya jiya Bayan kuntafi
kuje manema aurenta sukazo, Wai zasu kawo gaisuwa nace suhado Har kayan Saka Rana
kawai babu maganar wata gaisuwa, ita bikin Nata sai nanda wata biyu
Shikam Dr Bilal sallama yayi musu yace zaije yadawo saiya daaukesu sutafi
Yana zuwa gidansu momy yakira daddy awaya yace Yana da baqo
Daddy ya yi mamaki wanne baqo kuma? Haka de yafuto, Yana ganin Bilal yace a a Dana
ashe Kaine, yamiqa masa hannu
Dr Bilal yabashi haannu aamma saiya tsugunna bai tsaya a tsaye ba🤣🤣shide daddy
mamaki
Ya Sosa qeyarsa yace a a daddy ba wajan haneef nazo ba, wallahi yau zuwan nakane,
wajan ka nazo, 🤣🤭
Daddy yace masha Allah, to ko daaga wajan daurin aure kake Naga Kaci manyan Kaya
harda babbar riga🤣.
Saida yayi murmushi kin furucin daddy sannan yace a a daddy, Dama Samah ce taturoni
wajan ka 😳😲
Munyi magana da ita, to sai tace nazo wajan ka duk yanda mukai de, mun dedeta kanmu
nida ita, ni inso saamu nema inaso ahada bikin danasu yar'uwarta da yayanta
Daddy yayiwa murmushin su na manya, ai sai yanzu yagane dalilin Saka manyan kayan🤣
ashe wajan surukai za'a zo shine dalili
Amma fa yayi mamaki Jin sun dedeta kansu shida Samah, yaran da agabansa Saida sukai
fada a asbiti lokacin dasuka je Bilal yarakasu wajan haneef? Koda yake yaran zamani
ne qila sun shirya din
Ya kalli Bilal yace to Bilal babu damuwa zaaka Iya turomin magabatanka
To daddy insha Allah zan turo su, Amma daddy Dan Allah kada afamada Mata, inaso
nayi Mata surprise
Daddy baice komai ba yayi murmushi gamida girgiza kai yajuya gida 😃
Dr Bilal na zuwa gidan mami yace su hajiya su futo su tafi, sady ta ware acikin su
shalele sunata firarsu, tayi Mata murna Sosai Akan auren Miji kamar haneef shazali
Saida suka rakosu Har wajan Mota, shalele tace hajiya kinqi yimin kwalliya de
kisamin kwalli🤣🤣
Sady tace hajiya Dama ai itace, dahaka sukai sallama cikin farin ciki
********
Washe Gari kuwa iyayen Dr Bilal sukaje akai komai aka Gama, aka tsaida lokacin biki
danasu shalele, momy tayi farin ciki Sosai zata aurar da yaranta Dukansu
Dr Sulaiman ma dayaji wannan labari sai yace to tunda duka za'ayi wannan auren na
dangi Shima Ajmal idan yashirya kawai yafuto, idan kuma bai shiryaba sai ayi nasun
daga baya, to Dama gwanin naku kamar Akan qaya yake 🤣🤣baisha wahala ba wajan yiwa
iyayen nasa bayanin komai, sukazo suma aka tsaida bikin lokaci daya
Anty jidda tayi murna Sosai, Gara tayi gajiya daya tahuta 🤣
Alhaji Tahir da daddy sunyi magana Akan zuwa siyaiyar kayan Yara
Daddy yace haneefa tazauna saboda karatunta babu inda zataje ta yanke karatunta
Mami taji dadin Hakan Sosai, Koba komai tasan idan yarinyar taxo gidan ma bazai
Bari karatun Nata ya tabarbare ba
Sajida ma tazauna agida tunda ga jiddah nan zataje, yatura Mata kudin komai,
furnitures na yanbiyu, da zata siyo musu, sai kuma na sajida ma dazata siyo duka
Har ita, uku Kenan
Daga can wajan su mami kuwa itace da Kanta zata tafi, zata hadowa haneef lefe da
Bilal data dauke masa nasa, 🤣tunda Yan biyu suka dauko Mata Gara taje dakanta
tahado musu komai iri daya, sai kuma furnitures din haneefa, lefe biyu daa kayan
daki daya
Ita Kuma anty jidda kayan daki uku, sai kuma lefe daya na haneefa, haneef yace zai
tura Mata kudin tasiyo komai, haka ta dage tace wallahi sai yaje, bawani kudi dazai
tura Mata zuwa zasuyi yahadowa yarta Kaya nagani nafada
Tayayama zaice zai Bata wani kudi, ai kawai ita shine kudinta suje kawai tana jidar
Kaya ga ATM dinta haneef akusa🤣🤣
Idan taje tasiyo masa ma ai yadan samu sauqi, ita Kuma tafi so yaji a jikinsa yasan
cewa mace Mai tsada zai aura
Dole sai sake daga tafiyar sukai zuwa Bayan kwana uku tajirashi🤣🤣 yagama ayyukansa
sannan suka tafi Dubai ita dashi kafarta kafarsa
🤣
Saikuma Mami
Bataso suyi kwanaki dayawa a Dubai, tana so suyi sudawo tafara gyara yaranta ciki
dabai
(gaskiya anty jidda zan turo Miki kidnappers 🤣🤣🤣irin wanna tafiya haka ai kinyi
tsada dayawa)
47&48
Kwanansu anty jiddah biyar suka Gama hada komai suka yo gida, ammafa jiki yaji, dan
ba qaramin Kaya suka siyo ba
********
Mami na zaune afalo da yaran Nata maza Dr Bilal da ameer suna ganin kayan, ameer
yace gaskiya Mami sunyi kyau Sosai, kamar safah🤣
Iyee lalle ameer wato nema kake yanzu kakoyi rashin kunya, sunyi kyau kamar matarka
Ajiyar zuciya yayi, ai Naga kin kashe kudi dayawa ne Mami, wannan marar kunyar
yarinyar zaaki siyawa Kaya dayawa haka 🤣
Haba Bilal, kaida ameer ai duk daya kuke a wajena, kada ka manta kariqe yata Amana
a lokacin data rasa Wanda zai tallafa Mata, tana nemanka a lokacin da take cikin
tsaka me wuya
Dr Bilal yajanye tagumin dayayi, ai Mami bakisan rikicin Dana hadawa kainabawa,😣
😣😣
Yaarinyar nanfa batasan komai ba, sannan nace daddynsu kada yafada Mata, nide kawai
mun Riga mun dedeta kanmu😢😢
Tace zancen banza, to me zatace kuwa Bilal, anriga ansiyo kaya an tsaida ranar biki
kuma zasu ce sun fasa ne? Impossible 🙅
Mami kemafa lokacin da'aka yanke ranar bikin yarki, da ranki yabaci, haka kika
tubure kikace sai an maida musu kayansu 🤣🤣
To Kinga Nima zasu Iya fadar haka idan ran yarsu yabaci
Mami tai jimm🤣🤭takasa magana, Saida tayi tunani sannan tace eto babu dadi de
gaskiya, Amma nide Dan Allah kasaki jikinka ayi farin ciki a lokacin da ake cikin
sa, banaso Naga jikinka a sanyaye
Kaje kasameta kayi Mata bayani cikin fahimta, zata fahimceka idan kuma taqi
sauraronka kahadata da Safah
Daga shi Har Bilal suka hada baki wajan fadin Safah kuma!!? 😳
Tace Bilal Kenan, yar'uwata cefa, sufa Yan biyu ne, Safah tana son dangantakarka da
Samah, tun suna Yara nasan halin Yara idan daya tanason Abu daya bataso, to zasuyi
cece kuce dinsu lokaci daya, ammafa daga baya duk suna dawowa suso Abu dayane
Ina tabbatar ma kosu momy saisu Mata magana Tari biris sabanin Safah
Kaje ka gwada, ba'a shiga tsaakanin yanbiyu, idan mutum yashiga ma kunya zaiji,
Shiyasa Yan gidan basa shiga sabgar su🤣🤣
Kafin tace komai shalele tayi sallama tashigo falon, cikin murna ta qarasa wajan
su, Mami kayansu Yaya ameer ne? Ba'a Bata amsa ba tafara dagawa Kai ammafa Mami kin
Iya zabe, kayan sunyi kyau, kuma komai iri daya
Toba dole nasai ko Mai Iya iri dayaba haneefa, sun je sun dauko min yanbiyu🤣🤣
Wayar Mami tayi qara, tana dauka suka gaisa da anty jiddah, banji me jidda tace ba,
Mami tace to shikkenan, kawai Saita dinga zuwa daga nan ba, eh, Toba damuwa, akwai
wata Mata ma Dana Mata waya, zan turota nan gidan naki kawai sai tayi Miki bayani,
Dahaka sukai sallama
Ta dubi shalele tace haneefa jidda tace kidauki uniform dinki da sauran kayan
amfani driver yakaiki can, zakici gaba da tafiya school ta gidanta
Shalele tace to Mami, ta daga wani takalmi da jaka tace Kai wannan kuwa kamar
kinsan kafar Yan biyu wallahi zai hau kafar nan tasu🤣🤣
Mami ta kalli ameer da Bilal tace kungani ko? Bafa zata Dena wannan sururin kayan
ba, 🤣inajin idan taga Nata haukacemin zatayi, dan jidda Ina ganinta tana tisa qeyar
Yaron nan komai siya Mata yake saikace Wanda zasu Bude shago
Suna nan a zaune hartaci abinci tafuto da yar qaramar Jakarta, Afrah tarakota sai
hamma take da alama daga bacci tatasheta
Dr Bilal yace Mami Nima Bari inwuce wajan yarinyar nan duk yanda mukai zan Miki
waya, tace to kawai kutafi da haneefa idan kasauketa gida jiddah saika wuce
Yace to, ya karbi jakar Tata a hannun Afrah sannan yayi gaba
Shalele Saida taje ta rungume Mami sannan taace bye bye Mami, tabi bayansa da gudu
********
Anty mu kinsa andauko mu daga gida, kuma ni wallahi kallo nakema momy tasa saida
muka taho
Anty jiddah ta kalli Samah, me yarinyar nan take nufi? Takirasu nefa gaba daya duk
tahadasu ayi musu komai lokaci daya Amma kuma taga kamar ma ita batasan komai ba
Tace Samah, gyaran jiki fa za'a muku, sannan munyi waya da maminku yanzu tace akai
wata Mata ma dazata turomin ita takanas kawai dantazo tayi muku komai Har gida,
Amma Dan iskanci kina min maganar kallo, Waye yahanaki dauko system din Taki
Sannan tasake duban Samah cikin nutsuwa tace Samah, nasan kece Samah nake Miki
maganar ba ganeki ne baanyiba, Samah kinaso kicemin bakisan dake za'a hada ayi
auren ba?
Aure Kuma anty? Kai anty kinada abin daria wani lokacin wallahi 🤣🤣🤣to dawa za'a min
wani aure?
Tamaida hankalin ta Kan wayar dake hannun ta tana dannawa
Anty me kikace? Bilal kuma? Yaushe? Yaushe mukai haka dashi? Yaushe nace masa Ina
sonsa?
Anty jidda oho muku, Amma kinsan de aure babu fashi, tunda iyaye sun shiga maganar,
bazaki maida mana daddy qaramin mutum ba
Kuka tafashe dashi, kukanta ne yaja hankalin Safah da sajida dasuke daki
Cikin kururuwar Kuka tace wallahi ni Bana Sansa, Allah bazan aure shi yaje ya kashe
niba, Yaushe mukai haka dashi daza'ace za'a Bani shi, Bayan kullum cikin yimin
mugunta yake, Allah bazan yardaba
Girgiza Kai Safah tayi, taqarasa wajan Samah ta dago ta, tace kiyi hakuri mana
Samah, menene aibun Dr Bilal? Yana sonki, Samah bazaki gane hakanba sai nan gaba,
fadan dakuke Bana komai bane sai soyaiya Samah
Cikin hawaye ta kalli Safah tace dayake ke anbaki Wanda kikeso ba dole kice hakaba,
nafasan halin Bilal din, wallahi mugunta ce dashi, mutumin dayake budar baki yace
zai zaneni tayaya da hankali na zan yarda naje gidan sa, nace Miki Bana Sansa ko
dole ne?
Ran Safah yabaci tace shikkenan tatashi tsaye tadauki wayarta tana dannawa
Sajida tace Safah Wazaki Kira? Dan Allah karki fadawa daddy
Safah tace ba daddy zan kiraba sajida, Ameer zan Kira in fada masa nafasa aurensa,
inyaso nisai na auri Bilal din
Samah tanajin haka ta miqe tsaye tafara kokari qwace wayar, Safah ta hanata, tace
Samah wallahi bazan baki wayar nanba, bakince saboda zan auri Wanda nakeso ne yasa
nafadi hakaba? To daga yau Nima nafasa auren ameer din, taqarasa maganar tana
fashewa da Kuka
Itama Samah din cikin Kuka Safah nace ki Bani wayar nan ko?
Itama ta kalleta cikin ido tace Samah Abaya Kam duk na Miki biyaiya amatsayinki na
yayata, Amma Banda yanzu, kije kiyi abinda kikaga Dama Nima zanyi abinda nagadama
Zan auri Dr Bilal, Kema kije ki auri ameer, Kinga anyi 50 50 kowa ya auri Wanda
baya so, tunda haka kikeso
Anty jiddah tayi shiru tana kallansu, yau Kam tasan ran yanbiyu yabaci, Bata taba
ganinsu suna sa'insa Har hakaba
Suna wannan koke koken Haneefa tashigo itada Dr Bilal, sun danna door bell sunji
shiru Dan haka kawai sai suka shigo
Haneefa ta kalli kowa tace mama lafiya? Meyake faruwa? Naganku duk a tsaye?
Ya amsa Mata idonsa nakan Yan biyu dasuke Kuka, yakasa gane wacece Samah dinma
acikin su
Harara Samah ta wullo masa, tayi cikin daki da gudu tana Kuka
Anty jidda tace itada yar'uwata ne, fada sukai saboda Kai
Yace subhanallah
Kafin Safah ta bashi amsa anty jidda tace saboda munyi Mata magana Akan auren ku
shine taketa Kuka Wai bataso, shine itama Safah din tace to itama zata fasa Nata
auren tunda haka takeso
Yace kashPAida kunyi hakuri anty, karkuga laifinta laifinane daban sanar da itaba,
kuma wallahi yanzu haka Dama niyyata idan na ajiye haneefa anan inwuce can gida
inyi Mata bayani
Ya dubi Safah, yace kiyi hakuri kinji Safah, nasa kinsamu sabani da yar'uwarki Amma
insha Allah komai zai wuce kinji?
Ya sassauta murya yace kiyi hakuri, nasan namiki laifi, but sabanin fahimta ne
yakawo Hakan, Amma wallahi Ina sonki
Samah tun lokacin Dana Dora idona akanki naji nakamu da matsanancin sonki, Amma
kuma sai fada yahadamu a lokacin, na lura idan nasakar miki rainani zakiyi, nikuma
babu abinda na tsana arayuwata irin raini, inada son girma Samah
Shiyasa zakiga Ina Miki wasu abubuwan Wanda basu da dadi, Nima ba'a son Raina nake
Miki ba, dole ce tasa Samah
Dan Allah kada kice bazakice aure niba, zan Iya fuskantar damuwa Akan haka
Kalamansa sun ratsata, kuma ta gamsu Sosai, sai yanzu ne tagane dalilin sa naayi
Mata wani abun
Yace kiyi hakuri ki Dena Kuka haka kinji? Kanki zaiyi Miki ciwo, karkiga ni doctor
ne rikicewa zanyi nakasa baki Koda pracitamol ne🤣🤣
Hawaye suka sake zubo Mata, Yana ganin haka yasa hannu yadago ta, ya rungumeta a
jikinsa
Mutsu mutsun kwace Kanta tafara, bai hanataba yasake ta, dan Shima dole ce tasa
yayi Hakan, taqiyin shiru, Shiyasa zai lallasheta ta wannan sigar, Amma Banda haka
babu abinda zaisa yayi abinda zai daga masa hankali
Yace kokinga Dena wannan hawayen kokuma yanzun nan na shanyesu anan
Maganarsa tabata daria, tasake murmushi tadauki fillo agefe ta buga masa
Babu musu tayi masa murmushin, yace yawwa kokefa, saina kiraki zuwa anjima kinji?
Daria tayi tace Dr yazaka tafi bakayi mana bayani ba? Tahuce ne?
Yace Wayyo anty ked sai anjima mana, yayi sauri yafice daga falon
Samah kuwa haka kawai taji wani irin farin cikin ya mamaye ta, Kenan Dama tana
Sansa kawai rashin fahimta ne yakawo haka, yanzu da wanne ido zata kalli anty da
Safah?
Tab wallahi Gara tayi baccin qarya kawai🤣🤣🤣Aida kunya tafita falo
Anty jiddah tatashi tashiga Dakin nasu, taga Samah a kwance ta rufe ido tayi
murmushi tafice
Suma su shalele sukayi cikin Dakin, suna shiga sajida ta Daka Mata duka tace wallah
idonki biyu malama
Bawani basaja da Zaki mana
Ku Gama soyaiyar adaki kiwani rufe ido ke me bacci
Sajida tace haka Nima wallahi kibar uncle Dina yahuta ehe
Tace eh naji
Safah ta miqawa Samah wayarta tace ga wayarki nan, Iya masifa, sai ihu kike bakya
sonsa gashinan daga zuwansa kinyi luff dake, Dana sanima shina Kira tun farko
********
Washe gari me gyaran jiki tazo tun safe, take ta musu, dole shalele sai izni ta
nema a school, kuma dayake ma satin karshe ne exam zasu fara ba'a hanata ba
Yau ma me gyaran jiki tatafi duk suna zaune afalo suna kallo, ayaz na gefe wayarsa
tayi qara yadauka yafita
Gaba dayansu sun sauya, sai sheqi suke, musamman shalele, Har wani shining take
jikinta kamar ka latsa jini yafuto, anty jiddah tazauna a gefensu tahada musu komai
tabasu
Babu Wanda yayi musu kowa ya karbi nasa, sai shalele tace mama ni wannan jiqe jiqen
wallahi ya isheni, bawani dadi ne dasuba kekuwa kin dage kullum saikin bamu 😣😣
Anty jiddah ta kalleta cikin ranta tace a a haneefa kinzo da bidi'a🤣🤣yanda qanina
yakashe wannan uban kudin ai dole na zage nagyaraki kada raini yashiga tsakani
Afili kuma saita daure fuska tace ke bansan shirme, karbi ki Shanye ni
Washe Gari ma haka tatura wa wata qawarta kudi, aka hado musu kazar amare, kowa Dai
Dai, wannan Karan Kam Dukansu ba Wanda baiyi mita ba
Kowa fada yake shi bazai Iya cinyewa ba
Anty jidda tace wallahi bazasu sata asarar kudin taba saisun cinye
Aranar de Har yamma haka sukaita fasin fasin da kaza, idan ka ajiye taka da nufin
anjima ka qarasa kana dawowa idan kabude zakaga anqarama 🤣🤣kaima saika dauke ka
jefata Ata wani 🤣haka sukai tayi, daga qarshe de dolansu suka cinye
********
Ango kasha qamshi, shazali sai wani farin ciki kake kakusa aure
Ajmal banason wulaqanci kaji ko, Kai Baka kusa auren ba?
Ahha nakusa mana, aini nine ma nakusa aure, Har na matsu akawo min amaryata mu bare
junaanmu aleda 🤣🤣
Kafada yadaga yace banaso muzauna agida gaskiya, but banji su daddy sunce komaiba
Akan maganar wajan zama
Murmushi yayi, dimple dinsa suka loba, yanuna kansa da hannun sa yace ni in zauna
anan gidan? Haba Ajmal ai nafisan gidanmu daban, babu me takuramin
Babu me takura maka kokuma kafison gidanku daban dankaji dadin kashe yar mutane?
Haba Ajmal wanne irin kisa Kuma Ana zaune lafiya, kaima kasan yarinya ce Saida
lallama, infact ma ni bansan wajanba wallahi
Murmushi Ajmal yayi, kaikuma shazali nagama lura dakai arayuwarka inbaka renamin
hankali ba, bakajin dadi🤣🤣
Dabakinka kazo nan kake cemin Har kissing yarinya kayi, toshima kiss din itace ta
koyama Kenan?
Ajmal Kenan kayarda ds abinda nake fadama, bansan wajanba, dasafe na fita office,
nadawo da yamma, naci abinci a wajan momy da daddare na tisa computer agaba Ina
aiki, bazan denaba saide in bacci naji, na kwanta nayi bacci banma samu time din
kula wayaba, yau meeting gobe Ina wancen campany jibi Ina wata qasar, kafadamin
tayaya nakeda lokacin dazan Bata wajan sanin mace?
Zuciyarsa daya yace toshikknn, Shiyasa fa nakeso tayi tagama karatun nan
Haneef mekake nufi da tayi tagama karatu? Kanaso kacemin jiranta zakai Har sai
tagama karatu?
Emana, kokana mamaki ne, zanjirata kawai, daga nan ko daddy yayi maganar gida ko
baiyi ba, nide bazan yi rashin kunya inyi musu maganar ba, kawai saina dauki abata
mutafi wata qasar honeymoon
********
Karfe shabiyu nadare Yana kwance adakinsa, Daka kalli fuskarsa zaka tabbatar da
cewa Koda wa yake wayar to wani me muhimmancin ne
No, no, Kinga ni ban yardaba, kawai kisanar Dani qasar dakike so, kokuma take baki
sha'awa saimu tafi Bayan bikinmu, muyi honeymoon daga nan musamo me sunan baba
Yayi murmushi shine kikai shiru ko? To bakya son me sunan baban?
Look baby kidena fadaamin wannan sunan, nasu sajida ne, kekuma ai antyn sajida ce
To uncle naji
Yanzu me kikeyi?
Azaune kuma? Kidena yin waya da mijinki Azaune, nafiso kisamu waje ki kwanta, ki
rungume fillo kina waaya Dani ta yanda zakiji kamar kina kirjin mijinki ne
********
Ayaune dibban mutane, Yan siyasa da manya manyan Yan kasuwa, masu kudi, masu fada
aji afadin nahiyar Africa gaba daya suka shaida daurin auren Haneef bukar shazali
da amaryarsa Haneefa suraj
Saina Sajida Sulaiman da angon ta Ajmal is'haq, dakuma Safah bukar shazali da
angonta Ameer Tahir, saina Samah bukar shazali da angonta Dr Bilal Usman Adam, Akan
sadaki naira dubu Dari Dari, lakadan ba ajalan ba
Angwaye kowa yasaka manyan Kaya, gaba dayansu sunyi bala'in yin kyau, musamman
haneef daban taba ganinsa da manyan kayaba
Mutane ta ko'ina sai tururuwar zuwa suke, masu photuna sunayi, Banda masu yin selfi
🤳awayarsu
Gidajan talabijin dayawa sunzo daukar labari musamman saboda Haneef bukar shazali
da sunansa yazaga wajaje dayawa
Maroqa kuwa dayawa kamar me, wajan daurin aure yacika yayi albarka danqam da mutane
Acan gida ma haka abun yake, yanmata da qawayensu na makaranta duk sunzo
Anzanawa kowa qunshi Banda gashi dayaci uban gyara, Dukansu suna gidan anty jidda,
sai daga baya ne kowacce aka kaita gidansu
Shalele adon doguwar Riga tayi gown light green, rigar Har qasa takeja daga
bayanta, gashin nan yaci gyara kamar ba gobe
Kowa sai photuna yake da ita, Afrah kuwa ta riqe ta duk inda tasa kafa tana maida
Tata
Ita Kuma sajida Tata blue, su kuma Yan biyu pink ce tasu
Haka aketa shan photuna da yan'uwa da abokan arziqi, Har yamma tayi suka sake sauya
Kaya zuwa atamfa, wannan Kam Dukansu iri daya sukayi
Aka wuce wajan walima, waje yayi waje, angayyaci malamai sunzo sun baje kolin
wa'azi Akan haqqin mijin Akan matar sa dakuma haqqin Mata Akan mijin ta, Har wajan
magrib sannan aka tashi
Da dadare sukayi Arabian night 🌃, kowacce mace kagani a wajan taci uban gayu, kowa
yajiqu da kudi, duk wuyan wadda ka kallah qyallin gold ne zaima maraba
Wannan Kam shazali baijeba
Yana can tare da baqinsa dasukazo daga qasashe daban daban
Kowa Yana zuwa gida ya kwance saboda gajiya, haneefa tawuce gidan mami, ita Kuma
sajida Dama tare take da yanbiyu
Washe Gari akai wuni,kuma aranar aka kaiwa kowa kayan lefanta, Kowa dozin Dai Dai
Shalele ce me dozin biyu gaskiya Kaya sunyi ba qarya, tsayawa fadar Sama Bata
lokaci ne ,
 aranar duk Wanda ka kallah da kalar nasa ankon, yanmata daban, yayu manya irinsu
anty jidda daban, sai kuma na iyaye Mata suma daban, masoyan shalelan baba ma ba'a
barsu abayaba, group group suke shigowa anayin komai dasu, danma de shazali yaji
qansu yafitar dasu kunya yayi musu anko 🤣🤣
Amare kuwa ankon material sukayi Dukansu, masu kwalliya sun kwashi kudi, domin kuwa
zubata ake da gasken gaske
Su momy da Mami sunso ayi mother's day, Amma daddy yahana yace bidi'ar kartayi yawa
Da daddare aka shirya kowacce tsaf, cikin shirin tafiya dinner daga can kuma
kowacce za'a wuce da ita gidan mijinta
Kwalliyar yau Kam haneefa gwon tasaka fara, sai net da aka Dora Mata Akan rigar
Sajida kuma material, Yan biyu kuma Swiss less, wajan dinner ya qawatu kowa da
amaryar sa agefensa
Saida akayi tarihin kowacce amarya da ango
Sannan aka Saka kida Ana yanka kek
Kowa yabawa matarsa, shazali Kam da akazo kansa hannunsa yasako ta bayanta yariqe
hips dinta
Suka tako ahankali sukazo Har wajan kek din, itace zata fara bashi Amma saiya
hanata ya karbi wuqar , daya tashi yankowa kuwa yayanko dayawa Wanda yafi karfin
bakinta yasaka Mata
Kafin taayi yunkurin wani Abu yakai bakinsa Kan Nata Shima yaci Kek din ahaka
Waje yadauki ihu da tafi, Mami de tana ganin haka takama hannun momy tace hajiya
Amina, yakamata mubar wajan nanfa tunda yarannan suka fara haka
Daga nan akaci gaba da shagali, bangaren cin abinci kuwa save yourself ne, Dakanka
zakaje kadebi abinda kakeso
Waje yayi Sosai, yacika da gogaggun mutane Yan boko da sauran mutane
Har wajan Sha daya da kwata suna wajan, sannan aka tashi
Alhaji shazali 🤣yadauki matarsa sukayi gidan momy dagashi sai ita Abaya, dakuma
anty jiddah agaba sai Saminu driver
Samah yan'uwan Dr Bilal suka dauketa da anty Fadila, da angon ta sai gidanta Dan
madedeci Mai kyau
Ita kuwa Safah dasu Afrah, sai Anty iklass, suka tafi 🤣
Sai sajida da angonta Ajmal da yayunsa Mata biyu, daya macan na driving daya agaba
sukuma abaya
49&50
Cikin gidan da mutane Sosai Yan biki, Kanta Yana lullube cikin mayafi hawaye suna
Dan zubo Mata kadan kadan, basu qaraso gidaba sai wajan shabiyu
Direct Dinsa anty jidda takaita, ba furnitures din da bane, wasu yasake Sabi launin
milk, anty jiddah tayi qasa da muryar ta tayi Mata fada sannan tayafa mayafinta
zata tafi, cikin Kuka ta riqeta mama Dan Allah karki tafi, Allah ni tsoro nakeji
Dan Allah mama ki tsaya
Anty jiddah tayi murmushi, cikin ranta tace inani Ina zama tun a wajan dinner
mijinki yanayin rashin kunya
Afili kuwa sai tace haneefa, kiyi hakuri mana,kiyi shiru zan turo Miki haneef
yanzu, kinji ko?
Ke bansan shirme, kuma shikkenan Dan gidan momy ne shikkenan da girmana saina zauna
godai godai Daniel adakin qanina, kiyi hakuri bari inje bansan inda yayi bane,
saina dubashi naturo Miki shi, idan kuma banganshi ba saina dawo muyi zamanmu
kinji? Taqarasa maganar cikin sigar lallashi
********
Cikin kunya tatashi suka gabatar da sallar, sannan yakawo musu Dan abin motsa baki
sukaci, Bayan sungama komai, yakama Kanta Yana karanta adduah, daga nan nabar musu
dakinsu
********
Wai yau shine da mace adakinsa, macenma tashi halak Malak, a hankali yatashi yacire
babbar rigarsa tare da hula, yakama hannunta yace amarya yakamata muje muyi alwala
ko
Cikin kunya tatashi suka shige toilet din, agabansa tayi alwala sannan suka dawo
yajasu sallah
Duk abinda take Bata Iya kallan qwayar idonsa, shi dinma daqyar yake Kallanta,
Bayan sun Gama yabata waje yashirya ta kwanta sannan Shima yazo ya kwanta Yana
Kallanta, zuciyar sa ce take qara bashi shawara Akan yaqarasa gareta, a hankali
yatashi yadora kansa Akan Nata fillon, daga nanfa labari yasha bam bam, Haji ameer
aka adana kunya agefe
********
Ta girgiza Kanta
Cikin yanga taci gaba da tura naman bakinta, Yana qara Saka Mata Shima, harsaida
yaga tana yatsina fuska sannan yarabu da ita
Bayan sunyi sallah, da kansa yakeyi Mata tambayoyi dangane da ibada tana bashi
amsa, sannan sukai shirin bacci
Murmushi yayi Yana Kallanta, daga baya yatashi Shikam yarage kayan jikinsa ya
kwanta
Hannu yasa yajanyota jikinsa, yarage muryar sa yace ke Bazaki cire wannan kayan ba
Tace um barshi
Um um uncle Bilal kabar.... Maganar ta ce ta tsaya a lokacin dataji Yana zuge Mata
zif din rigarta
Laushin dayaji jikinta nayi yasa yakasa dauke hannunsa daga jikinta
********
Yace good Dama da kinyi ma dole zan tasheki kici abinci, nasan kinajin yunwa
Oya taso
Shiru tayi taqi tashi, wanne irin ango ne wannan, dan mayafin da ake cirewa amarya
ma shi baya cirewa 🤣🤣. (Ina ruwan shazali)
Tsayawa yayi Yana Kallanta, metake jirane? A hankali yataka ya qarasa gabanta, ya
tsugunna agaban ta, hannunsa yadora Akan cinyarta cikin sigar rada yace haneefahh
Tayi shiru
Yace kosai nasiyi bakin ne? Tayi qasa da Kanta batace masa komai ba, Shima shiru
yayi Yana Kallanta, idonsa yasauka Akan kirjinta, yakasa dauke idonsa akai
Zuciyar sa ce tafara gargadinsa Kai haneef, a a karkai komai, kace bazakai komai ba
Zuba masa ido tayi, uncle kamar qaramin yaro harda kwanciya Akan cinya, sumarsa ta
kallah ta birgeta, kamar tasa hannu ta shafa Amma kuma bazata iyaba
Saida yadanji yadawo daidai sannan yakama hannun ta suka koma qasa, yacire babbar
rigar ajiye a gefen gadon, sannan yamiqa Mata hannu yace ciremin agogon nan
Saida ta kalleshi sannan takama hannun tacire masa, yabude musu naman kaji yace to
bissmillah kici abinci
Ni banajin yunw....
Yasaka hannunsa yafara Bata da kanshi, dan qaramin bakinta yake kallah, kamar
yakamashi yayi kissing
Haka ya dinga Bata hartace ta qoshi sannan yace, Saura ni
Yace emana tunda nabaki ai ramawa kura aniyarta zakiyi, Nima yau kece Zaki Bani
Babu yanda ta'Iya haka tasaka hannu tafara bashi, idan tadauko dakanshi yake riqe
hannun ta harsai yacinye
Itade duk ta takure, takasa sakewa dashi, tasan yau Kam me rabata da shi kuma sai
Allah
Itace taita bashi harya qoshi, sannan tatashi zataje ta wanke hannun ta
Dasauri ya dakatar da ita,yakama hannun yakaishi cikin bakinsa Yana sha daya Bayan
daya, gaba daya taji jikinta yana saki, Ahankali ta qwace hannun ta daga bakinsa
tace uncle ni wani iri nakeji
Kitchen sukaje suka maida sauran kayan can, sannan suka dawo, yace ta dauro alwala
suyi sallah
Haka kuwa akayi, sunayin alwala sukai sallah, ya yi musu adduah sannan suka tashi,
toilet yashige, tana ganin shigarsa tacire kayanta tasaka wani ta kwanta
Shima wanka yayi, yafuto daure da towel sannan yayi shirin bacci
Tunanin maganar da Ajmal yayi masa yakeyi, Anya kuwa zai Iya tambayar yarinyar nan?
Toma Suda akace suna tsoron abun tayaya zata Iya masa bayani, wannan kawai zancen
Ajmal ne, yadauki wayarsa yafara danne danne
Shalele taji shiru tasaki ajiyar zuciya, Allah yasa yayi bacci
Shikuwa tuquru yashiga internet Yana karanta komai, wani ilmin ma na Mata baisaniba
sai yanzu, haka yaita bincike harya Gama gane ko Mai Sosai sannan yakashe wayar
"kinyi bacci?
Tana jinsa ta yi shiru, hannunsa yakai Kan idonta yashafa, yaji tayi motsi da
idonta, yayi murmushi yajawota jikinsa
Hular data rufe Kanta da ita, ya janye, gashinta ya baiyana, yasaka hannu yafara
shafawa, cikin sigar rada yace inason ki,bai saurari amsarta ba yafara kissing
dinta, hannunsa yadora a inda yafi komai daukar hankalin sa yafara matsawa, nan da
nan tafara Kuka
Yanajin kukanta Amma ya shareta, saima Dora bakinsa da yayi akai Yana sucking,
cikin Kuka tace uncle pls kabari Dan Allah
Dan kansa yasaketa ya rungumeta, tsam a jikinsa, cikin rashin kuzari yafara bubbuga
bayanta alamar lallashi
Sorry, sorry nabari, tana jikinsa Yana lallabata hartayi bacci, sannan Shima ya
sumbaci goshinta yalumshe idonsa, gaskiya dasake bazai Iya jiraba.
(kuma de🤣🤣🤣)
********
Washe Gari suna tashi sallah, takasa hada ido dashi, Shima Yana Mata kallan zakiyi
bayanine yarinya, 🤣🤣
Saida yayi wanka 🙈sannan yafita masallaci, Yana dawowa yatarar tana Kan sallaya, ta
gaidashi ya amsa
Tayi mamakin tambayarsa, tace nanda 3days zamu Gama waec Saura neco kuma
Wanka yasake yashirya yadubeta zanje wani waje nadawo, Kanta aqasa tace to uncle
Idonta tarufe, yatako yazo gabanta ya janye hannun ta, yadora bakinsa Akan Nata,
yasaakar Mata kiss sannan yafita
Shazali na fita yakira wayar Ajmal, bakwai da rabi a lokacin, Ajmal na kwance Yana
maida baccin gajiya yaji waya tana qara, tsaki yasaki yadauka Wai Waye ne yaketa
Kira haka? 🤣
Haneef yacire wayar daga kunnansa yakalla, Anya kuwa Ajmal ne?🤣
Au shazali Dama Kaine? Shazali da wannan asubar zanbar iyalina in futo wani waje? 🤣
Shazali, Naga alama Kai ba ango bane, dan Allah kabar angwaye su huta, dif yakashe
wayar
Haneef yabi wayar da kallo, ikon Allah 🤣🤣, yau kuma me yake damun Ajmal? To da
zaice Shiba ango bane me yake nufi, Ajmal yacika shirme wani lokacin,
Domin Jin yanda za'ayi, dakuma Jin interval din exam din nasu, kozai samu yadauki
matarsa su Dan samu su fita daga qasar koya huta.
********
Eh naje nanema Mata parmission, sati biyu kawai zamuyi insha Allah
********
Malam yahai Kenan, angama muku komai, tafiya zamuyi gobe insha Allah
Baba Malam da Inna sabuwa lokaci daya suka fara kukan dadi, Afrah da Safah kuwa
saints daria suke musu
Mami tace Amma idan kundawo ba kuje zaku wuceba, zaku sauka agidan yarku haneefa
idan Kuka Mata kwana biyu saiku tafi, zataji dadin Hakan Sosai, Inna sabuwa ta goge
hawaye tace ai hajiya duk yanda kikace haka za'a yi, mungode hajiya Allah yasaka
muku da gidan aljanna, yau gashi sanadin shalele mune zamuje mu ziyarci Dakin Allah
********
Tunda sukazo qasar nan takasa gane kansa, tarasa dalilin wannan tafiya da uncle ya
tsira,Itade Nata kallo,tana kallan ikon Allah
Da dadare suka sauka, saboda haka suna zuwa kwanciya sukai, saboda gajiya
Tana manne a jikinsa, duk motsin da tayi sake riqeta yake kamar wani zai qwace ta
Asuba nayi suka gabatar da sallah, karatun qur'ani sukayi Har Saida Gari yayi haske
sannan suka sake kwanciya,basu tashiba sai karfe Tara nasafe
Da kansa yaje yayi musu ordering abincin dazasu ci, sannan yadawo Dakin, alokcin
tana toilet tana wanka, tasande yafita Amma ba tasan yadawo ba
Dan haka zuciyar ta daya tafuto dawaani Dan qaramin towel iyakarsa cinyarta gaba
dayansa
Da gefen towel din take goge kunnanta
Dagowar dazatai taga mutum ya kafeta da ido
Dama haka yarinyar nan take da diri me kyau? Ashe da dayake ganinta cikin Kaya
baiga komai ba?
Takawa yayi a hankali Har yaje inda take, gashin Kanta da ruwa yadan jiqa wani
wajan ya liqe Mata afuska yasa hannu yakawar dashi
Yaci gaba da fadin Dan Allah ki riqeni Amana, Ina mutuqar kaunarki, bazan Iya
rayuwa batare dakeba, Kema kina sona?
Gyada masa Kai tayi, yace no kifadamin da bakinki, a hankali Tabude bakinta tace
inason ka uncle
Dasauri takwace bakinta ta tsugunna qasa tasa hannu tana kare kirjinta
Shima binta yayi ya tsugunna,yasaka hannu ya dauketa cimak, yayi Kan gado da ita
Rigar jikinsa yacire tana ganin qirar jikinsa abaiyane da gashi sai gajeren wando
ta runtse idonta, bargon dake Kan gadon taja tarufe jikinta dashi
Shima binta yayi cikin bargon, yafara nuna Mata kalar soyaiyar dayake Mata
Awannan lokacin Kam haneefa ta gurzu Iya gurzuwa, taji a jikinta, muryar ta ta
dashe saboda Kuka, Amma haneef kamar kurma baya jinta
Tana Kuka tana roqarsa Amma saiya hade bakinsu, dif tayi shiru
Gaskiya dole Ajmal yace bazai rakashi ko'inaba, to ai inshi nema sai yayi sati Bai
fita ko inaba🙈🙈
Kallanta yayi tana Kuka qasa qasa, Ahankali yasaka hannu yajanyota jikinsa ya
rungume ta Sosai
Jijjigata kawai yake, Ahankali yake rada Mata dadadan Kalamai dakuma shi albarka
Har tayi shiru
Daga nan bacci ya dauketa
Tana Kallansa ta runtse idonta, abinda yafaru dazu Yana dawo Mata Sabo
Yayi Mata wanka, sannan yabarta tayi na tsarki, Tsayawa yayi a wajan Yana jiranta,
harta futo tana dingishi
Kallan tafiyarta yayi, to tayaya ma zai yarda yayiwa yarinyar nan wani Abu agida,
ai dole saisu momy sun Sani
Gyada masa Kai tayi, yasake cewa kiyi hakuri to zai daina
Cikin shagwaba tace uncle Saida nace mafa akwai zafi, akwai zafi, kayi hakuri Amma
kaqi ji
Haka suka wuni Yana riritata, da dare yayi ma sunyi shirin kwanciya, haka ya dinga
tabe tabe, cikin faduwar gaba tace na shiga uku, uncle Allah ban warke ba
Haka ya kalallameta Saida yasamu abinda yakeso, Tasha Kuka harta godewa Allah,
Shikam saaida ya mori sadakinsa sosai
Awannan sati biyun dasukai amasar Sosai sukasha amarcinsu, lokaci kankani suka fara
sauyawa, tun tanajin zafi hartazo tafara dainaji
********
Rayuwa tasauya tayi dadi, kwanciyar hankali ya wanzu atsakaninsu, suna ziyartar
junansu Sosai
Idan haneef yasamu lokaci Yana kaita kuje da kansa taje tagano su baba malam
********
Daddy ya karbi takardun ta, ya hada Dana Yan biyu da sajida yanema musu makaranta,
kowaccensu tana tafiya daga gidan mijinta
Idan suka hadu kuwa anan ake baje kolin firar duniya dakuma irin kulawar dasuke
samu a wajan mazajaansu
Yan biyu kuwa kamar hadin baki watan nasu 'Dai 'Dai
Har cikin su ya Isa haihuwa, sajida tasamu danta namiji, masha Allah ansha bidiri
awaajan suna
Daanma kowa tanaji danata cikin
Shalele daqyar take komai, duk yanayin ta yasauya tasake zama babbar mace
Bayan wata daya da sati biyu itama tahaifi twince dinta mace da namiji
Ranar suna Yara sukaci sunan iyayen shalele malam Surajo, dakuma Zainab
Suma Yan biyu Bayan wata biyu suka haihu, Safah ta haifi Yan biyu maza, daya sunan
Alhaji Tahir, daya sunan bukar shazali, Samah kuma ta haifi Yan biyu Mata, daya
taci sunan hajiya daya taci sunan momy
*Abin* *lura*
Kada ka tsanaanta soyaiyarka Akan yaranka dayawa, Koda kana sonsu dayawa kada
kanuna musu Sosai qarara, Hakan Yana yiwa yaranmu illa
Bayan barinka a duniya, bakasan hannun da Danka zai fada ba, kasabar masa da samu
da rashi, dadi da rashin dadi, bawai Jin dadiba gaba dayaba kamar yanda *Malam*
*surajo* yayi
Abu na biyu riqon alqawari yanada kyau a wannan rayuuwar kamar yanda Manzo ya
umarce mu dashi, *marka*Bata riqe alqawari ba ga qarshan tanan
Kada kaga kanada kudi ilimi kyau, Jin dadi na rayuwa kadauki masifa kadorawa kanka,
*haneef* ya nuna wannan halin, daga karshe yakaamu dason yarinyar daba yar kowan
kowa ba, kuma kudin nasa baisa yasameta yanda yakeso ba
Yanuna Mata iko ya dauketa amatsayinta na yar aiki yayi tafiya da ita, yayi Mata
abinda yaso
Tsanaanta tsana ga mutumin da bakasan Shiba baida amfani, kamar yanda *momy* da
*daddy* sukayi
Allah yasa mun dauki darasin da littafin ya qunsa, abinda yake marar kyau kuma
ubangiji Allah yabamu ikon watsi dashi
Wadanda suke cikin group Dina na WhatsApp zan rufeshi gobe ko jibi idan Allah
yakaimu sai kuma Allah yasa nasake wani novel din saina Bude wani
Idaan akwai Wanda nabaatawa rai yayi hakuri ya yafemin Dan Adam ajizi ne, kuskuren
danayi acikin wannan littafi Allah ya yafemin, sai mun sake haduwa asabon littafi
na idan ubangiji yabamu iko🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻🙏🏻
✍🏻
Amina Muhammad El yaqoub Jigawa State